Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 9
shi akansa, nan takedutsen a fashe ya tarwatse ya zamakamar kasa kura ta turnuke ta tashisama, ta sake fusata ta yunkura kansa tare da wata irin iska mai karfi ta sure shi ta makashidakasa,itacen da yake hannunsa ya fadi gefe ta sanya kafarta ta taka kafadarsa ta daga sandar ta za ta narka masa bugu a tsakiyar kansa ta hallaka shi, Muzaffar yay i kokarin kwacewa daga gareta,ammay aji ya kasa kodamotsi bare ya ture kafarta daga kansa,yana ganin sanda ta daga sandar zata hallaka shi amma bashi da ikon gocewa sai dai ya rintse idanunsa ya saduda yana jiran abin da zai wanzu gare shi, tare da nadamar abin da ya aikata na mantawa da maganar da dattijo Zarkiyu ya umarce shi da kiyayewa, nadama mara amfani gare shi a lokacin da takeshirin zuwa a gareshi. Kafin sandar ta sauka akansa Dattijo Zarkiyu dake kokarin kawo masa dauki yay i sauri ya sanya kibiyar cikin azama da zafin namaya harbeta a tsakiyar kirji,tsinin kibiyar ta huda kashin hakarkarinta ya fito a bayanta, tsohuwar nan ta yi wata irin kadaitacciyar karamai tsananin karfi da ban firgici sannan ta yi sama akan iska saboda karfin harbin kibiyarta tarwatse sassan jikinta ya watsu a kasa yana ci da wuta nan take ta hallaka. Da ganin abin da ya faru ga wannan tsohuwar sai ragowar ayarin da suke tafe tare da ita sukayunkuro cikin karaji da gunji fusatuwa suka taso kan Muzaffar da dattijo Zarkiyu da nufin hallaka su, kamar yadda suka hallaka wannan tsohuwa Muzaffar yayi sauri ya tashi ya dauki makaminsa tare da salkar ruwansa dake yashe a kasa ya daureta a damarar ya ja daga cikin jarumta da karfin zuciya yana mai sauraron karasowar wannan jamaʼ'a gare shi, shima dattijon zarkiyu ya zare takobinsa ya karaso kusa da Muzaffar suka tari wadannan tawaga baki daya akasomakafsawa,nan takewaje ya 96 harafi Tafiyar ajali hargitse kura ta tunuke ta tokare sararin samaniya, Muzaffar na kai bugu da fekakke itacen da yakehannunsa duk wanda ya samu koya soke shi da tsinin itacen sai ka gay a wafcewani sashi daga jikinsakamar saran takobi ya haklaka shi. Shii kuwa Dattijo Zarkiyu saransu kawai yake yi da takobinsa cikin tsananin kwarewa da jarumta duk wanda kaifin takobinsa ya sauka akansa sai ka gayatsarge shi gida biyu kokuma ya sare wani sashi daga jinsa, ya hallakashi duk inda yak eta tsakanin wadannan runduna sai dai ka ga gawarwakinsu suna zuba kasa matattu tamkar busassshen ganyen bishiyar da guguwa ta zubo da shi kasa. Haka suka dauki lokaci mai tsawo suna gabza artabu dda bakin gumurzu mai tsananin a tsakaninsu da wadan nan tawagar jama'ar aljanu da suka juyo garesu, amma babu alamar zasu kare bare su sa ran zasu sasmu nasara akansu saboda tsananin yawa tamka ba daga cikinsu suke hallakawa ba. Da dattijoZarkiyu ya ga haka sai ya maida takobinsa cikin kubenta ya fiddo kwari da bakaya sanya kibiya ya harba tsakaninsu kibiyar ta tafi kan iskatana ci da wuta ta tunkare su,su kuwa da sukaga hakasai suka tarwatse sukaba ta waje ta wuce ta tafi ta samu jikin wani katon tsauni dake kusa da wajen ta nutse a cikinsa,tsaunin yay i wata irin kara mai sananin karfi da ta yi amsa kuwa da amo mai hauhawa da ya gauraye dukkanin dajin sannan ya fashe kura da wani irin bakin hayaki suka dunkule suka tashi sama kan iska nan take wajen ya gauraye da duhu mafi tsaanin daga yankinduhu dare sannan sai sukadaina jin hayaniya da hargowar tawagar da suke kafsawa da su. Bayan ani lokaci kurar da ta turnuke wajen ta lafa sais u Muzaffar suka ga babu jama'ar aljanu da suke kafsawa da su a wajen daga su har gawarwakin wadansa su Muzffar suka hallaka, alamar sun bace daga wajen sun a da baya saboda razanar da suka yi ta jin karar fashewar wannan tsauni, bayan wani lokaci da bacewarsu su Muzaffar da Dattio Zarkiy u suna tsaye a wannan waje basu sake jin motsin komaiba bare su ga wani daga cikin jama'ar aljanun nan ya bayyana garesu, alamar sun bar wajen don haka sai Zariyu ya maida kwari da bakarsa ya juya ya dubi Muzaffar cikin hasala da fusatuwa у ace da shi. 97 harafi Tafiyar ajali Kaicon wanda ya zama mai mantuwa da kauda kai ga barin abinda aka umarceshi da kiyayewa kai dai ka kasance daga cikin ma'abota shu'ummanci da wofintar da duk abin da na umarceka da kiyayewasai da na haneka da yiwa wani Magana ko kuma sauraron wani daga cikin wadannan jama'a tun a farkon marra, saboda kasancewar ba jama'ar mutane bane, kamar yadda kake zato, don babu wani mutum bil'adama kamar ka da zai iya shiowa cikin wannan tsibiri ya rayu batare da ya hallaka ba, amma sai ka zamo mai bijirewa abin da na umarce k aka aikata abin da kake ra'ayi na daga soye-soye zuciyarka, to ka sani cewa wannanshi ne laifi na karshe da zan iya yi maka afuwa daga cikin laifukan da ka aikata gare ni tunda muka fara wannantafiya tare da kai don haka matukar ka kara aikata kuskure ka bijirewa abin da na umarceka da aikatawa, to kuwa karshen tafiya tsakanina da kai yazo zan rabu da kai a cikin wannan tsibiri ka hallaka bа zan sake taimaka maka ba". Muzaffar yayi shiru kansa a sunkuya bai ce komai saboda kasancewarsa mai laifi na aikata abinda aka hanashi da aikatawa, daga nan dattijo Zarkiyu ya juya ya kama hanya Muzaffar ya bi bayansa suka ci gaba da tafiya a cikin wannan tsibiri. ** Shi kuwa Najiranu dan gidan Waziri Hawaisu tun bayan ruwan nan na aikin sihiri da yayinufin zubawa Gimbiya Zuhuriya ya kawo kansa ya zuba a jikinsaya fado daga kan dokinsa,baisake sanin abin da yake faruwagareshi ba, har Gimbiya Zuhuriya ta tafi ta bar shi a wanan waje tamkar sumamme, sai da ya dauki lokaci mai tsawo can da kusan faduwar rana sannan ya dawo hayyacinsa, ya dubi kansa ya ga halin dayakeciki ya ganshi yashe a kasa gefe guda takobinsa da kumagarkuwarsa suma gefe guda ga dokinsa tsaye a gefe, sannan bai gajarumin da sukekafsawa da shi ba, gashi har rana ta kusa faduwa alamar ya dade a wannan waje, nan take ya fahimci abin da yakefaruwa gareshi na rashin samun sa'a 98 harafi Tafiyar ajali akan wannan jarumi, bakin cikida takaicimara misaltuwa ya turnuke zuciyarsa ya tashi ya dauki takobi da garkuwarsa ya tafi ya kama dokinsa yah au ya kama hanyar komawa gida. Da isarsa ida ya tafi ga mahaifinsa Waziri Hawaisu ya sanar da shi abin da ya faru a gare shin a rashin samun nasara akan wannan jarumi karona biyu, mahaifinsa Waziri Hawaisu yayi matukar bakin ciki da takaici na jin wannan labari, ya sunkuyar dakansa kasa yayi shiru yana tunanin wani lokaci ya dago kansa ya dubi dansa Najiranu y ace da shi. "Haika mun yi rashin sa'a na kasa samun nasara akan wannan jarumi sai dai ba zamu zama masu nuna gajiyawa ba akan abin da muka sag aba har sai mun tabbatar da samun nasara, don haka zan nemi boka Musaila na sanar da shi abin da ya faru domin neman shawararsa akan wannan al'amari". Yana gama wannan bayani sai ya ciro zoben nan na sihiri da boka Musaila ya bashi, ya sanyashi a danyatsansa ya urza zoben tare da ambaton sunan Boka Musaila sau uku ba dadewa ba said akin da suke ciki yayi duhu mafi tsananin daga yankin duhun dare yadda waziri Hawaisu da dansa Najiranu bas a iy aganin junansu, bayan wani lokaci sai suka ji iska mai karfi ta keto cikin dakin ta shigo daga nan kuma sai duhun da ya gauraye dakin sai ga Boka Musaila ya bayyana a gabansu zaune akan buzunsa na aikin sihiri tamkar yadda waziri Hawaisu yake tarar da shi ad uk sanda yaje gare shi cikin bbukkarsa dake tsakiyar daji. Najiranu dake zaune kusa da mahaifinsa yay i matukar mamakin wannan al'amari da yake gani a gabansa tamkar mafarki,shi kuwa waziri Hawaisu da ya ga Boka Musaila ya bayyana a gabansu sai ya kai Gaisuwa gare shi riin ta girmamawa sannan ya ce da shi. "Girma da martaba ya tabbata gareka yahamshakin masani na alkaluman sihiri cikamakin bokaye da matsafa na wannan karni, ka sani cewa na bukaceka ne domin neman taimako a gareka kasancewarka ne abin dogaro a gareni cikin wannan lamari. 99 harafi Tafiyar ajali Ya kwashe labarin abin da ya faru tsakanin dansa Najranu da jarmi da ya tafi gareshi domin karbo takobin da take tare da shin a rashin samun nasara ya sanar dashi, sannan y ci gaba da cewa "Idan Njranu ya koma wajen Gimbiya ZUhuriya ba tare da wannan takobi bashi kenan maganar aure a tsakaninsu tarushe kamar yadda sukayi alkawari,kuma idan Najrau bai auri Gimbiya Zuhuriya ba, burinmu na mallakar sarautar birnin Ambar ba zai cika ba, don hakana dawo gareka domin neman taimako Da Boka Musailamatuyaji wannan bayani na waziri Hawaisu sai yayi shiru ya sunkuyar da kai kasa yana tunanin bayan wani lokaci ya dago kai ya dube shi y ace da shi "Rashin samun nasara danka Najiranu akan jarumi ba zai sa mu zamamarasa samun nasara akan shirin da muka yin a mallakar sarautar birni Ambar ta dawo hannunka ba, na rantse dagirman daraja kakana Boka fikilu da ya hallaka a wajen tabbatar da bautar gumaka da tsafi a doron kasa sai danka Najiranu ya auri Gimbiya Zuhuriya bisa alkawarin da suka yi idan ai mata takobin dake hannun wannan jarumi. Yana gama fadar wannan maganar sai suka ga wani farin haske maikama da hasken walkiya ya gifta ta gabansu sannan sai suka nemi boka Musaila suka rasa ya bace tareda bacewar wannan haske, waziri Hawaisu yay i kiran sunansa har sau uku baiji ya amsa ba bare ya sake bayyana a gare su don haka sukajinkirta suna masu sauraron su ga abin da yake shirin aikatawa. Bayan wani lokaci da bacewar Boka Musailamatu sai suka sake ganin farin hasken nan ya keto bangon dakin ya shigo ya fadi gabansu sannan sai suka ga boka Musaila ya bayyana a inda hasken ya sauka, har a sannan yana zaune akan bakin buzunsa na aikin sihiri sai dai ya daga hannayensa sama idanunsa a rue yana karanta wadansu dalasumai irin na alkaluman sihiri da tsafi,iskaai kaarfi ta keto ta shigo ta kofar dakin da suke zaune tare da wani duhu a tsakiyar duhun ya sauka akan tafin hannun Boka Musaila sannan sai ya daina 100 harafi Tafiyar ajali karanta dalasuman aikin bokancin da yake karantawa, duu da ya sauka akan hannunsa ya bace sai ga takobin wannan jarumi da Najranu ya kasa samun nasara karbo ta daga gareshi, ta bayyana kaan tafin hannunsa, marikar takobin tana haske da sheik saboda adon da aka yi mata na zinare. Boka Musaila ya buda idanunsa ya dubi takobin sannan ya dubi waziri hawaisu y ace da shi, wanan itace takobin da Gimbiya Zuhuirya ta ce da danka Najiranu ya karbo a hannun wannan jarumi ya kasa samun nasara a kansa, na sanya ma'abota hidima a garemu sun dauko takobin daga inda aka ajiye ta sun gabato da ita a gareni, saboda haka danka Najiranu ya karbi takobin ya tafi da ita ya kaiwa Gimbiya zuhuriya akan wannan aurensu kamar yadda sukayi alkawari, koda wannanjarumiya ce Najranu bai samu nasara akansa ba, hakika bashi da wata hujja tunda gashi ya kawo takobin gare ta,wadda it ace takobin da take hannunsa. Tun da takobin ta bayyana a hannun Boka Musaila Najranu yake dubanta cikin matukarmamaki da al'ajabi ya kuma tabbatar da cewa it ace takobin da ke hannun wannan jarumi da yakekarbota daga gare shi, bai samu nasara ba. Shi ma waziri Hawaisu ya cika da matukar murna farin ciki ya karbi takobin ya mikawa dansa Najranu. Najranu ya karba yana mai matukar mamaki tare da kara yin imani da karfin tsafi da sihirin Boka Musaila, daga nan waziri yay i masa godiya suka yi saama da shi ya bace cikin alkaluman sihirinsa ya koma inda bukkkarsa take tsakiyar dajin dake bayan birnin Ambar. Bayan tafiyar Boka Musailasai Najranu ya tashi ya komadakinsa tare da wannan takobi yana mai jiran wayewar gari ya tafi ga Gimbiya Zuhuriya take fita ambun mahaifinta tare da kuyanginta domin shakatawa, si Najranu ya shirya ya dauki wannan takobi ya nannadeta a cikin wnai farin yanki ya kama dokinsa ya hau ya tafi wannan lambu domin kaiwa gimbiya Zuhirya takobi. 101 harafi Tafiyar ajali Ita kuwa Gimbiya Zuhuriya tun bayan da ta bar Najiranu a bayan gari inda suke kafsawa ta koma gida, sai ta yi nufin ta bayyana masa abin da ta ganshi ya aikata na daga aikin sihiri domin ta tabbatar masa da cewa babu maganar aure a tsakaninsa da ita,kasancewarsa ma'abocin aikin tsafi da sihiri wanda shirk ace da bata mabayyana. Washe gari da yamma da za ta tafi lambun mahaifinta dominjiran zuwan Najranu gareta sai ta sanya kaya nan da take sakawa a duk sanda zata fita bayan gari su hadu da Najiranu sannan ta kawo wani farin mayafi ta rufe jikinta gaba daya yadda ba za a ga kayan da ta saka daga ciki ba, bata sanya hular karfe da take rufe fuskata da it aba sai da ta risketa a hannun sannan ta dauki gorar nan na aikin shiri da ta dauka daga wajen Najranu tare da zobensa na azurfa ta cire daga danyatsansa, domin su zama shaida ga abin da da zata bayana a gare shi, ta duba inda ta ajiye wannan takobi da ta umarce shi da cewa ya je ya karbo a hannun wannan jarumi,amma ba ta ganta ba, da yake takobin mahaifinta Sarki Sa'adulgamidi ce da ya gada a wajen mahaifinsa sai ta yi zaton cewa shi ne ya dauki takobin domin yin wani amfani da ita, kamar yadda ya saba don haka ba ta damu ba daga nan ta fita ta hau dokinta tare da suaran kuyanginta suka tafi wannan lambu kamar yadda ta saba. Bayan ta isa lambu ta zauna zaman jiran Najranu bada jimawa ba sai ga Najiranu ya iso tafe akan dokinsa, yay i shiga ta alfarma da sutura mai kyau, irin wadda 'ya'yan sarakuna da 'ya'yan attajirai suke sanyawa ya isa wajen da ake daure dawakai ya daure dokinsa sannan ya karasa gare ta hhannunsa rike da wannan takobin dake nannade a cikin farin yanki, ya nemi iso gare ta ta bashi izini zaman akan kujerar dake fuskantar ta ya zauna sukafuskanci juna ta yi mamakin ganinsa cikin sakin jiki da nuna rashin damuwa tamkar wanda ya samu nasarar karbo takobinsa da ta umarce shi da karbowa,kafin ta yi Magana sai Najranu y ace da ita. 102 harafi Tafiyar ajali "Da girman darajarki Gimbiya Zuhuriya tauraruwa a cikin 'ya'yan manyan sarakunan duniya,yau dai na kasance mai cika alkawari bisa ga abin da kika umarce ni cewa na je na karbo takobin da ke hannun Jarumin da ki ka turani gareshi, domin ki amince da maganar aure a tsakanina da ke don haka sai ki zama mai cika naki alkawarin da kika dauka tunda ni na cika nawa" Yana gama fadar wannan maganar sai ya warware farin kyallen dake hannunsa ya fito da takobin da take ciki ya mikamata. Gimbiya Zuhuriya ta dubi takobin cikin matukar mamaki tare da mamakin maganar da ya ambaa na cewa ya samu nasara akan wannan jarumi yakarbo takobin da ta ke hannunsa, ta karbi takobin ta rike a hannunta sai ta ga babu shakka takobinta ce da ta neme ta ta rasa a inda ta ajiyeta yau da za ta zo wannan lambu su hadu da shi, ta sake cika da matukar mamaki sannan ta kara tabbatar da cewa babu shakka akwai wani al'amari na aikin sihiri a cikin lamarinsa, kuma ya samu nasarar dauko takobinne ta hanyar aikin sihiri. Bayan ta gama duban takobin ta juya ta dubi Najiranu ta ce da shi "Kai dai ka kasance daga cikinmutane masu yaudara da ha'inci cikin lamarinsu, kuma ba ka zama mai samun nasara akan jarumin da na turaka gareshi ka karbo takobin dake tare da shi ba, sannan akwai alamar wanzuwar wani al'amarina kunshin aikin sihiri a cikin lamarinka,wanda aikata hakan shirk ace da bata mabayyani da nake fatan Allah ya tsare ni da kusanci da masu aikatawa.kuma koda ka samu nasarar karba takobin ta wannan hanya b azan amince na auri ma'abocin aikin tsafi da sihiri ba". Najiranu yay i farat y ace da ita "Ka da ki zama mara cika alkawari ko juya baya ga abinda kika ambata da farko bayan na samu nasarar karbo takobin da kika umarce ni da karbowa akan maganar aure a tsakanina dake kuma kada ki zama mai yin zato ko yadda da abin a wani zai fada na batanci da suka a kaina,kuma idan har wannan jarumi ne ya sanar 103 harafi Tafiyar ajali dake cewa ban samu nasara a kansa ba,to taw ace hanya na samu wannan takobin jar na kawota gare ki". Gimbiya Zuhuriya tace da shi "Ban zamo mai yadda da abin da wani zai ambata a gare nib a, illa dai abin da na gani da idanuna, ka sani cewa ba kowa bane jarumin da na turaka ka karbo takobin da take hannunsa face ni da kaina". Tana fadar wannan Magana sai ta mike tsaye daga kan kujerar da take zaune ta warware farin mayafin da ta rufe jikinta da shi sai ga akaken kayan tare da sulken yakin da take sanyawa a duk sanda zata fita tare shi idan ta ce da su ya je ya karbo takobin dake hannunsa wannan jarumi sannan ta dauko hular karfen nan da take sakawa ta rufe fuskarta yadda ba zai iya gane cewa mace ce ba ta saka nan take sai gashi ta zama tamkar yadda yake ganin wannan jarumi a duk sanda suka hadu da shi. Najranu yay i matukar razana da karayar zuciya saboda abin da ya gani, ya kuma tabbatar da cewa babu shakka gimbiya ZUhuriya ce takeyin wannan shiga ba wani jarumi daban ba kamar yadda yake zato da farko, nan takejikinsa yay i sanyi har ya rasa abin cewa saboda rashin gaskiya, ita kuwa Gimbiya ZUhuriya da ta gay a karaya sai ta cire hular karfen da take kanta ta ci gaba da cewa. "Hakika na san da cewa baka gane cewa n ice nake yin wannan shin a tafi na tare ka a bayan gari shi ayasa ka ambata cewa kasamu nasarar karbo takobin daga hannun wannan jarumi,kumasaboda ka daka gane hakan ne yasa bana yi maka Magana ko na maidamaka raddi aduk sanda mukahadu da kai ka yi Magana gare ni domin kada ka ji muryata ka gane ni kо gane cewa mace ce, kuma duk abin da ka aikata na daga cikin sihiri domin kasamu nasara akaina na gani idanuna ba wwani ne ya labarta min ba,kuma na taho da shaidar da zata tabbatar da hakan gareka a duk sand aka zo. Tana fadar wannan maganar sai ta sake dauko gorar nan na aikin sihiri tare da zoben azurfa da ta cire a hannun Najiranu sanda ruwan nan na aikin sihiri ya zuba ajikinsa ya fadi kasa, ya zama tamkar 104 Tafiyar ajali matacce, ta ajiye masaa gabansa ta ce da shi "Wannan shi ne shaida". Najiranu ya sake rudewa saboda rashin gaskiya nan take gumi ya soma keto masa ta ko ina tamkar wanda akajika da ruwa ita kuma gimbiya Zuhuriya sai ta ci gaba da cewa da shi "Hakika ka kasance mai aikata kuskure na fkawa cikin aikin sihiri da shirka domin neman samun biyan bukatarka to son ka aureni,wanda idan b aka nemi gafarar ubangijinka ba katba to kuwa kana cikin halin hallaka da bata mabayyani,kuma ka sani babu maganar aure tsakanina da kai tunda b aka samu nasarar karbo takobin da ta hanyar jarumta da bajintar k aba, sai ta hanyar aikin sihiri,don haka ka koma ka sanar da mahaifinka ka janye akan maganar aurena kamar yadda mukayi da alkawari da kai tunda farko idan har baka samu nasarar karbo takobin bа". Tana gama fadar wannan maganar sai ta juya ta bar wajen ta bar Najiranu a zaune ya kasa ko daga kansa ya dubeta saboda rashin gaskiya ta koma wajen da sauran kyanginta suke ta umarce su da cewa su ka kama dawakansu su hau suka fice daga lambun sukakama hanyar komawa gida. ** Byan Muzaffar da dattijo Zarkiyu sun ci gaba da tafiya daga inda sukahadu da wannan jama'ar aljanu a cikin wannan tsibiri, ba su sake tsayawa ko in aba si da suka kwana suka wuni suna tafiya sannan suka yada zango domin su huce gajiya. Da gari yaw aye a inda sukakwana bayan sun yi sallar asuba suka yi shiri suka ci gaba da tafiya a cikin wannan tsibiri, suka yi tafiya mai nisa har rana ta kusa faduwa sannan suka riski wani katon kogi ma'abocin girma da fadi, ruwan da yake cikinsa yana ambaliya da toroko idan iska ta ta kada da karfi sai ka ga ruwan yayi tsiri sama kamar tsauni ya tabo tamkar zai rufe doron kasa baki daya, sai ya zo gabar kogin sannan sai yayi kasa ya koma baya. 105 harafi Tafiyar ajali Ruwa da yake gabar kogn yayi ambaliya kan doron kasa, tun kafin su karasa bakin kogin Muzaffar ya duba iya ganinsa bai hangi gabar karshen kogin ba, da suka karasa bakin kogin sai suka tadda wasu jiragen ruwa kwale kwale ababen sassakawa da itace guda biyu a jiye a bakin kogin daya daga cikin jiragen sabo ne, alamun sa ba a dade da sassakashi ba, dayan kuwa tsho ne sannan jikinsa ya tsattsage yadda ruwa zai iya shiga cikinsa idan ana tafiya da shi a cikin ruwan kogin. Dattijo Zarkiyu ya dubi ruwan kogn nan sannan ya dubi Muzaffar y ace da shi "Babu wata hanya da zamu iya bi mu wuce wannan kogin har sai mun ketara ta cikinsa, kuma tafiyar kwanaki biyar zamu yi kafin mu ketare wannan koi, saboda haka za mu hau wannan irgin ruwan mu ketare wannan kogin a cikinsa, ya nuna daya daga cikin jeragen ruwan nan wanda ya tsufa tsiyarsu ya tsage yace da shi za su hau a cikinsa zasu yi wannan tafiya akan ruwa ta tsawn kwanaki biyar. Da jin wannan Magana ta dattijo Zarkiyu sai Muzaffar yadube shicikinmatukar mamakin ganin yadda wannan tsoho jirgin ruwan ya lalace tsakiyarsa ya tsage yadda ba zai yiwu su iya tafiya a cikinsa ba har tsawo kwanaki biyar su ketare wannan kogin matukar dai ba so suke jirgin ya nutse dasu su hallaka ba, ya dubi Dattijo Zarkiyu y ace da shi "Me yasa zaka ce mu shiga wannan tsohon jirgin ruwan wanda ya lalace tsakiyarsa ya tsage bayan cewa gas abo wanda bashi da wata illa a tare da si matkar dai ba kana so mu nutse a cikin wannan kogi mu hallaka ba. Dattajo Zarkiyu ya dube shi cikin fushi y ace da shi "Umarni nake baka akan maganar da na ambata ba ina neman shawara a gare k aba, kuma na hanake da yin 106 harafi Tafiyar ajali tambaya a garei akan duk abin da na umarce ka amma baka zama mai kiyaye wannan sharadi ba, kai dai ka zamo daga cikin mutane Bil'ada masu yawan tambaya da rashin kiyaye abin da ake umarta a kowane lokaci". Muzaffar ya sunkuyar da kai kas ayayi shiru kamar yadda yake yi a duk sanda ya yiwa dattijo Zarkiyu laifi ko kuma ya aikata kuskure har dattijo Zarkiyu ya juya ya tafi bakin kogin ya kama wannan tsohon jirgin ruwa turashi akan ruwa ya shiga cikinsa, shima Muzaffarya kama ya shiga dattijo Zarkiyu ya umarce shi da cewa yayi amfani da fekakken itacen da yake hannunsa ya tuka jirgin su tafi. Muzaffar bai yi masa musu ba, ko yayi tambaya a gare shi sai kawai ya aikata abin da aka umarce shi da aikatawa nan take jirgin ruwa ya soma tafiya da su akan ruwa suka kama hanya suka ci gaba da tafiya akan ruwan kogin wata irin sika mai karfi tana kadawa igiyar ruwa ta murda ruwan kogin yana ambaliya da tsira sama jirgin ruwan ya rika tangadi da tangal-tangal tamkarzai kife dasu su hallaka, wani lokacin sukan hangi ruwa yayi tsiri sama kamar tsauni ya taho ya nufo inda suke kamar zai rufe su su nutse kasa su hallaka amma idan ya zo usa da su sai ya dare su ratsa ta cikinsa su wuce ba tare da wani abu ya faru gare sub a. Haka suka yi ta tafiya a cikin wanna kogin wannan kogi ba dare ba ran aidan Muzaffar ya gaji da tuka jirgin ruwa sai dattijo Zarkiyu ya karbe shi kuma ya zauna ya huta kuma abin da yabawa Muzaffar mamaki shi ne ko da digon ruwa bai keto ya shigo cikin jirgin ruwan ba ta tsakiyar jirgin inda ya tsage har suka shafe tsawon tafiyar kwanaki biyar suka isa bain gabar kogin. Da isarsu bakin kogin suka sauka akan tsandauri kusa da wnai daji mai yawan tsaunuka da kwazazzabai 107 harafi Tafiyar ajali kamar wanda suka wuce baya, sai dai wannan yana da itatuwa da ciyayi da sarkakiya mai duhu da suka gewaye ko ina. Dattjo zarkiyu ya dubi dajin bangaren hagu dana damansa sannan ya umarci Muzaffar su bi bangaren dama su ci gaba da tafiya. Kafin su bar bakin kogin su fara tafiya sai suka ga an jefesu da wani irin bakin mashi ma'aboin girma da tsaye, tsinin mashin da yayi jajawur tamkar karfen da aka ciro daga wutar makera mashin yana tafe akan iskayana huci da kugi tamkar ana ruru wuta a jikinsa, dattijo Zarkiyu yayi sauri ya zare takobinsa ya tari wannan mashi ya kade shi gefe daya, mashin ya tafi ya fada cikin kogin nan dake kusa dasu ya nutse a cikinsa, nan take ruwan kogin nan dake kusa dasu ya nutse a cikinsa,nan take ruwan kogin ya soma zabalbaala da tafarfasa saboda musiba. A ka sake jefansu da wani bakin mashin irin wanda aka jefesu da shi da farko Zarkiyu ya sake sanya takobinsa ya kade mashin efe mashin ya fada tsakanin wasu bishiyoyi dake kusa da wajen nan take bishiyoyin suka kama da wuta ciyayi da sarkakiyar dake wajen duk suka kone kasar wajen ta yi baki saboda musiba danga nan sai suka ji an sakar musu ruwan kibiyoyi ta ko in aba tare da sun a masu harba kibiyoyiyin ba dattijo Zarkiyu ya ci gaba da karwa da takobinsa yana kade kibiyoyin suna faduwa kasa, shi ma Muzaffar ya soma kare kibiyoyin don kar kansa yana kade su suna faduwa asa da fekakken itace da yake hannunsa. Bayan wani wa'adi mai tsawo ana harbinsu da wannan kibiyoyi ba a samu daya daga cikinsu ba, sai suka ga an dakata da harbor wadannan kibiyoyi da basa ganin masu

Chapter 8 of 9