Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 10
sam ta ki yadda da hakan bata wuce ya rungumeta sai kiss daya ke kai wa bakinta kuma shima sau 17 AKWAI KURA 2 daya farkon zuwan ta gidan ta yarda ya mata kiss baki da baki shima Ahmad din ya shammace ta ne. Ita da shi sun zamo, aminai su kwana daki daya su tashi tare tun zuwan al'adarta ta samu salama game da son taba jikinta dan shi din yana da kyaman mace sosai lokacin da take al'ada, hakan ya sanya ita kanta Amrah ta samu nutsuwa dan babu abunda ta tsana irin Ahmad ya taba ta, tun washegarin zuwan ta ita ke musu girki shi da yaran nashi duk wani hidiman gidan ita take yi su kansu yaranshi suna jin dadin kwasan girkinta tu ni suma sun zamo na hannun damanta cikin dabara Amrah keshan cikin yaran tana sanin abinda take nema a wajensu, musamman in sun sha kwaya sun bugu haba tiryan tiryan suke mata bayani cikin maye. Da misalin Karfe 4pm Gabadayansu zaune suke a falo Ahmad da yaran suna ta shan Hayaki ya yin da suke hira suke kyakyata dariya Amrah ita ma da tuni ta koyi irin maganarsu na yan tasha ta yi babban dariya tare da furta Oga Babyna, Meye next plan din mu ne akan Saleem ?? Ahmad ya kalleta babyna Saleem na gab da shiga hadari, domin Laifin da yake shirin kamani da shi shi ne kaikayi zai koma kan mashekiya, Domin Yanzu hakan muna da labarin hukumar DSS dakanta tana tuhumar Saleem da laifin Shigo da hodar iblis, Saleem ya shigewa mutane da yawa hanci da kudundune bani kadai nake neman daukar fansa ba Daga majiya mai karfi Akwai wanda hukuman bincike na fasa kauri ta yi ram da shi ganin Saleem shine sila na kama kayan 18 AKWAI KURA 2 sa wannan dalilin yasa ya sanar da hukumar cewa Saleem ne Mai gidansa ba kowa bane face Alhaji Musa dan chanji, ko kina nufin kice min baki saniba? Amrah ta yi fari da ido kamar gaske ta sani ta yi ta mike tana taku a hankali kamar dawisu aini nan dakake gani babu sirrin daban sani ba ciki har da naka Shiyasa ka godewa Allah dana zamo taka billahillazi da munjima da gamawa da kai ni da Maigida dan chanji. *** Ina kika samu wannan labarin, ya fada cike da tsoro tare da kokarin rike hannunta, Amrah ta-fisge hannunta tana kare masa kallo, a bagaren Ahmad yau babu Maganar kyamarta a gareshi, sai tsananin tashin hankali daya nuna a fuskar shi, Amrah ta kalle shi ta yi babban dariya, Oga duk sirrinka a tafin hannunmu yake ni da Oga na. da Sauran yaranshi koda ka gama da ni, tofa ka kashe-macijine amma baka sare kansa ba. Amrah ta Kuma kallonsa,- kana-mamaki-ne-ko-tsoro,- No, ai tsoro bai dace da hatsabibi irin ka ba, ko ni da nake, mace babu maganar tsoro a tsari na saboda duk wanda ya-sai rariya ya san zata zubar da ruwa, in ko haka ne Babu maganar tsoro, cikin duk wata harka ta dabanci musamman irin tamu mai dauke da hatsari, Ta fada tare da-juyi tana girgiza jikinta. Ahmad ya busar da iska mai zafi daga bakinsa tare da mata kallo mai cike da ma'ana da yawa, tabbas yau ya kara aminta da ita musamman da ya hango hatsabibanci a kwayar idanunta uwa uba da alama dukkan sirrinshi a tafin hannun 19 AKWAI KURA 2 ta suke ita da ogan ta, ta kalleshi da gefen ido ganin yadda Ahmad ya shiga firgici, cikin tafa hannu ta karaso gareshi, hannu tasa ta zaunar da shi, kan kujera tare da furta masa baka da case Oga, tun da kana da ni, ni ba ni da Oga kudi sune Oga na duk wanda ya bani su, a farashi mai tsoka t ofa shi ne ubangidana dan haka ka kwantar da hankalinka babu mai ganin bayanka Matukar zaka bani hadin kai akan duk kan umarni da hanina. ***** Sosai Anas ya takurawa iyayen sa kan maganar Son Auren Amrah, Anas ya damu sosai kwana biyu musamman daya rasa ta a waya wannan dalilin ya sanya ya kara uzzurawa kan lallai akai sadaki gidansu Amrah, dan Yana kirge da Da kwanakin da Amrah ya rage mata Ta kammala school gabadaya, Mama Ganin damuwar dan nata ya sanya ta yi Na'am da kudurin sa tare da lallaba Mahaifin nasa kan maganar lallai ya dace akai sadakin, Ba tare da bata lokaci ba Aka fara shirin kai kudin gaisuwa gidansu Amrah tare da maganar sadaki, kamar yadda Angon ya dage, Ganin Ita ma Zahra ta samu mai sonta da gaske Abban nasu a boye ya yi bincike kan Halin Maheer din kamar yadda addini ya koyar damu ayi kafin Tabbatar da maganar aure, Alhamdulillah Maheer ya samu shaida mai kyau, a gurin wanda Abban ya wakilta, ba tare da bata lokaci ba wannan yasa Mahaifin nasu yace Yana bukatar ganin Maheer, Maheer bai yi kasa a guiwa ba ya amsa kiran na Abba, Bayan sunyi gaisuwa Abban ya bashi damar turo magabatansa, tare da masa bayanin, yana son a tsaida rana dai dai dana dan uwanta jin maganar Abba ba karamin dadi ya lullube Maheer ba, tuni ya washe 20 baki yana fara'a ya AKWAI KURA 2 manta ma a gaban Abba yake cikin doki ya kira Mahaifinshi yana masa Albishir an bashi mata, Abba ya yi gyaran murya tare da jindadi yadda Maheer ya nuna farinciki kan auren diyarsa, Mahcer ya yi godiya sosai wa Abba kan karamcin da ya yi masa Maheer cike da farin ciki ya bar gidansu Zahra ko jira ganin Zahran na shi bai yi ba ya bar gidan cike da daukin Auren na sa tare da Babyn tasa. **** Abban Amlah sam hankalin sa baya kwance na rashin sanin inda Amrah take duk hanyar da zai bi wajen ganin ya samo ta kafin Mutane su farga ya yi shi da yaransa na wajen aiki, sai dai shiru kake ji har yanzu babu kwakkwaran labari kan Amrah, Abun mamaki shiru kake ji Babu labarin na Amrah, Numbern ta da ta turo masa sako tuni sun yi tracking Sai dai inda Hashashen ya kaisu Sun yi binciken duniyar nan babu Amrah a yankin daga karshe ma har suka cimma inda wayar take yashe a cikin wata tsohor rijiya. Ummy a halin yanzu ta yi fushi sosai da diyar tata Ji take in har Amrah ta dawo lallai ne zata canza salo wajen koyar da diyar ta ta Tsoronta dan ta yi imanin akwai sakacin ta cikin raini da Amrah ta yi mata, Tabbas Maraicin Amrah shi ke sanyawa take daga mata kafa sai dai ita Amrah bata ga hakan ba. Ummy ta ci alwashin sake sabon tarbiya wa duyarta dan baza ta yarda da wannan debewar albarkan ba, Ace diya mace tabar gida tsawon kwana 6 Babu sanin kowa cikin magabatanta ai wannan lałacewa ce mai girma. 21 AKWAI KURA 2 Cikin wannan halin, iyaycn Anas suka zo kan maganar Auren Amrah da Anas...... **** Da hantsi Granny tana zaune kan tabarma kofar dakinta, tana shan hantsi kasancewar lokaci ne na sanyi, Mama ta yi sallama a gidan granny ta washe baki tana marhaban da Hajiya Fatima, kece a tafe da hantsin nan, Mama ce Ech Wallahi Iya ni ce ta fada tana shigowa cikin gidan, itama tana barka wa Granny da gida. Kokarin zama Maman take kan tabarmar da Granny ke zaune, tace a'a Hajiya fatima mu shiga daga ciki, Mama tace Iya nan ma, ai ya isa bar ni ni ma in sha hantsin ai garin akwai sanyi GRANNY ta koma mazauninta ta zauna tana mata sannu da hanya, bayan yan gaishe gaishe Mama tasanar da granny in sha Allah gobe Iyayen Anas maza za su kawo kudin gaisuwar Amrah har ma da sadaki. Ayiririhhhhh ! Granny ta-fada tare da, kama hanci tuni fuskarta ya-kara washewa Da tsananin farin ciki, murna sosai granny ta yi-har sai da ta yi kukan Farin ciki, Mama tana rarrashinta, granny tace bar ni in yi hajiya Fatima Lokaci ne Allah ya nufa zan gani banni inyi kukan farin ciki, yau Jikata Gudan jinin Amaduna, Hasken idanuwana Zainabu na itace ake maganar Aurar da ita. ai dole inyi kukan dadi, granny taci gaba da fyace majina tana jan hanci Sai da ta yi mai isar ta kafin ta yi shiru, Mama ita ma cikin murna tare Tambayar granny ina diyar nata Amrah Granny tace ai yau kwananta 13 gidan uwanta tun da ta dawo asibiti take can, Mama tace ayya Allah yakara sauki in ji ba jinkin 22 AKWAI KURA 2 bane har yanzu ke damun taba, Iya tace tawarke ras gulman tane yasa ta gujeni ja'ira ai yau kafata kafarta zan je in dauko ta, gara inji duminta sosai kafin Anas ya dauke mun ita, Mama ta yi dariya aikuwa gara kam Kodayake ai auren tare dake Iya zaku tare, Iya ta kama baki ni Hapsatu raba ni da yaran zamani marasa kunya, Ai in da zamanin mune da tsohuwa ko da yar gaba ake hadaki Amma wannan zamanin yaran sam basu da, kunya in yar ga ban aka basu sun ta muntsine miki ya tare da sanya ta aikin wahala har sai ta gudo gida, in tsohuwar aka kai, rashin kunya sai ya kore ta. hahahahaha mama ta yi dariya tare da mata sallama ta bar gidan. **** Nan da nan granny dauko wayarta alamun da aka sanya, mata a jikin kowace Number ta shiga, yan uwan mijin nata ta fara kira Wanda sukeda alhakin Karban Sadakin na Amrah, ta sanar da su gobe Su hallara kan maganar auren Jikar ta ta, Granny kira sosai ta yi yan uwa na nesa dana kusa duk mai hannu cikin auren Amrah sai da ta sanar daga karshe gyalenta ta yafa ta rufe gida ta kama hanyar gidan Ummyn Amrah. Granny ta sauka akan adaidaita sahu kofar gidan Alhaji Usman, Da sauri mai gadi ya bude mata get, yana dariyar ganin ta saboda mutuniyar sa ce yana shan dariya in tsohuwar tazo, kofar ya bude yana fadi Iya ke ce a tafe, da ranar nan, Iya ta yi dariya yo Isihu ai dole na Banga ta zama ba Shalelena Aure ya tashi, Maigadi ya washe bakinsa yana murna kai ma shaa Allah kice tare da goro na kike tafe Daman yau ban da kwandalan saya, Iya ta kama baki kaji 23 AKWAI KURA 2 makiri da na ni nake kawo maka goron? to yau sai dai kar kaci goron sisi na bazan baka ba ja'iri, Maigadi ya bushe da dariya har yana rike ciki Kai iya aina san ba zaki hanani Goron Auren jikallen kiba dan nima ina taya murna sosai. Ta kama hanyar wucewa cikin, gidan tare da fadin kana da gaskiya Isihu dan haka ka jira naka in sun kawo Amman kwandala bani baka Dan yau kam ban yi niyya ba. Da sallama Iya ta shiga falon tana fadin ina Zainabun Fito kiji abun alkairin da ya same mu Yanzun nan shiyasa na taso dan ba maganar salula bane, yar aikin Ummy ce ta fito daga kichin tare da russunawa ta gaida Iya baki ta washe Iyan ta amsa tare da tambayarta masu gidan, Yar aikin tace Bara in kirata yi sauri ki je Iyan ta fada, da sauri ta haura saman bata jima ba ta sauko ta sanar da Iya tana zuwa, Ummy da Abban Amlah na-zaune-falon-sama Sakon iyan ya riskesu, da sauri suka kalli ju **** Ummy ta ajiye tray a gaban Iya, tare da zama kan Carpet din cup ta dauko-ta. zubawa Iya lemo tare mika mata Iya sannu da hanya Bismillah ruwa, Ummy ta fada tare da matso da filet na dambun nama gaban Iya, Iya ta karbi ruwan lemon ta kurba tana Nagode Zainabu, Ummy ta yi dariya haba Iya ke da gidan danki ai baki bukatar Godiya, Iya tace matso nan kusa da ni Zainabu Ummy ta matso tana dariya. Alhamdulillah Allah ya kawo mu shekara ta kawo mu, Ummy ta yi shiru tana sauraran Iya cikin nutsuwa Iya ta sanar dasu dalilin zuwan nata kan maganar turo magabatan 24 AKWAI KURA 2 Anas gobe, Abban Amlah ya washe-baki Alhamdulillah fuskarsa cike da farin ciki, Ita ko Ummy kai ta sunkuyar zuciyarta cike da farin ciki Alhamdulillah ta fada a ranta Gara ma ai mata auren ko za ta yi hankali, afili kuwa ba tace komai ba ta sunkuyar da kai tana jin kunya saboda nuna- kawaici kan yar Fari. Iya tace dan haka shiyasa nazo da kaina saboda shirin zuwan nasu In kuma tafi da Zainabuna dan na gaji da zaman kadaici, Abban Amlah yace hakane Iya kina da gaskia, ai kin mayi kokari, ya cigaba da magana kai Ma shaa Allah nayi murna sosai, Allah ya tabbtar da alkhairi Allah yasa ace gara da aka yi, Ameen Iya ta fada, ita dai Ummy bata ce komai ba, Iya ta kalleta ni fa bani son gulma da kini bibi, Ameen din ma ba zaki fada ba saboda gulma, yo komu 'yan da masu kunyar gaskiya Ameen kan kan fatar arziki ma diyarka ai za kace, Abban-Amlah ya yi dariya yana kallon Matar tasa to kinji Ummyn yan uku Iya fa tace a ce Ameen, Ummy ta yi dariya, kasa - kasa ba tace komaiba. Iya ta jawo filet din dambun Nama ta kai bakinta, tare da fadin kya ji da ka difurinki, Zainabu na dai Aure Allah ya yi sai dai yan bakin ciki su mutu, Dariya sosai Abban Amlah ya ya yi har da kwalla Ita ko iya ko a jikinta kamar ba ita ta yi maganar ba taci gaba da cin dambun ta, Abban Amlah ya tsagaita da dariyar tare da sassauta murya Iya ina rokon arzikin, ki bar Mun dota in yaso in har bakin sun zo sun tafi, ni da kaina zan kawota a cikin satin nan kinga bai dace amarya tana gida ana maganar auren ta ba, Iya tace yaran zamani ai ba kunya ce dasu ba wasu ma dasu ake shirin komai, To Amma ba komai ita Zainabu na ai mai kunyace, 25 AKWAI KURA 2 Na bari Allah Ya kaimu satin ina nan ina jiranku, Iya ta mike to ni barin wuce tun da babu Zainabuna Ummy tace haba Iya keda ki ka ce wuni za kiyi, Iya tace na fasa ai daman ba wani ya sani wunin ba nice nan nace hakan saboda Zainabuna, kuma tun da Babu ita bazan wunin ba, Ummy ta yi murmushi Allah ya huci Zuciyarki Iya, Abban Amlah yace Iya muje in kaiki gida garin akwai rana. **** Saleem rayuwa ta masa tsanani mafarki ya sanya shi a gaba, ko yaushe yana cikin mafarkin Yar budurwa -mai neman taimakon shi, Abun mamaki kullum fuska daya yake gani wato fuskar yar aikin sa, a wani-bangare ga tsananin soyayyar Dream girl dinsa dake Addabar rayuwar sa, Duk Jarumtaka irin ta Saleem ya kasa jure Wannan abu mai girma dake addabar rayuwarsa. Saleem tun yana iya danne damuwar har yazo ya kasa, Yau kwana 5 kenan babu labarin Amrah a gun aikinta, Wayewar garin na yau tun safe Saleem ya tashi baya jindadin jikinsa tsananin ciwon kai ke damunsa tare da bugawar zuciya, wanda shi kansa bai san daliliba, a hakan ya yi shirin-tafiya aiki, domin yana da abinda zai yi a office mai matukar muhimmanci, a daddafe ya gama shiri sanye yake da shiga na suit ya yi kyau sosai kamar bature, Sai dai ga wanda ya sanshi sosai da ganin fuskarsa zaka gane akwai damuwa a tattare da shi, cikin Sallama ya shigo falon na Mommy, Tun shigowarsa kallo daya, tai masa Mommy ta gane Dan nata yana cikin damuwa, A tsaye yace da ita Mrng Swthrt, Mommy ta kalle shi da kulawa, tare da mayar masa Mrng hw yhu my Son? Fine Mom yace da ita, Yana kokarin daura 26 AKWAI KURA 2 agogon hannu Mommy Zan wuce Office, Dawuri haka? Mommy ta fada yes Mom in Dad ya fito kice masa na wuce ina saurinc. Mommy ta kalle shi break fast din-fa? am ok Mom ya fada yana shirin fita daga falon, wait_Son tace da shi a hankali Saleem ya juyo yana kallon ta tare da yamutsa fuska, Mommy tana kallon shi amma bata ce komai ba, ta girgiza kai tare da daukan cup ta zuba masa kunun gyada karba kasha bani son zaman ka da yunwa, Saleem ya karba tare da kafa kan sa a hankali ya fara shan kunun yana yatsina fuska alaman akwai damuwa, Ga Saleem sam baya jin dadin Kunun daci daci ma yake ji a bakin-sa sai da ya sha rabin kunun ya daga kai tare da ajiyewa kan table Swthrt sai na dawo ya fada yana fita daga falon, Mommy ta bishi da ido A dawo lafiya rabin raina. **** Da ido Mommy ta bishi har ya fita daga falon kamar kwai ya fashe masa a ciki, Mommy ta yi murmushi Son zurfin ciki, I knw ur problem. Wayarta dake kan table din ta dauko ta danna kiran Number Amrah, sai dai kamar kullum yau ma a kashe Wayar Amrah take Mommy ta ja karamin tsaki Mtsweee ! rashin Amrah na damunta Jin ta take kwana biyun nan itama kamar bata da lafiya, sai daga bisani ta gane kewan Amrah ke damunta, musamman in ta yi tunanin Watakila jikin Amrah ya kuma tashi shiyasa bata samu zuwa wajen aiki ba, Ita dai tana kaunar yarinyar jin Amrah take sosai a ranta, ita kanta tana mamakin Kaunar yariyar yanda take har cikin zuciyarta. 27 AKWAI KURA 2 Fitowar Abba shiya katsewa Mommy zancen zuci, dariya ta yiwa Abba tare da bashi wajen zama, Abba ya zauna yana murmushi Habibty Lafiya irin wannan farin ciki dana gani a fuskarki? Mommy ta yi dariya Daddyn yara lafiya lau Tare da fara sabing dinsa. Saleem tun da ya dawo aiki nan falon Mommyn ya yada zango anan ya ci abinchi tun da yaci bai fita ba yana nan dafe dakai, har aka kira sallar Magriba sannan ya tashi ya tafi sallah a masallacin dake cikin gidan nasu ya wuce dan gabatar da Sallah, sai da yas allaci isha'i kafin ya mike dan shigowa cikin gida, sai dai me ? Jirine ya debe shi da sauri ya koma ya dauna, Daya bayan daya -mutanen dake masallacin, suka dinga fita har liman ya fita sai Daddy dake zaune yana lazimi, Saleem Na zaune dafe da kai yana jin jiri duk da a daune yake Daddy har ya gama Lazimi ya tashi da niyyar fita Amma Saleem na Zaune dafe da kai, Son Daddy ya-fada tare da tsayawa yana kallon-shi, A hankali Saleem ya daga kai ya kalli Daddy Kanshi tuni jijiyoyin sun tashi idonsa ya yi ja alaman damuwa. Da sauri daddyn Ya karaso Lafiya Son Saleem, ya ciza lebba yana son daurewa Dad Ya rungume shi a jikin shi tare dafa kan shi sosai kan nashi ya dauki zafi, Da sauri dad ya daga Saleem, tare da masa kyakkyawan riko a hankali suke takawa Saleem na layi kamar zai fadi Dad yana taroshi, masu gadin second get sune suka taimakawa Daddy wajen shigo da Saleem gida direct Falon Mommy suka wuce da shi, Mommy na zaune tana kallo A falo sai ganin ta yi masu gadi 28 AKWAI KURA 2 tallafe da Saleem a jikinsu -da gudu ta karaso garesu tana tambayar Lafiya? Kira dr Daddy yace da ita tare da karban Saleem din ya kwantar da shi a kan 3siter. **** Gabadaya gidan Hankalin su a tashe yake kama daga masu aiki har Masu gadi da suka shigo da Saleem, Mommy tafi kowa damuwa baka jin sautin komai a falon sai kukan ta, tun da aka shigo da Saleem Mommy ta kira Family Doctor dinsu, Amman har yanzu-bai karaso ba a karo na uku Mommyn ta kuma kara waya a kunnenta ganin numfashin Saleem din ya na shirin daukewa da sauri tace Daddy ruwa a guje Yar aikinsu hajara ta dauko ruwa ta mikawa Mommy. Ruwan Mommy ta karba ta bude tare da zubawa a hannunta tana shafawa Saleem a fuska bakinta dauke da addu'ar nema masa sauki a hankali Saleem-ya-ja Numfashi-da alamar ya dawo daga karamin suman da ya yi a hankali ya furta Mom kirjina Tare da kai hannun shi ya dafa wajen dake masa ciwo, yana sauke numfashi mai wahala, Daddy ya kuma rungume shi yana tofa masa addua, tare da yi masa sannu. Cikin wannan halin likita ya zo ya same su, Ba tare da bata lokaci ba ya fara bawa Saleem taimakon gaggawa tsawon Mintuna 30 Doctor nakan Saleem kafin ya yi nasarar gano meke damun sa cikin sauri ya yi masa Allurar bacci, Tuni bacci ya dauke Saleem Tare da Sauke Ajiyar Zuciya na wahala, Alhamdulillah Dukkan su suka fada, Ganin Saleem ya samu bacci hakan yasa masu gadi da sauran ma'aikatan dake cike a falon Mommy saboda rashin lafiyar Saleem 29 AKWAI KURA 2 gabadayansu suka fita tare da yiwa iyayeb na sa fatan Samun lafiyar Saleem. Doctor meke damun Dana Daddy ya fada yana kallon Doctor, Doctor yace, Alhaji garin yaya Saleem ya samu damuwa haka wanda har yake baradana da rayuwarsa? Nayi mamakin da naga jinin sa ya hauhawa mai yawa wanda mu likitoci bama kaunar hakan ga maras lafiya, Subhanallah Daddy ya fada Hawan jini dai Son din nawa ?? Doctor ya daga kai tare da tabbatarwa Daddy hakan yake nufi, MOMMY ta kuma, fashewa da kuka na shiga uku na Son Ban dauka kayi nisa hakan ba Please Son kar ka bari in rasaka saboda Soyayya pld Son ta fada tana kuka sosai, Gabadayansu-suka kalleta Daddy da Doctor-! Mommy ta cigaba da kuka tana Kiran Saleem kar ka-Mutu kan Soyayya Daddy ya jawota jikin sa yana rarrshin ta Mommy kuka take har da sheshsheka ta Kasa yiwa Daddy bayani hakan yasa Doctor ya ya katse mata kukan Alhaji zan wuce ga takarda nemo wadannan magungunan kafin ya farka, Alhaji ina baka shawaran ka dauna da danka kaji-damuwar sa-indahali a bashi abinda ya ke so kar matsalar ta shafi zuciyarshi Daddy ya gyada kai tare da godiya ga Doctor, sallama suka yi sannan ya fita dan basu guri su tattauna watakila maganar su ce ta cikin gida shiyasa Mommy ta kasa sanar da mijinta a gaban sa. **** Hankalin Iyayen Saleem ya tashi sosai Musamman Mommy, da tun da Doctor ya fadi matsalar Saleem take kuka kamar karamar yarinya, Cikin kuka take fadin Laifi nane Daddy, tabbas laifina ne gashi yaro na yana shirin rasa ran sa akanta. 30 AKWAI KURA 2 Wallahi banyi zaton Abun zai yi tsanani haka ba na manta ni uwace addu'ata karbabbiya ce akan dana, ta cigaba da kuka ta nuna kirjinta ni da kai na nake rokon Allah ya dorawa Son kaunar Amrah, bakomai ya jawo hakan ba sai kaunarta da Allah ya doramin a cikin raina kullum addu'a ta Son ya sota ban yi la'akari da rokon Allah ita ma Amrah ta so shi ba sai gashi Allah ya karbi Addu'ata kamar yadda na roka wayyoni na shiga uku Son ka yafe min, Daddy rungumeta a kirjin sa yana rarrashinta Habibty kukan ya isa haka is okay, uwa ba za ta taba cutar da danta ba sai dai shashashar uwa. Mommy ta gyada kai Ban yi da niyyar cutar da dana ba, sai danna hango Alkairi sosai a tsakanin su, kuma ban tsananta addu'ar ba har sai da nayi istihara naji na samu nutsuwa akai, Allah sarki Son ashe Addu'ata a matsala-zata jefa-ka ka yafemin Son ta fada tana-share hawaye, Daddy ya-yi murmushi, Mata kenan sarakan wauta Ai da kin masa addu'ar zabin Allah, kinga in Amrah alkhairi ce a gareshi sai kiga da kanss yace ita yake so, but nebertheless, Allah ya bawa Son lafiya, Allah kuma yasa yadda yake sonta itama ta so shi haka Ameen in ji Mummy ta fada. Saleem, bai farka ba sai karfe 11pm na dare a hankali, ya bude ido Sosai ya ke jindadin jikinsa yana karewa dakin kallo a halin yanzu babu inda ke masa ciwo sai dai rashin karfin jikinsa da sauri Mommy dake kan sallaya tana sallar nafila ta sallame, tare da tashi tazo kan gadon Sannu Son ta fada tana rike hannunsa, a hankali Saleem yake magana Mom, meya sameni na ganni a dakin Daddy? Mommy ta girgiza masa kai tana share hawaye Son soyayyar ta ce sila 31 _ - AKWAI KURA 2 ko? ta fada tana kallonsa, Saleem runtse ido yabude tuni ya tuno dalilin da ya kai shi kwanciya a dakin Daddyn nashi, a hankali kamar bai son magana ya furta Mom I **Lo6e her* **somuch** but ina ta je Na rasa inda zan ganta ! Mom kusan duk garin kaduna na kewaya but banganta ba why! Ya fada yana lumshe ido, Karar bude kofar bandaki shi tasa Mom ta tsaya bata ce komai ba sai ma idonta data mayar kan kofar tana kallon Daddy daya fito daga Toilet, Ganin Saleem ya farka da sauri Daddy ya karaso yana masa sannu Saleem. ya gyada kai tare da kallon Daddy, Dad ku nemo min ta ina son ta sosai Dad ji nake dazu kamar zuciyata zata fashe Saboda kaunarta, Dad Mom in babu ita Mutu...Mom ta rufe masa baki, baza ka-mutu ba, Son da kaina zanfita in nemota duk inda ta shiga a garin nan, pld Son ka kwantar da hankalin ka badan jure ganin ka cikin ciwo-ba, Saleem ya-yi Murmushi a hankali yace Thakns swthrt. -Son yakamata-ka ci wani abu ko da shayi ne Daddy ya-fada, Habibty a hada wa *JARUMINA** Shayi Mommy ta yi dariya Ah ah yanzu kam ya fita daga layin jarumai, tun da gashi kwance saboda kauna, Saleem ya turo baki yana shagwaba Daddy kaji Swthrt ko? Rabu da ita Daddy yace in dai kan Soyayya ce koni da tsufa na ai sai in kwanta In har Habibty tace bata yina, Dariya Mommy tana jin kaunar dan ta da mijinta tana ratsa ruhinta, tace aini ban isa ba mutu ka raba nida kai, Saleem ya yi murmushi yana jin dadin yanda Iyayen nasa suka tsufa da soyayyar junansu. 32 AKWAI KURA 2 Daddy ne ya taimaka masa ya tashi zaune, Mommy ta hada masa shayi a hankali take bashi a baki, cikin shagwaba Saleem yake sha tare da jaddadawa Mommy lallai fa in bata so ta rasa shi a nemo masa Amrah, Daddy na musu dariya ai dolen ta Son kai dai Allah ya kaimu gobe da rai da lafiya. a dakin Daddy Saleem ya kwana tare daddy saboda tsoron kar ya kwana shi kadai tunanin Amrah ya hanashi bacci gashi bai da lafiya, Ita ma Mommy bata bar dakin Daddy ba Sai Karfe 2am sannan ta koma dakinta Asuba tagari. **** Ranar Juma'a tun

Chapter 2 of 10