Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 9
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels TAFIYAR AJALI SHEHU USMAN MOHD Tafiyar ajali Sa'adul gamidi wani Sarki ne dake sarautar birnin AMbar can gabas da kogin basara. Allah yay i masa baiwa da kwarjini da kamala tare da soyayya daga jama'ar da yake shugbanta, don bin umarnin abin da ya shardanta musu sabda adalci da kyautatawa mutanensa, mai son addini tare da tabbatar da an kiyaye hukuncin ubangiji a dukkanin masarautarsa, tun bayan da ya zama Sarki a daular AMbar ya kawar da duk wata bidi'ata al'da da jama'ar birnin suke aikatawa. Yasa aka fatattaki bokaye yan tsubbu da masu aikata duk wani nau'l na aikin sihiri a cikin birninsa. Ya kuma tabbatar da shari'ar musulunci a dukkanin masarauyun dake karkashin birnin Ambar. Tun daga wannan lokaci manyan-manya bokaye ma'abota aikin sihiri da tsafi, wanda Sarki Sa'adya sa aka atattake su daga birnin AMbar suka shiga yunkurin daukar fansa a kansa. Dan ganin bayansa su hallakashi ko kuma su raba shi da sarautar birnin AMbar, amma cikin hukuncin ubangiji da kiyayewarsa babu wani abu na cutarwa da ya taba samun Sarki Sa'adul Gamidi bare su sa ran samun nasara akan hi. Sarki Sa'ad yana da wata kyakkyawar 'ya mai suna ZUHURIYA wadda it ace babba c ikin 'ya'yansa. Kasancewar bayan da aka haife ta Sarki Sa'ad bai sake samun haihuwa ba, har sai bayan shekaru goma sha takwas, sannan dukkanin matansa suka ci gaba da haihuwa. Dan haka Sarki sa'ad bas hi da wani da babba a gabansa, ban da gimbiya Zuhuriya. Dukkanin sauran 'ya'yansa yara ne kanana masu karancin shekaru. Gimbiya Zuhuriya ta taso cikin samun tarbiya da kulawa irinta soyayyar da da mahaifinta Sarki Sa'add 2 harafi Tafiyar ajali yake nuna mata kasancewar babbar ya a gare shi ta farko, da yake tana sha'awar koyan fada da makami da yadda ake afatawa a fagen fama. Ta samu horo daga mahaifinta Sarki Sa'ad kasancewarsa cikakken jarumi kuma sadauki da ya shahara a fagen iyya fada da kowane irin makami. Tun bayan da gimbiya Zuhuriya ta tasata kai munzalin isa aure. Sai masoya suka fara bijiro da bukatarsu ta neman auranta ga Sarki Sa'adul gamidi 'ya'yan sarakuna da manyan attajirai masu abin hannu duk wanda ya gabatar da bukatarsa ta neman auran gimbiya Zuhuriya gare shi sai Sarki Sa'adya bas hi dama cewa ya tafi ya nemi soyayyar daga gare ta idan Gimbiya ZUhuriya ta amince tana kaunarsa, shi kuma yayi masa alkawarin zai bashi auranta. Masoya Gimbiya Zuhuriya da dama sun gabatar da kansu gare ta dan neman soyayyarta, amma ita taki mallaka tata soyayyar gare su, saboda tana ganin babu wanda ya dace da irin mijin da take muradin ta aura. A ra'ayin Gimbiya ZUhuruiya ta fi son ta auri namiji mai ilimi addini kuma cikakken jarumi da zai iya gogąyya da kowanne irin Sadauki a fadin duniya koda kuwa bad an Sarki ba ne shi ko kuma attajiri da yawa daga cikin 'ya'yan Sarakuna da attajirai da suke zuwa gare ta da zummar neman auranta, babu wanda ya iya koda kwakkwaran rikon takobi irin na Jarumta, bare ace ga wanda aka taba fita da shi fagen yaki a ka ga irin jarumta da bajintarsa. Dan haka taki amincewa ta nuna begen ga daya daga cikin wadannan 'ya'yan sarakuna da attajirai da suke neman auranta. Sarki Sa'adul gamidi yana da wani waziri mai suna HAWAISUL_MUNAN da yake a matsayin waziri tun zamanin mahaifin Sarki Sa'ad yana sarautar kafin ya rasu a nada Sa'adul gamidi Sarki. Waziri Hawaisu mutun ne mai nuna kyakkyawan hali ga Sarki Sa'ad da sauran jama'ar birnin a zahiri amma a badini mutanne mai mummunan hali na fajirci da rashin tsron Allah 3 harafi Tafiyar ajali babu abin da yake buri a rayuwarsa illa ya ga sarautar birnin AMbar ta dawo hannunsa tun zamanin mahaifin Sarki Sa'ad yana Sarauta kafin ya rasu a nada Sa'adul gamidi Sarki. Bayan rasuwar mahaifin Sarki Sa'ad Waziri Hawaisu ya so a maida sarautar hannunsa, a nada shi Sarki, amma sai 'yan majalisar masarautar suka ki amincewa da kudirinsa. Suka nada sa'adul hamidi Sarki kasancewar shi ne mai gadan sarautar, Waziri Huwaisu yay i matukar bakin ciki da faruwar wannan lamari nakin nada shi Sarki da yan majalisar masarautar suka yi, amma daga baya sai yay i farin ciki da ya ga cewa Sarki bas hi da wani dan uwa, ko kuma kani da zai gaje shi, idan ya rasu, hakan kuma bas hi da wani babban da namiji da zai zama magajinsa bayan ransa. Don haka tilas Sarautar birnin ta dawo hannunsa da zaran an ce babu ran Sarki Sa'adulgamidi. Tun daga wannan lokaci sai waziri Haiwausu ya shiga bin manyan bokaye. Matsafa da masana aiki sihiri musamman wanda Sarki Sa'ad ya sa ake fatattake su aka kore su daga birin. Don neman taimakonsu aka yadda zai samu nasarar hallaka Sarki Sa'adul gamidi Sarautar birnin ta dawo hannunsa. Tsayin kowacce rana Waziri Haiwaisu bas hi da wani aiki sai shirye-shiryen makirici da kulla yadda za su haklaka Sarki Sa'adaul gamidi da shi da manyan bokaye da yake neman taimako daga gare su. Amma cikin kiyayewar ubangiji da buwayarsa babu wani abu na cutarwa da ya taba samun Sarki Sa'adbare su saran samun nasara akan kudirinsu na hallaka shi Manyan-manyan bokaye masana alkaluman sihiri da dama sun sha sanar da shi cewa dole sarautar birnin Amzar za ta dawo hannunsa wata rana daga cikin wa'adin rayuwarsa. Amma har yanzu lamarin yaki tabbata, kuma bai ga wata alama ta samun nasara ba. Daga ire iren bayanan da bokayen suke yi masa na bincikensu cikin alkalaman sihiri da suka sanar da shi, tun yana yarda da maganar bokayan yana gasgata abin da suke sanar da 4 harafi Tafiyar ajali shi, har zuciyarsa ta soma rauni ya karaya saboda rashin samun nasara cikin wannan lamari tsawn lokacin da ya sanya kudirin hallaka Sarki Sa'adulgamidi a ransa. Daga cikin masoyan gimbiya Zuhuriya akwai babban dan waziri Hawaisu mai suna najiranu da yake matukar kaunarta ammaita gimbiya Zuhuriya daidai da bugawar numfashi ba ta kaunarsa a zuciyarta, ya gabatar da bukatarsa ta neman begenta a gare shi amma ta nuna masa rashin amincewa da karbar soyayyarsa a gare ta dan yay i hakuri da Najiranu ya fahimci hakasai ya koma ga mahaifinsaWaziri Hawaisu ya sanar da shi irin begen da yakeyiwa Gimbiya Zuhuriya yar Sarki Sa'ad da bukatarsa ta ya nema masa auranta wajen mahaifinta Sarki sa'ad Da waziri Hawaisu ya ji wannan bayani na dansa Najiranu sai wani tunani irin na makirci ya fado a ransa, yay i hangen cewa wannan ma wata hanya ce ta samun nasarar dawo da sarautar birnin AMbar gare shi, idan har dansa yana auran Gimbiya ZUhuriya babbar yar Sarki Sa'adul gamidi. Yana daga abin da zai kara tabbatar da si ya zama Sarki idan ya samu nasarar hallaka Sarki Sa'ad kuma da yake tsufa ya fara cin karfinsa dan ya fi Sarki Sa'ad yawan shekaru idan ma ba'a nadashi Sarki ba dole dansa za a bawa Sarautar tun da shi ne yake auran babbar yar Sarki dan haka Sarautar dai tana tare da shi. Da ya gama wannan tunani sai y ace da dansa Najiranu 'hakika nay i matukar farin ciki da kai yi tunani ka auri Gimbiya Zuhuriya yar Sarki sa'ad. Dalilina kuwa shi ne na dade ina buri da muradin nag a na karbi sarautar birni nan ta dawo hannu na tun zamanin mahaifin Sarki Sa'adyana sarauta kafin ya rasu a nada sa'ad Sarki dan haka zan nemamaka auran gimbiya ZUhuriya saboda na kara samun damar mallakar sarautar birnin nan ta dawo hannuna. Idan ma yan majalisar masarautar basu yarda na zama Sarki ba dole dai kai za a nada Sarki a birnin tun da kai ne kakeauran babbar yar Sarki kuma bas hi da maigadan sarautar 5 harafi Tafiyar ajali daga danginsa. Sannan ba zai yuwu a nada mace sarauta a babbar daular musulunci ba" Da Najiranu ya ji wannan bayani na mahaifinsa sai ya cika da matukar murna da farin ciki saboda jin cewa idan ya auri Gimbiya Zuhiya zai iya zama Sarki a birnin AMbar bayan rasuwar Sarki Saʼad da yake Sarki Sa'ad yay i tafiya a wannan lokaci dan kai ziyarar birnin amininsa d ake yamma da kogin basra sai Waziri Hawaisu y ace da dansa idan Sarki sa'addulgamidi ya dawo zai gaatar da bukatarsa ta neman masaauran gimbiya Zuhuriya. Najiranu ya sake cika damatukar murna da farin ciki sannan ya tashi ya fita daga dakin mahaifinsayana mai alfahari da jin dadin abin da mahaifinsa ya ambata tun daga wannan rana Waziri Hawaisu ya kasance cikin shirin ganin dawowar Sarki dan ya gabatar da bukatarsa gare shi ta neman auran gimbiya Zuhuriya ga dansa Najiranu ** A cikin birnin akwai wani matashin Jarumi, kuma Sadauki mai suna Muzaffar, mahaifinsa shi ne babban limamin birnin kuma yanada wadatar ilimi addini.allah ya halicci Muzaffar kyakkyawan kuma ga jarumta da rashin tsoro ko fargaba a babu a tare da shi sai dai kuma Muzaffar yay a kasance hatsabibi, kuma shhu'umin gaske a cikin lamarin rayuwarsa babu abin da yake so illa ya ga wani abu da ya addabi jama'a ko kuma yake hallaka mutane ana tsoron tunkarar inda yake shi kuma ya tafi gare shi ya haike masa ya hallaka shi. An taba samun wani gawurtaccen maciji da ake tunanin yana tare da aljanu a jikinsa. Cikin wata tsohuwar rijiya tsawan shekaru ashirin ya addabi jama'a, yak an fito daga rijiyar ya hallaka mai karar kwana.ga duk wanda ya kuusanci inda yake, amma Muzaffar ya tafi gare shi ya shiga har cikin rijiyar ya hallaka macijin ya Π6 harafi Tafiyar ajali raba jama'a da musiba. Wannan ne ya sa jarumtrarsa ta shahara a wajen dukkanin jama'arbirnin aka sanshi. Koda baka taba ganinsa da idanunka ba z aka ji labarinsa ya karade ko ina. Muzaffar yana da matukar karambani da rashin ji, kasancewar shi ne babban dansa da yake fatan ya gajesi ya zama babban limamin birnin koda bayan ransa amma babu abin daya sauya daga dabi'ar Muzaffar da hatsabibancinsa. Sai dai mahaifin nasa ne ya hakura ya ci gaba da yi masa addu'a akan Allah ya raba shi da wannan hali na shi. Duk abin da yake faruwa a birnin AMbar na labarin Jarumta da bajintar Muzaffar gimbiya ZUhuriya tana samun labara sai dai bata taba ganin Muzaffar da idanunta ba, bare ta a wani abu a jarumta da ya aikata. А ka yi sa'a wata rana dayammaci Gimbiya Zuhuriya da kuyanginta suka fita bayan gari dan yawan shakatawa, irin na nishadi. Suka yi ta tafiyar har suka iso bakin wani kogi da jama'ar birnin sukedibar ruwa a cikinsa. Gimbiya Zuhuriya ta sa suka tsaya a nan sukasauka a gindin wata bishiya da kekusa da kogin. Ta zauna suna hira cikin kuyanginta Can da kusn faduwar rana sai ga wata tsohuwar Damisa a gigice, ciwon hakori ya bazamo ta daga cikin daji bayan wasu tsaunuka da ke kusa da wannan kogi. Damisar ta nufo bakin kogin ta taso kan jama'ar da ke bakin kogin da suka hangi damisar ta nufo inda suke, sai suka razana suka tarwatse kowanensu yay i ta kansa. Aka shiga guje guje da neman hanyar tsira, nan take waje ya hargitse kururuwa da hargowar mutane ta cika wajen kowa ka gani yana neman hanyar tsira kada Damisar ta hallaka shi. 7 harafi Tafiyar ajali Muzaffar yana bakin kogin yana bawa dokinsa ruwa yaji haniya da hargowar jama'a ta gauraye bakin kogin. Yana dago kansa dan ya ga abin da yake faruwa sai ya hangi damisa ce ta taso kan jama'a suka razana suka shiga gudun neman tsira. Ya ga damisar nan ta tasarwa wani tsoho mai neman, yawan shekaru da ya kasa guduwa zata hallaka shi. Nan take Muzaffar ya tashi cikin hanzari da jarumta ya nufi inda Damisar take dan ya kaiaw wannan tsohon dauki kada Damisar ta hallaka shi kuma ba tare da wani makami a hannunsa ba. Ita ma gimbiya da ke zaune a gefen kogin cikin kuyanginta. suna hira. Da ta ji hayaniya da ta gauraye wajen ta juyo ta ga abin da yake faruwa ta hangi damisar nan ta tasar ma wannan tsohon da ya kasa guduawa za ta hallaka shi. Da ganin haka saita mike cikin sauri ta nufi inda suka daure dawakansu ta dauko takobinta da ke duare a jikin sirdin dokinta. Ta tasar ma wajen da wannan damisa take cikin tsananin jarumta da karfin zuciya, dan kaiwa wannan tsoho dauki kada damisar ta halaka shi. Kafin ta karasa wajen tuni Muzaffar ya isa ga damisar ya sanya hannu ya fizgeta daga cikin tsohon yam aka ta da kasa. Damisar ya yunkura a fusace ta rabu da tsohon ta taso kan Muzffar tana wani irin gurnani da gunji na masifa. Ta yi tsalle kansa da nufin bangaje shi ya fadi kasa ta turmushe shi. Muzaffar ya café Damisar ya sake makata da kasa, sannan ya turmushe ta ya kama habar bakinta ya sanya dukkanin karfinsa yak eta bakin gida biyu, ya kuma karya kashin wuyanta lokaci guda bata ko shuruba. 8 Tafiyar ajali Yana gama hallaka Damisar gimbiya zuhuriya tana karasowa wajen rike da takobi azare, da nufin taimakon say a hallaka damisar amma sai ta tarar da tuni ya hallaka damisar ba tare da wani makami ba. Ta yi matukarmamaki da jarumtar wannan jarumi har abin ya burgeta. Duk da cewa ba ta san shi ne Muzaffar da ake bada labarin jarumta da bajintarsa baа dukkanin fadin birnin. Muzaffar ya dago kansa ya dubi wanda yake tsaye a kusa da shi bayan ya saki Damisar a kasa matacciya. Ga mamakinsa sai ya ga mace rike da takobi da ta taho don taimaka masa a hallaka damisar yayi matukar mamaki na jarumta da bajintar wanan mace saboda kokarin da ta nuna na rashin tsaro bayan da mazaje da dama da ke wajen suka arce da tsira dadaga hallaka. Suna hada ido sai suka tsaya suna duban juna gimbiya Zuhuriya ta ga Muzaffar kyakkyawa ga diri da sura irin na mazaje Sadaukai, zuciyarta ta kasa jurewa har sai da ta yi masa murmushi ya bayyana jeren fararen hakoranta. Shi ma Muzaffar tuni kyawun surarta ya dauki hankalinsa har sai da yay i kirari da tasbihi ga ubangiji cikin zuciyarsa da cewa. "Tsarki ya tabata ga mahaliccin wannan kyakkyawar mace a duniyar kamarta ba, shi kansa bai san sanda yay i mata murmushi ba kamar yadda ta yi masa. Sai dais hi ya fita karfin zuciya yay i auri ya dauke idanunsa yak au da kai ga barin dubanta. Ya tafi ga tsohon nan da ya fadi kasa ya tayar da shi ya debo ruwa a cikin kogin y aba shi ya sha. Ya ci gaba da kula da shi har tsahon ya dawo hayyacinsa, sannan ya tambaye shi inda 'yan uwansa suke dan ya maida shi gida. 9 harafi Tafiyar ajali Da tsohon nan ya gay a kubuta daga hannun Damisar bai hallakata ba sai yayi NUzaffar godiya tare da sanya masa albarka. Ya kuma ce da shi ya barshi zai iya komawa gida da kansa ba sai ya kais hi ba. Ya mike ya dauki sandarsa ya soma dogarawa yakama hanyar komawa gida. Yana tafe yana yiwa Muzaffar addu'a da shi masa albarka har ya bar bakin kogin. Duk abin da yake faruwa Gimbiya ZUhúriya tana tsaye tana duban Muzaffar, nan take sai ta ji begensa ya shiga zuciyarta, saboda yawan tausayi da jarumtarsa, da tsohon nan ya tafii Muzaffar ya juyo sai ya ga wannan mace tana tsaye tana dubbansa, yay i matukar mamaki da irin kallon da take yi masa. Ita kuma sai ta yi masa godiya abisa taimakon da yay i wa wannan tsoho ya kubatar da shi daga hannun da Damisar ba ta hallaka shi ba. Da yake Muzaffar bai san cewa ta ce Gimbiya ZUhuriya yar Sarki Sa'ad da ke sarautar birnin AMbar ba, sai ya ya amsa godiyar da ta yi masa ya kada kansa ya tafi ya koma inda dokinsa yake, ita kuma tana tsaye tana dubansa Jana'a suka soma dawowa bakin kogin daga gudun tsira daga hallaka da suka yi. Saboda ganin Muzaffar ya allaka wannan Damisar da ta taso kansu.kuyangin Gimbiya ZUhuriya suka karaso gare ta ta dube su tana mai yin tambaya a gare su da cewa. "Shin ko kun sani da wannan jarumi da ya hallaka Damisar nan a cikin birnin nan? Hakika jarumtarsa ta yi matakur bani mamaki. 10 harafi Tafiyar ajali Daya daga cikin kuyangin ta amsa mata da cewa "Ranki ya dade ai babu abn mamaki cikin lamarin Jarumtar wannan Jarumi don kuwa ya aikata abin da yafi haka, shi ne Muzaffar dan babban limamin birnin nan wanda labarin Jarumta da bajintarsa ya gauraye ko'ina saboda karfin zuciya da rashin fargaba ko tsoro na tunkarar kowanne irin abin cutarwa komai gagara da shu'umancinsa". Da Gimbiya ZUhuriya ta ji wannan bayani na Kuyangarta. Sai ta sake jin begensa ya dada karuwa a zuciyarta. Ta ga ya dace da irin namijin da take muradin ya kasance miji a gare ta, sai dai ta yi tunanin a ranta cewar kafin ta bayyana masa abin da yake zuciyarta na daga begensa sai ta sake jarrabashi dan ta ga irin jarumtarsa a fagen iya fada da takobi da sauran makami da akeamfani da shi a wajen yaki. Daga nan ta umarci kuyanginta su koma inda suka daure dawakansu su kama su hau su nufi hanyar komawa hanyar gida. ** Bayan kwanaki biyar da faruwar wannan al'amari gimbiya ZUhuriya tasa aka samo mata sahihin labarin akan Muzaffar cewa yak an fita kilisa bayan gari akan dokinsa cikin kowanne yammaci.don haka ta yi shiri wata rana da yamma ta sanya sulkedasauran kayan yaki ta rufe kanta da hular yaki ta bakin karfe wadda ta kare fuskarta yadda ba za a iya gane kowane ne ba. Ta dauko takobi, kwari da baka, garkuwa da sauran kayan fada ta daure a damarta sannan ta tafi 11 harafi Tafiyar ajali ta kama dokinta ta hau ta zagaya ta kofar bayan gidanita ta fita ta kama hanyar bayan gari ita kadai ba tare da wasu masu yi mata rakiya ba. Idan ka ganta cikin shirin yaki da ta yi zaka yi zatan wani hamshakin jarumi ne da ya fito dan karawa da rundunar barada a fagen fama ba mace ce ba. Ta yi tafiya mai nisa har ta isa kan mahadar hanyar da aka ba ta labarin cewa Muzaffar yana wucewa ta wajen, ta samu cikin duhun wasu itatuwa ta shiga cikinsu, ta labe tana jiran tahowarsa ya zo wuce ta wnanan hanya. Bayan wani lokaci da zuwanta tana tsaye tana jiransa, sai ga Muzzaffar tafe akan dokinsa ya biyo wannan hanya zai wuce, yana sassarfa yana karowa daidai inda Gimbiya Zuhuriya take labe sai ta fito daga cikin duhun itatuwa ta sha kansa ta tare masa hanya. Muzaffar ya cika da matukar mamaki da ya ga wani mahayi cikin shirin yaki ya bayyana a gabansa, ya tare masa hanya ba tare da ya san ko wane ne ba, ya ja linzmin dokinsa ya tsaya suka yi kallon-kallo sannan sai ya ga mahayin nan ya zare takobinsa ya taso kansa a fusace da nufin kai masa sara ya hallaka shi. Cikin azama da zafin nama Muzaffar yay i sauri ya zare tasa takobin ya tari mahayin d abai san kowanene shi ba a tsakanin sanda yake kokarin kai masa sara. Suka yi arangama irin ta hamshakan sadauka da sukeji da kansu a fagen jarumta da kwarewa ta iya fada da makami kafin takubbansu su 12 harafi Tafiyar ajali jini yana daukarsa, mahaifinsa Waziri Hawaisu da ke zaman jiran dawowarsa idan sun samu nasara hallaka Muzaffar ya ganshi cikin wannan hali, ya taso cikin hanzari da gigita ya tare shi Najiranu yana zuwa ya fada jikinsa ya suma, saboda tsananin galabaita. Hankalin Haiwasu ya sake tashi, zuciyarsa ta kidima ya shiga rudani da gigita, cikin sauri ya dauki dan nasa Najiranu ya kais hi dakinsa ya kwantar da shi, ya yi kiran wasu hadimai maza da ke yin hidima a gare shi suka taho gare shi cikin sauri dan amsa umarninsa. Waziri Hawaisu ya sa su suka cire sulken yakin da ke jikin Najiranu da rawanin da ke kansa, aka wanke masa jini da ke jikin raunin dake kafadarsa inda Muzaffar ya sare shi da gatari, sannan aka sama masamagani. Bayan wani lokaci Najiranu ya farfado daga suman da yayi, ya soma dawowa hayyacinsa Waziri Hawaisu ya dan ji sanyi a ransa saboda ganin dansa ya farfado daga Suman da yayi. Da Najiranu y agama dawowa hayyacinsa sai ya kwashe labarin dukkanin abin da ya faru tsakaninsu Da Muzaffar da suka tafi gare shi domin hallaka shi, da kasa samun nasara da suka y a kansa, har ya hallaka baradan da suka farmasa baki daya. Da waziri Hawaisu ya ji wannan bayani na dans Najiranu sai ransa ya kara baci bakin ciki da takaici ya sake yawaita a zuciyarsa. Ya dubi Najiranu y ace da shi. Tun da har wadannan baradan sun kas samun nasara akansa to kuwa zan hada shi da manyan bokaye masna alkaluman sihiri dan su salwantar min da ruhinsa ya hallaka. Don kuwa b azan bari ya samu nasarar auran gimbiya Zuhuriya ba shirina na son mallakar masarata Birnin Ambar ta dawo hannuna ya rushe, don haka na dauki alwakarin sai nag a bayan wannan yaro na hallaka shi da salwantar da ruhinsa ko ta wane irin hali. Da Najiranu ya ji wannan bayani sai ya sake yin farin ciki da matakin da mahaifinsa ya ce zai sake dauka akan 28 harafi Tafiyar ajali nasara akansa ba. Ta yi sauri ta fiddo da kwari da baka ta zari kibiya ta saka ta harba masa ita da kanta sai da ta yi garfabar irin harbin da ta yin a kwarewa kada kibiyar ta same shi ta yi masa illa. Amma sai ta ga Muzaffar ya sanya takobinsa yak ad kibiyar ta tafi ta cake a kasa, ba ta same shi ba. Ta ci gaa da zarar kibiyoyin tana harba masa shi kuma Muzaffar yana sanya takobinsa cikin azama da zafin nama yana kade kibiyoyin har sai da suka kare. Da Muzaffar ya ga kibiyoyin sun kare sai ya zabiri dokinsa cikin fusatuwa ya tasarma wannan mahayi da nufin gamawa da shi, ita kuma gimbiya Zuhiriya kafin ya iso gare ta sai ta yi sauri ta cire hular karfen da ke kanta fuskarta ta bayyana. Yana karasowa inda take sai ya ga wannan mahayi da suke fafatawa da shi macece kuma wannan kyakkyawar budurwa da ya taba gani a bakin kogi sanda ya kwaci wani tsoho daga hannun damisa da tasar masa zata hallaka shi. Ya ja linzamin dokinsa yay i tirjiya a gabanta ya tsaya ya dube ta yana mai mamaki wannan al'amari ita kuma sai ta yi masa murmushi irin wanda ya tabayi masa a haduwarsu ta farko da sannan ta maida takobinta cikin kube da yake har a wannan lokacin Muzaffar bai san kowacece it aba sai ya yi mata Magana da cewa "Wacece ke,kuma mene ne makasudin tunkarata cikin shirin yaki da nufin hallakani, a hirdinki" 14 harafi Tafiyar ajali Cikin wannan batu Muzaffar bai zamo daga mazajen da mace zata iya yin mubazzara da shi dan samun nasara akansa ba. Gimbiya Zuhuriya ta sake masa murmushi sannan ta ce da shi, Ni ce Gimbiya Zuhuriya yar Sarki Sa'adul gamidi dake sarautar wannan birni, kuma ban tareka da nufin hallaka k aba said an na kara jarrabaka na tabbatar da jarumta da bajintarka, kamar yadda nake jin labarinka a dukkanin birnin nan, tun ranar da na fara ganinka a sand aka kubutar da tsohon da Damisa ta tasar ma hallaka shi a bakin kogi, na tabbatar da cewa ka cika jarumi sai dai na sake tareka a wannan waje dan nag a irin kwarewarka a fagen iya fada da makami kamar yadda na gani a yanzu. Ta ciro wani zobe na azurfa daga hannunta ta mika masa, sai da Muzaffar ya karba sannan ta ci gaba da cewa. "Zany i maka wani albishir akaina nay i alkawarin cewa b azan auri kwanne namiji ba, dan sarki ne shi ko attajiri

Chapter 1 of 9