Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 9
kuma ya hadu da wasu jama'amatafiya yayi tambaya a gare su koza a samu wanda ya san hanyar da zai bi ya koma birninnsu da zai ci gaba da tafiya sai ya dauki akushin abinci tare da wannan salkar ruwa dan yin guzuri da su tunda abincin da ke ciki tare da ruwan basu kare ba, kuma gas hi baai san inda zai sake samun wani abincin ba a cikin wannan dajin. Ya ci gaba da tafiya yana keta duhun itatuwa tsaunuka da kwazazzabai a cikin wannan bakin daji ba tare daya hadu da wata halitta dake da rai ba koda dabba bare ya ga mutum bil'adama a cikin sa da rana ta yi zafi sosai Muzaffar ya sake jin yunwa ya tsaya a bude akushin nan ya ci abinci ya koshi ba 42 harafi ka do id bi y y k k こ Tafiyar ajali tare da abicin ya ragu ba, ya dauki salkar ruwan ya sha itama kamar da farko ruwan da yake cikin salkar bai ragu ba bare yayi tunanin zai kare. Yayi godiya ga Allah sannan ya tashi ya ci gaba da tafiya tare da wannan salkar ruwa da akushi da yak e ci yake sha daga gare su. Ba taree da abinda yake ciki yak are ba. Haka Muzaffar ya ci gaba da tafiya har tsawon kwanaki uku ba tare da ya hadu da wata halitta da ke da rai ba koda kuwa tsuntu dake shawagi a sararin samaniya ban da kasusuwan gawarwakin mutane da suka dade da hallaka babu abinda yake gani a duk inda ya wuce a cikin wannan daji, ya ci gaba datafiya sallah da cin abinci ne kawai yake tsayar da shi, amma bai ga alamar zai riski wani gari gabansa ba, a rana ta hudu daga cikin ranakun tafiyarsa ne ya isa bakin wani kogon dutse yana zuwa daidai wajen sai ya ga takun sahu tamkar takun sahun mutum ya shiga cikin kgon dutsen ya bi wannan sawu da ya gani ya shiga cikin kogon dutsen, ko zai yi sa'a ya riski wani mutum bil'adam a cikinsa, da shigarsa cikin kogon dutsen sai ya tadda wani farin dattijo tsoho tukuf da shi mai alamun tarin shekaru da dadewa a duniya, zaune akan farin buzu yana jan tasbaha Muzaffar yayi matukar mamaki da ganin wannan dattijo dake zaune a cikin wannan kogon dutse dake tsakiyar daji ba tare da wasu jama'a makusantan sa da zasu taimaka mas aba, da ya sake dubansa sosai sai ya ga yayi kama da tsohon nan da ya taba taimakawa ya kubutar da shi daga hannun Damisa da ta tasarwa hallakashi wata rana a bakin kogon dake birninsu, ba don a tsakiyar daji ya ga wannan dattijo ba babu shakka da ya tabbatar da cewa shi ne ya taba taimakawa a birninsu wata rana. Bayan ya gamadubansa ya matsa kusada shi yayi masa sallama. Dattajon ya dago kansa ya amsamasa sannan yay i masanuni da wata shimfida dake kusa da shi y ace "Zauna" Muzaffar ya bi umarnin dattijon ya zauna ba tare da jayayya ba, tsohon nan bai sake yiwa Muzaffa Magana bay aа 43 harafi Tafiyar ajali kau da kai ga barin dubansa ya ci gaba dajan casbaharsayayi addu'a ya shafa ya juyo ga Muzaffar y ace da shi. "Yaro rayuwarka tana cikin hadari da musiba mara misaltuwa kasancewarka a cikin wannan tsibiri na Hijusiya da babu wani mutum bil'adama da ya isa shigowa cikinsa ya kubuta ba tare da ya hallaka ba". Muzaffar yayi matukar mamaki da jin maganar wannan tsohon nan takeya maidamasa da cewa "IDan kuwa har wannan daji ya kasance mai matukar hadari da musiba a cikinsa yadda har babu wani bil'adam da zai iya shigowa cikinsa ya fita ba tare da ya hallaka ba, to kuwa kai meen ya kawo ka cikinsa ka ke zaune ba tare da musibar ta halaka ba? Kuma ka yi sani cewa duk abin da zai hallaka jarumi kama ta kuwa zai hallaka dattijon mai tarin shekaru irinka ba batare da adadi ba" Tsohon nan yayi shiru yana duban Muzaffar sannan ce da shi "Kai dai ka kasance mutum mai Gadara da jarumta ta kuruciya da take dibanka b aka san da cewa a cikin halittun da ke raye a doron kasa akwai da yawa da suka fika tsananin ¡arumta da karfi ba, ka kasance mutum mai yawan tambaya da rashin tsoro babu abin da z aka ga ni ka kauda kai baka yi tambaya a kansa ba, ko kuma ka ce zaka je ka taba komai hadarin da yake tare da shi, kuma ka kasance mutum mai yawa shu'umanci da rashin nisantar abin da zai cutar da kai. Wannan shi ne abin da ya jam aka kasancewar a cikin wannan hali da ka riski rayuwarka acikin,da kana kiyaye maganar mahaifinka da ya kasance mai yin naisha a gare ka da hanaka aikata wannan dabi'a taka da baka kasance a cikin wannan mummunan hali da ka tsinci kanka a ciki ba". Muzaffar ya sake yin mamaki da jin kalaman wannan lattijo cikinsari ya sake tambayarsa cewa "Ya aka yi ka san abarina da abin da ya faru a gare ni amma kai ka kasance daga ikin mutane ma'abota bincike na alkaluman tsafi da sihiri , 44 harafi Tafiyar ajali wanda aikata hakan shirka ce da bata mabayyani Allah ya tsare mu da aikatawa". Dattijo nan y ace da shi "Ban zamo daga cikin ma'abota bincike na alkaluman sihiri ba, sai dai ni na kasance ba mutum bane bil'adama irinka kamaryadda ka ke zato, kasancewar wannan daji da kake cikinsa ba zaka tabaganin wani mutum bil'adama irinka kamar yadda kake zato, kasancewar wannan daji da kake ctkinsa, ba z aka taba ganin wani mutum bil'adama kamar ka a cikinsa ba, koda aljanu sai wanda suke sadaukai suke iya shigowa wannan tsibiri su fit aba tare da sun hallaka ba, duk wani bil'adama da kagani a cikin wannan tsibiri ko kuwa an kawo shi ne don ya hallaka a cikinsaa kamar yadda ake nufi da kawo ka wannan waje domin ka halaka saboda wanda suka aikata hakan a gare ka sun tabbatar da cewa ba zakat aba kubuta daga cikin wannan tsbiri ka koma birninku ba, har sai ka hallaka, sai dai kada wannan ya s aka razana ko ka zama mai raunini zuciya ni zan taimakamakakakubuta daga rikin wannan tsibiri kamar yadda ka taba taimaka ka kubutar da ni daga hannun Damisa, waa rana matukar ka kiyaye abin da zan sanar da kai". Muzaffar yayi shiru yana sauraron dattijon nan ya ci gaba da cewa da shi. Da farko dai suna MUBASSHIR BN SHARKIYU ni ne tsohon da ka taba kubutar da ni daga hannun Damisa, wata rana a bakin kogin dake birninku wand aba don taimakon daka yi a gare nib a da kuwa na hallaka,saboda duk sanda na wanzu cikin siffar mutane bil'adama bani da tasirin kubutar da kaina daga dukkan abin cutarwa saboda tsufa da yawan shekaruna har ssai na koma siffata ta aljani, ni ne na tsawatar maka ga barin taba wannan batta da ka gani a tsakiyar daji ka tafi gare ta da nufin dauka ka buxe don ganin abin da yakecikinta.idan da ka bi umarnina ka kiyaye abin da na ambata a gare ka na san cewa hallaka zata tabbata a garekada kuwa baka kasance a cikin wannan hali da ka riskikanka a ciki ba, don kuwa wani tsohon ifiritu ne dake hidima ga wani boka a cikin wannan 45 harafi Tafiyar ajali battar da ka gani kumashine ya daukoka ya kawo ka wannan tsibiri na Hujisiya don ka hallaka kamar yadda akenufi da wanda aka kawo shi wannan waje, sabbin bude wannan batta da ka yi, kuma an alkata hakan a gareka ne don kada ka auri Gimbiya Zuuriya 'yar Sarki Sa'adul gamidi da aka sanya ranar aurenka da ita, wanda yasa aka aikata hakan gar shi ne waziri Hawaisu don yana so dansa ya auri gimbiya ZUhuriya saboda ya hallaka Sarki Sa'adulgamidi sarautar binin AMbar ta dawo hannunsa". Ya kwashe labarin dukkan abin da yake faruwa tsakanin waziri Hawaisu da Boka Musailamatu na makircin da suke shiryawa don su hallaka Sarki Sa'ad sarautar birnin AMbar ta dawo hannunsu ya sanar da Muzaffar sannan ya ci gaba da cewa. "Ni ne na hallaka Ifiritun da ya taso gare ka da nufin hallaka na jefe shi da hasken na addu'a yak one ba don haka ba da kuwa ka hallaka ni na zuba maka ruwa ka farfad daga suman da ka yi bayan da ka fadi kasa sakamakon karajin da wannan ifiritu yay i lokacin hallakarsa,ni ne na kawo maka akushi da salkar ruwwan da ka gani a usa da kai, a lokacin da kake cikin halin suma,kuma kake ci kake sha, daga gare su har Eya zuwa wannan lokaciwanda ba don sub a d akuwa yunwa da kishirwa sun hallaka ka saboda babu inda z aka samu abinci ko ruwa a cikin wannan tsibiri da kake ciki, yanzu haka mahaifanka da sauran yan uwanka suna can suna nemanka a brnin Ambar basu san inda kake ba,hankalinsu yayi matukar tashi sosai saboda rashin sanin halin da kake ciki an tsinci dokinkatare da takobinka ta yaki bayan gari amma ba a ga koda sahunka ba, ko a san inda kake daga wannan tsibirin na Hijusiya zuwa birnin Ambar tafiyar shekaru goma ce daidai ga mutum bil'adam kamar ka, idan bai hadu da wani abin cutarwa ya hallakashi ba, sai dai zan taimakamaka kakare awannan tafiyar cikin sauri ka koma brninku a tsakanin kwanaki ¡kalilan idan ka kiyaye abin da zan sanar da kai. 46 Tafiyar ajali "Da farko dai b azan iya daukarka na fitar da kai daga wannan tsibiri ba, haka kuma babu wani mahaluki daga jinsin aljani da zai iya daukarka ya fitar da kai daga wannan tsibiri said an uwana Zarkiyu don haka zan tura ka gare shi don ya taimaka makaya maida kai birninku, ka zauna nan tare da ni har zuwa wayewar gari da safe zan sanyaka a hanya da z aka tafi gare shi don ya maida kai birninkи" Da Muzaffar ya ji wannan bayani sai ya amince da shawarar dattijo Mubasshir ya zauna tare da shi kamar yadda ya aumarce shi. ** Can kuwa a birnin AMbar baya wasu kwanaki da samun labarin bacewar Muzaffar, sai waziri Hawaisu ya shirya ya tafi wajen Boka musailamatu don sanar da shi abin da yake faruwa yay i ta tafiya a cikin daji har ya iso inda bukkar Boka Musailamatu take a cikin tsakiyar daji. Da isarssa wajen ya sauka daga kan dokinsa ya shiga cikin bukkar ya tadda Boka Musaila a zaune a gefe kafin yay i Magana sai Boka Musaila y ace da shi "Muna sane da dukkanin abin da yake faruwa da kuma abin da ya kawo ka gare mu, hakika ka aikata abin da muka umarceka har ma hadimin dake hidima ga wannan batta ta aikin sihiri da nab aka.ya dauki wannan Jarumi ya kaishi tsibirin Hujisiya ya yasar da shi a can ya dawo gare mu". Ya nuna masa attar nan ta aikin sihiri da ya bawa Waziri Hawwaisu a jiya a geensaa ta dawo gare shi ba tare da Waziri Hawaisu ya dawo da it aba, sannan ya ci gaba da cewa. "A duk sanda na tura hadimin dake hidima ga wannan batta don aikata wani al'amari da zarar ya aikata 47 harafi Tafiyar ajali abin da aka umarce shi to kuwa zai dawo gare ni, sannan nay i sani da dukkanin abin da ya aikata" Ya dauko izga da yakeamfani da ita wajen Surkullensa na aikin siiri ya tsoma ta a cikin ruwan kwatarniyar dake gabansa sannan ya cire ta ya yarfa ruwan a jikinsa farin dutse dake kusa da shi, nan take farin dutsen yay i haske kamar madubi daga jikin hasken sai ga Muzaffar ya bayyana a inda yake cikin tsibirin Hijusiya. A lokacin yana kwance a halin suma sanda tsananin yunwa da kishirwa suka ci karfinsa. Boka Musaila ya dubi Waziri Hawaisu ya cce da shi "Wannan shi ne tsibirin Hijusiya inda aka kai wannan arumi aka yasar da shi kuma anan zai hallaka ba zai taba dawowa wannan birni ba, don babu wani mahaluki daga insin mutane da ya taba shiga wannan tsibiri ya fit aba tare da ya hallaka ba, ka yi duba ya zuwa inda yake akwance z aka ga babu komai sai tarin kasusuwan gwawarwakin mutane da suka dade da hallaka tun Emanin mai tsawo kamar yadda shima zai hallaka a vanzu, don haka shi an gama da lamarinsa ke nan tasa ta kare". Waziri Hawaisu yay i matukar murna da farin ciki da jin wannan bayani sannan y ace da Boka Musailamatu Godiya nake a gareka abin dogarona cikamakin bokaye masana alkaluman tsafi da sihiri yanz me ya kamata mu Bikata don ganin Sarki Sa'ad ya amince da auren dana Najiranu da yarsa Gimbiya Zuhuriya tunda mun gama da batun wannan jarumi". Boka Musaila yayi dariya irin ta mugunta da calunci sannan ya dubi Waziri hawaisu y ace da shi. "Wannan shi yafi komai sauki a cikin lamarina zan aka wata gora dake dauke da ruwan na aikin sihiri a 48 harafi f Tafiyar ajali cikinta idan ka koma gida ka samu wani daga cikin bayi ko hadimanka ka hallaka shi, ka jefar da gawar a wajen da aka tsinci dokin wannan Jarumi a bayan gari, sannan ka zubawa gawar ruwan dakeciki wannan gora da zan baka, kamanni da siffarsa zasu zama irin na wannan jarumi ba tare da banbanci ba, idan aka tsinci wannan gawa za a yi zaton Muzaffar ne ya hallaka babu wanda zai iya gane cewa bas hi bane daga cikin jama'ar birnin saboda wannan aikin sihiri dake tare da gawar. Idan yan uwansa suka daki wannan gawa suka binne shi kenan an tabbatar da cewa Muzaffar ya hallaka, maganar aurensa da gimbiya Zuhuriya yar Sarki Sa'ad ta rushe kena, bayan wasu kwanaki sai ka sake komawa da maganar neman auren danka da gimbiya ZUhuriya ga Sarki Sa'ad tunda wannan jarumi ya hallaka, idan bah aka muka aikata ba, ka san cewa Sarki sa'ad ba zai taba amincewa da maganar aurar da yarsa ga danka Najiranu ba duk da cewa Muzaffar ya bata komai yawan shekaru da za a dauka ba za a ganshi ba, idan kuwa aka tabbatar da labarn mutuwarsa shi kenan maganar aurensa da gimbiya zuhuriya ya rushe." Waziri Hawaisu ya sake cika da matukar farin ciki da jin wannan bayani na Boka Musailamatu. Boka Musaila ya kawo wannan gora y aba shi Waziri Huwaisu ya karba yay i masa godiya sannan ya tashi ya kama hanyar komawa gida. Da isar Waziri Hawaisu gida ya kira dansa Najiranu ya sanar da shi abin da yake faruwa da yadda suka yi da Boka Musailamatu da abin da ya umarceshi da ya aikata ya kawo wannan gora ya bawa Najiranu y ace da shi zai hada shi da daya daga cikin hadimansa su tafi bayan gari tare da shi, idan sun isa wajn da Ifiritun nan ya dauke 49 harafi Tafiyar ajali Muzafar ya tafi da shi aka tsinci dokinsa a wajen ya hallaka wannan hadimin ya jefar da gawar a wajen sannan ya zuba masa ruwan dake cikin gorar sihirin amar yadda Boka Musaila ya umarce shi. Najiranu ya karbi wannan gora da mahaifinsa ya anso daga hannun Boka Musaila sannan Waziri Hawaisu yay i kiran wani hadiminsa dake sharer wajen da ake daure dawakai, ya kawo tufafi na alfamarma masu matukar kyau da ya bashi, sannan y ace da si ya shirya da yamma ya zo ya raka Najiranu kilisa bayan gari.Hadimin nan yayi godiya sannan ya tashi ya tafi. Da yamma ta yi dai-dai lokacin da Waziri Hawaisu ya umarci Hadimin nan ya zo, sai gashi ya iso sanye da kayan da Waziri Hawaisu ya bashi, ya tadda Najiranu у agama shiri suna jiran isowarsa, ya kai gaisuwa gare shi Waziri ya amsa masa sanan ya sa aka bashi doki yah au, suka tafi tare da Najiranu suka kama hanyar bayan gari, suka yi tafiya har suka isa wajen da aka tarar da dokin Muzaffar bayan da wannan ifiritu dake cikin battar nan ta aikin sihiri ya dauke shi. Da isarsu wajen sai Najiranu ya ja linzamin dokinsa ya tsaya shima wannann Hadimin yaja linzami dokinsa ya tsaya. Nan take sai Najiranu ya zare takobin daketare da shi cikin zama da zafin nama, ya kaiwa Hadimin sara ya same shi a tirken dokin wuya hadimin nan ya yi karaji da kururuwa mai tsananin karfi sabda azaba, Najiranu ya sake kafta masa wani saran a kafada jini yay i tsartuwa sama hadimin ya fadodaga kan dokin da yake kai ya soma shure shure d akakarin mutuwa da haka har ransa ya fita ya hallaka, daga nan sai Najiranu ya sauko daga kan dokinsa ya bude bakin gorar da mahaifinsa ya bashi ya juya ruwan dake cikin gorar akan 50 harafi Tafiyar ajali gawar wannan Hadimi nan take sai gawar ta soma rikida daga siffar wannan hadimi ya zuwa siffar Muzaffar har ya zama tamkar gaawar Muzaffar baki daya shi kansa Najiranu sai da yay i matukar mamaki faruwar wannan al'amarin ba don shi ne ya zuba masa ruwan gorar sihirin lamarin ya faru a gabansa ba da kuwa ya gasgata cewa gawar Muzaffar ce baa war hadimin da ya hallaka ba,saboda tsananin kama da siffarsa ta yi da ta Muzafar. Daga nan ya juya ya koma dokinsa yah au, ya hada da dokin da Hadmin ya zo a kansa, ya nufi hanyar komawa gida da isarsa gida ya sanar da mahaifinsa dukkanin abin da ya faru da yadda kamain wannan hadii sukarikida ya zuwa irin siffar Muzaffar ba tare da wani banbanci ba. Waziri Hawaisu ya cika da matukar murna da farin ciki na samun cnasara akan dukkanin makircin da suke shiryawa don ganin sarautar birnin AMbar ta dawo hannunsa.daga nan suka zauna cikin saurare su ji labarin cewa an tsinci gawar Muzaffar kamar yadda Boka Musailamatu ya sanar dasu. Bayan kwana daya da hallaka wannan Bawa aka tsinci gawarsa a wajen da Najiranu ya hallakashi, wani maharbi daga cikin jama'ar birnin ya zo da labarin ganin gawar a bayan gari ya tafi fadar Sa'adulgamidi ya sanar da shi abin da yake faruwa nan take Sarki Sa'ad ya tura baradansa don su dauko wannan gawar su kawo ta fadarsa don yin cigiya a nemi dangin mamacin, baradan suka kama hanya suka tafi suka isa inda wannan gawa take, da zuwasu 51 harafi Tafiyar ajali suka duba sai suka ga gawar Muzaffar ne duk wanda ya sanshi idan ya ga wannan gawa sai ya tabbatar da cewa shi ne, daga nan suka dauki gawar suka koma adar Sarki Sa'ad suka sanar da shi abin da yake aruwa. Shi kansa Sarki Sa'adulgamidi da ya ga wannan gawa sai da ya tabbatar da cewar Gawar Muzaffar ce dan gidan liman Adnan da ya bashi yarsa Simbiya Zuhuriya, kuma aka ce ya bace tsawon wanaki masu yaw aba asan inda yake ba, don haka hima ya shiga cikin jimami da bakin ciki ya kua tura asanar da mahaifinsa Liman Adnan abin da yake aruwa. Kafin yan aike su isa gidan Liman Adnan su anar da shi abin da yake faruwa tuni labarin tsintar awar Muzaffar ya isacikin gidan Sarki Sa'ad har ya ai ga kunnen Gimbiya ZUhuriya,da jin wannan abara sai ta taso dagadakinta a firgice ta nufi fadar nahaifinta cikin halin kidima da rudewa tana zuwa a ga wannan gawa sai ta fashe da kuka irin na akaici da bakin ciki saboda tsananin kaunar da take iwa abin begenta Muzaffar, ta yi ta kukamai sananin har akarasa wanda zai iya rarrashinta, Sarki a'ad ya bada umarnin amaida ita cikin gida saboda awan kukan da takewanda ya cikadukkanin fadar. Da za a maida ita gidata sake duban wannan awa da aka kawo fadar mahaifinta, sai ta ga babu hakkaya yi matukar kama da masoyinta Muzaffar mma sai ta ji zuciyarta na tare da shakku da rashin adda akan cewa shi ne, ta duba hannunsa ba ta ga 52 harafi Tafiyar ajali zoben nan na azurfa da ta bashi ba, wanda a kodayaushe yana tare da shi a duk inda yake baya rabuwa da shi hakan ya kara saya wais-wasi da shakka a cikin zuciyarta, har akafita da ita daga cikin fadarakamaidaita gida bata gasgatacewa wannan gawar masoyinta Muzaffarbace. Shi ma mahaifin Muzaffar Liman adnan da ya samu labarin abin daya faru na tsintar gawwar dansa da ya bace tsawon kwanaki masu yaw aba a ganshi ba, ya kama hanya ya isofadarSarki Sa'ad cikin jimami da bakin ciki hallakar dansa, da zuwan say a dubi wannan gawa da aka kawo fadar Sarki Sa'ad ya ga babu shakka yay i matukar kama da dansa Muzaffar a kamanin na siffarsa, amma kuma tsayinsabai kai tsayin dansa Muzaffarba kuma akwai wani tabo na kuna wuta atsakiyar tafin hannun dansa Muzaffar da yak one tun yana karamin yaro ya duba bai ga tabon a jikin wannan gawa ba, nan take sai ya shiga rudani da rashin tabbas zuciyarsa ta kasa amincewa da cewa wannan gawar dansa Muzaffarce,duk da tsananin kama da suka yi da yake ya san bayyana maganar na iya kawo rudani da rashin fahimta a tsakanin jama'ar jama'ar birnin kasancewarsa babban limamin gari, kuma hujjarsa ba zata zamakarbabbiya abar gasgatawa ba, saboda ganin yada dukkanin jama'a suka yadda cewa gawar dansa Muzaffar ce sai ya hakura ya bar maganar a ransaya sa akadauki wannan gawa aka kaita gidansa aka yi masajana'iza aka binne gawar. 53 harafi Tafiyar ajali Duk abin da yake faruwa a fadar Sarki sa'add Waziri Hawaisu yana fadar akayi komai a gabansa, da ya ga dukkanin jama'a sun yadda da cewa garwa Muzaffar ce aka kawo adar kuma mahaifin MuzaffarLiman Adnan ya dauki gawar don yi masa jana'iza sai ya sake cika da matkar murna da farin ciki ya kuma yadda cewa shi mai samun nasara ne akan makircin da yake shiryawa don sarautar birnin AMbar ta dawo hannunsa, kamar yadda Boka Musailamatu ya tabbatar masa. Labarin rasuwar Muzaffar ya gauraye ko ina acikin birnin Ambar saboda shahara da yayi a fagen Jarumta da bajinta,wadanda suka sanshi suka yi ta jimami da yay i masa addu'a babu wanda bai yadda cewa Muzafffar ya rasu ba a duk daukacin birnin AMbar ban da mahaifinsa Liman Adnan dakuma Gimbiya Zuhuriya dake cikin halin shakka da rashin yaddda sai dai babu wanda ya bayyana abin da yake zuciyarsa suka bar maganar a ransu, mahaifinsa ya mikalamarinsa ga ubagiji yana mai addu'ar Allah ya bayyana inda Muzaffar yakeya dawogare su, matukar yana raye a doron kasa. ** Shi kuwa Muzzaffarbayan da ya kwana daya tare da wannan dattijo da ya tarar a cikin kogon dutse kamar yadda ya umarce shi,da gari yaw aye Muzaffar ya kammalashiri don ci gaba datafiya,dattijo Mubasshir ya dube shi ya ce da shi ** 54 harafi Tafiyar ajali Shi kuwa Muzaffar bayan da ya kwana daya tare dawannan Dattijoda ya tarar a cikin kogon dutse kamar yaddaya umarce shi da gari yaw aye Muzaffar ya kammalashiri don ci gaba da tafiya,dattijo Mubasshir ya dube shi ya ce da shi. "Zan sanyaka a hanya da zaka bi har ka riski inda dan uwana Zarkiyu yake zaune a ckin wannan daji,shi ne zai daukeka ya fitar da kai daga cikin wannan tsibiri da kakeciki ya kaida kai birninku,kuma zaku iyi wannan tafiya ne cikin kwanaki ashirin da uku ku gamata baki daya, kasancewarsa mafi sauri daga cikin jinsin aljanu da suke shigowa cikin wannan tsibiri ko su fita daga cikinsa, amma sai ka kiyaye da dukkanin abin da zai sanar da kai ko kuma ya umarce ka da aikataawa cikin tafiyar da za ku yi tare da shi, ka kasance mai yin taka-tsantsan da lura cikin lamarisadon zarkiyu yana da saurin fushi mafi girman Harzuka da fusatuwa idan ka aikata abin da ransa zai baci babu shakka zai tafi ya rabu da kai ka hallaka ba zai taimakamaka ba,kuma idan ka yi kuskure ka rasa shi ya tafi ya barka babu sauran wanda zai iya daukarka ya fitar da kai daga cikin wannan tsibiri a cikin tafiyar kwanaki ashirin da uku sai dai bayan wasu watanni koma shekaru idan ka yi sa'a wani abin cutarwa bai salwantar da ruhinka kahallaka ba, don haka ka yi hattara kuma ka kiyaye gudun bacin ransa". Da ya gamamasa wannan bayani ya daga karkashin shimfidar buzun da yake zaune ya dauko 55 harafi Tafiyar ajali wata takobi tare da zobe na azurfa ya mika masa sannan ya ci gaba da cewa da shi. "Ka rike wannan zobe a tare da kai sai dai Π kada ka sake ka sanyashi a danyatsanka, kuma kada ka sake ka rabu da shi, komai rintsi da tsanani a duk tinda kake haka itama wannan takobi tana da Imatukar amani gareka cikin wannan tafiya da zaka yi 'kafin a maida kai birninku sai dai b aka da ikon amfani da ita har sai an sanar da kai yadda za kayi amfani da ita,don haka kada ka sake ka zareta daga gidanta har sai an baka umarnin kayi amfani da ita, sannan z aka ci gaba da tafiya wannan akushi da salkar ruwa da kake ci kake sha daga gare su a masayin guzuri, abincin da ruwan da yake cikinsu ba zai taba karewa ba, har sai ranar da ka koma birninku ko kuma idan ka yi kuskure zoben nan da na bakaya bata daga gare k aka rasa shi. Idan ka fita daga cikin wannan kogon dutse z aka yi tafiya har ta tsawon kwanaki uku da yini daya sannan ka isa inda dan uwana Zarkiyu yake saka riske shi cikin wata bukka a tsakanin wasu manyan tsaunuka da zaka tarar a gabanka, idan ka riske shi ka yi masa sallama sannan ka mika masa zoben da nab aka, da zarar ya karbi zoben ya rike a hannunsa zai yi sani da cewa ni ne na turo kagareshi tare da taimakon da zai yi maka ya maida kai birninku ba sai kayi masa Karin bayani ba, daa nan zai dawo maka da zoben gare ka ya kuma sanar da kai shharudan da yake so ka kiyaye cikin tafiyar da zaku yi tare da shi idan har kana so ya taimaka maka ka koma birninku, 56 harafi Tafiyar ajali kuma shi ne zai sanar da kai yadda za ka yi amfani a wannan takobi da nab aka da irin amfanin ta gareka idan ka bi umarninsa, don haka sai ka yi hattara kuma ka kiyaye da abin da na sanar da kai". Da ya kare bayaninsa Muzaffar yayi masa godiya sannan dattijo Mubasshir ya raka shi har bakin kofar fita daga kogon dutsen ya nuna masa hanyar da zai bi don risker inda dan uwansa Zarkiyu yake, daga nan suka yi sallamada bankwana Muzaffar ya kama hanyar da akaumarceshiya bi,ya ci gaba da tafiya yana

Chapter 4 of 9