Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 10
safe gidan Iya ya/fara cika da Yan uwan Iya, itama Ummyn Amrah da wuri tazo gidan Iyan saboda aikin taryan bakin, Girki sosai suka shiryawa baki tare da abun sha kala kala, da-misalin karfe- 4pm dai dai iyayen Anas suka iso gidan Iya, Abban-Amlah-da Baba Auwalu Wanda yake Dan uwa, makusanci sosai ga a marigayi Mijin Iya, sai Yayan Baba Auwalu guda biyu Sani Da Nasiru Sune suka karbi bakin, Suma bangaren Anas Maza ne dattijai biyu sai Samari biyu, bayan gaishe gaishe tsakanin su daga bi sani, mata suka fito da abinci Kala kala tare da kayan sha daga cikin Gidan Iya, Bismillah Abban Amlah yace dasu tare da dan basu guri domin suci abinci, Amma sai daya daga cikin dattijan yace Ah ah ai tare daku za muci, Abban Amlah yace wannan na kune namu yana cikin gida zamu je mu taras, Amma sai Dattijan nan ya tubure har saida Su Abban Amlah suka hadu tare da su suka ci Abincin tare da hira a tsakaninsu, Sosai suke hirar kamar sun san juna, gabadayan su Bangare biyun kowa ya ji dadin yadda lyayen suka kasance masu mutumci, Musamman Iyayen 33 AKWAI KURA 2 Anas sun yi na'am da tarbar karamcin da aka yi musu sosai suke Taya Anas murnar samun surukai nagari, ba tare da bata lokaci ba suka gabatar da kudurin su na nema wa Anas dansu Neman Auren Amrah. Baba Auwalu yace A matsayinsa na waliyin Amrah, ya bawa Anas auren Yarsu Amrah, Ma shaa Allah gabadayansu suka fada tare da godiya, Daya daga cikin dattijan yace Nawa kuka yanke wa yar ku sadaki? Kuma mu naso in har babu damuwa a sanya mana auren anan kusa dan yaron yana bukatar abun da wuri Abban Amlah yace Ba komai bazai gagara ba Allah yasa abokiyar zaman sa ce, Alhaji Auwalu Bismillah Sai abinda kace, Baba Auwalu ya yi dariya tare da shafa gemun shi Da alaman ustaz ne, yace na yankewa Anas sadaki Naira 50,000 kacal, domin Anmabi s.a.w. yace mafi karancin sadaki an fi samun-albarkar aure a cikinsa. Sosai Iyayen- Anas suka ji dadin Maganar-Baba-Auwalu a take suka bada sadaki Naira Dubu Hamsin tare da kudin gaisuwa shima dubu hamsin, sai katan - katan na minti dana alawa sai huhun goro manya guda 5, Cikin mutunci da dattako aka gama komai na Karban sadakin take Baba Auwalu yace ya sanya rana wata 5 chif, lokacin ita Amrah tagama skl Sosai Bakin suka yi farin ciki Tare da sanya albarka wa auren cikin jindadi suka yi sallama da junansu, har jikin Mota Abban Amlah da Baba Auwalu suka rakasu suna musu godiya har sai da suka ga tashin su a mota. 34 AKWAI KURA 2 tafiyar bakin keda wuya Baba Auwalu, suka shigo cikin gidan Iya, Dakin Iya suka yada zango Iya ta hakimce akan kujera ta sha kwalliya kamar yaune bikin na Amrah, Dakin Matane da yawa yan uwanta na kusa, Sai Ummyn Amrah dake daune kan Sallaya ta idar Da sallar la'asar, da sallama suka shigo dakin Iya, Aiko Iya tana ganin su ta hau washe baki tare da fadin An gama, komai Auwalu ? Baba Auwalu yace sosai Iya ga sadaki an karóa, kuma mun tsaida rana aure nan da watan Babar Sallah in shaa Allah, Iya ta kama hanci ta yi guda "Ayyiriri! Zainabuna Lokaci yazo kaiii Allah yai muku Albarka, Allah ya kara zumunchi sannun ku da kokari. **** Zahra tana kwance a dakinta, ta kasa bacci sai juyi take akan gado, zuciyarta cike da-farin ciki, gama wayarta kenan da Maheer din ta, ba dan sun gaji ba sai dan dare ya yi akalla karfe 12 na dare, sun sha lobe sosai ta waya ita da bbynta Maheer, gabadayan su ita da shi kowa murna yake kasancewanr Iyayensu sun yarda suyi aure. Uwa uba tana da labarin jiya an kai sadakin dan uwanta Anas, wa babbar Aminiyarta na rai da rai Amrah, tun jiyan take kiran Bestyn nata a waya dan su taya junansu murna, Amma wayar a kashe, saboda ita ma cikin satin nata sadakin na zuwa daga gidansu masoyinnata Maheer. Sai dai yau kwana biyu kenan take kiran wayan Wayar Amrah shiru karshe ta kira Mommy, sai Mommyn tace da ita Amrah ta wuce gurin aiki. Sako ta turawa Bestyn nata kan cewa tana kewarta musamman da suka kwana 6 basu ji muryar juna a waya ba please in ta kunna wayar ta kirata 35 AKWAI KURA 2 akwai labari tare da mata shakiyanci amaryan yayana Kin sha kamshi. WhatsApp ta bude ta yi making hotunansu da Amrah Masy yawa, wanda kowanne Amrah ta sha kyau sosai, akalla sun kai kala 15, cikin su har da wanda Amrah ta dauka sanye da babyn nata Maheer Abaya kanta babu dan kwali gashin kanta ya zubo, har gadon bayanta a jikin photon ta yi kyau sosai kamar diyar larabawa, rubutu Zahrah ta yi a kasan photon, Amaryan Big bro kin sha kamshi, ko madara bai kai ki fari ba lolz. Bai fi minti uku da sanya photon ba Frnds na Zahrah da yawa suka fara comment akan photon na Amrah, wow -beautiful, Fantastic, Wow Hurul en, Sune ire iren da mafi yawan abokan na Zahra suke fada wajen comment, daya bayan daya Zahran ta rubuta musu tnz. Maheer dake kwance kan gado yana Tunanin- Zahra da sauri ya rubuta mata sako Babyna Mu hadu a whatsapp.na kasa bacci, Tare da kunna datan shi abun mamaki Zahra din tana online, sabbin status ya gani Zahra tasa da sauri ya fara budewa, a tunanin shi na Zahran ne. Dasauri ya yi zooming photon yana kare mata kallo, Ko tantama babu wannan gashin irin shi ne ya gani a bayanta ranar da ta cece su shida Abokinshi, Daya bayan daya-yake kallon photon yana zooming, Tabbas fuskan nan ya santa sai dai a inah ???. **** Yau laraba satin ta guda cur a gidan Ahmad, duk da Wannan gida Ahmad ya saye shi ne saboda ta'addancin sa, ya kan fita yaje harkar sa ya dawo sau da yawa ba kodayaushe yake kwanan gidan ba ya kan tafi can gidansu ya kwana saboda 36 AKWAI KURA 2 babu wanda ya san wannan gidan daya saya cikin abokan aikinshi bare yan uwan sa. Ahmad ya sanya tsaro sosai a gidan, ko ta ina Yan ta'adda ne, masu gadin gidan yan jiran ko ta kwana, ba kowa ne yasan wannan gidan ba sai Abokan harkallar shi a cikin kwanakin da ta yi a gidan ta yi mamaki sosai, da ganin manyan mutanan da suke zuwa gurin ahmad kan harkar hodar iblis wanda mutane, ne masu mutumci a idon Jama'a, Ahmad duk wani abokin harkan shi da zai zo sai ya gabatar da Amrah a matsayin Gwana a cikin harkar ya yin da da yawan abokan harkar shi suka mata maganar bata aiki in ta gama da aikin Ahmad, hakan ba karamin dadi ya yiwa Amrah ba, a kasan zuciyarta sam babu dana sanin sace ta da Ahmad ya yi saboda duk wani sirrin da yakamata ta rike kan hujja a gidan Ahmd ta same su, wannan lokacin Amrah ta gano Saleem bayi da laifi ko kadan illa-ma neman-ran sa-da mahassada suke yi, A karan farko kenan Da Amrah, ta fara jin tausayin Saleem, Sosai Saleem yake bata tausayi, Amrah ta kan bata lokaci wajen tunanin Saleem, A duniya bata taba ganin dan adam daya tara makiya irin Saleem ba, Gareta yanzu babu burbudin kiyayyar Saleem a ranta sai dai ma Jinjina da take masa kan gaskiya da rikon Amanar shi. Ido ta runtse tana tuno kyakkyawar surar shi, Amrah ta rufe ido kamar yana kallon ta A hankali ta furta Handsome guy i lyk ur...Da sauri ta bude idonta ganin Ahmad ta yi tsaye akanta yana murmushi, Ahmad yace yes my baby I knw ni din kyakykyawa ne sai dai Ban tabbatar da hakan ba sai da naji a bakin Babyna, sai dai babyna ke din first class ce wajen kyau nasan kin dara ni a kyau nesa ba kusa ba, Amrah 37 AKWAI KURA 2 ta langwabe kai tana kallonshi tare da cewa really? Ahmd yace 6ery sure my baby. Wuri ya samu ya dauna dan nesa da ita Yana murmushi baby na yaushe za aban kayan dadi ? Rass gaban Amrah ya fadi, cikin jarumta ta daure Soon dear kasan abun bai dauke ba Yes babyna aina sani i knw baki wasa da Sallah kota nan wajen ai zan gane, Amrah ta yi fari da ido Saura 3days. Ahmad ya kada kai kice in na aure ki dan sha wuya har 9days ?? Amrah ta tabe baki tana Yamutsa fuska dan hirar ta isheta, Baby barin dan runtsa kaina ciwo, ok babyna ki kwanta ki huta barin watsa ruwa, Amrah ta rufe ido alaman bacci Ahmad ya bude bandaki ya shiga. A hankali Amrah ta bude ido taja karamin tsaki, dan mahaukaciya, jaki, dakiki, Baka san burina In gama hada hujjar da- za'ayi ram dakai ba, kafin in-bar -gidan nan, mtswwweee taja tsaki, zata bar gidan tabbas tasan abu ne mai wuya sai dai ta shiryawa hakan, Ko ana h amaza ha mata dole in bar gidan nan kafin in samu tsarki, hyege dan Iska ta fada tana huchi...... **** MAHEER, yau da wuri ya fito daga gida zuwa office, sauri yake domin yana Allah - Allah, yaje office ya shafawa Saleem labari, kasa hakuri ya yi ya karasa office din, Wayarsa dake gaban Aljihunsa ya ciro. Lambar Saleem ya kira, sai dai har ta gama ringin ba'a dauka ba, bai gajiba ya sake dannawa lambar kira, Saleem dake bacci karar ringing din wayarsa ne ya tashe shi, cikin bacci ya daga wayar tare da jan karamin tsaki, Maheer ganin an daga ya sa ya sanya wayar a loudspeaker, Abokina da 38 AKWAI KURA 2 fatan kana office nima gani a hanya ina zuwa maka da babban labari, Saleem Ya kuma jan tsaki Gaye ina gida fa wallahi banji dadi ba daren jiya, Subhanallah Mahcer ya fada barin zo gidan yanzu tare da juya kan motar shi, ya kama hanyar gidansu Saleem. Cikin minti kadan ya iso Gidan Masu gadi suka wangale masa get kasancewar shi dan gida ne a gidansu Saleem, Tare da mika gaisuwa a gare shi hannu ya dinga daga musu kafin ya nemi wajen parkin ya ajiye motarsa, da sauri ya shiga sashin Saleem Dan cimma abokin na shi, sai dai a hanya suka hadu da mai aikin Saleem Grace tace da shi Oga baya ciki, Waya Maheer ya ciro ya kira Saleem tare da cewa gani a side naka. Saleem kamar ba zai yi magana ba yace kazo Side din Dad, Da sauri Maheer ya juya bangaren Dad-yana-mamakin Lallai jikin Abokin nasa ya yi tsanani tun da har ya bar dakin nashi, Da sallama ya shigo Falon amma babu kowa hakan yasa kai tsaye ya yi dakin Dad ya kwankwasa kofa ya yi Tare da jiran ai masa izinin shiga. Saleem ya daga murya abokina shigo mana, dasauri Maheer ya bude kofar ya shiga, tare da fadin Abokina yaushe jikin naka ya kai hakan? Wallahi nayi mamaki da kace mun wai ba kada lafiya, Saleem ya tabe baki hmmm ! Kai dai bari Beb tana shirin kai ni kabari saboda tsabar kaunarta, Maheer ya yi dariya kace ciwon lobe kake, ayya har na tausaya maka, MAHEER dafa kafadar shi tashi abokina tashi kaga abinda nagani. 39 AKWAI KURA 2 Saleem ya tabe baki kai fa dan iska ne ina fama da cuta kana shirin karamin damuwa, please bar ni in ji da hakurin rashin dream girl dita..... **** Sallamar Mommy shi ya katse musu hirar da suka fara, da sauri Maheer ya durkusa har kasa ya kwashi gaisuwa wajen Mommy Mommy ta amsa fuskarta cike da fara'a, Ah ah Maheer yaushe kazo ? Ai gara da kazo Ko Son zai samu abokin hira na fiso ya ware, Maheer yace Mommy kwantar da Hankalin ki ai nazo da maganinsa, kin ganshi tun dazu nake maganar ya tashi yaga wani Abu Mom yaki wai in bar shi ya huta Mom bara ki gani ya fada tare da danna wayarsa, Gallery ya shiga yana duba photo sai da yazo da-idai kan wanda yake so ya mika mata, Mom Kinga. -INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJIUN! Mom ta fada tana Washe baki wannan ai Amrah ce, da sauri Saleem ya tashi akan gado wayar hannun Mom ya sanya hannu ya kufce tare da kai idanunsa kai dan ganin photon, Saleem ware ido yana Kare mata kallo Abokina wallahi ita ce, Maheer ya yi dariya Tare da matsowa kusa da Saleem Abokina kaje gaba daka ga abinda nayi mamaki, Saleem Ya zare ido tare da fadin na shiga uku ! My dream grl, Yes ! Maheer ya/fada Mom da sauri ita ma ta matso tana kallon Wayar, dariya ta yi tana kallon sa ai Amrah akwai gashi, ni kaina ranar dana fara ganin kan ta nayi mamaki sosai dan ko ni baturiya bani da yawan gashin ta, Maheer ya kalleta Tare da Kallon Saleem abokina in har ita ce to fa lallai itac e Dream grl din ka Wow, 6ery fantastic As how ? Ikon Allah, Mommy tace kuyi min bayani, kun bar ni a duhu Saleem ya 40 AKWAI KURA 2 kalli Mom da shanyeyyun idanunshi Mom Am totally comfused ! MAHEER ya yi dariya Abokina ni kaina jiya kwanan Mamaki nayi Sau daya naganta ranar data ce ce mu Amma tabbas wannan gashin da farin fuskar ita ce na gani ranar da aka ce ce mu, Mom ta zare ido Tare da kallon Saleem Son kuna nufin Amrah itace ranar da ta taimake mu gabadaya ?? SALEEM ya daga kai yana Jin tsananin farin ciki, Mom No wonder nake tsananin kaunarta ashe ita ce ta ce ci rayuwata Wow mum i can't beliebe, she is the one that help us, for that, please mum i want uh to help me nd get her, because i started to feel i can't do without her, i lobе her damn mch mum ! ***** Maheer ya dube shi, abokina Sai dai hanzari ba gudu ba, In har wannan itace Abar kaunarka to fa, *AKWAI KURA.* Domin ita ce wadda Anas bro na babyna zai aura, in fact ma An biya sadaki har rana an saka, shiyasa Dad nasu yace in turo magabatana domin yana son a hada-Aur...Saleem ya shako wuyan rigar Maheer tare da daka masa tsawa dan ubanka matar tawa kake fadin wani banza dai aureta, Daman ashe kai makiyina ne tun fil adal ban sani-ba ?? to wallahi sai na harbe duk wanda ya rabi matata koma waye shi, Ina son Amrah sosai kauna mai-yawa bare yanzu dana ke da tabbacin ita ce dream grl dina sai dai a mutu ko ayi rai Amrah tawa ce Ni kadai, ya fada yana kara shako wuyan Maheer, Maheer kala bai ce ba bai kuma yi yunkurin kwace kwalar rigarsa a hannun Saleem ba, Dake kallon su ganin Saleem yaki sakin wuyan Maheer, cikin bacin rai ta yi wa Saleem Tsawa Son baka da hankali ne? abokin naka kake kokarin duka Sakar masa wuyan riga tun kafin in saba maka, 41 AKWAI KURA 2 Sai da Saleem ya yi nisa da alama baya cikin hayyacin sa, yaki sakin Wuyan rigar Maheer da sauri Mommy ta fara kokarin kwatar Kwalan Mahcer a hannun Saleem. Ya yin da Maheer ya kasa magana sai bin Abokin nasa yake da kallon tausayi, ko kadan Maheer bai ji Haushin Saleem ba sai ma tausayin sa daya cika zuciyarsa, SALEEM ya saki wuyan Maheer tare da fashewa da kuka mai karfi, Mom Wht is wrong wt mie am die 4 her. **** Da sauri Maheer yava karasa gaban Saleem, tare da rungumeshi a jikinsa, Abokina ba lafiya gareka ba please ka daina kuka mu bi abin a hankali, Saleem ya fusge a jikin Maheer yana Nuna shi da yatsa ba za'ayi hakurin ba dake kai ka samu taka abar kaunar ba, ai dole kace in bi a hankali to bazan bi a hankali ba akan matar tawa kake-fadan haka to da karfi dan bi wallahi tallahi koma waye shi sai ya bar mun matata, domin Amrah rayuwata ce in babu ita babu ni, Mom dauko mayafi muje gidan su Mom Akwai kudi a dakina ki bude durowata ki dauko sadaki, yau ba dan dawo gidan nan ba sai an bani Matata. Gabadaya Maheer da mom suka yi dariya Jin sumbatun Saleem, Mom ta share hawayen tausayin dan nata Tare da kamashi ta rungume a jikinta Son kayi hakuri Magabatanka, su kai maka sadakin Amma ai mace bata kai sadaki, Saleem ya langwabe a jikin Mom, tare dacewa No Mom ga abokina namiji ne ya isa shaida please Mom muje kar lokaci ya kure kinji ana maganar wani banda yana zuwa wajen matata, Please Mom kinsan badan jure ganinsu tare ba kawai muje a daura auren a bani matata, Mom tashiga lallashin Saleem 42 AKWAI KURA 2 tare da fadin Son ai dole sai mun nemi yardar Amrah ko ? Tun da ai bata san kana yi ba, ya zamo dole ka fara neman soyayarta kafin maganar manya, dan haka Maheer ka sanya ya yi wanka ya shirya sai kuje ku fara ganin ita Amrah in ta amince sai a sanya manya ciki, Maheer yace haka ne Mom Abokina Shirya mu wuce office daga nan sai in kira babyna ta bamu address din gidansu dream girl din taka koya? Saleem ya daka masa harara ai sai ka kai ni gurin aikin dan ubanka, Mom pld shirya muje tare ya fada yana langwabe kai, kinga Mom tana jin maganarki na san data amince, Mom ta harareshi Ah ah maganar soyayya babu alfarma Son, sai dai barin shirya muje saboda ina kewar Daughterna. **** Fitar Mom keda wuya Saleem-ya takurawa Maheer-ya kira Zahra dan ta basu address din gidansu Amrah kafin ya yi wanka, Maheer yana-dariya tare-da tsokananr Saleem Uhum -Uhum su ba sa bun ba an fada soyayya haha kai soyayya bata da hankali, Soyayya-mai sanya babba-kuka, Saleem ya Galla masa harara kaga zaka kira ta ko sai na ci mutuncin ka, Maheer ya masa gwalo tare da danna kiran Lambar wayar Zahra. A handsfree, ya sanya wayar yadda Saleem-zai ji komai, ringin biyu Zahra ta daga wayar, Cikin yanga kamar Maheer na kallon ta ta Amsa wayar, Hy Abokin rayuwata, ka tashi lafiya? Bata jira Amsar da zai bata ba ta ci gaba da magana babynah ! Kamar kasan yanzu nake rubuta maka Morning text. Maheer ya amsa Ayya abokiyar rayuwa ta kece always a rai na hakan yasa na kiraki lokacin da kike cikin tunani na, nida ke din Abu daya ne soyayya ta sanya mun fara tunani daya, 43 AKWAI KURA 2 Maheer ya kalli Saleem ya kanne ido daya, I lobe yhu so much babyna ya fada yana lumshe ido. Saleem da Ransa ya fara bacci ganin Maheer ya manta da shi a wurin, sai waya yake yana masa tsiya, Duka ya kaiwa Maheer dan iska bani da lokacin wannan karamar soyayyar taku bani wayar in tambaye ta labarin Abar kaunata, tun da kai iskanci ya hanaka tambaya, Maheer ya yi dariya tare da kara matse wayar a kunnensa, ah ah ban yarda kaji min muryar mata da sassafe ba, kuma sau nawa ina ce maka gata ku gaisa amma baka taba karba ba sai yau saboda taka bukatar. Zahra dake jin duk abin da suke yi ta waya ta yi dariya Babyna, kar dai Yau Babban Abokin mu ne ke son magana da ni ? Maheer ya yi dariya tare da nutsuwa sosai, Babyna Bestyn mu tana nan kuwa ? Zahra tace da shi wallahi babyna tun ranar da muka dawo shopping har yau bamu hadu ba, Maheer yace gaskiya bamu da kirki pld gani nan zuwa ki shirya zanzo ki kaimu. nida abokina Zahra, tace Aikuwa ina kewanta gashi bana samun wayarta barin yi sauri in shirya kafin kuzo. Tabar ya zuka, tare da busar da hayakin ta sama *MAIGIDA* daga majiya mai karfi Yarinyar nan Ahmad *FIYA FIYA* takewa aiki Goje, yace da ni ya ganta jiya a gidan Ahmad din dan hakan Maigida ina ganin tazo gidan sauki Tun da duk tafiyar iri daya ce ko ya kace MAIGIDA ?? ya fada yana busa hayakin sigari. Alhajin ya mike tsaye tare da zaga falon Hakan meke nufi Kenan? wato Ibrahim ya cu ce ni kenan ya karbi kudina kan 44 AKWAI KURA 2 labarin karya, kaiiii inaaa ba zai yiwu ba Maigida to magana ta tabbata karyar ya yi dan ya samu rabonsa. Domin in har yarinyar hukuma ce suka turo ta, lallai ba zamu ganta a cikin harkokin mu ba bare har mu ganta dumu dumu a cikinmu, kuma Goje ya sanar da ni har barasа yarinyar take sha domin jiya a gabansa tasha Goje ya sanar da ni gari yar hatsabibiyace ta karshe Maigida kaga haka ya tabbatar yar hannu ce ko ya ka gani Maigida ?? Kiramin Goje ya fada yana hura hanci angama Maigida, Wayar Goje ya kira tare da sanyawa a kunne a daya bangaren Goje ya dauki waya tare da fadin sai Mushe Uban Shaidanu yaya ake cikine? Wanda aka kira da mushe ya yi dariyar manyan Arna Maigida ne yake son magana da kai, ta mikawa da mikawa Alhajin wayar.- "Allah ya taimaki Maigida" Goje ya fada tare da cigaba da masa kirari irin nasu na-yan iska, ka hada ni confrence call da Ahmad yanzu wani abu nake son tabbtarwa inna samu amsa mai kyau kana da kyautar dubu 100,000 Hahhahhhhh Goje ya yi dariya sai Maigida an gama baka da case yanzu yanzu ma kuwa, Goje ya danna wayar dan kiran Ahmad, ringin biyu Ahmad Ya daga Wayar. **** A hankali ta sai ta nutsuwar ta bayan ta gama, kare masa kallo ta mirrow, kai ta jinjina tana yaba kyau da Aliah ya bashi a ranta take fadin duk matar data aureshi ta more, cikin nutsuwa tace Ina kwana ba tare da ta kama suna ba Maheer ya amsa lafiya klau. 45 AKWAI KURA 2 Zahra ta harare shi ta cikin Mirrow ta turo baki tace waya ce da kai nake ? Maheer ya yi murmushi ohh ! Abokina ashe fa da kai ake, Saleem ya amsa lafiya ba tare da ya juyo ba. Maheer ya kalle ta Beb naji dazu kin ce Bata gidan granny, Yes Zahra tace ta bashi amsa da tana gidan Ummy, Ok Ya fada tare da daukar hanyar Gidan Ummy, a hanya sosai Mum ke jan Zahra da hira sai dai Zahra a cikin kunya take amsa wa tare da jin nauyin Mommy. Tafiyar minti 23 ce ta kawo su bakin get din gidan Ummy, da sauri Saleem ya kalli Maheer Meye hakan wai sai ka bata min rai ne kafin ka kai ni gareta mtswwwweeee yaja tsaki, Na kusa in ci ubanka wallahi dan iska kawai Maheer ya yi murmushi mai da wukar abokina nan shine gidan. Da sauri Mom ta kalli Maheer Amrahtu na fa mai aikin Saleem, Maheer ya kalli Mom yes Mom nan shi ne gidan Mahaifiyarta sai dai akwai gidan kakan ta da suke tare a Mando* Ikon Allah Mom tace, tana jinjina kai Son kaga Abun mamaki ko ?? Saleem ya lumshe ido Mom am eager to c her. Horn Maheer ya yi da sauri mai gadi ya zuge musu get ya futo, jikin motar mai gadi ya kara so tare da dan leka kai gaban motar, Cikin sauri ya mika musu gaisuwa tare da raba ido ko ya san su sai dai bai gane kowa a cikin su ba. Ganin hakan yasa Zahra ta sanya baki ta gaishe shi mai gadi, bayan motar ya leka in da ake gaishe shi da sauri ya fara dariya tare da cewa ah ah Fatima Zahra ke ce tafe Zahra tace eeh nice Baba mai gadi, maza ku wuce ai naga motar bakuwace dan bantaóa ganinta a wajen bakin hajiya ko Alhaji ba. 46 AKWAI KURA 2 Da sauri ya koma jikin get tare da wangale musu kofar get din, hancin Motar Mahcer yasa tare da shiga cikin get din ya yi parking din motar a Parking Space din gidan, Tare suka fito gabadayansu Mom, tace ku jira mu anan daughter muje ciki **** sai ki musu iso in masu gidan sun ba mu izini. Tabar ya zuka, tare da busar da hayakin ta sama *MAIGIDA* daga majiya mai karfi Yarinyar nan Ahmad *FIYA FIYA* takewa aiki Goje, yace da ni ya ganta jiya a gidan Ahmad din dan hakan Maigida ina ganin tazo gidan sauki Tun da duk tafiyar iri daya ce ko ya kace MAIGIDA ?? ya fada yana busa hayakin sigari. Alhajin ya mike tsaye tare da zaga falon Hakan meke nufi Kenan? wato Ibrahim ya cu ce ni kenan ya karbi kudina kan labarin karya, kaiiii inaaa ba zai yiwu ba Maigida to magana ta tabbata karyar ya-yi dan ya samu rabonsa. Domin in har-yarinyar hukuma ce suka turo ta, lallai ba zamu ganta a cikin harkokin mu ba bare har mu ganta dumu dumu a cikinmu, kuma Goje ya sanar da ni har barasa yarinyar take sha domin jiya a gabansa tasha Goje ya sanar da ni gari yar hatsabibiyace ta karshe Maigida kaga haka ya tabbatar yar hannu ce ko ya ka gani Maigida? Kiramin Goje ya fada yana hura hanci angama Maigida, Wayar Goje ya kira tare da sanyawa a kunne a daya bangaren Goje ya dauki waya tare da fadin sai Mushe Uban Shaidanu yaya ake cikine? Wanda aka kira da mushe ya yi dariyar manyan Arna Maigida ne yake son magana da kai, ta mikawa da mikawa Alhajin wayar. 47 AKWAI KURA 2 "Allah ya taimaki Maigida " Goje ya fada tare da cigaba da masa kırari irin nasu na yan iska, ka hada ni confrence call da Ahmad yanzu wani abu nake son tabbtarwa inna samu amsa mai kyau kana da kyautar dubu 100,000 Hahhahhhhh Goje ya yi dariya sai Maigida an gama baka da case yanzu yanzu ma kuwa, Goje ya danna wayar dan kiran Ahmad, ringin biyu Ahmad Ya daga Wayar. **** "Ka jima ka yi karko Oga Allah ya tsone idon Makiyanka, ba zaka fadi ba sai a gadon baccin ka, Goje ya fada yana karka da hannu kamar Ahmad din yana kallonsa, a daya bangaren Ahmad yace an amsa gaisuwarka Goje Meke tafe da kai? Dan alamu sun nuna bakin ka akwai magana. Goje yace kwarai kuwa Oga Maigida *DAN CHANJI* ne yake son magana da kai, Ahmad ya gyara wayar zuwa daya kunnen nasa saboda jindadin maganar da ya ji tare da sake tambaya Goje kace me ? sa ke maimaita masa

Chapter 3 of 10