An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
Gani Ga
Wanest
NA
ZAHRAU BABA YAKASA!
(Mrs. Dan Ringim)
GANI GA WANE.
1
NA
ZAHRA'U BABA YAKASAI
(Maman Shurcem)
08020863615
1
GODIYA
Ga Allah Subahanahu wata'alah, wanda cikin
yardarsa da ikonsa muke baza muku irin baiwar da
ya yi mana.
SAKON TAYA MURNA
Ga Uncle dina da Allah ya sauki Auntyna lafiya,
Allah ya raya mana MARIYATUL KIFDIYA
Tasi'u D. Yakasai (Baba Wali)
INA TAYA KA MURNA ALLAH YA RAYA
MANA
Hauwa'u Ibrahim Umar Makaruma
(Malam Sabo)
GORON AMARCI
Kinsha kamshi tsohuwar gidanmu.
SAFIYA DAHIRU YAKASAI UMMI
da Angonta
NURA ABUSAKA YAKASAI
Allah ya kawo kazantar daki.
INA SANE DA KAI
Bashir Sa'id Kyautah
2
MASOYA NA GARI, ALHERIN
ALLAH YA KAI MUKU
Hauwa K. Umar College of Education Minna.
Hussaina B. SKK
Hauwa Ali Gwambe
Abubakar Haruna Albasu
Asiha Ishak 'Yar Magaji
Ibrahim A. Bauchi
Maryam Suleman Giade (Ummce)
Hadiza Adam
Hajara Abdullah Baba Sokoto
Hadiza Usman (Hadee Queen)
Zahra Ahmad
Babangida Kumo
Bello M.
Hauwa Mohd Loddo (Maman Ukasha)
Suwaiba Musa
Faruk Umar Gamawa
Fa'iza Moh'd Gaya MJB
Hauwa Usaini Bichi
Maimuna Musa Soja
Abdurrashid Abdun kwallo
Amina Abdullah Ghana
Ahmad Paris Bookshop
Samirf Sha'aibu Jangulu Kazaure
Fatima Adamu Yana
Rukayya Mai dinki D/Kaigama
3
Deeni Alasan Yana
Mudansuri A. Badamasi
Hadiza Ali Sokoto
Aysha Sokoto
H.J.A
Sumayya Mohd Sury (Maman Fadila)
Ahmad Tijjani (Abban Mohd)
Abdullah Dalhatu (Abban Humaira).
GAISUWA TA MUSAMMAN GA MASOYANA
Na kasashan ketare kamar:
Kamaru, Ghana, Abijan, sannan Saudiyya, Paris, da
kuma Libiya.
4
SHIMFIDA
mota cc kirar Jeep baka kirin sai M
daukar ido takc kamar wanda aka
shafc ta da mai (oil), ya fito daga
cikin wannan mota, abisa dukkan alamu da akwai
masu gidan rana (kudi), dogo ne fari mai dan kauri
irin mazan da akc kiran su tall man din nan ne
fuskar shi ta kunshi annuri kasancewarshi mai
sakakkan fuska.
Cikin iko da takama irin na ma su akwai, ya
fito ya rufe motarshi, ya doshi cikin gidan. Gida ne
hadadde flat irin ginin zamani wanda aka dauko
hotonshi daga London, gida ne wanda ya kunshi
kayan more rayuwa na bil-Adama domin tsayawa
misalta wannan gida 6ata lokaci ne sai dai ku biyo
ni a sannu ku ji komai.
Ya na shigowa cikin gida kwatsam ya yi for
cyes da wacce ya tsana ko kuma in ce aka cusa
mashi tsanarta don ba wai a son shi ba ne.
"Sannu da zuwa." Ta fada mashi amma ko ya
kulata, sai shigewa bedroom dinshi ya yi, kulawa
Mà yabawa ne in ji Hausawa.
Ya danna inter come ya kira ta musamman
kamar yadda ya ke kiran amaryarshi wato (ta
musamman) a maimakon sunanta na yanka wato
Ummulthum, ta fito cikin yanga da jinkai a daidai
falo ta hadu da wacce ta tsana kuma ta ki jinin ta
5
Fafi ido ta ganta harara ta sakar matga ta shiga
dakinshi cike da kwarkwasa da kissa, shi kuwa tuni
va rude nan ya rungumo ta jikinshi ya fara
sumbatarta nan da nan su ka manta a wace duniya
suke.
Bayan sun nutsu ne ta dube shi cikin kashe ido
ta ce "Darling yunwa nake ji." Ya zaro ido, Shema'u
ba ta baki abinci ba ne.?" Jikinshi na 6ari bai jira
amsarta ba ya fito falo ya iske ta na kallon TV
tashan Aljazeera ya dube ta "Ke me yasa ba ki ba
wa Ummu abinci ba? Ta dago kai ta dube shi da
kyau, ta ce a baki zan bata ko me? Ran shi ya бaci
wane irin zancen banza ne kike min haka? Cewa ta
yi tana jin yunwa sai ta ajiye remote din hannunta
ta kara ganinshi da kyhau cike da mamaki da
al'ajabi ta ce to ai sai ta shiga kitchen din ta duba ko
anyi mata dokar shiga ne? Sai Ummu ta fito amma
kin san ba a nuna wa ido bacci da har za ki ce na shj
madafi na diba, ta juya, darling rabu da wannan
matar duk bakin kishi ne ya ke damunta, kuma a
haka zata kare. Shema'u ta ci gaba da canja tashoshi
ba ta sake kula su ba, yana tsaye ranshi ya dada baci
yaje ya kashe TV din to ba zai yiwu ba, Shema'u na
ga kina son kawo min matsala gidana ki shiga
hankalinki ban da abunki ai Ummu yarinya ce kuma
naga kina so ki saya wa kanki raini amma zan yi
maganin ki, ya juya zai koma dakinshi ta dubi
6
ummu ta ce ki kuma kiji tsoron Allah, nan na fito da
abinci na kira ki amma kika cc min ba yanzu ba, shi
ne yanzu don makirci za ki ce na hana ki abinci?
Nan Ummu tasa kuka wa Shen a'u da zage ta ya fito
ranshi a 6accd ya cc "mujc Mr. Biggs." Ta shiga
dakinta ta dauko gyalen da shi da babu duk daya,
irin gyalen da mazan da ba sa kishin matansu su ke
saya musu ta sa takalmi masu tsini zai fita Shema'u
ta cc ga abincinka can fa ya cc sai ya dawo su ka
fita.
Bayan dawowar su nc Ummu ta cc, ai wannan
abincin Shema'u ta saka magani kuma idan ya ci
gaskiya ranta ba zai mata dadi ba. Nan ya hakura
kasancewar baya iko da kanshi a takaice duk sanda
Shema'u ta yi girki Nazir ba ya ci, wai ana saka
masa magani bai san yana kwana cikin magani ba,
karewa ma ba ci ba.
Kullum kwanan duniya Ummu ba ta san yau
kwanta ne ko na 'yar uwarta ba, don kafin ya shiga
dakin Shema'u sai ya gama komai da Ummu sannan
ya shiga dakin Shema'u, wataran sai ya kai karfe
daya sannan ya fito daga dakin (ta musamman) ya
shiga in da ba ya son, wataran kam sai ya dau
kwanaki bai leka dakin Shema'u ba, Shema'u ta bi
ta lalace duk ta rame ta rasa yadda zata yi.
Yau ta na dakinta kwance da baby dinta tana
tunanin yau nice Nazir ya ke gasa wa gyada a
7
hannu, alhalin da kyar ya yarda ya aurı Ummu, duk
da 'yar uwarshi ce amma da cewa ya yi mcyc zai yi
da wannan mace ba wani diri ba komai sai kace
(tabarya) amma yanzu ka shi mai kama da tabarya
ta fita mutunci a gun miji amma sai dai komin daren
dadewa gaskiya zata yi halinta, karya furc take
kuma komai na duniya ya na da iyaka.
Ummu ta fito ta iske baby Nur tana zaunc akan
keken yara na koyan zama, tana zuwa tra fara mata
wasa tana tura ta akan keken da yake baby yarinya
cc nan ta fara 6al6ala dariya. Nazir ya na shigowa
yaga Umu na yi wa 'yarshi wasa, nan ya ji dadi ya
ziyarce shi a take ya sake jin son Ummu a ranshi,
sai ya shiga tsokanar su ya na yiwa babyn wasa ya
dauki baby su ka shige dakin Ummu, nan da nan
bakin ciki ya ziyarce ta ta 6ata fuska ta karbi babyn
ta aje ta ta ce gyara na maka tausa, don yanzu
lokacina ne ba na baby na ba dariya ya yi ya ce (ina
son haka tawan) nan ta shiga yi mashi kissa da
kisisina, shi ko dadi ya ke ji.
Duk wani dangin Nazir Ummu ta gama dasu
duk sun fi sonta akan Shema'u duk in da ta zauna
sai ta yi ta bakanta Shema'u kasancewar Ummu 'yar
uwa ce a gidan su Nazir amma ta wajen Hajiyar
Nazir.
Kullum idan ta shiga gidansu Nazir abun da
zata ce shi ne, gaskiya ita fa idan tana bacci takan yi
mafarkin abun tsoro har wani yana zuwa mat ata
windonta yana cewa ta fita nan ba gidan zamanta ba
ne, to anan fa gurmi ya farfa tashi wai a ne ma mata
taimako kada yar uwarta ta haukatata ko ta yi mata
lahani, Allah Sarki.
Ita ko Shema'u da take zaune a gida ita da
babu dun daya bata son ma me ke faruwa ba ashe
dangin Nazir har cewa suka yi Ummu ta daina
amfani da ruwan famfon gidan da abu ya yi abu har
ta daina shan ruwan gidansa (pure water) ko maltina
ko swan. Kasancewar Nazir Business ya ke daga
Yola zuwa (Dubai), a duk san da zai tafi to kudin
kashe ko na dawainiyar gida yana hannun
Ummulkulthun, gaba daya dangin mijin sai su ka.
fara (Respicting) dinta don duk wanda ya ce ga
bukatarshi to zata dau kudin Nazir ta yi musu ko
nawa ne, shi kuma ba shi da bakin yin magana, ba a
kwana uku sai mahaifiyar Ummu ta aiko a karba
mata kudi sai ka ce (bank).
Kuma koda Nazir ya tashi yin tafiya dole sai
yaje ya sallami mahaifiyar Ummu don dolen shi ne
ya je in ba haka ba ya gamu da bacin ran Ummu.
Kawar Ummu tazo gidanta ta kawo mata
ziyara suna cikin daki sai Hani ta dubi Ummu ta ce
Anutynki bata nanne? Ummu ta yatsina fuska ta
tura baki tana dakinta kinsan yanzu falon ya mata
zafi don ba na ragar mata. Hani ta ce gaski, ba kya
9
kyautawa don Allah ki dinga ragar matga kada wata
rana kashinki ya bushe, Ummu ta yi dariya ta ce,
wallahi karya take yi, domin naje fa ba cafe kuma a
haka zata kare sai bakin cikin ya kashe ta tunda
dani zata ja, kuma na riga na zame mata kadangaran
bakin tulu a karni akar tulu a barni na 6ata ruwa.
Hani ta yi dariya tace "To Allah ya shirye ki
Ummu." Ta tabe baki dama can a shirye nake, Hani
ta ce "To amma dai wannan takun saka ya yi yawa
ku dan sassauta ke fa kece karama, hum zancen
kishi fa ba wata waye-waye, kuma kishiya ba abun
yarda ba ce ko kanwarka ne ta zama kishiyar ka to
sunanta kishiya, Hani ta katse ta, to sarkin kwaba
me ya kawo maganar kanwar ka ta zama kishiyarki
in ban da shirmen ki, Ummu ta yi dariya ta ce, to ai
ke kin zake da yawa irin wannan ketente ne gida
haka, azo garin ku a fiku iya rawa, hum ke ma kin
san kowa samu rana...dole ta yi shanya, in ji
Tani.
Ummu ta nisa ta ce, to ai ni ba ki sani ba wai
jibi Nazir zai tafi (Kwatano) kuma wallahi ni yanzu
bana so ya yi nisa dani da kullujm idan ba na tare
dashi bana jin dadi kuma gashi ya riga ya sabar min
da wasu abubuwa...Iye? Ummu me kike fada?
Lallai na yarda shiru-shiru a layi amma yanzu d
akika yi aure duk sai ki ka zama iwa uwar mata su
ka wakwashe da dariya su ka tafa, Hani ta ce to
10
Allah ya shirye ki Ummu ta ce dama can a shirye
nake.
ASALIN LABARI
Nazir da na ga Alh. Yusuf amma ba shi ba ne
babban dan shi, shi ne kusan dan shi na shida amma
a gun mahaifiyarshi shi ne na uku mata, Alh. Yusuf
uku ne H. Aisha ita ce uwargida sai H. Halima sai
amaryar su Hauwa amma ita b ai kai ta Makka ba,
Alh. Yusuf dan kasuwa ne kuma shahararren mai
kudi amm ba ya nuna wa duniya wai shi mai kudi
ne sabanin sauran masu kudi.
Alh. Yusuf mutumin Zaria ne a wani kauye da
ake kira (Hunkuyi), ba zazzage ne na asali amma
sai Allah ya sa arzikinsa yana garin (Yola) a nan ya
auri Aisha 'ya'yansu biyu ya auro Halima su ka fara
jera haihuwa da uwargidanta Aisha har Allah ya
kawo Hauwa. Nazir ya na da yayu maza uku mata
biyu Rakiya da suwaiba sai Ibrahim, adam Nura, sai
kanne Abdullahi, Khadija, da kuma Halima,
takwarar Hajiya karama wato Hajiyar su Nazir,
Nazir dangata ne a gun mahaifiyarsu amma shi fari
ne, sauran yayun shi da ya ke bi masu bakeke ne
babbar 'yarshi Hajara ta na aure a Zaria sai 'ya'yanshi Abbakar sai sauran kannenshi to
kasancewar shi ne ya karanci Business sai
mahaifinshi ya dora shi akan dukiyarshi tun suna
11
safara tarc har Alh. Yusuf ya daina komai Nazir ne
mai yi ya na tafiya Kotono, Fatakol, da sauransu to
kasancewar shi ne dan zirga-zirga a garuruwa, sai
ya samu daukaka a gidan don komai shi ne mai yin
hidima a gidan sabanin yayunshi, Nazir irin
mutanen nan ne masu kamun kai ba shi da
hayaniya, nutsattse ne.
Nazir ya na da wata yarinya da su ke soyayya
Jamila, kowa ya san su tare kwatsam Malam Jibrin
aminin mahaifin su Nazir ya na zaune tare da
1yalansa gwanin ban sha'awa suna dan taba hira ya
dubi matarsa ya ce "Ya kamata yan wannan yaro
Zakariyya ya fito a gama magana da yarinyan nan
don ina so ta yi azumi a dakinta. Nana Bilki ta dube
shi wato matarsa ta ce "Hum, ai an ba shi
'yar'uwarsa wai hadin gida zasu yi amma shi ya ce
baya sonta, Malam Jibrin yayi dariya ya ce yaro
kenan, lallai zamani ya canja har iyaye su ce ga
wacce za su ba ka amma don taurin kai irin na yaran
zamani sai su ce ba haka ba. Gaskiya bai kamata ba,
an sai dai Musulunci ya ba da dama ka zabi matar
da ka ke so to amma dole ne ayi musu biyayya ko
dan samun kyakkyawan karshe, Nana ta ce kai ma
dai kasan yaro idan ya kafe sai dai addu'a ya ce to
Allah ya rufa asiri.
Su na cikin hirar su yaro ya yi sallama, wai
Shema'u tazo in ji Zakariyya da ma ta na daki Baba
12
nc ya ce wa yaron je ka cc ya shigo, Zakari ya shigo
msu ka gaisa Baba ya cc Zakariyya ba mahaifinka
ya yi maka mata ba? Kanshi a sunkuye ya ce Baba
ai ba mu daidaita da ita ba, Baba ya yi dariya ya ce
ba mahaifinka ba ne ya zaba maka ita ba? Shi ne,
sai Baba ya fara mar nasiha kamar haka.
"Ina so ka kasancc mai biyayya ga iyayenka
kayi hakuri ka karbi tayin da su ka yi maka, insha
Allahu ba za ka tabe ba, kuma ka zama mai yarda
da kaddara kairi wa sharri (mai kyau ko
mummuna), kayi hakuri kuma insha Allahu idan
Shema'u rabon ka ce sia kaga ka aura idan kuma ba
rabon ka ba ne to Allah ya sa haka shi ya fi alheri,
Zakariyya na tsugune ido sun kada har tausayinshi
ya kama ni saboda nasan ciwon so.
Da Baba ya gama yi mashi nasiha, ya mike jiki
babu laka ya yi zauren mu, gurin da muke hira,
Baba ya ce "Shema'u ga Zakariyya ya na jiranki,
Nana Bilki ta ce ko akwance ta ke, Shema'u ta fita
jiki babu kwari tashi ta yi hanyardakin zaure wato
dakin Kabiru yayanta, ta shiga da sallama ya na
une kan kujera a sanyaye ya amsa kasancewar
asan halin da ya ke ciki bai nuna masa komai ba, ta
ya zakariya sannu da zuwa, ya dube tga da kyau ya
kare mata kallo a zuciyarshi ya ce zan yi missing
dinki amma a fili ya ce da girman kujerar ki, ta yi
dariya yaya kake? Ya yi tsaki mits, babu yadda nake
13
Shema'u ta zaro ido mc ya faru? Ajiyar zuciya ya yi
ya cc, "kina nufin ba ki san komai ba ne, a game da
halin da nake ciki? Ranta ya dan baci da ya tuna
mata wannan takkin orber da ake shirin yi musu, ta
dan kanne damuwar ta ta ce, to meye what? Kina
nufin ke bai dame ki ba? ashe dai ni kadai nake
haukana? Please Zakariyya ba haka ba ne kasan
komai mukaddari ne to amma tunda da abu ya zo
haka ina mai baka shawara komai ka gani daga
Allah ne, so dan haka kayi fatan alheri a game da
wannan lamari, ni kam Allah ya na gani ba ni na ki
ka ba......dakata Shema'u wannan yarinyar da aka
ba ni fa tafi ni a haife kusan sa'ar uwatayes
ana haka ai, tunda Annabi Muhammad (S.A.W) ya
auri matar da ta fi shi shekaru, so ashe don ka aure
ta ba laifi ba ne, ranshi ya dagule ya mike zai fita ta
tsaya a bakin kofar kayi hakuri idan ranka ya baci
ba wai na fada da wata manufa ba ne bai saurare ta
ba ya fice ran maza ya 6асі.
**
Hadiza ce ta shigo da sallama Shema'u zo ki
raka ni School dinmu na karbo testimonial dina
nayi nayi yaya ya kaini ya ki na ced ki fada wa
Nana Hadiza ta shiga daki ta gaida Nana Bilki,
Nana Bilki ta tambaye ta su Hajiya da sauran yara,
ta ce duk lafiyarsu kalau, suna gaishe ku muna
14
amsawa idan kin tashi tafiya ga sako zan ba ki ki
kaiwa Hajiya Babba, to dama ina son Shema'u ta
raka ni School ne zan kar6o takardana naji 'yan
ajinmu sun ce wai an fara raba (testimonial) Nana
Bilki ta ce to kada kudaďe Baba zai muku fada ku
dawo da wuri su ka cc to Nana mun gode suna
murna su ka fita a hanyar su ta tafiya ne su ka hadu
da Zakariyya Hadiza ta tsaya suna gaisawa Shema'u
kuwa ta wuce ba ta tsaya ba Hadiza ta ce, ranka ya
dade yaya yau nagan ka beari lazyhate me ya faru?
Ya yi dariya ya ce babu komai kawarki ce take
waina ni ta yi dariya ta ce mc ka mata take
wainaka? Yo ina na sani kinsan ku mata da mulki
my bc mulkin ce yau ta motsa, a'a Zakariyya ruwa
ba ya tsami banza amma dai ka bari mu dawo kada
mu yi latti ina zaku je haka? Wallahi zamu school
din mu ne naji an ce wai 'yan JSCE ana raba musu
(testimonial) dinsu shi nr zan jc na karba, to ko
nazo na kai ku ne? A'a bari kawai yanzu zamu
dawo, to sai kun dawo zan jira ku ta ce to Hadiza ba
ta samu Shema'u anan kusa ba sai da ta yi nisa
sannan ta ji rata ta iso ta same ta, amma kin ban
kunya mutum ya hadu da masoyinshi amma ko ya
kula shi yau an gan ku a rana, Shema'u ta ce, share
shi kinsan meye? Sai kin fada." In ji Hadiza,
Shema'u ta karkata kai ta ce ai tun da naga kin tsaya
kuna ta wani surutai nasan ba ki san komai ba a
15
game da lamarin shi ba, ni kam faďa min don Allah
ba na son wani dogon sharhi, hum "Zakariyya
ammashi mata, wai aure dangi za'ayi mashi Hadiza
ta zaro ido da gaske wallahi ke kinsan waye matar
shi? Hadiza ta ce a'a sai kin fada ta tabe baki ta cс
wai Ruky, Rukaiya zai aura wannan 'yarshi ce da
gaske kike ko da wasa? Da gaske nake miki wannan
zance to amma shi ya nuna min wai ba ya son
wannan aure ni kuma duk jinshi nake kinsan su
maza su na ba sa son mace amma da zaran an yi
biki za ki ji su shiru Hadiza ta ce to 'yan keya ya ku
ka yi? mtsi....ta yi tsaki wai yanzun ina tausar
zuciyata ne tun daga yanzu na fara hakuri da son sa
kin san ma meye? wai yanzu yazo ya na ce min wai
shi me zai yi da Rukayya da sauransu ni kuma na ce
masa ai komai nufin Allah ne.
Sun dawo sun iske Baba a gidan Alh. Yusuf ya
na ta yi mana fada wai mun dade ranar a gidan su
Hadiza mu ka kwana saboda nasan Zakariyya zai zo
gidanmu sai na tura Hadiza taje ta fadi wa Nana
Bilkisu.
A washe gari da safe kawai sai ga Nazir ya
shigo, muka gaisa da shi sai na ji su Hajiya su na
cewa yaushe ka dawo? Ya ce shigowar dare mu ka
yi aka kwance tsaraba mu ne yan fasa kwakwa,
muna cikin yin haka aka kawo abarba mu ka hau
yankawa, muna ta sha na dubi Hadiza na ce "Hadiza
16
ina ma acc na auri Nazir ya yi ta kawo min tsaraba,
Hadiza ta dauko min kujera ta sa a bayana muna ta
dariya wai santin zakin abarba nake yi muka yi
dariya son ranmu har su Hajiya su na cewa wannan
dariyar haka ai sai ace kunyi gamo ne. Da ya ke
Hadiza ta fi ni wayo, ko a haife ma ta dan fini sai ta
yi ta zuga ni wai wallahi na fada wa Baba ni har na
manta sai ta ce wai na fada ni kuma da ya ke bani
da wayo sosai, don duka-duka shekaruna sha hudü
ne, ranar mu na zaune ni da Baba na ce "Baba
wallahi ni kam ina son Nazir din gidan Alhaji, Baba
ya yi dariya ya ce "Allah Shema'u? Da gaske kina
son sa?" Na ce "Wallahi Baba ina sonsa."
Baba yazo ya- samu Alhaji Yusuf a gida bayan
sun gaisa ya sanar da shi na ba wa dana Nazir
Shema'u, Alh. Yusuf ya yi murna ya ji dadi sosai,
ya ce Allah ya saka da alheri na gode, Allah ya dada
girma, Allah ya sa a yi damu. Baba ya ce "Babu
komai, Allah ya ba su zama lafiya."
Alh. Yusuf ya shiga gida ya shaidawa matansa,
ai kuwa kowa ya yi murna da farin ciki Alh. Yusuf
ya kira danshi ya shaida masa, nan Nazir ya rude
saboda ya ji abu ba zata gashi kuma ya na da tashi
masoyiyar wacce su ke soyayya unguwar su daya
ya ce Alhaji ina da wacce na ke so, kuma mun yi
alkawari, to ka yi hakuri tunda ga wanda mu ka
zaba maka, tashi kaje.
17
Dakin Hajiyarshi ya shige ya sanar da ita
komai, ta ce to meye ne don an baka Shema'u?
Gaskiya ni Hajiya ba na sonta, ina da wacce nake so
kowa ya sani a gidan nan, Jamila na ke so shi kanshi
Alhaji ya sani, to kuma shi ne yanzu a ce na auri
Shema'u, ni kam ba na sonta, Hajiy. ta harare shi
tunda ba ka sonta sai ka je ka samu Alb ji ko Baban
ku Jibrin ka fadi mashi, tashi ka bani guri ya na
tsugune bai tashi ba ta share shi ta ci gaba da
gararinta.
Nazir kai ya dau zafi, ya rasa meye abun yi ya
samu Sulaiman abokinsa ya sanar dashi halin da ya
ke ciki, Sulaiman ya bashi hakuri, Nazir wannan
zabi da iyayanka su ka yi maka insha Allahu ba za
ka yi deegreating ba, so don haka ka yi hakuri ka
karba me laifin Shema'u? Mace ce har mace duk in
da ka ke son haduwar mace Shema'u iyaka cе.
Nazir ya katse shi cafanen Likita ce fa? Meye
abun sha'awa ga farar mace? Na ji ban ga abun
sha'awa ba, amma dai ya zama dole kayi biyayya ga
iyayenka, me ka gani? Nazir ya na shiru bai kula shi
ba, can ya nisa ya ce "Sulaiman ina son Jamilash
don babe din ta hadu sosai, Sulaiman ya ce to ka yi
hakuri dai mu mika lamarin mu ga Allah Ubangiji
ya zaba mana abun da ya fi alkairi, Nazir ya nisa ya
ce amin.
18
Nazir ya samu Hajiyarsu a daki ya gaishc ta ya
na tsugunc a gurin bai ce kala ba, ta dubc shi ta ce
lafiya? Ya sunkuyar da kai kasa ya ce Hajiya ni fa
gaskiya ki fada wa Alhaji wannan magana na
Shema'u a barta, tsawa ta daka mashi ba ka isa ba,
ai mu mukia haifc ba ba kai ka haife mu ba, kuma
na ji ka ce za ka bar garin, to duk in da kaje za ka
dawo kuma ka same ta don haka dabara ta rage
naka, aure babu fashi nan da sati biyu tashi ka bani
waje.
A rude ya shiga dakin Sulaiman ya yi bala'in
gigicewa ya fada wa Sulaiman duk abin da ake ciki,
Sulaiman ya ce don Allah ka nitsu ka kwantar da
hankalinka komai ya yi farko zai yi karshc, Nazir ya
katse shi wallahi Sulaiman na tsani Shema'u, kai
duk wani