Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 10
maganar Gojen ya yi, Ahmad ya matse wayar a kunnen sa tare da Murmushin Mugunta. A ran sa ya fada dama wannan ranar nake jira dan nasan zata zo amma a fili sai Ahmad ya bushe da dariya Tare da furzar da iska daga bakinsa Alhajin Allah na san zaka neme ni, ba saboda komai ba sai saboda hajar ka da take hannuna na. Ahmad ya kuma bushewa da Dariya Sai dai nayi mamakin da kayi jinkiri wajen nema na dan hakan ina maka Albishir da ni *Ahmad Fiya-fiya* na rubanya Farashin/ka, Tuni 48 ง AKWAI KURA 2 hajarja ka ta zamo tawa ma'ana Yarinyar ka Ta Zamo mallakin Ahmad. Rasssssss! Gaban Alh. Musa dan chanji ya fadi an zo wajen ya fada da karfi tare da Neman kujera ya zauna dan ba zai jure sauraron maganar da suke yi a tsayeba saboda Firgicin da yake cikinta. Amrah Tun wayewar garin yau gaban ta yake ta faduwa Ita kanta bata san me yake damunta ba, sai dai daga bisani ta Allaka damuwarta akan tsarkin data samu wayewar garin yau, tuni ta yi na'am da abinda zuciyarta ta tunatar da ita, tabbas Taji tsoron samun tsarkin nata ba dan komai ba sai saboda takadirancin Ahmad. Ita kanta tasan in har ya farga ta samu tsarki to fa Allah ne kadai zai kare ta daga sharrin Ahmad, daga karshe ta yanke hukuncin komai rintsi yau zata tsere daga cikin gidan Ahmad koda baza ta tsira da rayuwar ta ba tabbas za ta yi yunkurin hakan in ta yi ruwa Rijiya. Kaurin indomien da ta daura ne ya dawo da ita hayyacinta da sauri Amrah ta sauke Indomien ta juye a filet din tangaran, dafaffen Kwai guda uku ta dauko a cikin tukunya da ta dafa ta hau 6arewa, tana gama-6arewa ta-jera-a gefen indomie, Flask din ruwan zafi ta dauko tare da neman madaidacin tray ta jera a kai, cikin nutsuwa ta dauki indomie din da niyyar kaiwa Ahmad a falo kamar yadda ya yi mata umarni. Chak Amrah ta tsaya jin sunan Dan Chanji da Ahmad ya kira a hankali ta fara komawa da baya Cikin Ikon Allah ta koma kichin da sauri ta ajiye tray din dake hannun ta Matattakalar benen ta haura cikin sauri ta kai ga dakin da yaran shi ko in ce yan daban sa masu masa aiki, cikin ikon 49 AKWAI KURA 2 Allah ta samu dukkan bacci suke da alamar ko sallah babu wanda ya yi a cikinsu. Da sauri ta janye kofar window tare da sanya kan ta tana hango tazarar dake tsakanin ta da Kasan dakin, Amrah ta runtse ido tabbas in ta fado nan raga raga data kakkarye, da hanzari taja windon tare da canda tunani, wayoyin su dake makale jikin charji ta sanya hannu ta dauki daya a ciki. Tare da fita daga dakin a hankali take takawa har ta iso falo in da Ahmad ya cigaba da wayarsa yana dariyar mugunta, da sauri ta shige dakinsa direct kasan gadon ta shige cikin sauri ta dauki bindiga, Sanyi taji a ranta ganin Akwai harsashi a ciki da saur ta soke bindigar ajikin wandon, Bata tsaya wani tunani ba Amrah ta tun kari bakin get din gidan gadan gadan. **** Cikin bakin ciki tare da kulewa da dariyar da Ahmad yake masa, Bai san lokacin da ya daka masa tsawa ba Shashasha ka saurare ni, Dan Chanji ya fada cikin ihun Masifa. Ahmad dake kyalkyala dariyar mugunta ya ji kalmar *Dan CHANJI* ta doki dodon kunnuwansa tuni ya ji ran sa ya baci, wani tukukin bakin ciki ya ziyarci zuciyarsa, shi ma cikin Fada ya amsa In saurare ka akan me? maganar daya ce ni da kai gaba ce ta har abada, Ba gudu ba ja da baya ka fito filin yaki, mu fafata Sai dai alamun nasara sun fara nuna yar manuniya cewa ni ne da cin gasar, kuma ni ba dan cikin ka ba ne da zaka dinga daka min tsawa, please Mantain ur self ya fada tare da kokarin katse wayar. Shima dan chanji cikin bacin rai ya cire wayar daga Kunnensa yana kokarin kashe wayar, da sauri Goje ya yanke musu hanzari Oga rike waya Maigida Bata kai ga nan ba kubani 1 minute Alfarmar Annabi Muhammadu, duk 50 AKWAI KURA 2 maganar da suke tun dazu yana sauraron su kasan cewan shiya hada confrence call din. Ganin wayar zata kare bai samu Alkawarin Dubu 100 da Dan chanji ya masa Alkawari ba cikin sauri ya yanke shawaran katse musu hayaniyar, ya damo dole ya sasanta maganar da suke, musamman daya fara hango Ahmad yana so ya masa asarar dubu dari chas da Dan Chanji ya masa alkawari kafin kiran wayar, cikin muryarsa ta mashaya ya fara Magana. Oga kaina a kasa kai min alfarmar sauraron Maigida dan nasan ruwa baya tsami banza fa Oga, Harkallar dayace Mu duka watarana ai za ai wa juna rana, Oga ka ankare. Ahmad ya sassauta-murya-ina-jinka -Alhajin Allah *Dan Chanji*. **** Bakin get din Amrah ta tunkara, cikin jarumta da rashin tsoro, Amrah ta riga ta kuduri aniyar barin gidan kota halin kaka musamman da ta san yau karyar ta ta kare, asirin ta yau ya tonu ga daukacin mazauna gidan Ahmad, Cikin sauri ta dunfari get din zuciyarta cike da rashin tsoro, ta riga ta shirya duk abinda zai faru ya faru wajen barin ta gidan. Cikin ikon Allah babu kowa a bakin get din mamaki sosai ta yi tare da murnar hakan, a fili ta furta Alhmdulillah, Cikin sauri ta yi hanyar fita mai gadi kadai ta hango zaune kan benci yana sauraron kida a wayarsa tare da kada kai alamar wakar ta yi gaba da imanin sa. katoton inyamuri ne kakkarfa mai cike da Rashin tsoro fuskar sa daka gani zaka hango rashin imani a tare da shi, Amrah ta kuma lekawa da kanta karo na biyu bakin get din 51 AKWAI KURA 2 ta kalla dan nemawa kanta mafita, get na rufe sai dai karamac kofar shiga da fita a wangale tame Amrah ta yi murmushi ganin hanyar fita a free lolz ðÝ €. A hankali ta koma ta labe jikin mota tana hangoshi, mai gadi yana kada kai yana jin dadin wkaar daga karshe ma mike wa ya yi ya bar wayar akan benchi ya fara taka rawa, gabadaya ya shagala yana tikar rawa tare da bin wakar cikin muryansa mara dadin Sauraro. kamar kiftawar ido Amrah ta fice daga gidan sam mai gadi bai lura ba sai da Amrah ta fita daga gidan kafin mai gadi Yaga alamu kamar giftawar inuwar mutum da sauri ya daina rawar tare da leka kansa bakin get ta waje sai dai bai ga komai ba, babu alamar wani a wajen kofar ya rufe ya koma mazauninsa tare da cigaba da sauraron wakarshi yana kada kai. **** Bakin get din Amrah ta tunkara, cikin jarumta da rashin tsoro, Amrah ta riga ta kuduri aniyar barin gidan kota halin kaka musamman da ta san yau karyar ta ta kare, asirin ta yau ya tonu ga daukacin mazauna gidan Ahmad, Cikin sauri ta dunfari get din zuciyarta cike da rashin tsoro, ta riga ta shirya duk abinda zai faru ya faru wajen barin ta gidan. Cikin ikon Allah babu kowa a bakin get din mamaki sosai ta yi tare da murnar hakan, a fili ta furta Alhmdulillah, Cikin sauri ta yi hanyar fita mai gadi kadai ta hango zaune kan benci yana sauraron kida a wayarsa tare da kada kai alamar wakar ta yi gaba da imanin sa. katoton inyamuri ne kakkarfa mai cike da Rashin tsoro fuskar sa daka gani zaka hango rashin imani a tare da shi, Amrah ta kuma lekawa da kanta karo na biyu bakin get din 52 AKWAI KURA 2 ta kalla dan nemawa kanta mafita, get na rufe sai dai karamae kofar shiga da fita a wangale tame Amrah ta yi murmushi ganin hanyar fita a free lolz öYE. A hankali ta koma ta labe jikin mota tana hangoshi, mai gadi yana kada kai yana jin dadin wkaar daga karshe ma mike wa ya yi ya bar wayar akan benchi ya fara taka rawa, gabadaya ya shagala yana tikar rawa tare da bin wakar cikin muryansa mara dadin Sauraro. kamar kiftawar ido Amrah ta fice daga gidan sam mai gadi bai lura ba sai da Amrah ta fita daga gidan kafiın mai gadi Yaga alamu kamar giftawar inuwar mutum da sauri ya daina rawar tare da leka kansa bakin get ta waje sai dai bai ga komai ba, babu alamar wani a wajen kofar ya rufe ya koma mazauninsa tare da cigaba da sauraron wakarshi yana kada kai. **** Wace haja kake magana kar dai kace min hajar dama ba taka ba ce? To lallai in har hakane kace AKWAI KURA Sharrin 'ya mace da yafi na shaidan ta rufta da kai, Ahmad cikin firgici ya zabura tare da mikewa tsaye ban fahimce ka ba? Fitar da ni daga duhu domin ina hada abu daya yana bani dari. Dan Chanji tuni hankalinsa ya yi bala'in-tashi shi ma cikin Tsoro yake magana kashin mu-ya bushe ka cuce mu ka gama damu, asirin mu da ke rufe tsawon shekaru yau ka buda mun shiga 3, ya cigaba da magana cikin fada kai ne mafita Ahmad kai ne Zaka warware matsalar cikin ruwan sanyi, i knw kuna tare da ita yanzu please Ahmad Do something i will gibe u anytin u want. 53 AKWAI KURA 2 Ida. yarinyar nan tabar gidan ka a raye mun kade har ganyen mu, ni da kai har duk masu harka damu, Ahmad ya katse shi dama wai ba yarinyar ka ba ce? No Ahmad Ina da labarin hukuma sun wakilta mace kan bincike daga majiya mai karfi, tun lokacin da na samu labarin na bada kwangilar a kashe ta sai dai kash yara na sun gaza wajen kawar da ita, a tare da haka kullum suna cikin farautar rayuwarta. idan kwakwalwar ka tana ja ba kwakwalwar kifi ce da kai ba yanzu nasan ka gane lissafin, No Ahmad ya fada yana ihu No, impossible, She is there i will kill her now now, Bai saurari amsar da dan chanji zai bashi ba ya kashe wayar tare da tunkarar kichin cikin zafin nama, sai dai wayam bata kichin, cikin sauri ya haura sama dakinsa nan ma bata nan bandaki ya bude ko tana ciki sai dai babu ko alamarta. karkashin gado ya daga da niyyar daukar bindiga abun mamaki babu ajiyar ta sa, Cikin zaro ido da damuwa Ahmad ya dafe kai cikin sauri ya bude durowarsa wata bindigar ya dauka, ya bar dakin tuni ya gaskata maganar da dan Chanji ya fada masa akan Amrah, Da gudu ya bude dakin yaransa bindiga ya harba sama da sauri a tare suka farka daga bacci, cikin fada yake sanar dasu su fito Akwai damuwa. **** Tun da Amrah ta samu nasarar fita daga gidan Ahmad da gudu ta arce, ita kanta ba ta san in da ta nufa ba gaba jeji baya jeji, A rikice take direct gabas ta nufa tare fatan dacewa da alkharin dake gabas din, Sosai ta samu balance wajen gudu kasancewar tun da tazo gidan Ahmad bata da sutura sai 54 AKWAI KURA 2 riga da wando kamar yadda Ahmad din ya fita ya sayo mata, a cewar sa shigar yake so ya rinka ganinta da shi. Sai dai abinda bai sani ba dama can ita gwana ce wajen dress na kananan kaya gashi yau shigar tai mata rana, in zani ne ko skirt ba ta san ta yaya zata fara gudun ba, kamar daga sama taji alamun ana biyo bayan ta dan rage gudun ta yi tare da juyowa bayanta dan ta tabbatar da hakan aiko da sauri ta kara kaimi wajeb gudun, daga can nesa ta hango alamun ana biyota a bata. Gata can Oga daya daga cikin yaransa ya fada Ahmad cikin karaji yace dasu ku kara gudu Kai Mai malfa in ta kama ku harbe ta babu matsala, gabadayan su har Ahmad suka kara kaimin gudu tare da son su cimma ta, Amrah gudu take falfalawa bata san in da take sanya kafarta-ba-ko kadan bata damuwa da kaya da take soke tafin kafarta ba wanda tuni kafar ta ta fara zubar da jini kasancewar jikin ta bai saba shan wuya ba, sai dai ko a jikinta illa ma kara kaimin gudun da take burinta daya shine tai misu fintinkau sai dai ina da alamu sun kusa cinmata. Abin ka da mace da kuma wahalar gudu da Amrah bata sa ba ba kafar ta ce ta- fara sarkewa tare da numfashi mai wahala, tsananin kishin ruwa da gajiya sune suka hadar mata lokaci daya, A hankali ta fara rage gudun ta fara rage karfin gudun tari ne ya fara turnike ta Amrah ta rike ciki tana matsawa kafin kace kwabo t. fara kelaya amai, yi takeyi sosai babu kakkautawa..... **** Da sallama Zahra ta ku tsa kanta falon Mommy dake bayanta ita ma sallamar ta yi tare da bin bayan Zahra cikin falon Ummy dake daune kan dinning table ita da Abban 55 AKWAI KURA 2 Amlah suna breakfast sai yan uku dake tsaye rataye da jaka Zasu tafi skul, Ummy ta amsa sallamar fuskanta cike da fara'a tare da fadin Bismillanku gaskiya kun iya sammako ta fada cikin wasa, Mum ta yi dariya Alhmdulillah sai da mukaci muka baro gida, kuyi hakuri mun doka muku sammako ko breakfast ba ku yi ba mun dirar muku a gida. Ummy ta yi dariya Wallahi ba komai ai samun bako da wuya, bismillah ku zauna hajiya Ummy tace, bayan sun dauna ido ta mayar kan yan uku Oya ku je direba yana jiran ku. Kuje kada ku makara, Bye Ummy Bye Abba gabadaya su ukun suka fada kafin suka Fice daga falon domin tafiya skul. Mommy da tun shigowarta falon ta yi arba da yaran, sosai suka burge ta tare da bata sha'awa tabbas kamar su daya da Abbansu, haka tana kallon matashiyar matar gidan anan taga kama sosai ita da Amrah ko tantama babu ita ce mahaifiyar Amrah. Da sakin fuska Mommy ta gaida Abban Amlah, ya yin da Ummy ta gaida Mommyn Zahra ce ta mike daga mazauninta, Ita dawo kujera kusa da Ummy cikin sakalci ta gaida Ummyn tare da tambayarta, Ummyn mu ina bestyna? yau fada nazo muyi inji dalilin da yasa ta kashe wayarta ehee, Ummy taji gabanta ya fadi amman sai mazeee Tare da kirkiro murmushi tace Zahra ai kunfi kusa da Amrah sai dai kinyi rashin dace Amrah din tana gurin aiki. Mommy ta yi dariya tare da sanya musu baki AMRAH bata gurin aiki wannan shi ne dalilin da yasa nazo takanas ta kano, gida domin in duba ko lafiya? Saboda last tym, da bata zo aiki ba ta sanar da ni bata da lafiya, shiyasa yanzu 56 AKWAI KURA 2 da naga ta yi 10 days bata doba na yanke shawarar biyo ta gida inji lafiya? gabadayan su suka kalli Mommy daga Zahra har Ummy shi kanshi Abban Amlah da ya kasa tashi akan dinning, tun shigowar su ya ji gaban sa ya fadi shiyasa bai tashi ya bar falon ba haka kawai yake jin faduwar gaba na zuwan bakin musamman daya gansu da sassafe. Innalillahi wa inna ilaihirraji'un !! Ummy ta-fada tare da dafe kirji na shiga Uku, Kuka ta fashe da karfinta Dama zuciyata bata yarda Amrah tana cikin lafiya ba wayyo ni na shiga uku na kasa rike amanar marainiya, da gudu ta yi wajen dinning Abban Amlah daya gama jin komai cikin tashin hankali ya riketa Amma sai ta fusge sakeni ka fada min inda ka kaimun 'yata? Wallahi tallahi Amrah ta rasa ranta kan wannan banzaan aikin naka Sai nayi shari'a Dakai, Wayyo na shiga uku ta fada tare da kwalla kara luuu ta yanke jiki ta fadi..... **** "Subhanallah, Mommy ta fada tare da rike Ummy data suma, Ihu Zahra tasa tare da fashewa da kuka mai tsuma zuciya shi ko-Abban Amlah girgiza Ummy yake kamar mahaukaci da alamar baya cikin hayyacinsa, kiran sunan ta yake da karfi Zainab karki mun hakan ki taimakeni ki saurareni Zainab banyi hakan dan in cutar da Gudan jinin ki ba. Ni ma ai nasan dadin yara kuma nasan zalunci haramun ne a musulumci Zainab koda zan cutar da wani to wallahi ke bazan miki ba, please ki-saurare ni in miki-bayani nasan zaki fahimta ki saurare ni Ummyn yan uku ta fada tare da kara jijjigata sai dai Ummy ta yi nisa ba ta san meke faruwa ba. 57 AKWAI KURA 2 Da sauri Mom ta saki Ummy tare da bude firinji ta dauko ruwa bakin goran ta bude duka tare da watsawa Ummy duka a jikinta, sai dai Ummy bata farka ba ganin hakan Zahra ta kuma fashewa da kuka. Da gudu Zahra ta yi waje tana ihu, wayyo Allah kuzo ku taimakemu, Saleem da tun dadu yake jin kamar alamae hayaniya a gidan da sauri ya bude murfin mota ya fito da sauri shima Maheer ya rufa masa baya, da gudu suka shiga falon shigar su ya yi dai dai da bude idon Ummy a zabure ta mike cikin second daya ta tuno da meke faruwa aiko da gudu ta kuma tunkarar Abbban Amlah tana ihu ka fito min da yata, Wallahi tallahi Usman ka salwantar mun da ran Amrah sai na kashe duka yaranka sai nayi shari'a da kai har kotun koli wayyo na shiga uku..... ***** Mommy ta yi tari Ummy tana Rarrashin ta sai dai Ummy ina bata san in da hankalin ta yake ba saboda damuwa, sosai ta cigaba da kuka iya karfin ta. Yi take tana fadar maganganu masu kaushi game da Abban Amlah da alamar bata cikin hayyacinta, Maheer da Saleem Kallon - kallo suke wa juna fuskar su cike da son karin bayani, Ummy ko kuka take bata jin lallashi tare da cigaba da aiba ta mijin nata a cikin surutun da take nan take Gabadayan su suka fara daukan haske kan inda maganar ta nufa, Amrah ta bata, Zahra ta fada da karfi, Wayyo na shiga ukuna besty ina kika shiga? wayyo na banu sautin kukan ta kara tare da faduwa akan kafet tana burgima. Can kamar an tsikare ta ta mike da gudu ta karasa gaban Maheer, hannun shi ta rike tana kuka baby In hakane muna da alhaki ciki batan bestyna, ranar mune mu kazo har gida 58 AKWAI KURA 2 muka dauki Bestyna da niyyar zuwa shopping baby ranar Abun ya faru ta fada tana kuka Baby help mie wayyo ni ina dan saka kaina?" Salecm ya zare Ido cikin tashin hankali yace ban fahimta ba matar tawa ce ta bata sai kace Allura? Ban fahimce ku ba? Maheer ya rike shi ganin yadda yake karkarwa yana shirin fitina, Zahra ta kalleshi matar ka ta a ina? besty matar Yaya Anas ce ta fada tare da kara sautin kukan ta, kamar mutum mutumi Abban Amlah ya damo a falon saboda tsananin tashin hankali ya rasa ta ina dai fara ya yin da Zainab take kuka kamar data mutu. Kamar walkiya Saleem ya yi tsalle ya dira a gaban-Abban Amlah cikin fitina yake magana Ka fito min da matata ko in harbe ka bindiga ya ciro tare da shako wuyan abban Amlah, Maheer ya yi Tsalle ya rike hannun Saleem tare da kokarin kwace bindigar a hannun shi, Amma ya kasa cikin bacin rai Mommy ta saki Ummy, ji kake tas - tas ta/gaurawa Saleem kyawawan mari hagu da dama, Saleem ya saki bindigar yana kallon Mommy da sauri hawaye ya fara zarya a fuskar Mommy Son baka da hankali ne ? yaushe ka zama haka? **** Cikin fada Mommy take magana Son ashe baka da hankali, da girman ka da wayonka kake abu sai kace jahili, wannan uba ne ga Wacce kake ikirarin kana so in banda rashin hankali irin naka maganar ai ta gida ce bata shafe ka ba muda muka zo neman iri sai kuma mu bige da fada da manya, Kayi na farko kayi na karshe karka kuma wannan shirmen. Ummy ta katse Mommy cikin kuka tare da fadin Hajiya barshi ya masa rashin mutumci, barshi ya tuhumeshi domin 59 AKWAI KURA 2 yau ya tabbtar min shi ba mahaifin Amrah bane, nayi imanin uba da yasan darajar haihuwa ba zai kai yarshi ga halaka ba bare har rayuwarta ta salwanta, to bari kaji a wannan lokacin ba dan taba daga maka kafa ba Usman wallahi tallahi duk inda diyata take kayi gaggawar fito min da ita kafin muje ga hukuma, kuma ina mai tabbatar maka da cewa duk wani matsala da ya samu Amrah, ba dan barka ba sai kotu ta karbar mata hakkinta. Abban Amlah ya katse ta cikin fada Zainabu ni kike fadawa wannan magangunan ? kin fara shaye shaye ne nine fa Mijinki uban yayanki, aiko dan darajar yayan dake tsakanin mu, zaki saurari uzurina wallahi tallahi koni mugune bazan cutar da Amrah ba koba komai taci darajarki da muke daman aure harda karuwar ya ya a tsakaninmu dake. Ummy ta cigaba da kuka tana fyace majina a baya ka yaudareni da kalamai irin wannan har nayi sakacin yarda da kai amma fa kasani a wannan lokacin dai dai nake da inyi sharia da kai har kotun koli akan diyata, inda alkhairin kake nema mai ya hana ka sanya taka diyar? Sai tawa ce bata da gata saboda ka ganta marainiya? ***** To wallahi tun kafin duniya ta jimu ka fito min da diya ta domin nasan kasan in da Amrah take bisa ga hujjar da kai ka sanar da ni, wannan karon Abban Amlah bai kara maganaba sai ido da yake bin Ummy tare da ajiya zuciya na bacin rai Mamaki tabashi sosai na yadda ta todarta shi a gaban baki, Sosai Ranshi ya baci na rashin bashi damar kare kanshi da Ummy ta yi. Saleem tun da Mom ta yi magana ran shi ya kara baci bai sake cewa komai ba daga karshe kamar kububuwa fuuu ya 60 AKWAI KURA 2 fita dada falon, Direct mota ya fada yana sauke mumfashi, Maheer da sauri ya bi bayan Saleem zuciyar sa cike da damuwar wannan badakala, Salcem yana ganin Maheer ya fashe da kuka mai cike da tausayi, tare da fadin No wonder ashe mata ta tana cikin hadari shi yasa Allah ya sanar da ni ta hanyar mafarki, Abokina wake son ganin bayana da mata ta? Tabbas hakuri na ya kare zan iya jure a taba raina sai dai har abada ba dan daga kafa Ga wanda ya taba iyalina ba; Oya tada mota muje Koma waye yau Ya tada *KURA* nayi imani saina buleshi da kasa Mace ko Namiji, Oya Muje ya fadawa Maheer cikin fada, tamkar Maheer din shi ke da alhakin laifin. **** Jin karar tashin mota ya sanya Mummy fitowa da sauri Mommy ta fito daga falon ga mamakin ta Motar Saleem ita ce ta futa daga get din, Mom- ta yi-ajiyar zuciya tare da tausayin danta, Ko bata tambaya ba tasan Saleem na cikin tashin hamkali. Tana sa ne ta zage shi tass a gaban mutane dan kaunar da take ma danta baza ta iya ganin-ya baci ta kau da kai ba, ita din uwa ce ta gari mai son yayan ta da basu kulawa still kaunar bata rufe mata ido da data ga hani kan barna ta yi shiru ba, uwa uba Abun da ta yin shi zai kare kimar ta a gun Iyayen Amrah, wannan ya nuna Saleem na da tarbiya bacin rai ya sanya ya aikata abunda ya yi a gidan. Ita kanta Mommyn tana cikin damuwa na rashin sanin ainahin inda Amrah take, sosai take cikin dimuwa tun da Ta farga da Abunda yafaru da Amrah wayar ta ta dauko a jaka 61 AKWAI KURA 2 ta kira Numbern daya daga cikin direban gidansu tare da masa kwatancen inda zai zo ya dauke ta. A hankali ta juya cikin gidan dan tai musu sallama, Koda ta koma falon Ummy bata daina kuka ba hakan Zahra shima maigidan yana tsaye ki kam kamar Nonon Maza lolz, inda ta barsu hakan ta kuma tarar dasu, Mommy ta yi gyaran murya cikin nutsuwa ta fara yiwa Ummy nasiha kan ta kwantar da hankalin ta, su bi komai a hankali ta wannan hanya shine zasu Fahimci juna har a kai ga Cimma burin ganin Amrah. Haka shima Abban Amlah nasihar tai masa tare da bashi hakuri kan abinda ya faru, kuma tana bashi shawarar su zauna su fahimci juna fitinar ba ita ce zata fito musu da Amrah ba, Daga karshe tai musu sallama tare da alkawarin itama da danta zasuyi iyakar kokarin su wajen neman Amrah. ***** Cikin kuka har da majina ta shigo gidan, da gudu ta fada dakinta tana kara sautin kukanta, Granny dake zuba zobo a jarka da sauri ta mike lafiya Zahra'u? Waye ya mutu ta fada tana zare ido, Zahra ta cigaba da kukan ta tana Ihu kamar wadda uwarta da ubanta suka mutu. Granny data gaji da lallashi kan meke faruwa har ranta ya fara baci, cikin kufula tace kya yi ki bari a koke Ke ni fitamin a daki kin isheni da ihu tun da bazaki fada min abinda ya faru ba sai kace gidan mutuwa, Yo inma mutuwar akayi ai kya sanar da ni, Ni nan da kika ganni tun ina tsumman goyo Ubana ya mutu haka mijina da yarinta ya bar duniya, ga Amaduna Ina sonshi mutuwa ta dauke shi, Mutuwa ai mu mun jima muna ganinta. 62 AKWAI KURA 2 Zahra ta harari Granny tare da share hawaye, Granny ke mutum ma na cikin damu wa bazaki rarrashe shi ba sai fada, To naji kin saba ganin mutuwa Amman ai baki taba ganin na Bestyna ba, Granny ta ajiye jarkar zobon kaji ja'irar yarinya yau kuma da fatan tsiya kika zo ? Maza zoki fice min daga daki tun kafin in man gareki, Yo aiko mutuwar ba zata rabani da Zainabu na yanzu ba sai naga yaya da jikokinta, Zahra ta kuma fashewa da kuka jin anyi maganar Bestyn ta, cikin kuka ta sanar da granny abunda ya faru. Iya ta dafe kirju tana salati Inna lillahi wa inna ilaihirrajiun !. Tuni ta fashe da kururuwa tana kuka, ya yinda Zahra ke ta ya ta kukan itama cikin ihu, Usmanu ashe sharrin daya kulla kenan Abunda Usmanu zai min kenan, Wayyo Ahmadu Usmanu ya ci amana Allah ya isar mana Allah ka tona asirinsa Zahra'u, Tashi muje ki rakani barikin sojoji yan sanda sunyi kadan wajen matse Usmanu ya fito mun da jikata, maza tashi muje-Yau mai-raba ni da Usmanu sai Allah. kai duniya ina zaki damu, ashe makashinka yana tare dakai Wayyo Yar marainiyar Allah, Allah ya isar mana.... ***** Saleem Da Maheer suna fita daga gidan Ummy, Saleem ya kira wayar

Chapter 4 of 10