Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 9
har sai ya zama cikakken Jarumi da zai iya gogayya da kowanne irin sadauki a fadin duniya, kuma wanda yake da ilimin addini, daga cikin wanda suka bijiro da bukatarsu ta neman aurena babu namijin da ya kai wannan mataki dan haka ban fidda ko daya daga cikinsu ba. Ina da sahihin labara game da kai cewa mahaifinka shi ne babban limamin birnin nan, kuuma kana da ilimin addini sannan ga jarumta kamar yadda na tabbatar don haka kai ne ka dace da irin namijin da 15 harafi Tafiyar ajali nakemuradin na aura, kuma zuciya ta ta amince da kai a matsayin abin bege menene makomarzance na cikin lammarinka?' Muzaffar ya ji maganar tamkar bada shi take ba, dan yana ganin matsayinsa bai kai a ce gimbiya ZUhuriya za ta so shi ba a matsayinta na yar Sarki, ya dubeta y ace da ita. "Makomar zancen ki cikin lamarina shi ne zuciyata ba tare da da makantar da za ta afka cikin begen abin da baza ta iya mallaka ba. Na san cewa baki kasance daga cikin matayen da za su ambata begensu ga kowanne irin namiji yay i watsi da sub a, amma ni ina da sahihancin baki kamaci auran namiji kama ta ba don kuwa nib a dan sarki bane kuma ba attajiri ba....." Gimbiya Zuhuriya ta tari numfashinsa da cewa "Bari ga ambaton irin wannan kalami dan kuwa ni ban kasance daga 'ya'yan Sarakuna da ke dorawa kansu alfahari da tunkaho cewa sai yayan sarakuna ko kuma attajira za su aura ba, ka sani cewa sarautar da dukiya ALlahshi ke ba da su, ga bayinsa kuma bad an yafi kaunar wanda ya bawa wannan baiwata sa ba. Sai dan ya ga shugaba da zaiyi adalci ga jama'ar da yake shugabanta da mai dukiyar da zai kyauyata ga talakawa mabukata gare shi. Dan haka kai ne wanda zuciyata ta zaba kuma nake fatan kasancewa tare da kai ka zamomiji a gare ni,kuma nay i imani da cewa idan na sanar da mahaifina kai ne wanda nake so a cikin wanda suka bijiro da bukatarsu ta neman aurena ba zai ki amincewa da zabina ba, 16 harafi Tafiyar ajali kuma zai yi matukar farin ciki da jin hakan zai kuma amince da kai ka aure ni dan kuwa mahaifinka mutum ne mai daraja da martaba a wajen mahaifina, menene ra'ayinka akan haka?" Muzaffar yayi shiru bai yi Magana ba sai dai murmushi, ita kuma tana ganin haka sai ta ce da shi "Na san akwai begenma a cikin zuciyarka dan na gani kwayar idanunka, dan haka idan na koma gida zan sanar da mahaifina kai ne wanda nake so duk a cikin masu neman aurena zai kuma neme ka dan tabbatarwa". a Tana gama wannan Magana sai ta maidahular karfen da ta cire daga kanta ta rue fuskarta kamar yadda take tun da farko, sannan ta kada linzamin dokinta ta juya a sukwane ta kama hanyar komawa gida Muzaffar ya bita dakallo yana mai mamakin abin da ya faru tsakaninsu da irin kalaman da ta ambata a agare shi,na nuna begensa a matsayinta na yar sarki da bai taba zaton haka zai iya faruwa ga wani mutum kamarsa ba.\yana tsaye a wannan waje yana hangenta har sai da ta bace ya daina ganin koda kurar gudun dokinta, sannan shi ma ya kada linzamin nasa dokin ya kama hanyar komawa gida. Gimbiya Zuhuriya tana isa gida ta daure dokinta, ta tafi ta cire sulki da dukkanin kayan yaki da yake jikinta, ta sanya wasu tufafin irin na ado masu matukar kyau ta koma cikin kuyanhinta ta zauna suka ci gaba da al'amuran sub a tare da wani ya san cewa ta fita daga gidan ba. 17 harafi Tafiyar ajali Da yake mahaifinta Sarki Sa'ad bai dawo daga tafiyar da yayi ba sai ta yanke shawarar cewa idan mahaifinta ya dawo za ta sanar da shi cewa ta fidda Muzaffar a matsayin wanda ta keso ta aura daga cikin masu neman auranta. ** Bayan kwanaki uku Sarki Sa'addulgamidi ya dawo daga tafiyar da yayi ta kai ziyarar birnin aininsa, bayan yayi kwanaki biyu ya huce gajiyar tafiya ya soma fitowa fada. Waziri Hawaisu ya shirya dan zuwa gare shi ya sanar da shi kudirinsa na neman auran gimbiya Zuhuriya ga dansa Najiranu. Yana isa fadar ya tadda Sarki Sa'addul gamidi da sauran yan majalisarsa ana fadanci ya kai gaisuwa ga Sarki aka amsa masa sannan ya nemi waje ya zauna aka ci gaba da zaman fada tare da shi. Da lokacin tashi daga fada yayi yan majalisar Sarki Sa'ad suka tashi. Waziri Huwaisu ya matsa ga Sarki Sa'ad y ace yana son ganawa da shi bayan yan majalisar Sarki sun gama fita suka kadaita su biyu a cikin fadar Waziri Hwaisu ya dubi Sarki Sa'ad y ace da shi. "Allah ya baka nasara daman ina san ganawa da kai ne dan neman wata alfarma ta neman auran yarka gimbiya Zuhuriya ga babban dana Najiranu, da yake daga cikin masu begenta, idan ka amince mas azan yi matukar farin ciki saboda kusancin da ke tsakanina da kai, kuma hada auran yayanmu zai kara dankon zumunci da amintaka a tsakanin Zuri'armu. 18 harafi Tafiyar ajali waziri Da Sarki Sa'ad ya ji wannan bayani na Hawaisu sai y ace da shi, "Hakika nay i matukar farin ciki da wannan shawarar taka dan kara dankon amintaka da ke tsakanibmj, sai dai kuma kafin nay i saurin yanke hukunci, akan al'amarin ka bani lokaci zan ji daga gimbiya ZUhiriya idan ta kasance tana begen danka to kuwa zan ba da auranta gare shi, ta zama matarsa idan kuwa tana da wanda take so ti kuwa sai mu bar wannan Magana matukar dai wanda ta zaba bai zamo daga mutanen da shari'a ta haramta bada auran 'ya a gare sub a. Da waziri Hwaisu ya ji abin da Sarki y ace, sai yay i sauri y ace da shi "Allah ya taimaki Sarki ya ja zaminka, ai ina ganin ba sai ka nemi shawara daga gare ta ba idan hark a amince da da n aka bas hi aurenta duk irin ukuncin da ka yanke akanta ba zata aki amincewa bad an kuwa nay i sani da cewa ita mai biyayya ce a gareka cikin dukkanin lamarinta" Sarki Sa'adya ce da shi "babu shakka abin da ka ambata haka yake, duk irin hukuncin da na yanke akan gimbiya Zuhuriya ba zata ki amincewa da shi ba, amma zan bada dama ta dan ta bawa zuciyarta abin da take muradi matukar dai abin da ta zaba bai sabawa shari'aba, don haka kayi hakuri daga nan zuwa kwanaki biyu zaka ji irin hukuncin da na yanke akan lamarin". Waziri Hawaisu bai sake cewa komai ba daga nan suka yi sallamadaSarkiyatashi ya fice daga fadar ya kama hanyar komawa gidansa, shi kuma Sarki ya shiga gida. 19 harafi Tafiyar ajali A wannan rana da yamma Gimbiya Zuhuriya tana zaune a dakinta cikin kuyanginta sai ga sako daga mahaifinta ya turo a kira ta, yana son Magana da ita ta tashi ta tafi gare shi ta gaishe da shi sannan ta zauna ta na mai sararann abin da zai ce da ita. Sarki Sa'adyadubi Gimbiya ZUhuriya y ace da ita "Yak e yata Zuhuriya na saa kira ki ne saboda na ji daga gare ki game da maganar wanda za ki aura, hakka na baki dama ki fidda wanda zuciyarki ta amince da shi dan na aurar da ke a gare shi, amma har yanzu ban ji wani sakamako daga gare ki ba, idan har yanzu babu wanda zuciyarki ta amince da shi to Najiranu dan gidan Waziri Hawaisu mahaifinsa bayyana bukatarsa ta neman auran ki ga dansa". Gimbiya ZUhuriya ta amsa da cewa "Ya Abbana mafi girman daraja da daukaka a gare ni, hakika ni mai yin biyayya ce a gare ka bisa ga duk wani hukunci da ka yankeakaina, ina da wanda nake bege kuma zuciyatata amince da shi kamar yadda k aba ni zabi amma idan kana ganin Najiranu dan waziri Hawaisu shi ne yafi dacewa k aba da aurena gare shi to kuwa na aimince da zabinka". Sarki Sa'ad y ace da ita "Ban yankehukunci akan ki ba, sai abin da kika zabarwa zuciyarki kuma tun da kina da wanda kike so sanar da ni wane ne shi idan har bai zamo daga mutanen da shari'a ta haramta bada aurenki garesu ba, to kuwa zan aurar da ke a gare shi" Zuhuriya ta sunkuyar da kai tana mai jin kunya sannan ta yi Magana da muryar kas-kasa ta ce da 20 harafi Tafiyar ajali mahaifinta Muzaffar na zaba dan gidan babban limamin birnin nan" Da Sarki Sa'ad ya ji wannan bayani na ta sai yayi matukar farin ciki, kuma nan take ya amince da zabinta, saboda yanamartaba babban limamin birnin mahaifin Muzaffar kumayanadalabarin Muzaffar game da jarumta da bajintarsa, kamar yadda yakeji a birnin ana fada. Sannan bai taba jin wani ya ambaci mummunan hali ko dabi'a da aka ce Muzafar yana aikatawa bay a dubi Gimbiya ZUhuriya ya ce da ita. "Hakika na amince da abin da kika yiwa kanki zabi kuma zan auar da keg a wanda kike so don ban taba jin an fadi wani abu na aibu ko mummunan hali daga gare shi ba, sannan kuma mahaifinsa mutumin kirki ne mai gaskiya da amana, don haka zan sanar da mahaifinsa abin da yake faruwa dan a tsaida maganar aure a tsakaninku, tashi ki je Allah yay i miki albarka". Gimbiya Zuhuriya ta cika da matukar murna da farin ciki da ta ji cewar mahaifinta ya amince da abin da ta zaba ya kuma yadda zai aurar da ita ga Muzaffar kamar yadda take so ta tashi ta koma cikin gida tana mai godiya ga Allah tare da farinc ikimisaltuwa. Washe gari da aka fita fada Sarki Sa'adul gamidi ya sa aka kira masa waziri Hawaisu da babban limamin birnin liman Adnan bayan da suka hallara a fada tare da sauran yan majalisar Sarki. Sarki yayi musu ayani da cewa yarsa gimbiya ZUhuriya ta fidda wanda take so, daga cikin masu neman auranta, 21 harafi Tafiyar ajali kuma Muzaffar ta zaba dan babban limamin birnin dan haka ya amince da shi yakuma bas hi auranta yan majalisar Sarkisu zama shaida Da liman Adnan ya ji bayanin Sarki sai yay i matukar mamaki,saboda bai san cewa dansa yana daga cikin masoyan gimbiya ZUhuriya ba don bait aba sanar da shi ba, kuma bai gawata alama ta cewa dansa yana bege ga wata mace ba, yayi godiua ga Sarki Sa'adulgamidi bisa ga amincewarsa ta bada auran yarsa ga dansa Muzaffar. Shi kuwa Waziri Hawaisu da yajimaganar da Sarki sa'ad ya ambata ta bada auran yarsa gad an gidan lima Adnan ba a bawa dansa Najiranu ba, kamar yadda yake so sai ransa y abaci, zuciyarsa ta harzuka da ganin cewa shirinsa zai rushe na mallakar sarautar birnin Ambar. Idan ba dansa aka baawa yar gidan Sarki Sa'ad auranta ba. Ya fusata da fushi mara misaluwa bakin ciki ya yawaita a gare shi, haka ya kasance ciki damuwa yayi shiru bai yi Magana ba, har lokacin tashi daga fada yayi Sarki ya salami jama'a kowa ya kama hanyar komawa gidansa. Da liman Adnan ya koma gida sai yayi kiran dansa Muzaffar ya sanar da shi abin da ya faru a fada da amincewar da Sarki yayi na bashi auranta bayan da Gimbiya Zuhuriya ta ce ta fidda da shi a matsayin wanda take so. Muzaffar ya ji wannan Magana tamkar mafarki duk da cewa gimbiya Zuhuriya ta fada masa,za ta sanar da mahaifinta,shi ta zaba a matsayin abin begen da take so ta aura, yayi godiya 22 harafi Tafiyar ajali ga Allah a bisa baiwa da ikonsa akan komai ya kuma yadda da cewa gimbiya ZUhuriya tana kaunarsa da gaskiya. ** Shi kuwa waziri Hawaisu da ya koma gida cikin bacin rai da bakin ciki.ya samu dansa Najiranu ya sanar da shi abin da ya faru a fada da hukuncin da Sarki ya yanke na bada auran yarsa gad an gidan babban limamin birnin Ambar.da Najiranu yaji wannan labara sai ransa ya baci zuciyarsa ta harzuka ya fusata da fushi mara misaltuwa, saboda jin Sarki Sa'ad ya ga wani ba a gare shi ba, ya tashi zai fice cikin bacin rai sai mahaifinsa waziri Hawaisu ya ce da shi. "Ya kai dana Najiranu hakika na san kana cikin bacin rai da damuwa kamar yadda nima nake ciki saboda wannan hukunci da Sarki ya yanke sai dai b azan bari ka rasa auran gimbiya Zuhuriyaba, dan kadda sharina na son mallakar Sarautar Birnin AMbar ta dawo hannuna ya rushe, don haka zan dauki mataki akan wanda Sarki Sa'adya bada auran yarsa gare shi don ganin bayansa, zan sa a hallaka shi ruhinsa ya salwanta, idan ya zamana babu shi a doron kasa, na san daga karshe doe sarki Sa'ad ya dawo da maganar auran gimbiya gare ka" Da Najiranu ya ji wanan Magana ta mahaifinsa sai zuciyarsa, ta yi sanyi yayi farin ciki da matakin da mahafinsa yayinufi dauka akan al'amarin. Cikin wannan ranar waziri Hawaisu ya samu wasu amintattun baradansa da ya yarda dasu, ya 23 harafi Tafiyar ajali sanar da suu abin da yake so su aikata masa na hallaka Muzaffar dan babban limamin birnin a boye ba tare da wan iya sani ba. Ya ce da su idan sun hallaka shi su haka rami su binne si yadda ba za a ga koda gawarsa ba, bare a samu labarin inda yake ko na mutuwarsa. Ya kuma yi musu alkawarinsa zai basu dukiya mai tarin yawa ta zinariya da azurfa idan suka aikata abin da ya umarce su. Baradan nan suka yiwa waziri Hawaisu alkawari za su aikata abin da ya umarce sun a hallaka Muzaffar kamar yadda ya sa su,daga nan Waziri ya hada su da dansa Najiranu dan su aikata komai a gabansa dan tabbatarwa. Da yakesuna da masaniyar cewa Muzaffar yak an fita bayan gari kilisa akan dokinsa cikin kowanne yammacin rana, sai suka yishiri da yamma suka fita bayan gari kan hanyar da yake wucewa suka nemi wani waje tsakiyar daji sukalabe dan jran karasowarsa. Bayan wani lokaci sai ga muzaffar tafe akan dokinsa cikin sassarfa yana mai matukar nishadi da jin dadin fitowarsa kilisa a wannan yammaci saboda abin farin ciki da ke tare da shin a bada auran gimbiya Zuhuriya a gare shi, da fidda shi a matsayin mijin da take muradin ta aura. Yana tsakiyar tafiya a wannan hanya da ya karaso daidai inda baradan nan suke boye a cikin duhun itatuwa sai suka fito gabaki daya akan dawakansu suka zagaye shi ta ko ina suka yi masa kawanya, hannayensu rike da 24 harafi Tafiyar ajali miyagun makamai irin na fada a filin daga, da yake sun tare shi ne dan neman rayuwarsa basu saurari komai ba, koda suka tsaya yi masa Magana kawai sai suka yunkura gabaki daya suka tasar masa. A fusace da nufin gamawa da shi tun a karon farko su hallaka shi da Muzzaffarya ga haka sai yayi sauri ya zare takobinsa ya karkata gare su dank are kansa da ganin wadan nan baradan sun taso kansa rike da makamai da nufin hallakasi,kuma ba tareda ya san kosu wanene sub a da dalilinsu na san hallaka shi. Baradan nan suka isa kansa cikin karaji da gunji suka far masa da sara da ko ina tamkar saukar ruwan sama.muzaffar ya tare su aka yi a rangama da kazamar faduwa mai muni da ta haddasa salwantar rayuka gawarwaki baradan suka soma silmiyowa daga kan dawakansu, suna fadowa kasa san da Muzafffar ya fantsama a tsakaninsu ya soma keta su cikin tsanain jarumta da kwarewa ta salon iya fada. Nan take wajen ya hargetse kura ta kuduru a tsakaninsu ta turnuke ta takore sararin samaniya, duk inda Muzaffarya kai sara da kaifin takobinsa sai kaga yak eta duk wanda kaifin takobin ya samu gida biyu, saboda karfin irin na jarumta da sadaukantaka, da ke tare da shi, haka yay i ta hallaka baradan nan da suka taso gare shi, har sai da ya karar da su baki daya, ya ja linzamin dokinsa ya tsaya akansu huci da haki irin na zaratan sadaukai da suka gama artabu a gafen fama. Najiranu dan gidan Waziri Hawaisu da aka turo don a hallaka Muzaffar a gabansa ya gani,dan tabbatar da ya ga baradan sun kasa samun nasara akan Muzaffar ya hallaka su,sai ya sake fusatuwa da harzuka mara misaltuwa zuciyarsa ta tunzura, ya zare wata bakar takobi daga damararsa ya rufe fuskarsa da rawai wadda 25 harafi Tafiyar ajali Muzaffar ba zai iya gane kowanene shi ba, ya fito daga cikin duhun itatuwan da yake boye ya saki linzamin dokinsa ya taso kan Muzaffar cikin karaji da gunji fusatuwa, da nufin hallaka shi da kansa. Muzaffar ya ji karaji da takun gudun dokinsa ta bayansa, ya juyo ya ga wani mahayi ne daga cikin baradan da suka tare shi yay i saura bai bayyana gare shi ba, sai yanzu. Cikin azama da karfin zuciya ya karkata a gare shi ya tare shi suka yi bahaguwar haduwa irin ta mashahuran jarumai da suke ji da kansu a fagen fama. Kaifin takubbansu ya hadu a kan iska suka soma kaiwa juna sara cikin nuna kwarewa da mugun nufi na son hallakaabokin karawa. Artabu ya rincabe a tsakaninsu suka dauki lokaci mai tsawo suna kafsawa babu wanda ya samu nasara akan wani, suka zabura akan dawakansu suka kaiwa juna wafta kaifin takubbansu ya sake haduwa akan iska, suka rike kaadun juna da hannuwansu marasa rike da makami suka yunkura gaba daya suka diro daga kan dawakansu, aka ci gaba da sokekeniya da bugayya fada ya dawo na kasa, sukayi ta kafsawa har sai dai kaifin takubbansu ya dakushe haskensu ya dasusashe saboda tsananin yawan kai sara da haduwa da suke yi. Suka sake yunkura suka kai dauki ga juna cikin fusatuwa Muzaffar ya banke Najiranu da kirjinsa da bangaza irin ta sadaukai. Najiranu ya ji ya ji kamar yayi karo da bakin dutse saboda karfin kirjin Muzaffar suka rike damtsan juna suka yi gwajin kwanji babu wanda ya murde wani.muzaffar yayi masa karo da kai a tsakiyar fuska sai da Najiranu yayi baya taga-taga kamar zai fadi, saboda tsananin buguwa, sannan ya turje ya zaburo a fusace ya suri Muzaffar zai maka da kasa, Muzaffar ya juye ya dire da kafafunsa, ya yiwa Najiranu dibar 26 harafi Tafiyar ajali karan mahaukaciya ya fadi da kasa. Ya zaro wani karamin gatari daga damararsa cikin tsananin zafin nama da jarumta ya kaiwa Najiranu sara da shi ya same shi a kafada. Najiranu yay i karaji da kururuwa mai tsananin karfi saboda azabar saran da shigar da kaifin gatarin yay i a jikinsa, Muzaffar ya sake daga gatarin da dukkanin karfinsa ya kai masa sara a tsakiyar kirjinsa. Kaifin gatarin ya sari wata damara ta karfe da ke daure a jkin Najiranu wadda bad an it aba, da kuwa Muzaffar ya ragargaza kashin hakarkarinsa, ya hallaka shi da kaifin gatarinsa, gatarin yayi tsalle sama ya firge daga hannun Muzaffar saboda tsananin karfin saran da kuma haduwarsa da damarar karfe da ke jikin Najiranu. Kafin Muzaffar ya café gatarin ya sake kai masa sara Najiranu ya yunkura ya ture Muzafffar daga jikinsa ya tashi cikin sauri ya tafi da gudu jini na daukarsa ya kama dokinsa yah au. Ya saki linzamin dokinsa ya kama hanyar komawa birnin AMbar asukwane dan ya tsira daga hallaka. Shì ma Muzaffar ya tashi cikin sauri ya tafi kama na sa dokin yah au yabi bayan Najiranu,da nufin cin masa,ya kama shi sai dai kafin ya isa gare shi tni Najiranu yay i nisa saboda tsakanin gudun dokinsa ya barshi a baya sosai, kurar gudun dokinsa kawai Muzaffar yake hange har ya isa cikin birnin Ambar ya shiga ya bacewa Muzaffar. Da Muzaffar ya isa cikin birnin AMbar sai ya rasa hanyar da baradan nan da ya biyo ya bi a cikin hanyoyin da ke cikin birnin. Ya dudduba bai ga koda sahun dokinsa ba bare ya gane inda yabi ya shiga cikin gari, yana yao da zagayawa ko zai ga wannan jarumi k kuma ya ga dokinsa daure a turke daga cikin turakun dounan jama'ar amma haka Muzaffaryayi ta zagayawa har rana ta fadi bai yi sa'ar ganinsa ba. Da ya gaji da neman wannan barde sai ganshi ba sai ya kada linzamin dokinsa ya juya ya kama hanyar koma wagida. Shi kuwa Najiranu bayan da ya tsrewa Muzaffar tun daga bayan gari yana shigowa cikin birnin Ambar bai tsaya a ko in aba sai cikin gidansu. Ya sauko daga dokinsa a galabaice 27 harafi Tafiyar ajali hadu akan iska tartsatsin wuya ya tashi sama tare da wata irin tsiwa mai tada tsigar jiki irin ta haduwar karfe da karfe suka ci aba da kaiwa juna sara da suka da takubban da ke hannunsu, kura ta turnuke ta kuduru a tsakaninsu tamkar dandazon barada ne suke kafsawa a fagen fama. Ga mamakin Gimbiya ZUhuriya sai ta ji duk sanda Muzaffar ya kai mata sara ta kare da takobinta sai ta ji tamkar takobin za ta kufce daga hannunta ta fadi kasa.saboda tsananin karfin sara karfin damtse irin na sadaukantaka da ke tare da shi. Sannan duk da tana takama da kwarewa ta salon iya fada da ta samu horo daga mahaifinta, sai ta ga salon fadan da Muzaffar yake amfani da shi ya zarcce saninta, kuma tun da take ba ta taba ganin salon fada makamancin nasa ba, ga shi da tsananin zafin nama da hanzari yadda yake saurin kai sara tamkar kaduwar iska. Tun gimbiya zuhuriya tana kokarin mubazara da shi ta kai mas asara, har ya zamana ba ta iya maida martani sai dai ta yi kokarin kare kanta, ta yi amfani da duk saln fadan da ta yi masa wani abu da za'a ga raunin jaruma da gazawarsa,ita da kanta ta tabbatar da fifikon da ke tsakaninsu na jarumta da kwarewa a fagen iya fada, ta kuma yadda cewa Muzaffar ya cika cikakken jarumi kuma sadauki da zai iya gogayya da kowanne irin barde a fadin duniya. Ta ja da ba baya ta yi turjiya cikin fafatawar da suke yi sanda ta ga ta soma jigata, ba za ta iya samun 13 harafi Tafiyar ajali wannan al'amari suka barmaganar akan cewa su hallaka shi ta hanyar aikin bokaye masana alkaluman sihiri da tsafi. Shi kuwa Muzaffar da ya koma gida bai sanar da kowa abin da ya faru tsakaninsa da wannan barada da suka tsare shi suka tasar ma hallaka shi ba, sai ya ci gaba da gudanar da al'amuransa tambar ba wani abu bai faru a gare shi ba" Bayan kwanaki biyu da faruwar wannan al'amarin aka saka ranar daurin aren Gimbiya ZUhuriya da Muzaffar, wanda za a yi tsakanin watanni biyu masu zuwa, tun daga wannan lokaci Muzaffar yak an ziyarci gimbiya zuhiriya a kowanne Ikkaci dan su yi hirarsu irin ta maʼabota bege da kaunar juna, kuma ya kann kasance cikin shiri ko ta kwana a duk sanda ya fita bayan gari dan bai san masu son fada masa da mugun nufi na hallaka shi ba, ka da su shammace shi cikin rashin sani su cutar da shi. Shi kuwa Waziri Hawaisu da ya samu labarin yin bako da sanya ranar auran Muzaffar da gimbiya ZUhuriya 'yar Sarki Sa'adulgamidi sai hankalinsa ya kara tashi. A wannan ranar ya shirya ya tafi ga wani amintaccen bokansa masanin alkaluman sihiri da yafi yarda da gasgata maganarsa daga cikin manyamahanya bokaye da yake mu'amulla da shi, don neman sa'a ya hallaka Sarki Sa'adulgamidi ya gaji sarautar birnin Ambar ta dawo hannunsa. Ya yi tafiya mai matukar nisa a tsakiyar daji yana keta sarkakiya da duhun itatuwa. Ya ketare wasu kwazazzabai ya shiga tsakanin wasu manyan tsaunuka sannan ya isa inda wata bukka take ita kadai a tsakiyar dajin wato bukkar da boka Musaiamau yake zaune a cikinta. Boka Musaila yana daya daga cikin manya Bokaye masana aikin sihiri da Sarki Sa'addulhamidi ya kora daga birnin Ambar don haka Boka Musaila bas hi da wnai abokin gaba da ya tsana a fadin duniya tamkar Sarki Sa'adul-gamidi kumashi ne wanda Waziri Hawaisu ya fi yadda da shi da gasgata maganarsa daga cikin bokaye masana alkaluman sihiri da yake 29 harafi Tafiyar ajali neman taimako a gare su, do ya hallaka Sarki Sa'ad sarauta birnin AMbar ta dawo hannunsa. Ya tsaya a bakin bukkar ya sauka daga kan dokinsa, sannan ya tafi ya shiga cikin bukkar kamar yadda ya saba a duk sanda ya zo are shi, yana shigaya tadda Boka Musaila zaune akan karaga da aka yi da itace, an shinfida buzun bakar fatar bauna a kansa,jikinsa babu riga sai fari mayani da ya daura a kugunsa kamar walki. Tsoho ne tukuf mai tarin shekaru babu gashi akansa, tamkar dutse, amma yana da dogon gemu da saje mai tarin yawa da ya zama fari fat, saboda yawan furfura da ta baibaye shi. Waziri Hawaisu ya isa gare shi ya fadi yay i gaisuwa boka Musaila ya amsa masa sannan ya zauna ya soma yi masa bayanin abin da yaketafe da shi akan maganar Gimbiya ZUhuriya da yake son aurawa dansa da kuma kudurinsa na son hallaka Muzaffar ruhinsa ya salwanta kafin a kai ga ranar auransa. Da Boka Musailamatu ya ji wannan bayani sai ya dauko wani kaho irin na barewa, mai matukar tsayi ya kafe shi a kasa sannan ya dauko wata kwarya ya dora a kan tsanin kahon ta zauna, ya zuba ruwa a cikin kwaryar har sai da ta cika ba tare da ta goce daga kan tsinin kahon ta fadi kasa ba, ya dauko wata izga ta jelar farin doki ya rike a hannunsa, sannan ya rufe idonsa ya soma karanta wadansu dalalusumaiirin na aikin sihiri da ilimin bokanci. Nan take jikin kahon ya turnuke da hayaki sannan ruwan da ke cikin kwaryar ya soma tiriri yana tafasa tamkar an dora shi akan wuta. Bayan wani lokaci boka Musailamatu ya bude idanunsa sannan ya sanya izgar da ke hannunsa a cikin ruwa da ke cikin kwaryar ya ciro ta ya yarfa ruwan da yakejikinta a jikin wannan farin dutse da kekusa da shi, duk inda ruwan ya zuba a jikin dutsan sai ka ga rubutu irin na aikin sihiri da ilimin bokanci yana bayyana a jikinsa. 30 harafi Tafiyar ajali Bboka Musaila ya soma karanta rubutun tare da dukkanin bayanan da suka bayyana sai yay i shiru bai ce komai ba, har zuwa tsawon wani lokaci. Sannan ya dago da kai ya dubi waziri Hawaisu yace da shi. "Babu shakka wannan lamari ne mai girma daga cikin al'amura masu wuyar aikatawa ga duk wani masanin alkaluman sihiri da ilimin bokanci idan ban i ba, hakika wannan Jarumi da kake so a hallaka shi dan kadayya auri gimbiya zuhuiriya yar Sarki Sa'addulgamidi bayanai sun tabbatar da cewa yana da yawancin kwanaki da ba zai hallaka lokaci guda ba har saiya kare tsawon wa'adinsa a duniya, babu sahihancin lokacin mutuwarsa kuma ba a san a inda zai mutu ba, sai dai duk da bayyanarwadanan bayanai ba zai hana nay i amfani da karfin tsafi da shirina ba

Chapter 2 of 9