Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 9
ya samu damar kufcewa, daga gareta a duk sanda yay i wani kwakkwaran motsi da nufin ya samu damar kubuta sai ya ji kamarmikiya ta kara nutsa farantanta a jikinsa, ta rike shi sosai kada ya kubuce daga gareta nan take Muzaffar ya kara jigata da galabaita saboda wannan tsanani riko da mikiyar ta yi masa har ya soa fita daga hayyacinsa Shi kuwa Zurkiyu yana cikin fafatawa da wadannan mikiyoyin yana ta hallakasu tun bayan fitowarsa daga kogon dutsen da ya baro Muzaffara a cikinsa tsawon kwana biyu da wuni daya yana cikin wannan hali ne sai ya hangi Muzaffar ya fito daga cikin kogon dutsen da ya hane shi da fitowa daga ciki, daya daga cikin mikiyoyin nan ta sure shi ta tashi sama da shi tana shirin hallakashi da ganin haka sai Zurkiyu yayi sauri ya dauko wata kwari da bakadaga cikin kayan fadan da yake tare da shi ya sanya kibiya harbi wannan mikiya da ta suri Muzffarta ke shirin hallakashi, kibiyar ta tafi same ta a kirjin mikiyar ta yi wata kadaitacciyarkara ta tarwatse asararin samaniya gashi jikinta ya kama da wuta ya bazu akan iska Muzaffar ya subuto daga sama ya taho ya fado kasa. Kafin ya kai ga fadowa kasa wata daga cikin mikiyoyin ta sake kai masa sura ta tashi sama da shi Zurkiyu ya sake sanya kibiya ya harbeta ta tarwatse a sararin samaniya, gashi 84 Tafiyar ajali jikinta ya kama da wuta ya bazu a kan iska Muzaffar ya subuto daga sama ya taho zai fado kasa. Kafin ya kai ga fadowa kasa wata daga cikin mikiyoyin ta sake kai masa sura ta tashi sama da shi Zarkiyu ya sake sanya kibiya ya harbeta ta tarwatse a sararin samaniya,gashin jikinta ya kamadawuta, Muzaffarya sake subutowa ya taho kasa ya fado akan wani kutturen itace dake kusa da wajen ya bugu da buguwa mai tsananin nan take ya suma,wata daga cikin mikiyoyin ta sake kai masa sura zata dauke shi ta tashi sama da shi, Zarkiyu ya sanya kibiya ya harbe ta itama ta hallaka,tun kafin ta kai ga daukarsa,yay i sauri ya tafi gare shi, ya girgiza shi ya ga baya motsi alamar ya suma, ya dauke shi ya maida shi cikin kohon dutsen da y ace masa kada ya fito daga cikinsa ya kwantar da shi,ya sake fitowa ya ci gaba da hallaka wadannan mikiyoyi da yake kafsawa da su har sai da ya karar da su baki daya. Bayan Zarkiyu y agama hallaka wadannan mikiyoyin ya duba ya ga babu sauran wata mikiya dake shawagi a sararin samaniya sannan ya maida takobi da sauran kayan fadansa ya koma cikin kogon dutsen nan da ya ajiye Muzaffar ya ta dashi har a wannan lokacin yana cikin halin suma bai farfado ba, ya matsa kusa da shi ya kwance gorar ruwar dake jikin damarar Muzaffar ya zuba a hannunsa ya soma shafa masa ruwa a fuskarsa bayan wani lokaci Muzaffar ya farfado daga suman da yayi ya bude idanunsa, da y agama dawowa hayyacinsa ya yunkura ya tashi zaune, da kyar saboda tsannin buguwa da yayi da kututturen itacen da ya fado a kansa ya duba ya ganshi a cikin kogon dutsen da Zarkiyu ya hane shida fitowa daga cikinsa gakuma Zarkiyu zaune a gefensa yana dubansa na take ya gane cewa Zarkiyu ne ya kubutar da shi daga hannun mikiyar da ta kusa hallakashi, ya dawo da shi cikin wannan kogon dutsen. Bayan Muzaffar y agama dawowa hayyacinsa sosai Zarkiyu ya dube shi cikin fushi y ace da shi "Kai dai ka kasance bil'adama mai matukar kafiya da bibiyar son zuciyarka ka 85 harafi Tafiyar ajali aikata abin da aka hane ka da aikatawa, sai da na haneka da itowa daga cikin wannan kogon duts har zuwa sand azan dawo gare ka, ko kuma nab aka umarnin ka fito daga cikinsa, amma sai ka zama mai bijirewa abin da na umarce k aka fito ba tare da na umarce k aba, wannan shi ne kuskure na uku da ka aikata a gare ni cikin tafiyar da muka fara tare da kai, kuma idan baka zama mai kiyaye abin da na umarce k aba ka ci gaba da aikata irin wannan kuskure,tokuwa na kusa rabuwa d akai zan tafi na barka cikin wannan tsibiri ka hallaka b azan taimaka maka ba”. Muzaffar yayi shiru yana sauraronsa cikin nadamar abin da ya aikata sai da Zarkiyu ya gama bayaninsa sannan ya bash hakuri akan kuskuren da ya aikata, Zarkiyu y ace da shi wannan ta wuce sai dai ka zama mai kiyaye abin da zan umarce ka nan gaba matukar kana son tsira daga hallaka ka fita daga wannan tsibiri ka koma birninku,idan kuwa ba zaka zama mai kiyayewa ba, hakika hallaka za ta wanzu a gare ka cikin wannan tsibiri, daga nan ya umarce shi da cewa ya tashi su ci gaba da tafiya domin su fita daga wannan da'ira kafin rana ta sake faduwa wata musibar ta sake wanzuwa a gare su,haka Muzaffar ya tashi suka ci gaba datafiya cikin wannanrana yana dogarawa da fekakken itacen da Zarkiyu ya bashi saboda tsanani buguwa da yayi sanda ya fado a kan kututturen itace. ** Al'amarin Waziri Huwaisu kuwa bayan da gimbiya ZUhiriya ta amince da shawarar da ya bawa dansa Najiranu ta amince da bkatarsa ta sake bashi damar ya koma ga wannan jarumi dmin karbo takobin dake hannunsa bisa ga sharadin da ta kafa masa na cewa ian bai samu nasara akan jarumi ba, ba zai sake neman wata bukata a gare ta ba, da gari ya waye tunda sanyin safiya waziri Hawaisu ya kama hanyar dajin da bukkar Boka Musalamatu take ya y tafiya har ya isa bigirensa yana zuwa sauka da ga kan dokinsa ya shiga cikin bukkar ya tadda boka Musaila zaune akan bakin buzunsa na aikin 86 harafi Tafiyar ajali sihiri,ya fadi gabansa ya kai gaisuwa tare da kirari irin na girmamawa kamar yadda ya saba a duk sanda ya zo da watabukata gareshi. Boka Musaila ya amsa masa tareda tambayarsa cewa "Me ke tafe da kai ya kai Wziri Hawaisu sanar da ni bukatarka yanzu na wanzar da ita akan duk abin da kake so". Waziri Hawaisu yace da shi "Na dawo gareka ne akan maganar auren dana Najiranu da gimbiya Zuhuriya yar SARKI Sa'adul gamidi ya kwashe duk labarin abin da ya faru tsakaninsu ya sanar da shi tare da sharadin da ta kafa masa na cewa sai ya karbo takobin dake hannun wani jarumi idan yana so ta amince da maganar aurensa da yadda suka yi da wannan jarumi a haduwarsa ta farko ya kasa samun nasara akansa daga karshe y ace da shi "Don haka na zo gare ka ne domin neman taimako dana Najiranu ya samu nasara akan wannan jarumi ya karbo takobin dakehannunsa, tunda Gimbiya ZUhuriya ta sake bas hi damar komawa gareshi don karbo wannan takobi". Da Boka Musailamatu ya ji wannan bayani na waziri Hawaisu sai ransa y abaci zciyarsa ta harzuka ya fusata da fushi mara misaltuwa, ya dubi Waziri Hawaisu y ace da shi "Yanzu a duniya akwai wani bul'adama da ya isa wanzar da rashin nasara a cikin shirin da mukeyi na mallakar sarautar birnin AMbar ta dawo hannunka, shin da akwai wani jarumi da jarumtakarsa zata hana danka Najiran ya cimma nasarar farautarsa zata hana danka Najiranu ya cimma nasarar samun amincewar Gimbiya Zuhuriya akan maganar aure a tsakaninsu, nayi rantsuwa da ababen bauta ta tare da karfin tasirin tsafi da sihirin da na gada a wajen mahaifina, sai na hallaka wannan jarumi idan hallaka shi ka ke so a yi, ko kuma na kaskantar da jarumtarsa, danka Najiranu ya samu nasara akansa" Waziri Hawaisu yay i sauri y ace da shi "Ba na bukatar ka hallakashi sai dai ka kankantar da jarumtarsa yadda dana Najiranu zai iya samun nasara akansa, domin kuwa sharadin da ta kafa masa ta ce da shi kada ya sake ya hallaka wannan 87 harafi Tafiyar ajali jarumi koda ya samu nasara akansa, abin da take bukata kawai shi ne ya karbo takobin dake hannunsa ya kawo mata domin ta amince da maganar aure a tsakaninsu". Boka Musailamatu ya ce da shi "Wannan ya fi komai sauki a cikin lamarina na aikin bokanci da sihiri, kuma mai wanzuwa ne cikinabin da na kudurta zan aikata daga alkaluman tsafina" ya daga karkashin bakin buzun da yake zaune ya daukowani farin garin magani kamar toka nannade a cikin wani ganye ya mikawa waziri Hawaisu sannan y ace da shi, Katafi da wannangarin maganin idan ka komagida sai ka zuba shi ac ikin gorar nan ta aikin sihhiri da ku ka yi amfani da ita ku kajuye ruwan da yakecikinta akan bawanka da siffarsata komairin ta Muaffardan gidan liman Adnan, ka zuba akan garin maganin ka bawa danka Najiranu ya tafi da shi wajen da za su hadu da wannan jarumi idan sun fara kafsawa da shi yayi kokarin ya watsa masa ruwan da ke cikin gorar sihirin a jikinsa, idan har ruwan ya taba jikin wannan jarumi duk wata jarumta ko sadaukantaka da ke tare da shi zata raunana ya kasa aikata komai hard an ka ya samu nasarar karbar takobin daga gareshi, kuma ba zai sake dawowa hayyacinsa ba,har sai bayan wani wa'adi mai tsawo danka Najiranu ya karbi takobin daga gare shi ya tafi,kuma daga yanzu idan kana da wata bukata a gare ni, da kake son ganina kada kace sai ka taso daga cikin birnin AMbar ka taho gareni zan baka wani zoben azurfa dake tare da dalasumai na aikin sihiri ka sanya a hannunka,a duk sand aka tashi nemana kake da bukatar ganina sai kamurza zoben da zan baka tare da ambaton suna na sau uku, ba dadewa z aka ga na bayyana gareka domin amsa bukatarka ba sai kasake tasowa ka taho gare ni ba". 88 harafi Tafiyar ajali Da y agama yi masa wannan bayani ya sanya hannnsa na hagu a cikin katuwar kwatarniyar dake ajiye a fegensa na dama cike da wani irin bakin ruwa ya tsoma zoben daga cikinta ya mikawa waziri Hawaisu. Waziri Hawaisu ya s hannu ya karbi garin maganin cikin matukar murna da farin ciki, daga nan kumayayi godiya ga Boka Musaila ya tashi ya kama hanyar komawa gida. Da isarsa gida ya kira dansa Najiranu ya sanar da shi yadda suka yi da Boka Musaila, sannan ya dauko gorar sihirin nan da suayi amfani da shi wajen zubawa bawan nan nasa ruwan da yake ciki gorar siffar ta rikida ta koma irin ta Muzaffar,ya zuba garin maganin a ciki tare da ruwa kamar yadda Boka Musaila ya umarce shi sannan ya baiwa Najiranu domin ya tafi da ita ranar da zai koma wajen wannan jarumi, ya watsa masa ruwan ajikinsa don samun nasarar akansa ya karbo wannan takobi dake tare da shi.Najranu ya karbi gorar ya ajiye a wajen da yana mai sauraron zuwa ranar da suka yi alkawari da gimbiya Zuhuriya akan cewa ya koma wajen wannan Jarumi don karbo takobin da take hannunsa. Bayan cikar kwanaki biyar kamar yadda suka yi alkawari da Gimbiya Zuhuriya, sai Najranu ya sake yin shiri don tafiya wajen da suka hadu da wannan jarumi da nufin karbo takobin dake hannunsa, da yake yay i imani da maganar mahaifinsa da ta Boka Musaila akan cewar shi mai samun nasara ne a cikin wannan ranar matukar ya watsa masa ruwan da ke cikin wannan gora na sihiri, bai dauki wani makamii ko kayan fadamasu yaw aba, ban da takobi da garkuwar sa sai wannan gora na aikin sihiri da aka bashi bayan y agama shiryawa ya tafi ya kama dokinsa yah au ya nufi hanyar da takefita bayan gari ta 89 harafi Tafiyar ajali kofar kudu ya tafi wajen da suka hadu da wannan jarumi a karawarsu ta farko. Ita kuwa Gimbiya Zuhuriya a wannan ranr da ta yi musu alkawarin ya koma wajen wannan Jarumi domin karbo takobin da take hannunsa, tun kafin Najranu ya gamashirinsa ya fito daga gida tuni ta gama nata shirin ta yi irin shigar da take yin a bakaken kaya tare da sulke da hular bakin kwalkwali da take rufe mata fuska yadda ba za a iya gane cewa mace ce ba, ta dauki wanann akobi da aka yi wa marikarta ado da zinare, ta kama dokintata hau ta fita ta kifar bayan gidan ba tare da kowa ya sani ba, ta nufi wannan waje da suka hadu da Najranu a karawar da sukayi da farko tana zuwa wajen ta sau cikin duhun itatuwa ta shiga ta buya tana jiran isowarsa. Bayan wani lokaci da zuwanta sai ga Najiranu tafe akan dokinsa yana sassarfa yana zuwa daidai wajen ya ja linzamin ya tsaya yana dube duben ya ga ta inda wannan Jarumi zai bayyana gare shi, ita kuma gimbiya ZUhuriya da ganin ya iso sai ta fito daga cikin duhu itatuwan da take boye ta bayyana a gare shi, Najiranu ya dubi wannan mahayi da ya bayyana gare shi, Nairanu ya dubi wanna mahayi da ya bayyana gare shi ba tare da ya san cewa Gimbiya Zuhuriya ce bay a ce da shi. "Na dawo gareka ya kai wnan bijirarren mutum makaskancin bawa, domin na karbi takobin da ke hannunka kamar yadda na sanar da kai tun farkon marra, samun nasarar da ka yi akaina tun a wancan okaci ya san а dawo gareka domin na maida ramuwa, tunda har gimbiya ZUhuriya ta sake bani damar na dawo gareka domin karbar wannan takobi to kuwa zan tabbatar da isa da karfin ikona akanka, zan kuma karbi wannan takobi daga gareka domin na kaiwa Gimbiya ZUhuriya saboda ta amince da maganar aurea tsakanina da ita". 90 harafi Tafiyar ajali Gimbiya tana jin abin da yake fad aba ta dau da maganarsa b aba tare da ta tanka masa don kada ta yi Magana ya gane cewa mace ce koma ya gane muryarta, shi kuma Nairanu da ya ga haka sai yay i sauri ya zare takobin da take hannunsa ya zaburi dokinsa ya tasar wa wannan mahayi a fusace da nufin far masa ya karbi takobin daga gare shi, da Gimbiya Zuhuriya taga haka sai yayi sauri itama ta zare tata takobin ta tareshi suka soma kafsawa, tun a haduwarsu ta farko gimbiya Zuhuriya ta kai masa wani gawurtaccen sara, Najiranu yak are da garkuwar dake tare d ashi, garkuwar ta yi karamai tsananin karfi irin ta haduwar karfee da karfe tartsastin wuta ya zubo daga jikinta saboda musibar kaifin takobin dake hannun gimbiya ZUhuriya. Najiranu yay i baya taga taga tamkar zai fado dagakan dokinsa saboda karfin sarar da ta kai masa wanda yayi matukar gigiza shi ta sake kai masa wani saran ya goce kaifin takobin ya bi iska ba tare da ta same shi ba, yay i kokarin maida martani da kai hari da ta sa takobin kafin ta sake kai masa wani sara Gimbiya Zuhuriya ta kare saran da tata takobin suka ci gaba da kafaswa cikin arangama da dauko ba dadi mai tsanani kura ta turnuke ta kuduru a tsakaninsu. Saboda yawan Zaryada zamiyar da zamyar da dawakansu suke yia wajen tamkar wata rundunar mayaka ne suke kafsa fada a filin daga. Sun dauki lokaci mai tsawo suna fafatawa ba tare da Najiranu ya ga alamar samun nasara akan wannan jarumi ba, don haka ya soma kokarin dauko gorar nan na aikin sihiri dake tare da shi yana kwantoshi daga damararsa ya tasarwa wannan mahayi da nufin watsa masa ruwan dake cikinsa, domin ya samu nasara akansa,ita kuwa gimbiya Zuhuriya da ta lura da abin da yake hannunsa tun kafin ya karaso gare ta don haka yana watso ruwan da yake cikin gorar sai ta yi sauri ta goce ruwan ya wuce ya zuba a kasa ba tare da ya same ta ba. Kafin ya sake watso mata ragowar ruwan da yake cikin gorar sihirin ta yi sauri ta tare shi cikin matukar azama da zafin nama ta sanya kasan takobinta ta daki gorar dake hannunsa, 91 harafi Tafiyar ajali gorar ya kubcedaga hannunsa ya tashi sama akan iska ruwan da yay i nufin watso mata ya komaya juye a ikinsa baki daya, nan take Najranu ya wuntsule daga kan dokinsaya fado kasa yay i wanwar tamkar wanda aka yiwa saran mutuwa da takobi a fagen daga. Gimbiya Zuhuriya ta sake daga takobin da niyar kai masa sara amma sai ta ga tunda ya fado daga kan dkinsa bai kara komotsawa ba, bare ya samu damar tashi ko kare saran takobin da zata kai masa, ta fasa kai saran gare shi ta ja linzamin dokinta ta tsaya a gabansa, ta dube shi ta ga yana numfashi kuma idanunsa a bude amma bay a iya motsawa ko dan yatsansa daga inda yakekwance tamkar wanda ya suma,ta yi matukar mamakin wannan al'amarin da ya faru gareshi, lokaci guda kuma sai ta fahimci cewa akwai wani abu na aikin sihiri tatare da wannan ruwan da yayi nufin watsa mata bai samu nasara ba, ruwa ya koma ya zuba a jikinsa ta yi godiya ga Allah da ya kiyaye ta daga sharrin da mugun nfin da Najiranu yay i nufin aikatawa a kanta hadi da aikin sihiri, wanda da ya zuba mata ruwan da ke cikin gorar nan it ace zata kasance a cikinw annan al'amarin ya samu nasarar karbar takobin aga gare ta ta hanyar aikin sihiri ba ta hanyarjarumta ba. Bayan gimbiya Zuhuriya ta gamawannan tunani tanashirin sakin linzamin dokinta ta tafi sai ta hangi wani zobe na azurfa a hannun Najiranu don haka ta sauko dag akan dokinta ta kama hannunsa ta cire zoben domin ta tafi da shi tare da gorar ruwan da yay i nufin watsa mata saboda su zama shaida a gare ta,a duk sanda Najiranuya sake dawowa gare ta bisa ga alkawarin da suka yi, daga nan ta kma dokinta ta hau ta nufi hanyar komawa gida tana mai tunanin yadda Najiranu ya wanzu a cikin aikin sihiri da shirka don kawai ya samu biyan bukatarsa ta neman aurenta. ** Su kuwa su Muzaffar da dattijo Zarkiyu dake tafiya a tsakiyar daji cikin tsibirin Hijusiya bayan da suka bar wajen da Zarkiyu ya hallakawadannan mikiyoyin suka ci gaba da tafiya, 92 harafi Tafiyar ajali basu sake tsayawa a ko in aba sai da suka fita daga cikin wannan da'irasuka riski wani waje ma matukar kyawun yanayi a wani karancin tsanuka da kwazazzabai a wajen, haka kumababu sarkakiya da duhun itatuwa irin na bakn dajin da suka wuce a baya, ga ciyawa ta yi kore shar tare da furanni masu dadin kamshi, sassanyar iskatana kadawa tare da wanzar da ni'ima a cikin wannan yanayi Muzaffar yay i mamaki da ganin wannan waje a cikin wannan tsibiri mai matukar kunci da musibu marasa misaltuwa, sai dai tunda suka shigo wannan waje ya lura da cewa dattijo Zarkiyu yana taka-tsantsan da kiyayewa a duk inda suka wuce kamarmai fargabar kada wani abu ya farmake su ya hallaka su. Haka suka ci gaba da tafiya har rana ta fadi sannan suka nemi waje suka yada zango domin su kwana kafin gari yaw aye, su ci gaba da tafiya, da dare yay i bayan sun idar da sallar magariba da isha'l Muzaffar ya kwanta barci don ya huce gajiya dake tare da shi, shi kuma dattijo Zarkiyu ya zauna daga gefe yana jan casbaharsa ya shiga lazimi, kafin wani lokaci barci mai nauyi ya dauke Muzaffar a cikin barcin nasa ya rika mafarki mahaifansa tare da yan uwansa da kuma masoyiiyarsa Gimbiya Zuhuriya wanda a yanzu yay i nisa su cikin wannan tsibiri na Hujiyasa da aka kawo cikinsa. Yana cikin wannan bacci ne can da kusan sulasainin dare sai Muzaffar ya ji dattijon Zarkiyu yana tashinsa daga bacci tare da umartarsa cewa ya tashi su ci gaba da tafiya, Muzaffar ya farka daga baccin ba tare da ya so ba, ya dubi Muzaffar Zarkiyu ya ce da shi. "Me yasa zaka ce mu ci gaba da tafiya a cikin wannan dare ba za a bari gari yaw aye ba, hakika na zamo gajiyayye saboda yawan tafiyar da mua yi ga kuma ciwo na buguwar da nay i a jikina". Dattijo Zarkiyu ya dube shi cikin tsawatarwa yace da shi "Umarni nake baka cikin lamarina ba ina neman shawarar a gareka ba, kuma na hane ka da yin tambaya a gareni tun a farkon marra, amma baka zama mai kiyayewa abin da na 93 harafi Tafiyar ajali umarce k aba, babu shakka kana cikin kuskre da zai ya sanyawa na tafi na barka cikin wannan taisbiri ka hallaka matukar b aka zama mai kiyaye abin da na umarce ka da kiyayewa ba" Muzaffar bai sake cewa komai ba, ya tashi ya bi Dattijo Zarkiyu suka kamahanya suka ci gaba da tafiya cikin wannan dare, kafin gari yaw aye sun fita daga cikin wannan dausayi mai maukar ni'ima sun shiga cikin wani lardi ma'abocin tsaunuka da duwasu, bbu itatuwa ko ciyayi a wajen sai dai rairayi da ya mamaye ko ina tamkar tsakiyar sahahara da gari yaw aye, bayan sun idar sa sallar asubahhi suka ci gaba da tafiya da rana ta keto sai gaba daya da'irar wajen ta dauki zafi iskar da take kadawa ta rika busowa da dumamar yanayi tamkar duk wata halitta da ke wajen zata kama da wuta, ta kone saboda musiba, gashi babu kotsiro na ciyawa bare wata bishiya da za su samu inuwar da zasu zauna su huta. Hhaka suka ci gaba da tafiya a cikin wannan lardi mai tsananin dumamar yanayi da zafi har sukashafe tsawon kwanaki biyar ba tare da sun fita daga cikinsa ba, a rana a shida daga cikin ranekun tafiyarsu ne sua tsakiyar tafiya sai suka hangi wata tawagar jama'a matafiya sun keto ta gabansu sun tunkaro inda suke, suna dauke da jajayen tutoci a hannunsa masu tambarin rana, tare d amakamai na yaki iri daban daban kumababu wanda yake sanye da wata sutura a jikinsa ban da bante da fata da suka daura. "Muzaffar yayi matukar mamamki da ganin wannan tawagar jama'a da suka tunkaro su, saboda ganin sun yi kama da jama'ar mutane kuma rabon da ya ga wani mutum bil'adama kamar sat un ranar da ya baro birninsu aka kawo shi wannan tsibiri, shi kuwa dattijo Zarkiyu da yake ya san cewa ba jama'ar mutane bil'adama bane kamaryadda Muzaffar yake zato wasu tawagar bakaken aljanu e ma'abota bautawa rana suka shigo wannan tsibiri domin gudanar da ayyukansu na bauta kamar yadda suke yi a kowacce shekara don haka ya dubi Muzaffar y ace da shi. 94 harafi Tafiyar ajali "Zany i gargadi a gare ka bisa ga wannan jama'u da suka tunkaro inda muke kada ka sake ka yiwa wani Magana daga cikinsu, kuma koda wnai yayi maka Magana kada ka kula al'amarinsa ko ka saurare shi, idan ka kiyaye abin da na umarce ka hakika zamu wuce ta cikin wannan ayarin jama'a ba tare da sun samu ikon aikata wani al'amari na cutarwa a gare mu ba. Muzaffar ya amsa da cewa "Zan kiyaye abin da ka umarce ni da aikatawa, a lokacin da yake maganar hankalinsa yana kan ayarin jama'ar ba akan dattijo Zarkiyu ba daga nan suka ci gaba da tafiya har suka karaso inda tawagar jama'ar suke tafe akahadu, suka ratsa ta cikinsu suna tafiya babu wanda ya yiwa wani Magana a tsakaninsu, jama'ar bas u ko dubi su Muzaffar ba bare su kula al'amarinsu tafiya kawai suke yi ya zuwa inda suka sag aba babu saurarawa daga cikinsu akwai mata da kananun yara da tsofaffi, amma sashin su baya yiwa sashin su Magana babu mai tausayin yaro ko tsoho tafiya suke tamkar babu wanda ya damu da wani a tsakaninsu. Muzaffar suka ci gaba da tafiya suna ketawa ta tsakanin wadannan jama'a babu wand aya damu da al'amarinsu da yake jama'ar sna da matukar yawa sai da rana ta kusa faduwa, sannan suka kai karshensu bayan wucewar wannan jama'a daga karshe sai ga wata tsohuwa daga cikinsu da suka barta a baya, tana tafe tana dogawara da sanda saboda yawan tsufa kuma gas hi ta yi matukar gajiya da galabaita sannan dafa cikin jama'ar da suke tafe tare da su babu mai tausayinta bare ya taimaka mata tana isowa wajen da Muzaffar yak e sai ta dube shi ta yi masa Magana cikin rawar murya irin ta stufa da galabaita tace da shi. "Yaaro kataimakamin da ruwa na sha kada kihirwa ta kaini ga halaka". Tausayin tsohuwar nan ya kama Muzaffar saboda ganin halin da takeciki,ya tafi gareta domin ya taimakamata dattijoZarkiyu dake gaba yana tafiya bai san da cewa Muzaffar ya tsaya ba, sai da ya juyo baya sai ya hange shi tare da wannan tsohuwa ya kwanto salkar ruwa dake tare da shi ya mika mata zata karba ta sha, dattijon Zarkiyu ya daka masa tsawa cikin madaukakiyar murya mai karfi domin kada ya bata salkar ruwa amma kafin Muzaffar ya ji tuni har tsohuwar ta karbi salkar ruwan ta kai bakinta ta soma sha. Da kai ruwan nan bakinta ta sha sai ta yi wani irin karaji da gunji mai tsananin karfi da ban firgice ta suri Muzaffar ta yi jifa da shi jikin wani karamin dutse dake kusa da wajen karajin da ta yi ya sanya sauran jama'ar 95 harafi Tafiyar ajali dake tafe tare da ita suka dakata da tafiyar da sukeyi suka juyo gare ta, ta sake yin karaji ta daga hannayenta sama nan take sai ta rikayin girma daga siffar da zaka iya kiranta mutum bil'adam ya zwa wata irin siffa maimatukar ban tsoroda razanarwa, idanuwanta suka koma ja jawur kamar garwashin wuta wasu zaro-zaro hakoramasu kama a fike suka fito daga cikin bakinta, tare da wnai irin gashi da ya lullube dukkanin fatar jikinta. Muzaffar yai matukar mamakin wannan al'amari ya zabura ya tashi cikin sauri ya dauki fekakken itace da yakeyin amfani da shi wajen yin fada ya tare ta kafin ta karaso gare shi,tsohuwar nan tana zuwa ta kaimasa dukada sandar da take hannunta, Muzafffarya kare da nasa makamin amma sai da yay i baya taga taga kamar zai fadi saboda karfin bugun da ta kawo masa nan takeya ji a ransa cewa wannan tsohuwa ba zata zamo daga cikin jinsin mutane bil'adama ba sai dai ta kasance daga cikin jama'ar aljanu,ya kuma tuna maganar dattijo Mubasshir da ya sanar da shi cewa duk wanda ya ganin cikin wannan tsibiri ba utum bane bil'adama irinsa sai dai Aljani domin jama'ar mutane ba za su iya shigowa ciki wannan tsibiri su rayu ba. Tsohuwar nan ta sake kai masa duka da sandar da take hannunta Muzaffar ya goce ta sauka a jikinwani karamin dutse da ta jefa

Chapter 7 of 9