Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 10
Daddyn shi, Dad yana daukan wayar kamar yaro karami Saleem ya fashe da kuka, Dad dake Office ya mike a radane yana tambayar Son din nasa lafiya ? cikin kuka Saleem ya sanar da Daddy Matar shi ta bata, Dad daya kasa gane inda Zancen dan nashi ya nufa, gabadaya hankalin shi a tashe Yake maimaita Tambayar meke faruwa kawai dad yake yi. 63 AKWAI KURA 2 Cikin kuka Saleem yake fadin Dad ba a gantaba matata ta bata Dad koma waye yake da hannu cikin batan Matata sai na harbeshi, Dad Na rike da waya cikin rarrashi yake tambayar Saleem me ya faru? Saleem, Ya kasa magana sai kuka karshe Maheer ne ya karbi wayar cikin alhini ya sanar da Dad abunda yake faruwa, Dad shi ma take hankalin shi ya tashi, Cikin damuwa yace da Maheer Please ka kula da abokin ka ba lafiya yake da its ba ka rarrashe shi kuje gida ina zuwa gidan yanzu, bawa Son wayar Maheer ya sanya wayar a kunnen Saleem Cikin rarrashi Dad ke fada masa za a sameta ya turo masa da hoton ta a WhatsApp zai tura a fara Bincike yanzu. A hankali Hankalin sa ya fara dawowa jikinsa sakamakon rarrashi da Abban ya masa a gefe kuwa-ga Maheer sai Lallabashi yake, a wayar Maheer suka samu photon Amrah funi ya turawa Dad a whatsApp, dad yana ganin sakon shima tuni ya yi forwarding zuwa ga hukumar bincike ta kasa baki daya Saleem bai yarda sun koma gida ba direct Office, na yan sanda suka nufa, cikin awa biyu kacal garin Kaduna ya cika da jami'an tsaro lungu da sako, kama daga kan Yan-sanda Sojoji hae Dama Jami'an Costum ba'a bar su a baya ba, Saleem ya-tura CONVOY din sa neman inda Amrah ta shiga, shima bai dauna ba wuni surrre suna zaga Kd da jajinta Neman Amrah, basu dawo gida ba sai bayan sallahr isha"i shima da kyar Mom ta lallabashi a waya ya dawo gida kan cewa gobe su daura daga inda suka tsaya, cikin lokaci kadan da sanin batan Amrah, Tuni Maganar Batan ya bazu ko ina cikin birnin KADUNA da kewayanta, gidan Radio da talabijin kowanne sai sanarwa suke na batan ta tare da 64 AKWAI KURA 2 fadar kyauta mai tsoka ga duk Wanda ya fanta ko ya kawo labarin ta. ****** Da kyar Zahra ta lallaba Granny ta janyc maganar dauko Sojoji, Zahra da kanta ta tsare keke napep tare da masa kwatancen inda zai kai Granny, Zahra ta ciro kudin a jakarta ta cire kudin ta biya mai keke napep, ita kan ta granny kuka shar shar take tana salati, tare da kiran Sunan Zainabu Ina zan ganki kamar Zainabun tana gabanta. Sai da mai Keke napep yaja ya tafi kafin ita ma Zahra ta hau dan acaba ta yi ta tafi nasu gidan, Mai keke napep yа ajiye granny a kofar gidan Ummy cikin sauri ta buga get din gidan, Malam isihu mai-gadi da sauri ya taso ya bude get tare da fadin ah ah Mutumiyar kece tafe Baki ya bude yana mamakin me yasa Tsohuwar kuka, ita ko Iya kala ba tace da shi ba ta sanya kai ta wuce cikin gidan, Ikon Allah mai gadin ya fada yau dai lafiya meke faruwa a cikin gidan ga? Iya Ta fada falon Ummy ko sallama babu cikin fada tana kuka ta fara magana ina Usmanu, fito yau bani ba kai Azzalimi tun da ka zamo algungumi, fito matsiyaci yau bani barin gidan nan sai ka -fitomin da Jikata Azzałumi macuci yau mai rabani da kai sai Allah. Da sauri Ummy ta fito daga daki jin maganar Iya ganin iya tana kuka Ummy taji kamar Yanzu abun ya faru, bata san lokacin da itama ta fadi a jikin Iya ta sake fashewa da kuka ba tare da fadin Iya mun rasa Amrah, Iya yau kwana 10 Amrah bata gida waya sani ma ko an cinye naman ta wayyo Iya na shiga uku ban rike Amanar Marainiya ba Na bu da namiji ya batar min da diya, Ummy ta fada tana kara sautin 65 AKWAI KURA 2 kukan ta tare da kankame Iya. Iya ta daga murya Ina Usmanun yake ya fito Ya fadamin inda ya kai min jikata Ni nan zanje in dawo da Jikata, ko Dajin Sambisa take ni zanje saboda ceto rayuwar diyar Amaduna, kuma insha Allah mun riga ka munce Allah jikata bazata mutu a hannun Azzalimai ba. Alhaji Usman da tun shigowar Iya ya jita amma kunya ta hana shi fitowa, duk kalar zagin da Iya take a kunnen sa gareshi san bai zargesu ba saboda ran mutum guda ba abun wasa bane ace an rasa, Shi kansa tun faruwar abun tsawon kwana Goma, bai zauna ba yana kan bincike tare da yaranshi kan inda Amrah take, inta son ranshi nema yaso a sameta kafin Kowa ya farga saboda gudun irin wannna rana. Muryar Iya ya dawo da-shi daga tunani Usmanu ka fito ko in biyo ka daki dan yau babu sauran mutumci a tsakaninmu Algungumi, Abban Amlah Cikin karfin hali ya fito falon yana sun sunne kai, kamar munafuki fuskansa dauke da Tausayi tare da damuwa na ganin halin da Tsohuwar da matarshi suke ciki, Cikin dauriya ya nemi kasan kafet ya dauna tare da gaisar da Iya sai dai Iya bata amsa ba illa harara data doka masa. Cikin lallashi Abban Amlah ya fara magana Iya ki yafe min domin Allah, Ni ban da abunda zan kare kaina sai dai Allah ne shaidata banyi hakan da niyyar cutarwa ga Amrah ba Ai nima Amrah diya tace Saboda Zainab Amrah ni Ubanta ne, sai dai baka tara sani da ikon Allah wallahi tallahi Iya da dana san hakan zai faru da ban fara ba...... Dakata Iya ta fada tana nuna shi da dan yatsa Kulllll nace maka kul kar in karajin kalmar baka san haka zata faru ba in hakane me yasa baka sanya yayanka ba. ? da aka samu 66 AKWAI KURA 2 matsala me yasa kamar yadda kazo ka sanar damu kafin aikin yanzu ma baka sanar damu an samu mishkila ba? To Azzalimi jinin diyata daci gareshi yafi karfin cin ka ai daman Masu kudi yanzu bana Allah da annabi banc Kudin tsafi neWallahi tallahi babu inda zanje saika fitomin da Jikata. **** Yau shi ne karo na farko da Granny Ta fara kwana a gidan Ummy a cewar granny babu inda zata je sai Abban Amlah ya fito mata da jikarta, Tun data zo bata saurara mishi ba har sai da ya bar gidan. tun fitar shi bai kuma waiwayar gidan ba Allah ya taimake shi ma yau, kwanar gidan Uwargidan dan haka can daya gidan ya wuce Tabbas ba dan haka ba da ya shiga uku a wajen granny. Shi ma koda ya fita bai dauna ba Shige da fice su kayi sosai shi da yaran sa na office su na neman inda Amrah ta shiga, bai samu kansa ba-har sai-karfe 11pm na dare kafin Uwargidan ta ganshi, Abun mamaki Da shigar sa gidan Uwargidan a zaune ya sameta tana jiran sa cikin tashin hankali, domin tu ni ita ma ta samu labarin batan Amrah ta sanadin gidan Radio, Abban Amlah na shigowa falon Hajiya mariya ta fashe da kuka tare da fadawa jikin mijin ta, tana tambayar shi ko an dace da ganin Amrah, Abban Amlah cikin damuwa ya sanar da ita har yanzu ba'a dace ba sai dai ana kan nema, cikin tashin hankali tana kuka tace da shi ya koma gidan Ummyn yan uku ita kan yau ta yafe kwanan saboda tasan Ummyn Uku ita ke bukatar kulawar sa yau, Amman sai ya yi murmushi tare, da sanar da ita karta damu Ummyn yan uku tana tare da lya. 67 AKWAI KURA 2 Washegari, family ukun sun tashi cikin tashin hankali na rashin samun labarin wanda yaga Amrah bare ita kanta Amrah, Ummy da granny yadda suka ga rana haka suka ga dare Maganar bacci babu shi cikin gidan Uku. Saleem Kuka sharshar ya yi wa Mom nd Dad na rashin ganin Amrah, Ita kanta Mom din tana bukatar mai rarrashi domin rashin Amrah ya taba ta sosai Mom da Amrah Akwai shakuwa mai girma a tsakanin su, Mom da kanta ta kira Mera tasanar da ita batan Amrah, Tare da halin da dan uwanta Saleem yake ciki na Tarkon Kauna. Mera ta fashe da kuka cikin tashin hankali Maman Affan Mun shiga Uku Mom ko masu garkuwa da mutane ne suka dauke ta, please Mom ko nawa suke bukata nayi alkawarin dan biya in fanshi ran Maman Affan. **** Zahra Da kuka ta isa gida, dan achaba yana sauketa a kofa get da gudu ta shiga gidan su, Mamah Mamah ta dinga kwala mata kira tana kuka da sauri Mama ta fito daga Kichin Zahra'u lafiya irin wannan kira hak. Zahra ta fada a jikin kujera tana kuka Mamah An sace bestyna Mama Bestyna bestyna Mamah ta fada-tana kuka sosai, Mamah ta riketa yi min bayani bangane an sace ta ba? Zahra tana kuka eeh Mamah ranar da naje na dauketa Mu kaje shopping Ashe Bestyna bata koma gida ba Cikin kuka ta sanar da Uwarta abunda ya faru, Innalillahi wa inna ilaihirrajiun. Mamah ta fada tana Dama akan kafet, Mun shiga uku dan mutum ya bata bat sai kace kaza, Ayya Amrah baiwar Allah tana mace ko a raye sai Allah a ce yau tsawon kwana goma da batan mutun amma ba'a sani ba kai Amma anyi sakaci 68 AKWAI KURA 2 ran mutum ai ba ran dabba bane Allah ya baiyana Amrah Allah yasa tana hannun mutanan kwarai. Mamah Bani wayarki in kira yaya Anas Wayata na barta falon Ummy, Mamah tace-ah-ah karki daga masa hankali ya kasa Tuki a kuma shiga wata matsalar barshi in ya dawo gida zai ji a tsanake kinsan Yayanku sarai da dimuwa, Zahra tace ah ah Mamah ki bani in ce yazo kina son ganinshi dan nasan in ma baiji labari anan gida ba zai ji a waje kuma a halin yanzu Yaya Anas yana bukatar jin lbrn dan ya dauki nashi matakin kafin wanda bai da alhaki akanta ya dauki Hidimar da ba tashi ba. Mamah ta kalleta waye bai da alhaki akanta Zahra ta yi shiru tana kifta ido Mamah bani wayar ta fada tana-share hawaye Mamah tace gata dan Allah ki tabbatar baki sanar da shi ba saboda dalilin dana fada miki, Zahra-ta karbi waya tana danna kiran lambar Anas. ***** A zaune ya kwana yana cikin saboda damuwa daga karshe Bandaki ya shiga ya dauro alwalah, bayan-ya fito darduma ya shimfida ya tada sallar Nafila, Saleem da ya kai karfe Ukun dare yana ibada tare da tsananta addu'a-cikin sujuda akan Allah ya baiyana Amrah, Karfe uku da rabi na dare ya kammala sallah, haka kawai ya ji yana kaunar ganin photon ta wayarshi ya dauka akan T6 tare da shiga Galary ido ya tsira mata cikin Tsananin *So Da kauna* Tuni zuciyarshi ta yi nisa wajen shaukin begenta, kamar an tsikare shi ya mike tare da futa daga dakin Kofa ya bude direct ma'adanar CCTB camera ya tafi Haka kawai ya ji yana kaunar yaga All shigarta da fitar daga gidan, Ba tare da bata lokaciba ya ciro SD card din laptop dinsa ya jawo tare 69 AKWAI KURA 2 da dama akan kafct tuni ya sarrafa komai cikin kwarewa, Ido ya duba yana kallon Laptop din cikin minti kadan 6ideo ya fara aiki. Saleem ya kai minti 18 yana kallo sai dai har yanzu bai ga abunda yake kaunar ganiba, hakan yasa ya jawo laptop din a hankali ya fara forwarding dasauri ya tsaya Cikin nutsuwa ya fara kallon ta tuni ya ji farin cikin ya ziyarci zuciyarshi, Kallon ya maida hankali kai a sannu yake ganin komai tun farkon zuwan ta gidan neman aiki cikin local dress. **** Yadda take komai nata a nutse da yadda take yin aikin nata cikin kwarewa abun ya burge Saleem, Babu abunda ya burgeshi irin yanda yake kallon ta da Mom cikin nishadi tare da Affan Da Meerah, Saleem ya lumshe ido yana jin nishadi Akwai kauna mai yawa tsakanin Matarsa da parent dinsa lolz öYTM Murmushi ya yi tare da cigaba da kallon ta a kichin tana girki. Amrah mai kyau ce abin son kowa ya fada yana kare mata kallo cikin kishigarta mai kyau, lsanye take da kayan girki Riga da skirt iyakarta guiwa ta yi kyau sosai cikin shigar duk wani baiwar kyau nata, tare da kyan halittar ta ya bayyana, kanta sanye da hula ya yin da gashin kanta yake zube a kafadar ta har gadon bayanta. Saleem ya sanya hannu ya yi screenshort-na gurin saboda tsananin kyau data masa, a hankali ya yi playing bideo din ya cigaba da kallo cikin nishadi yake kallon ta Abun ya burge shi lokacin da yazo inda ta shigo gidan ta labe tana kallonshi yana motsa jiki Baki Saleem yankama alaman mamaki, *Wash** ya fada afili yana lumshe ido saka 70 AKWAI KURA 2 makon ganin lokacin da ya take ma ta dan yatsa, a hankali kamar tana kallonshi ya furta "Sorry My Madam." Kiran Assalatu shiya fargar da-Saleem daga kallon daya shagaltar da shi cikin mika ya jawo laptop dai kashe sai dai me ? da sauri ya tsaya yana kallonsu tare da kankame Laptop din a jikinsa, cikin second uku Abunda ya faru ya fara baiyana masa Tun daga lokacin da Uwar da yarta suke zuwa gurin har lokacin da suka fara tone rami, Sosai Saleem ya ware ido tare da tsaida Hankalin shi dan ganin me zai faru, Abun kamar a mafarki Amrah ta tako wajen kunnanta manne da waya. Cikin sauri ta boye jikin garu tana leko da kai tana kallonsu, daga bisani Wayarta ta sai ta tana Bideo, komai daya faru a gun ya cigaba da gani Inda yaga Kanwar Dad nashi da diyarta sun ciro manya manyan layoyi, cikin sauri suka binne a cikin ramin tare da mai da kasar gurin, Da sauri suka bar wajen hankalin su kwance sun gama aiki. A hankali ta fito daga maboyarta-komai da ta yi Saleem ya gani Cikin tsananin mamaki ya gyara dama har saida daukan ya kare, ikon Allah ya fada yana tuno ranar da ta canda masa abinci, Wacece ita ?meyasa ban farga da komai ba sai yanzu? Lallai kinchi sunanki *JARUMA* Ko a films bai taba ganin kaddara irin tashi ba, da sauri ya mike tare da kallon Agogo karfe 6:30am na safe Saleem ya kashe laptop din tare da shiga bandaki dan dauro alwala. **** Cikin sauri ya gama shiri cikin simple dress Wayoyinsa ya dauka tare da fita falon Mom, a gurguje suka gaisa cikin kulawa iyayen nasa suka jajanta wa juna Matsalar tasu, Dad ya kara masa bayanin in shaa Allah za'a dace. AKWAI KURA 2 Tnz Dad ya fada yana korarin fita, Mom barinje ana nema na Office na yan sanda kan case din, Mom ta tsayar da shi Son ko ruwan tea kasha please kai ma ba lafiya gareka ba ta fada tana langwabe kai, Dad Ya amsa Ayi hakuri asha *JARUMINA* Saleem ya yi murmushi hakan kawai yake jin nishadi tare da jin kwarin guiwa kan Masoyiyar tasa, Owkhey ! yace da Su tare da jan kujerar Dinning ya zauna Cikin sauri yake shan tea din, kirrr wayarshi ta yi kara Cikin hanzari ya dauka Maheer ne ya kira Hellow abokina kana jina Saleem lumshe ido tare da fadin uhum Maheer ya cigaba da magana Yan sanda sun kirani yanzu ni da Madam dita wai Muzo mu amsa wasu yan tambayoyi banyi kasa a guiwaba naje na dauketa muka je But suna maganar kulle mu ni da madam har sai anga Amrah. Saleem Ya yi shiru yana sauraron Maheer Cikin nutsuwa ya furta bery good in deed, ashe yanzu sun san aikinsu. Cikin jindadi ya fara magana akwai farkon Tuhuma ne bayan kai da Madam dinka? Think tare kuka futa after dat har yau ba'a ga matata ba dan haka Hukuma suyi aikinsu kan duk wani mai ruwa da tsaki cikin batan matata bai saurari amsar Maheer ba ya kashe wayarsa tare da mikewa Baki Mom ta sake tana kallon Saleem fuskanta cike da zargin shi, Saleem ya mike yana kauda kai Mom Dad saina dawo ayi min addu'ar dacewa ya sanya kai ya bar falon. **** Numfashi ta cigaba da saukewa tare da kallon su, saura kadan su cimma ta, Amrah ta daga waya tana dan nawa cikin dace ta samu wayar babu Pasaword, Ita din gwanace wajen haddace number akanta duk wani contact dake 72 AKWAI KURA 2 wayarta dai dai ne bata dasu a haddace akanta, Amrah bata yarda da number a wayaba saboda bacin rana irin ta yau, cikin Jarumta ta yarda da shawarar zuciyarta na ta kirashi hakan kawai taji a ranta shi din zai taka rawar gani wajen kubutar ta a hannun Azzalumai... Ido ta runtse tana kallon number a idon zuciyarta, kamar yau Mom ta yi dialing, a wayarta Masu karatu in baku manta ba, last tym Mom ta karbi wayarta ta kira Saleem. Cikin Sauri ta fara Rubuta Number din a wayar ya yin da idonta yake kansu suna karasowa cikin gudu, Hannu tasa ta ciro bindiga a cikin aljihunta tare da sai ta bangaren su tana numfashi cikin sauri taji an daga wayar Nishi take fitarwa na wahala cikin muryanta mai Dadi tafara magana *Please help me OGА J.* Tas tas tas, ta harba bindiga Cikin nasara ta samu biyu a cikinsu Gabadayan su suka tsaya daga nesa tare da daga hannu alamar sunyi saranda, Amrah ta fara magana cikin wahala duk wanda ya karaso gareni sai dai uwarshi ta haifi wani, cikin wannan hali Ahmad ya karaso gurin da gudu Turuss ya tsaya yana kallonsu Kamar a filin yaki Ido ya kai kan yaransa da suke yashe cikin jini da alamar daf suke da mutuwa. Cikin izza ya fara magana kin ci amana Alkawari-bai ce haka ba Lallai na yarda mata shaidanu ne masu kwandon sharri, Amrah cikin fada ta fara magana cin amana ya wuce naka kai in kana da kunya har kana da bakin maganar Amana in ji amininka abokinka wanda ya sadaukar da komai nashi akanku shi ka ciwa amana. ? To kasani taka tazo karshe kai da duk wani azzalumi wallahi tallahi ko dan rasa raina sai asirinku ya tonu. 73 ****** AKWAI KURA 2 Tuni yan sanda suka yi ram da Abu Amlah, bisa ga umarnin Saleem Ummy ko da ta samu labari ko kadan bata ji haushi ba hasalima taji dadi abinda matashin saurayin ya yi duk da bata san shiba batataba ganin sa ba sai akan case din Amrah. Tun wayewar garin yau yan uwa da abokan Arziki suke zarya a gidan Saboda masu mata jeje kan abunda ya faru, Granny da taci kuka har ta godewa Allah tun faruwar lamarin bata samu nutsuwa ba ita ma taji dadi sosai na kama duk wanda yake da alhaki cikin batan Amrah. Anas shima tun da ya samu labarin batan Amrah yake cikin tashin hankali Shi ma ba'a barshi a baya ba kasancewar sa jami'in yan-sanda tuni ya baza nasa yaran kan nemo Amrah, Daga faruwar lamarin zuwa yandu duk wani majalisa ta daba a jihar Kaduna hukuma ta yi ram dasu, dai dai ku ne a cikinsu da suka samu labarin ana kame su sukа nemi maboya. Tun da iyayen Zahra suka samu labarin an rike Zahra hukumar bincike hankalin su yake tashe fiye da batan Amrah, Dakansu suka je office na yan sanda tare da jagorancin Anas daya kasance shima babbane cikin ma'aikatan na Yan sanda, Sai dai sawun giwa ya take na rakumi wanda yake da alhakin shigar da karar Babbane cikin ma'aikatan Custom, dan gidan babban Attajiri a kasar Alhaji Hamza shiyasa duk wani beli babu wanda aka bada daga Maheer, Zahra Harda Alhaji Usman. Faruwar wannan abu ya bata ran Iyayen duka musamman Iyayen Anas basu ji dadi kan abinda aka yiwa diyar suba ance mai da wawa tun da Dad yasamu labarin Yan sanda 74 AKWAI KURA 2 sun hana beli tuni ran sa ya baci- Cikin Tashin hankali dadamuwa ya kira Anas a waya gabadayan su suka dunguma gidan Ummy danjin ba'asi. Saleem Daga gida direct gidan Ummy ya nufa saboda sun yi mAbaba da yansanda kan ya kawo Ummy domin ta amsa wasu yan tambayoyi kan dalilin batan Amrah-musamman da take zargin akwai sanya hannun mijinta, Cikin sa'a da isa rsa gidan Iyayen Anas suka karaso ya yinda Uwar gidan Alhaji Usman tuni ta tsufa a gidan Ummy tun da garin Allah ya waye da Yan sanda suka je suka yu ram da maigidanta. Tun da Saleem ya fito a mota Anas ya tsura masa ido tare da mamakin mai ya kawo Young Millonia gidan, haka Abbansu ido ya tsura yana kallon Saleem fuskanshi cike da alamun kamar ya sanshi, Saleem bai ce kala garesu-ba-kallo daya ya yi wa Anas ya hango tsananin kamarsu da Zahra, take ya ramfo zancen wannan shi ne Anas barawon matarshi Saleem ya ji ran shi ya baci-tare da tsananin kishi ji yake kamar yaje ya fasa kan Anas da bindiga.... ***** Mtsw! Ya ja dogon tsaki tare da kama hanyar shiga falon ko Izini bai jira ba cikin muryar shi mai dadi mai tattare da damuwa ya yi sallama a falon, yan uku dake zaune suna cin abincin break da gudu suka rungumeshi kamar sun sanshi Oyoyo Uncle, Saleem ya ware hannu tare da musu alamin suzo da gudu Mazan suka fada jikinsa Saleem ya daga su sama tare da ajiyesu Hannu ya mikawa macen Oya ".come יי Amlah ta tsuguna har kasa tana gaida shi tare da make kafada Ummy ta hanamu Tace ba kyau ni mace ce Allah ya 75 AKWAI KURA 2 hana, Saleem ya yi murmushi tare da ya bawa Ummy kan tarbiyar da take baiwa yayanta. Bismillah ka dauna Ummy tace da shi tare da Amsa sallamar Hajiya fatima dake bayan Saleem Cikin nutsuwa Saleem ya gaida Ummy tare sunne kai wai shi kunya, Ummy ta amsa cikin sakin fuska tare da jin kaunar dan saurayin a ranta Duk da bata san waye ba Gareta tun jiya datai masa kallo daya taji ran yanaa sonshi-Musamman inda ya tsaya kan tsayin daka game da batan diyar ta. Mamah ta yi gyaran murya Iya tare muke da Abbansu Anas suna jiran ai musu idini su shigo, Ummy ta kalli yan uku Amat jeka shigo da baki da gudu Amat ya fita bai jima ba ya shigo da Anas da Abbanshi, Bayan gaisuwa tare da jajantawa juna abin da ya faru. Abban Anas ya fara magana Anas ya sanar da mu duk abunda ya faru kafin In daura dalilin zuwan mu, Anas ya sunkuyar da kai tare da satar kallon Saleem da wutsiyar ido lalli yau dole ya tona asiri Koda hakan yana nufin Saleem din zai dau mataki bada komai ba ya zamo dole ya fadi iyakar gaskiyar daya sani. **** Gabadaya falon ya yi tsit kamar babu halittar dan adam a ciki, dikin nutsuwa Anas ya fara sanar dasu tun-farkon zuwan Amrah har office din sa, kan alfarmar ya koya mata harbi da farko yaki amincewa Ammaa da Amrah ta rinka masa magiya ba dan ya so ba ya amince saboda tsananin kaunar ta da yake bai yi la'akari da risk din da zai jawo masa a gurin aiki ba. Ya cigaba da basu labari tun daga lokacin daya fara koya mata harbi har kawo yau da aka rasa Amrah sama ko kasa 76 AKWAI KURA 2 Anas yakara da fadin, koda kafin hakan ya faru bangajiba kullum ina cikin tambayar ta meye dalilinta na aikata hakan sai dai Amsa daya take bani in lokaci ya yi zan sani, da fari naji tsoro amma daga baya nima na ware saboda itama da take mace babu shakka ko tsoro a tare da ita sai dai kullum tana sanar da ni Babu kuskure cikin abunda ta keyi inlokaci ya yi dan shaida. Bantaba jin tsoro ba sai ranar da Muna cikin koyan harbi tsautsayi ya fado kan mu inda Amrah ta harbi assistant controller na Costum, Anas yaja numfashi tare da nuna Saleem da hannun shi. Gabadaya kallo ya koma kan Saleem Musamman Ummy data yi mamakin Ashe a TB take ganin fuskar Saleeem musamman da duniya ta yi shaida shidin mai gaskiya ne a cikin aikin sa., haka Abban Anas shi ma da sauri ya ramfo inda yasan Saleem, anas ya cigaba da magana. Na yi kuskure nayi wauta a matsayi-na-na namiji-dana biye mata ba tare dana san hujjarta na-aikata-hakan ba, Soyayya ta rufe min ido banyi la'akari da hatsarin da-zamu shiga daga ni har ita ba, sai jiya dana samu labarin batan Amrah... Salati gabadaya falon ya dauka Tare da kukan Ummy, Anas lallai kayi wauta Mamah ta fada ai wannan ba abun shiru ba ne gashi sai da abun yafi karfin mu ka fada Ohhh! Ni Fatima ta ina damu fara neman Wannan yarinya ? Granny ta fashe da kuka tana fadin Allah ya bayyanaki Zainabu na, Allah yasa kina hannun mutanen kirki, Ta nuna Anas da yatsa wannan anyi dan bandan yaro mai kwalelen kai da gani wannan baki naka har cikin zuciyarka ne, Ban san kwakwalwar kifi gare ka ba sai yau, ashe baka 77 AKWAI KURA 2 da tunani kai da kake namiji ai kai ne mai laifi da baka sanar da kowa ba yo inni Tsohuce aiko Uwarta kazo ka sanar mata. To kalleni da kyau na fasa baka auren Zainabu na koda Allah ya bayyanar da ita Aure babu shi tun da kaima shashasha ne ko auren kuka yi ba zaka rinka ganar da ita hanya madaidaiciya ba, da sauri Anas ya fara bada hakuri tare da tsiyayan hawaye dan yasan wannan tsohuwar tsab data iya aikata abunda ta fada, shi ko in ya rasa Amrah ai saidai ya hakura da Aure. *** Kirır karar kida mai dadi ya karade falon Saleem da gabadaya ransa ya baci jin Anas yana fadar magana sai kace mace saboda wauta Lallai ya zamo dole ya daure Anas domin harda gudunmowar shi wajen Batar-da- Amrah, Saleem sosai yake jin tsanar Anas da ya dage yana fadin yana son Amrah, ji yake kamar ya kama Anas ya yi masa dukan kawo wuka. Saleem cikin gajiya da karan kidan wayar nashi ya daga wayar tare kallon Number din wayar mtsweee yaja karamin tsaki tare da yarda wayar kan hannun kujera da yake zaune, Saboda bakuwar Number ce shi kuma baya daukar bakuwar number, Sai dai tuni duciyarsa ta tunatar da shi Halin da yake ciki na batan sahibar shi kowani Number halak ce a gareshi ya amsa, hakan kawai ya ji zuciyarshi na gargadinsa daya dauki wayar, Kamar ba daiyi magana ba yace hye !! What ya fada da sauri ya mike Gabadaya

Chapter 5 of 10