shiru maganar *Oga J* Babu kaunarshi ko
kadan a raina pld besty ina bukatar hutu kar ki rikita min
kwanyata ta fada tare da lumshe Ido, Zahra ta kallli Amrah
cike da mamaki dariyar gefen baki ta yi tana hango nasara
121
AKWAI KURA 2
tabbas Amrah sokuwa ce Ta fada kauna ba tare da ta sani ba
Hmm niko badan taba zabar wani kan dan uwana ba ya damo
dole in cusa mata kaunar Yaya Anas in kuma cusa mata tsanar Saleem Jarumi.
****
Cikin dabara Zahra take shafa kan Amrah, ya yin da Idon
Amrah ke lumshe kamar tana bacci besty na san idonki biyu,
dan so ki farga karki kai kanki inda za'a wulakanta ki, ki tsaya
a matsayin da Allah ya ajiye ki kinga masu kudin nan san basu
san darajar mace ba, ganinsu kudin su shi ne mutuncin su zasu
iya taka mace ko yaushe tun da suna kudin auran wata infact
sun mayar da mace tamkar hula a jos pld bestyna karki bari
Kyau da kudi su rinjayeki ki kai kanki inda da kiyi dana sani.
Amrah da ranta ke suya saboda kalaman Zahra ji take
kamar ta kwadawa Zahra Mari sai dai Zahra tafi karfin haka a
wajen Amrah Amana ce mai tsanani a tsakaninsu ta rai da rai.
A can karkashin zuciyarta kuma tana mamakin yaushe Zahra ta dawo haka ? In auren kudi ne yo ai ita ma Maheer iyayensa masu kudine me yasa ba ta yiwa kanta wannan
korafin ba ?Amrah ta gyara kwanciya tana sauke numfashi
alamar barci ya yi nisa sai dai ko na minti daya ba ta yi baccin
ba burinta Zahra ta bar tusa mata bakin ciki ta hanyar Maganganun ta kuma ma wai tace da Zahra din Tana Son
Saleem din ne ? Damm gaban Amrah ya buga kamar a mafarki
take tuno Saleem din tun farkon Saninta da shi da irin kiyayar
da yake nuna mata har ta kawo ceto rayuwarta da ya yi Amrah
ta ajiye maganar tare da Jin Dadin kalaman Saleem a ranta
musamman inda ya kasa boye soyayyaarta a gaban kowa.
Zahra ta dakata da maganar ganin Baccin Amrah ya yi nisa da sauri ta mike daga wajen tare da kara wayarta a kunne dake kara cikin lumshe ido ta fara watsawa Maheer kalaman kauna
122
8
AKWAI KURA 2
Tarr da nuna masa ba data iya rayuwa ba in babu shi fuk
maganar da takc Amrah tana jinta-Sosai take mamakin Zahra a
kasan zuciyarta tana al ajabin meyasa ita bata jin irin wannan
kaunar idan suna tare da Anas ko suna waya.
Amrah ta rufe ido da karfi tana dabarin bacci dan tunani na
shirin fasa kwanyar ta, Amma sai dai ina babu abunda take
gani cikin idonta sai surar Saleem mai kyau tare da kwarjinin
sa mai daukar hankali a hankali ta fara maimaita maganganun
shi a ranta, zan cigaba da sonki har sai na mutu.
****
Ummy gida suka wuce kasancewar dama Granny ke daune
asibiti tana jinyar Amrah, Tun a mota Ummy take bawa Abban
yan Uku hakuri tare da nuna masa tsananin jin dadinta na
nasarar da Amrah ta samu, Abban yan uku bai yi fushi ba ya
musu uzuri sosai ita da Granny ai batan-mutum sukutum ba
wasa ba koshi ba karamin damuwa ya- shiga sanadin rashin
ganin Amrah.
Cikin dariya yake fadin Ummyn yan uku Nayi hakuri sai
dai-yau fa hakkina da aka-cinye na tsawon kwanaki 14-yau dan
fanshe eheeeee Ummyn Amrah ta rufe ido tana dariya, cike da
kauna yake kallon ta Sosai kunyar Zainab tana burgeshi.
Abban Amlah ya katse mata kunyar ta hanyar jefo mata
tambaya ni kam Ummyn yan uku an ya bamuyi tuya mun
manta da albasa ba ? Ummyn yan uku ta kalleshi tana son jin
karin bayani Abban Amlah ya rage gudu tare da dan kallon ta
Ina nufin kafin Karbrn sadakin nan kun dauna da Amrah ta
fada muku ta amince da yaron nan Anas kafin tsaida rana.
Damm gaban Ummy ya buga cikin girgida kai ta furta ah
ah ni dai ba muyi haka da ita ba amma ina ga-ai sunyi da Iya,
Abban Amrah ya kama baki lallai lamarin mata sai ku Lallai
kunyi wauta ai ya dace ayi hakan dan fita hakkinta Ummy ta yi
123
AKWAI KURA 2
shiru yandu kam koma meye ai dole tai hakuri tun da an tsaida
rana, Hmm ya fada tare da kashe motar Bayan ya yi parking a
gefen hanya kina nufin dan yarda in yiwa diyata auren dole?
Babu wannnan maganar yan mata koke sai da kika garani
daga karshe da yardarki aka yi auren mu dan haka badan taba
auren dole wa diya taba ya fada tare da tada mota ya dauki
hanyar gida dama sai wajen 10 na dare suka fito daga asibitin,
kafin su karaso gida Yan Uku duk sunyi baccі.
Direct dakin Ummyn yan uku suka wuce domin ya karói
hakkinsa Lolz, suna shiga ya rungumota ta baya ya fara manna
mata kiss a wuya yana wasa da dukiyar fulaninta domin ya yi
tsananin missing dinta sosai...... Ni- dai daga nan na janyo
musu kofa na-koma falo ina daga falo da dinga jiyo ihun
Ummyn yan uku.
*****
Saleem ya figi mota da gudu ya bar asibitin kamar dai tashi
masa, Wani tulin bakin kishi ke cin duciyarshi game da jin
haushin Amrah tana kallo yana mata iskanci bata hana ba.
Kamar ya dare yake zancen zuci ya yin da ya fito fili Inaaaa
ya damo dole ayi komai cikin karamin lokaci a bani matata ba
dan jure ganin kananun marasa kunya suna furta kalamr so ga
Matata ba mtsweeeee yaja dogon tsaki in anyi auren ma kasar
dan bari in ga ubanda dai kallar min mata.
Cikin Bacin rai ya isa Airport din, Tun daga nesa Meerah
ta hango kanin nata da gudu Affan ya taka yana daga hannu
oyoyo uncle Saleem ya danne bacin ranshi cikin murmushi ya
mikawa Affan Hannu oyoyo my Dear Son.
Meerah da sauri ta tako hannu Saleem ya mika mata da sauri
ta cafke tare da masa katlon kurilla any problem my dear ta
fada tana shafa fuskar Saleem, Saleem ya kada ido Tare da jan
karamin tsaki kaina ke dan ciwo Meerah ta ce subhanallah
124
AKWAI KURA 2
muje gida bani key in ja Motar Saleem ya kada kai tare da
nufar motar karki damu sis dan iya kai mu gida.
Sorry Meerah ta fada cikin tana kallonshi yaya jikin Maman
Affan ya tabe baki da sauki Meerah ta kalleshi tana mamaki
Bro lafiya kan? Waya taba min kai ne i knw ba ciwon kan
kadai shine matsalar kaba..
*****
Bayan boot din ya bude ya yin da Mera ta loda kayanta
Mtswweee ya kuma jan dogon tsaki Sis ayi sauri a karbo min
auren ta ba dan jure ganin kananun marasa kunya suna kaiwa
matata hari ba, Meerah ta kunshe baki tana dariya tuni ranta
ya yi fari tass dama ta samu labari gun Mom kan haukacewar
da Saleem ya yi akan Amrah.
Yanzu ko maganar daya fada ya kara tabbatar mata da
kanin nata ya yi nisa cikin kogin-kauna, tuni ta ramfo dancen
kishi ne ke damun shi cikin dabara ta fara magana Ayya Sorrybro ai ya damo dole koma waye ya bar maka matar ka Amrah
ta ka ce kai kadai, ni nan shaida ce domin tun fara ganinta a
duniya da kai kuka dace.
sa
Saleem bai san lokacin da murmushi ya baiyana akan fuskar
ba Cikin Sakin fuska yace yawwa sis ashe kema kinga
hakan? Meerah ta daga gira sosai ma Ai Amrah tamu ce babu
mai ra bamu sai Allah kuma shima muna rokonshi daya bawa
kanina Amrah m nasan Allah dai ji kanmu dai bamu abar mu.
Cike da nishadi Saleem yake tukin-mota Ya yin da Meerah
ke jin tsantsar farin cikin Son da Kanin nata ke yiwa Amrah,
Tafiyar minti kadan Suka iso gida zuciyar Saleem tass ya
wanke saboda hirar da Sukayi da Meerah daga Airport zuwa
gida, koda ya yi parking da kanshi ya bude mota tare da- fadin
sis in kin huta ki mun magana in kaiki asibiti kiga jikin Matar
Saleem sannan ki kara mata lecture kan soyayya lolz dan taki
125
AKWAI KURA 2
sakewa da ni niko kan sonta ko gaban Waye dan fada ina
kaunar Amrah.
Meerah ta kama baki tana mamakin Saleem yadda soyayya
ta mai da shi mai surutu, Saleem ya kalleta nima bari in dan
runtsa kafin ki shirya, Meerah ta yi dariya no problem my bro
Allah ya kara kauna kai da Maman Affan Allah kawo mana
kannen Affan yan uku uku Ameen ya fada yana dariya.
*****
Da misalin karfe 4 na yamma Maheer ya koma asibiti dan
dauko Zahra ya maida ita gida, Saidai Amrah ta dage sam
bestyn bada ta bar asibitin yandu ba sai dare, ganin haka yasa
Maheer ya bukaci kebewa da abar kaunar shi a waje dan suyi
hirar lofе.
Amrah tace oho dai kuje minti 20 na baku in ban ganku
ba dan tako da kaina in do granny ta kama baki da wani
kafar ?jinake da duma sai da Aka taimaka miki kika iya
takawa kai yarinyar nan kin kware a gulma, Maheer da sauri
ya futa yana dariya kafin Granny ta dawo da fadan kanshi dan
a halin yandu ya gama sanin tsohuwar kan yarfa mutane.
Bayan Mota Maheer ya budewa Zahra bayan ta shiga shi
ma daya murfin ya bude na gidan bayan ya shiga tare da rufo
kofar yana murmushi gimbiyata Allah Allah nake ranar Auran
nan tado in huta da kewanki, Zahrah ta yi dariya Abokin
rayuwata nima haka na daku ayi abun nan ko dan huta da
rashinka a kusa da ni, Maheer ya ji dadi a ranshi na kaunar da
Zahra ke nuna mishi.
Am kina ji Babyna Inda hali Dan Allah ki baws yayanki
shawara kan Besty me dai hana ya hakura naga alamar bestyn
kamar bashi take yi ba, Zahra ta ware ido cike da mamaki take
kallon Maheer take ranta ya baci kallon raini tai masa cike da
masifa Lallai ka bani mamaki kana nufin danki dan uwana ne
126
AKWAI KURA 2
in dabi bare saboda yana abokinka ? to inma bacci kake ka
farka besty ta muce sai dai abokin naka ya hakuri daman
hawan kawara yakeson yiwa mana.
Maheer ya kalleta shima cikin bacin rai karo na farko tun
sanin shi da ita da suka fara samun sabani Cikin hade rai yake
magana Zahra'u yau ni ki kewa magana hakan sai kace sa'anki?
Karki sake kaunar da nake badan jure raini ba, kuma duk
wani mai hankali in yakalli Anas da Amrah yasan basu daceba.
dakata Maheer badan jure wannan cin fuskar ba kan abokinka
aiko kai da yake abokinka baka jure ba bare ni da Yaya Anas
yake dan uwana uwa daya-uba daya, da sauri ta balle murfin
motar bata saurare shi ba-ta yi dakin cike da fushi, shima
Maheer ranshi a bace bai dakatar da ita ba sai ido daya runtse
yana jin haushin kalamanta, mtswwweeee yaja tsaki. Akwai
ranar da dan baki nan na duwa amman nasan Amrah ta muce
alfarmar Annnabi Muhammad S.a.w
****
Sai da Zahra ta daidaita-nutsuwar ta kafin ta bude kofar ta
shiga tare da Sallama, sai dai duk boye damuwar da ta yi kallo
dåya Amrah ta mata taga bacin rai a fuskar ta, da ido ta mata
tambaya meya faru kasancewar Granny tana dakin, Zahra ta
kirkiro murmushi wanda yafi kuka ciwo tare da cida lebba ba
komai Kinsan bbyna da Naci-wai sai dai in-dauna muyi hira ni
kuma ba dan saba lokacin da kika bamu ba, Amrah ta yi
murmushi tana mai jinjina kai saboda dadi kan abunda Zahra
ta yi cikin dariya tace da Zahra ya kamata ya-barni da Bestyna
muyi hirar yaushe gamo dan ina kewar besty na, Zahra ta yi
dariya ita ma haka ne rabin ran suka yi dariya gabadaya.
Shigar Zahra dakin keda-wuya Motar- Saleem ta-shigo
asibitin tun daga nesa ya hango motar Maheer hakan yasa Ya
ajiye Motar sa kusa da ta Maheer cikin shigarsa mai kyau na
127
AKWAI KURA 2
riga da wandon danyen boyel kansa sanye da hula ya yi kyau
sosai hannunsa rike dana Affan wanda shi ma ya yi kyau cikin
kananun kaya na yara, Saleem ya fito daga motar Meerah da
Zahra biye da shi dukkansu cikin shiga mai kyau da kagansu
kaga wanda naira ta dauna musu, cikin girmamawa Maheer ya gaida Meerah antyn mu barka da duwa Meerah ta amsa tana
dariya ya yin da Zahra ta gaida shi Hannu Maheer ya mikawa
Saleem suka yi musabaha tare da daukan affan a kafada sukа
jera zuwa dakin da Amrah take kwance. ****
Maheer ne ya bude kofar tare da Sallama daya bayan
daya suka dinga shigowa dakin, ido cak Amrah ta tsayar kan
Affan cikin jindadin ganinshi ta ware hannu Oyoyo my Boi
Affan dake hannun Maheer ya fara kokarin sauka Duk da
kunburin fuskar ta hakan bai hana ya gane ta ba Maman Affan
ya fada tare da karasawa da gudu ya fada jikinta.
Meerah ita ma da gudu ta rungume Amrah tana jin dadin
ganinta ya yin da fuskarta ke cike da tausayin Amrah ganin
halin da take ciki, itama Zahrah Sosai Amrah ta bata tausayi
yau shi ne karon farkon da ta fara mata kallon arziki Cikin
nuna tausayi take gaida Amrah.
Sosai Amrah taji dadin ganinsu cikin murna take wasa da
Affan tare da fadin ina kewarka Swthrt, Zahra yar kallo ta
damo saboda ganin Meersh da Zahra cikn shiga na kece raini
da gani kudi ya dauna musu tuni ta raina ta ta shigar tun
shigowar su ta koma gefe ta damo yar kallo, Amrah ta mai da
hankali kan Zahra Anty Ga bestyna fa Da fara'a Meeah ta kalli
Zahra cikin jindadi ta jawo ta jikinta hehehehe yau naga
kyakkyawar bestyn Maman Affan-wadda kullum ake mana
hiranta.
128
AKWAI KURA 2
Zahra ta yi murmushin jindadi Cikin kunya ta gaida Meerah
ita ma Zahra Momy hannu ta mikawa Besty tare da fadin nice
to meet yhu namesake, take Zahrah taji bestyn ta burgeta
kamar yadda itama Bestyn ta yaba da rashin girman kan
familun su Saleem din, Saleem ya bata rai tare da hararar ta
Wato Madam ji amma manta da ni ko Farin cikin ganina ba ayi
ko? Amrah ta rufe ido cikin kunya tace da shi Barka da
Yamma Oga J
Gabadaya suka yi dariya saboda yadda Amrah ta yi,
Basket Zahran Mommy ta jawo Tana kallon Amrah besty ita
ma ta fada kamar yadda taji Zahra tana fada mata tashi kichi
abinci dan girkin Mom ne tace lallai mu tabbatar kin ci,
Amrah cikin jin dadin kaunar da Mom ke mata tace ay ko dole
na inci girkin uwata a hankali ta daunar da Affan kan gadon
Ckin shagwaba ta kalli Bestyn nata pld besty na Serbe mie.
Zahra ta harareta an ki-ayi-din ehee Saleem dake-kallonsu ya
karaso wajen tare da daukar plate ya bude Flask din Fefesun
kifi ne tare da dankalin turawa wanda ya sha naman kaji a ciki,
cikin tabe baki yake fadin ai ba da ayi mana gori ba tun da ina
kusa kwantar da hankalinki Wifeynah ya kalli Amrah yana
dariya.
****
Granny dake daune tana kallonsu darduma ta dauka barin
fita daga dakin nan, naga wa in nan yara sam baku da ta ido,
dariya gabadaya suka yi har da Zahran Mommy da alamar
lamarin Saleem ya fara bata saduda, itama bestyn sai da ta
dandara saboda kar ace kowa ya yi ita ba tai ba.
Matsa Saleem yace da Meerab bayan ya gama sanya
abincin a plate Meerah ta mike tana dariya Saleeem ya jawo
farir kujera gabanshi cikin sauri ya dauna a daidai gaban
Amrah abinci yana rike a hannunsa oya karbi ki ci, Ido Besty
129
AKWAI KURA 2
ta sanyawa Amrah ya yin da Amrah ta kalleta ido cikin ido
Besty ta kauda kai tare da bata rai taga iya kar gudun ruwan su.
Gabadaya jikin Amrah ya yi sanyi musamman tun da rana
duwan Zahran da ta ga yadda take mata abu tace a zubawa
Zahra, Amrah ta bata rai tana kallon gefe ni na koshi ba yanzu
dan ci ba Saleem ya shafa gemu eeh ba yanzu daki ci ba naga
kince asa miki ko? To wallahi ko kichi ko in matseki in miki
dura Allah kenan.
Gara ma ki sani na damo miki karfen kafa ni din mayen kine
badan barki ba ko mutuwa haka zata gan mu ta barmu ya fada
cikin bata rai dan yana sane da irin kallon da Besty ke wurga
mata plate din ya mika mata tare da kokarin tashi da ki ci ko
kinfi kaunar duran, Amrah da sauri ta kalli Anty Meerah cikin
dubar hawaye tace anty kin ganshi ko?
Mera ta yi dariya a'a maman Affan ko ni ina bayan bro kan
cin abinci dan girkin Mommy ne na musamman ta miki kin
ganni koni da nake bakuwa ba tai min girki ba sai ke yar gatan
Mo, Amrah ta yi murmushi tana share hawaye cikin nutsuwa
ta mikawa Saleem hannu Tare da kauda kai bani abincin,
Saleem ya tabe baki badan bada ba ki juyo ki kalleni dan ni ba
dodo bane Mijin Amrah ne, Amrah ta bata rai tana cin magani
ita fa rashin kunyarsa a gaban kowa ya fara bata haushi.
Saleem yamika mata plate din yana dariya ashe matata
matsoraciya ce mai kukan cin abinci Maheer ya amsa a'a fa
Bestyn mu ai ba duk mata ba jarumtar ta, Meerah ta amsa ai
har madan aradu gabadaya suka bushe da dariya.
***
Sosai Saleem yake shigewa Amrah ya yin da baya shakkar
kowa kan kaunarta tare da nuna mata kauna, Cikinhankali
Amrah take cin abinci tana yamutsa fuska Saleem na kallon ta
130
AKWAI KURA 2
bai ce komai. ba a ran shi ko fadi yake yarinya kichi abinci ko
in miki dura lolz......
Tsam Salecem ya tashi daga wajen da yake zaune kayan da
yazo da shi jiya yaje wanda babu komai da aka taba a ciki
Saleem ya dauko kwalin waya Cikin nutsuwa ya dawo gaban
Amrah ya dauna wato Matar Saleem naga alamar kina so muyi
fada dake ko?
Amrah ta bata rai tana kallonshi tare da barin cin abincin
wayar ya ciro akwali tare da kunnata ido ya mayar kanta tare
da mika mata nace a kunna saboda ina son in fara kiran-matata
mu sha hirar soyayyaa ta waya naga-mutane suna hanaki muna
min lobe saboda kunya, Amrah ta harareshi-tana sonyin kuka
ba dan komai ba sai dan yadda Saleem yake disgata a gaban
mutane musamman Bestyn ta data hade gabar da kudu saboda
kishin dan uwanta Anas, shi ko Saleem yana sane da kailon
bandan da Zahran ke jefa-mata shi yasa-ya sake yake abunda
yaso burinshi ya kunsa mata bakin ciki.
Karbi ya kuma fada karo na uku-Amrah ta sanya hannu ta
karba bata ce komai ba ta ajiye gefen gado ya yin da Dukkansu
suka bi wayar da kallo musamman Zahran Mom wow kai bro J
wayar nan ta kawo wuta ita naga ake tallan ta a TB iPhone
11pro mad pld yaya nima, Saleem ya bata rai yana kallon ta
ke bada kiyi hankali ba ko? Zahra eikin sauri ta fara bashi
hakuri bai ce mata kala ba ya kalli Maheer muje dan dawo da
magriba in daukesu Maheer ya-bi-bayan Saleem-tare-da-fadawa
Zahra zai dawo shima da magriba ya mai data gida.
Basu bar asibitin ba sai da magriba kafin su rabu shakuwa
sosai ya shiga tsakanin Amrah da Zahran Mommy hakan Besty
tuni sun daura Abota da Zahra hakan ba karamin dadi ya yi wa
Meerah ba dan taga alamar Zahra ta yarda makaman yakinta
tabi Allah dan tasan sarai kan Amrah Zahrah ita ce data sha
131
AKWAI KURA 2
wuya saboda yadda Saleem ya rikice kan Kaunar ta tana da
tabbacin in har Zahrah tai wargi kan Amran tsab Saleem dai
mata duka.
Tare suka fito zuciyoyinsu cike da kewar Amrah kamar su
kwana tare ita ma Amrah tafiyar nasu sai da taji babu dadi
saukinnta daya granny tana tare da ita tana debe mata kewa da
ban dariyar ta,
Bayan sallar Isha'i Anas da Dad na shi suka dawo duba
Amrah suma tsarabar maras lafiya su ka zo mata da shi mai
yawa, Granny ta dinga fadan- hidiman ta yi yawa suda suke
asibiti amma kaya kamar da a bude shago Abban Anas ya yi
dariya yace ba komai ai yiwa kaine basu jima ba suka tafi gida
tare da fatan samun Lafiya wa Amrah.
****
A bakin get na gidansu Maheer ya sauketa Zahra ta sanya
kafa ta fita daga motar ko ci kan ka bata ce da Maheer ba Shi
ma Maheer bai ce komai da ita ba da ido ya bita har ta bude
get ta shiga gida, Maheer ya yi kwapa zuciyarsa cike da jin
haushinta, hmm lallai wannan yarinyar ba ta san na fita jin kai
ba kawai darajar kaunarta da nake shi yasa nake daga mata
kafa mtswwwweeee yaja karamin tsaki.
A kan Saleem dan iya komai matukar bai sabawa Allah ba
dube ta kan bandan yayanta take fushi wani mummuna da shi
lolz ya fada yana tabe baki, mune da nasara in shaa Allah ya
fada a zuciyarsa sosai yake kaunar Amrah da Saleem in bai
manta ba ko ranar farko daya fara ganin Amrah gidansu
Saleem ya masa sha'awar auren ta sai dai lokacin Saleem din
bai ankare ba.
Saleem ya masa gata sosai a rayuwa wanda badai taba
mantawa ba, still ya daukeshi aboki kuma amini ba tare daya
duba bambamcin matsayin sa a gun aiki ba uwa uba bai nuna
132
AKWAI KURA 2
masa kudin ubanshi yafi abotar su ba, muje duwa Madam
nasan daki dawo hanya ya fada tare da juya mota ya bar kofar gidan.
Da sallama ta shigo dakin nashi sai dai Anas yana
masallaci bai dawo ba hakan yasa ta juya baya ta koma shashin Mamah tare da mata sannu hadi da fada mata ta dawo Mamah
take tambayarta jikin bestyn nata Zahra tace da sauki Mamah
barin je in yi sallah Mamah tace yi mada dan kina gab da
makara.
Zuciyarta cike da jin haushin Amrah tare da -Maheer daya
nuna mata abokinsa yafi dan uwanta, a wani bangare tana
mamakin yadda Saleem-bai da-kunya yake nunawa Amrah
kauna a gaban kowa, sosai abun ya bata sha'awa ina ma ita ce
Maheer ke mata hakan dan ita macece mai son a nuna ana
sonta a gaban kowa cike da wannan tunanin ta isa dakin nata
kaya ta cire a gurguje ta yi wanka ta dauro alwala da sauri ta
fara sallah saboda taji ana kiran sallar isha"i
****
Ta fada tana Juya kai-alamar haushi musamman data tuno
kan maganar Maheer ya yi fushi, Anas ya sassauta murya
kwantar da hankalin ki sis matsalar data do da sauki cikin
Rarrashi ya sanar da ita yadda suka yi da-granny.
Zahra taji dadi har ta dan sassauta fuska a hankali ta gyara
dama, yaya me dai hana ka daga hankali a dawo da bikin baya
ta wannan hanyar Saleem dai rabu da ita dan in ta damo
mallakin ka kana dai dai da kayi gadara da matarka kai kadai
in ko ya nuna dai mana wauta muna da ikon kai shi ga hukuma.
****
Yau Monday inda ya yi dai dai da kwanan Amrah 12 a
asibiti, yau ne kuma doctor Murja ta basu sallama Sakamakon
lafiya ta samu ga Amrah sai dan abinda ba da'a rasa ba Cikin
133
AKWAI KURA 2
wadannan kwanakin kullum Saleem da family nashi suna
hanyar asibiti wajenta harta Dad na shi sai da yado sau biyu ya
duba Amrah Mom kuwa tado dubiya yafi a kirga haka kullum
sai an kawo abinci asibiti daga gidan su Saleem Granny ta yi
bulbul ta kara haske saboda kayan alatu da ta kwasa a asibiti.
Tun da Amrah tado asibitin kama daga kudin jinya komai
Saleem ne ya ke biya, Ummy da kanta ta tambaya doctor na
wane charges din su bayan an sallami Amrah sai doctor tace ai
Saleem tuni ya biya, Jiki a mace Ummy ta dawo dakin saboda
dawainiyar da Saleem ya yi dasu ta yi yawa musamman da ta
san an bada Amrah ga Anas.
Itakanta Ummy duciyarta tana-son Saleem ban da Anas
yana tsakani da da kanta data baiwa diyar nata shawarar ta auri
Saleem ko dan kaunar da mahaifiyarsa take mata sai dai kash
ya damo dole su bai wa Saleem hakuri dan kar su zamo
kananun mutane.
Dakin Cike yake da yan dubiya wanda su ka do rakiyar
Amrah gida, Cikinsu harda Anty Meerah da-Zahra, Anty
Meerah ce-ta mikawa-Amrah leda tace-ungo Maman Affan
shiga bandaki ki sanya wannan er kyauta ce daga danki Affan
na murnar samun lafiyarki.
Amrah ta karba cikin murna tare da Kara rungume Affan
dake kusa da ita tnz so much swthrt, tajawo fuskar shi cikin
dariya ta masa kiss a kumatu Affan ya fara kyalkyala dariya
Mamah nima dan miki Aiko tuni yan dakin suka fashe da
dariya ya yin da Saleem ya ji wani yarr a jikinsa tuni bananarsa
ta mike ji yake dadin har kwanyansa kamar mashi Amrah tai
wa kiss, Amrah tana dariya ta sunkuya tare da mikawa Affan
kumatu aiko Affan ya kaiwa kumatun kiss yana tsallen murna
Ummy tana dariya take kallonsu cike da sha'awar yadda yaron
yake kaunar jinin ta, Zahra Tana kalllonsu sai dai ba tace
134
AKWAI KURA 2
komai ba ko dariyar da ake ta yi ba ta yi ba cikin kosawa tace
Besty yi sauri mana wuce ko daman asibitin bai ishe ki ba ne ?
Amrah ta dauki ledar kayan tare da furta sorry bestyna
bari in yi sauri, cikin nutsuwa tado ta wuce gaban Saleem ta
shiga bandaki dan canza kaya.
Amrah ta bude ledar kaya ne masu kyau masu tsada
doguwar riga sai pant Milk Colour sabo dal da skt da bra duk
sababbi a cikin ledar rigar da alama haka ake sai da shi ready
made, Sosai ta yi kyau cikin Dogon rigar yar dubai Milk
Colour kamar a jikinta aka dinka ko ina ya zauna cip - cop
nonuwanta sunyi cip a cikin rigar kamar an auna kasancewar ta
fara tass so sai kalar tai mata kyau sosaj Babban dankwalin ta
bude ta yafa wow ta fada ita kanta ba karamin kyau ta yiwa
kan taba.
Amtah ta dauki kayan data cire ta mai da cikin ledar sabon
kayan a hankali ta bude kofar bandakin ta fito, Ma shaa Allah
Shine