Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 9
don ganin bayansa. Ва zamu bari ya auri Gimbiya zuhuriya ba, don kada shirinka na son mallakar sasautar birnin AMbar ya rushe, saboda haka zan sanya a dauke shi daga birnin AMbar akai shi tsibirin Hihusiya a ajiye shi a can baya ya halaka idan nay i imani da cewa idan aka kais hi ba zai taba dawowa birnin AMbar ba har abada kuma rayuwarsa ta kare kenan komai nisan kwanansa, saboda Musaiba da ke tare da wannan tsiburi. Nahiya ce da ke da matukar nisa daga wannan lardi zuwa inda take har ma tsawon tafiyar shekaru goma akan ingarman doki ba tare da yada zango ba. Kuma waje ne da yake tare da matukar hadari, unci da musiba iri daban daban yadda babu wani mahaluki daga jinsin mutum ko aljani da zai iya fitowa daga cikin wannan tsibiri idan aka kais hi ba tare da ya hallaka ba. Idan aka kais hi wannan tsibiri aka batar da shi shi kenan aka samu damar dan kai zai auri Gimbiya Zuhuriya ka samu nasarar hallaka Sarki Sa'adulgamidi sarautar birnin ta dawo hannunka" Ya sa hannu ya dauko wata yar karamar batta an rufe bakinta da bakar fata ya mikawa waziri Hawaisu y ace da shi. 31 harafi Tafiyar ajali "Ka tafi da wannan battar ka ajiye a gefen hanya dai dai inda wannan Jarumi da kake so a hallaka yake wucewa, battar tana tare da abubuwa ta a ajibi da ban mamaki na daga alkaluman sihirina a cikinta, kuma akwai wani bakin ifiritu da ke yin hidimaa gare ta da ke cikin battar, ka kiyaye kada ka sake ka bude battar hark a kaita inda wannan jarumi yake wucewa ka ajiye ta, idan har wannan Jarumi ya ganta babu shakka zai ce zai je inda take dan ya dauka ya ga abubuwan al'ajabin da yake tare da ita. Idan har ya sake ya buxe wannan batta to kuwa bakin ifiritun da ke cikin batttar zai fito daga cikinta ya dauke shi ya tafi da shi, kuma ba zai aje shi a ko in aba sai a wannan tsibiri na Hijusiya da zai hallaka a can ba zai sake dawowa wannan birni ba har abada. Waziri Hawaisu ya karbi battar cikin matukar murna da farin ciki tare da yin godia ga boka Musaila sannan ya tambaye shi abin da yake bukata nadaga dukiya da zai bashi a matsayin ladan aikinsa. Boka Musaila ya ce da shi "Bana bukatar komai daga gareka na daga dujiya a matsayin ladan aikin da zany i maka, illah dai zan aikata wannan aiki ne dan ka samu nasarar hallaka Sarki Sa'ad sarautar birni ta dawo hannunka, saboda kiyayyar da take tsakanina da shi sakamakon cin mutumcin da yay i min na kora ta daga birnin AMbar da sauran bokaye yan uwana. Abin da nakebukata daga gare kakawai shi ne idan danka ya zama sarkia birnin AMbar to kuwa ni zan zama wazirinsa, kada ka yi hange ga yawan shekarako tsufana, aikata hakan shi ne zai san a tabbatar da biyayyar jama'ar birnn a gare shi,ta hanyar karfin tsafi da sihiri na, kuma wannan shi ne kawai abin da nake bukata daga gareka a matsayin ladan aikina". Da waziri Hawaisu ya ji wannan bayani babu ayayya sai ya amince da sharadin da boka Musaila ya kafa masa, ya sake jadda godiyarsa a gare shi sannan ya tashi ya fice daga Σ 32 harafi Tafiyar ajali bukkar ya bar Boka Musaila. Ya tafi ya kamadokinsa ya kama hanyar komawa gida Da isarsa gida yayi kiran dansa Najiranu ya sanar da shi abin da ya faru tsakaninsa da Boka musailamatu, sannan ya bashi wannan batta da boka ya bashi y ace da shi ya tafi ya ajiyeta a gefen hanyar da Muzaffar yake wucewa. Najiranu ya karbi battar cikin matukar murna da farin ciki sannan yay i shiri don tafiya ya kai battar kan hanyar da Muzafar yake wucewa idan lokacin wucewarsa yayi. ** A wannanrana da yammaMuzaffar yay i shiri don tafiya bayan gari kilasa kamar yadda ya saba, yana fitowa zai kamadokinsa yah au sai ga mahaifinsa Liman Adnan ya shigo gidan ya dubi Muzaffar ya ga irin shirin da yay i na fita Kilisa hadda sulken yaki da takobi tamkar wanda zai tafi kafsa yaki a faen fama,saboda shirin ko ta kwana da yake yi. Tun daga ranar da baradan nan suka tare shi a bayan gari suka tasar masa da niyar hallaka shi da Liman adnan ya ga irin wannan shiga da yayi, sai yay i kiran Muzaffar dan yi masa nasiha yanamai cewa da shi. "Zan yi nasiha a gare ka dank a zama mai kiyaye rayuwar duniya abin da yake cikinta, ka da ka sake ka shiga abin da bai shafeka ba matukar ba taimako za kayi gad an uwanka musulmi ba, ka guji duk wani abin hadari ko na cutarwa da zai iya kai ka ga hallaka kada jarumta da jin karfi na kuruciya su rike dibar ka kana tunanin cewa kai mai iya samun nasara ne akan komai,ka da k ace zakat aba duk abin da baka san mafarinsa ba, ko ka zama mai yawan tambaya a cikin lamarin daba shi da nasaba da rayuwarka". Da ya gama yi masa wannan nasiha sai Muzaffar yayi godiya ga mahaifinsa, sannan ya tashi ya tafi ya kama dokinsa yah au ya fita ya kama hanyar fita bayan gari. Yayi iyatafiya mai nisa akan dokinsa cikin sassarfa har ya iso wani waje da manyan bishiyu masu wadatar rassa da inuwa mai sanyi suke.ya hangi wasu kyawawan tsuntsaye suna raira kuka mai 33 harafi Tafiyar ajali dadin saurare tare da tashi daga wannan reshe ya zuwa wancan resi ya ja linzamin dokinsa ya tsaya yana duban waadan nan tsuntsaye cikin nishadi tare da jin dadin kukan da suke rairawa. Sannan ya sake sakin linzamin dokinsa ya cigaba da tafiya. Bayan yayi tafiya mai nisa daga inda ya fara tsayawa sai ya hangi wata batta ahiye a gefen hanya kusa da inda zai wuce, battar tana haske da walwali shekinta yana daukar ido tamkar madubi, wani Karin abin mamaki shi ne da ya matsa kusa da battar sai ya ga ba a jiye take akan doron kasa ba, tana tsaye ne a tsakanin sama da kasa, kan iska ba are da ta dogara da wani abu ba, kuma bata fado kasa ba. Yaja linzamin dokinsa yatsaya yana duban battar cikin matukar mamaki da ta'ajjibi na faruwar wannan al'amarimai kama da aikin sihiri.nan take sai ya ji zuciyarsa na sha'awantuwa da son ya je ya daukoo wannan batta ya bude dan ya ga abin da yake cikinta. Ya kuma san yadda aka yi har take tsaye akan iska ba tare da ta fado kasa ba. Ya sauk daga kan dokinsa ya nufi wajen da battar take, da zuwansa ya kai hanu zai taba battar ba tare da wani tsoro ko fargaba kamar daga sama sai yaji wat amurya mai matukar amo da hauhawa tana cewa da shi. "Kada ka sake kataba wannan batta da ke gabanka hallaka zata tabbata a gareka matukarka sake ka taba ta". a Muzaffar ya juyo cikin sauri bai ga mai yin maganar gare shi ba, ya duba kowannen bangare daga sashin da yake tsaye bai jikoda motsin wani a kusa da shi ba bare ya ga mai yin maganar,don haka sai ya sake kai hannu zai taba battar muryar ta sake cewa da shi "Ka zama mai biyayyar umarnin don kaucewa abin da zai iya kai ka ga hallaka ka guji tabа wannan batta idan ba so kake ajali ya gabata a gare k aba". Muzaffar ya sake dakatawa yana sauraren muryar da baya ganin mai ambatonta, sannan yayi Magana da cewa "Da zan iya ganin ma'abocin wannan furuci da na fi yadda da gasgata abin da yake ambatawa, shin wanene ne kai kuma シ 34 harafi 2 Tafiyar ajali daga wane jinsi kakasance mutum ko kuma aljan? Ka sani cewa nay i imani da Allah mahaliccin rayuwa da muttuwa, tare da gasgata cewa babu wani abin halitta idan bas hi ba, saboda haka ban zamo daga mutanen da za a bawa tsoro korazani da ikirarin tabbatar da hallaka akan sub a". Yana gama fadar wannan Magana sai ya kai hannu zai dauki battar muryar ta sake daka masa tsawa, don kada ya taba amma hakan bai hana shi aikata abin da zuciyarsa ta yi niyar bay a sa hannu ya daui battar da ke tsaye akan iska sannan ya bude bakar fatar da ke rufe da bakinta dan ya ga abin da yakeciki. Da budewarsa sai ya ji wata irin kara mai tsananin amo da hauhawa ta gauraye wajen, wani irin bakin hayaki ya taso daga cikin battar ya turnuke ya rufe ko ina a tsakanin inda suke, aka sake yin wata tsawa da rugugi mai matukar karfi da ban firgici sannan daga cikin hayakin sai ga wani bakin ifiritu ya bayyana a gaban Muzaffar tae da wannan rugugi da yake ji. Ifiritun na da matukar girmada munin gani idanunsa yayi jajawur tamkar garwashin wuta, yana da kaho a tsakiyar kansa wani irin bakin gashi ya lullube fatar jikinsa gaba daya yayi karaji da gunji mai matukar karfi da ban firgici feshin burbudin wuta yana fita daga bakinsa. Dajin yay i amsa kuwa da amo mai hauhawa kasa ta yi girgiza a raurawa mai karfi tamkar za ta tsage dukkanin abn da ke wajen ya nutse cikinta. Muzaffar yaja da baya dan ganin abin da ya bayyana gare shi,cikin azama da karfin zuciya iri na jarumta ya kai hannunsa kan damararsa da nufin zare takobinsa amma sai yaji babu takobinsa ya barota a jikin sirdin dokinsa.ya jyya a hanzarce da nufin komawa inda dokinsa yake da nufin dauko takibin sai dai kuma kaddara ta riga yi muradi cikin lamarinsa, kafin ya kai ga inda dokinsa sa yaketuni bakin ifiritun nan ya taho gare shi, ya wafci Muzaffar ya daue shida sasari, annan ya sake yin wani karaji da yafi wanda yayi da farko karfi da amsa kuwa,duhu mai tsananin ya lullube wajen sannan ifiiritun ya 35 harafi Tafiyar ajali suri Muzafar ya tashi da shi sama ya luluka da shi cikin gajimare ya kama hanyar tsibirin Hljusiya inda aka umarce shi da ya kai duk wanda ya buxe wannan batta da yake ciki. Muzaffar yayi iyakacin kokarinsa ya kufce daga daurin da akayi masa amma yai ya kasa koda motsa sasarin da aka daure shi da shi bare ya sa ran kubuta. Tun yana iya ganin abin da yake faruwa gareshi har numfashinsa ya daukebai sake sanin abin da yake faruwa gare shi ba. Ifiritun nan yay i tafiya mai nisa da Mzaffar har ta tsawan kwanaki biyar irin tafiya ta manyan ifirita da suka fi komai sauri akan iska, sannan ya isa tsibirin Hijusiya inda aka umarce shi ya kai Muzaffar ya jefar da shi a tsakanin wasu tsaunukacikin kwazazzabai ya kwance sasarin da ya daure shi Muzaffar yana cikin halin suma bai san abn da yake faruwa gare shi ba sannan ya sake tashi sama akan iska ya kama hanyar komawa inda ya fito Duk abin da yake faruwa akan Muzaffar lokacin da Ifiritun nan ya bayyana gare shi, Najiran dan gidan Waziri Hawaisu yana labe cikin wani duhu itatuwa da ke kusa da wajen da ya ga Muazaffar ya bude wannan battar Ifiritun nan ya dauke shi ya tafi da shi sai ya cika da murna d afarin ciki ya fito daga ida yake boye yah au dokinsa ya kamahanyar komawa gida. Yana zuwa ya sanar da mahaifinsa dukkanin abin da ya gani akan idanunsa. Waziri Hawaisu shi ma yayi matukar murna da fari ciki saboda ganin sun samu nasara akan Muzaffar suna masu tunanin cewa ya hallaka har abada Boka Musalamatu ya sanar da Waziri ** Shi kuwa muzaffarbai farka daga suman da yayi ba sai bayan tafiyar wannan ifiritu da ya kawoshi wannan waje, da kusan sa'a guda da ya farfado ya dawo hayyacinsa ya tashi zaune ya ganshi a wani bakon waje a gareshi tsakiyar daji da bai san wajen ba. Sai ya karewa wajen kallo babu komai sai manyan tsaunuka da kwazazzabai kuma hatta sararin 36 harafi Tafiyar ajali samaniyar da ke wajen ya banbanta d airin yadda ya saba ganin launin sararin samani tsawon rayuwarsa sararin saman yayi duhu gajimaran dake tafiya akan iska ya yi jajawur tamkar zai zubo da tafasasshen ruwan zafi. Ya dubi wajen da yake zaune, nan takeya shiga halin kidima da rudani saboda abin da ya gani, babu komai a wajen sai tarin kasusuwan gawarwakin muane da suka dade da hallaka awajen Muzaffarya mike tsaye cikin sauri yana duban kasusuwan gawarwakin cikin tsoro da razana hankalinsa yayi matukar tashi da abin da ya gani, sannan sai yaji wata kurya mai matukar karsashi da rashin dadin saurare tana cewa da shi. Hallaka ta gabata gareka ya kai wannan bil'adama sababin shigowarka wannan waje, kuma wannan waje da kake cikinsa shi ne tsibirin Hijusiya inda duk wani ruhi na bil'adama da ya shiga cikinsa kan salwanta, don haka babu wani mahaluki bil'adama kamar ka da ya taba shigowa cikinsa ya fitabatare da ya hallaka ba, ka yi duba zuwa kasusuwan gawarwakin da zaka ya iya gani a wannan waje na mutane ne bil'adam kamarka da akakawosu wannan tsibiri suka hallaka,tun shekaru masu yawa da suka gabata kamar yadda kai ma zaka hallaka yanzu a cikinsa. Wannan shi ne karshan mai jin kai da kafiya ta son aikata abin da zuciyarsa ta kuduru da son aikatawa.hakika da kabi umarnin mai Ambato da ya haneka da taba wannan battar da ka taba to da kuwa b aka kasance cikin wannan al'amari da ka riske kanka a cikinsa ba" Ana gama fadar wannan Magana sai ya ji an kyakyace da dariya cikin wata kakkausar murya marasa dadin saurare, harowar muryar tayi amsa kuwa da amo mai hauhawa da ya gauraye dukkanin dajin sai da aka dauk lokaci mai tsawo ana kyakyata wannan dariya sannan muryar ta tsagaita da dariya daga nan bai sake jin komai ba. Muzaffar yayi shiru yana tunanin abin da wannan murya ta ambata a gare shi, ya duba gabad da yamma bai ga 37 harafi Tafiyar ajali wata hanya da zai bi ba, ko kuma wata alama da za ta sada shi da inda zai riki inda gari ko wasu jama'arsuke ya rasa inda zai nufa daga wajen da yake tsaye. Ya hangi wasu kananun dawatsu a kusa da ind ayake yayi tunanin ya je yah au kan daya daga cikinsu ya duba ko zai hangi wani gari ko hanyar da zata sada shi da wai bigiri da zai riki inda jama'a suke yayi tambayar a gare su ko zai samu wanda zai sanar da shi hanyar da zai bi ya koma birnin Ambar. Ya tafi yah au kan daya daga cikin wannan duwatsu ya duba iyakacin ganinsa bai ga wata hanya da za ta kaishi inda zai riski jama'a ba, ko ina ya duba daji ne kawai mai matukar sarkakiya da duhu mara masaltuwa, wani abu da ya kara sanya shi fargaba shi ne bai ji ko da kukan tsuntsu ba, bare ya sa ran akwai wata halitta da ke da rai a cikin dajin. Ya dade a wannan waje yana tunanin da sake-sake cikin zuciyarsa, daga karshe sai ya yanke shawarar ya sauko daga kan dutsan ya bi hanyar da ta yi kudu ya ci gaba da tafiya cikin hasashe ko zai riski inda wasu jama'a suke zaune cikin wannan daji, idan kuma bai hadu da kowa bay a ci gaba da tafiya har zuwa inda hallaka zata rike shi cikin dajin idan Allah bai nufe shi da komawa gida ba Yana gama wannan tunani ya sauko dag akan dutsan ya kama hanya ya bi bangaran kudu ya ci aba da tafiya cikin sarkakiya da duhun itatuwa babu abin da yake gani sai kasusuwan gawarwakin mutane da suka dade da hallaka a duk inda ya ratsa. Tun da sanyin Safiyar ya soma wannan tafiya, amma har sai da rana ta kusa faduwa bai gama da ko da tsuntsuba daga cikin halittun da ke rayuwa a dajin ga tsananin yunwa da kishirwa da ya soma addabarsa, kuma bai riki koda rafi ba a gabansa,bare ya sa ran samun inda zai samu ruwa, sai dai idan lokacin sallah yayiyayi taimama ya gabatar da sallarsa ya ci gaba da tafiya a cikin dokar daji. San da rana ta gama faduwayunwa da kishirwa sun gama cikin karfin Muzaffar ga gajiyar tafiya da ta gama シ 38 harafi Tafiyar ajali galabaitar da shi.yana zuwa cikin wasu kwazazzabai sai juwa ta soma daukarsa saboda jigata daga nan ya fadi kasa ya suma. ** Can kuwa a birnin AMbar bayan da dare yay i mahaifan Muzaffar suka ga bai dawo gida ba, sai suka shiga nemansa an tura yan uwansa duk inda ake zaton za a riske shi amma ba a samu koda labarin wanda ya ganshi ba, tun bayan fitarsa da yamma hakamaafan Muzaffar sukakwana cikin fargaba da zulumin rashin sanin inda ya shiga. Da gari yaw aye aka saketura yan uwan Muzaffar nemansa ko za su yi dace a gabansa amma har rana tafadi dare yayi babu shi babu labarinsa.mahaifinsa ya sake shiga halin damuwą da fargaba saboda rashin ganinsa, kuma da yake sun san halin shu'umanci da hatsabibancinsa sai suka rika fargabar ko wani abu ne na cutarwa ya sameshia fitar da yayibayan gari cikin wannan yammaci. Washe gari da safe a rana ta biyu da bacewar Muzaffar wani matafiya ya zo da labarinsa cewa ya gawani farin doki da sirdi akansa yana yawo a daji amma bai ga mahayin dokin ba. Mahaifin Muzaffar ya turo aje a gani ko dokin Muzaffar ne da zuwan yan uwan Muzaffar suka ga cewa babu shakka dokinsa ne suka shiga nemansa a dukkanin wajen amma basu ga koda sahunsa ba, bare ssu san inda yake, suka yi ta nemansa har rana ta fadi basu ganshi ba. Da suka gaji da nemansa sai suka kama dokinsa suka tafi da shi gida suka sanar da mahaifinsu cewa dokin Muzaffar ne, amma sun yi dukkanin nemansa basu ganshi ba. Hankalinmahaifin Muzaffar ya kara tashi, suka sake shiga fargaba da tararradin halin da yake ciki,aka ci gaba da ttura yan uwansa nemansa har tsawon kwanaki biyar, amma ba a sam ukoda labarin wanda ya ganshi ba, daga karshe sai mahaifinsa ya hakura da tura yan uwansa nemansa ya mikalamarin ga Allah yana mai addu'ar Allah ya bayyana inda Muzaffar yake idan har yana raye a duniya. 39 harafi Tafiyar ajali Bayan wasu kwanaki labarin bacewar Muzaffar ya cikako'ina a birnin AMbar saboda shaharar da Muzaffar yay i wajen jarumta da rashin tsaro.maganar bacewar ta tafi ta kai har unnen Gimbiya ZUhuriya da ta samu wannan labara hankalinta yay i matukar tashi, ta shiga damuwa da fargabar halin da masoyinta Muzaffar yake ciki. Daga karshe ta shiga addu'a da fatan Allah ya bayyanashi a duk inda yake inda har yana raye. ** Al'amarin Muzaffar kuwa bayan da ya fadi cikin wannan kwazazzabai ya suma,bai farka daga suman da yayi ba sai bayan wayewa gari ya farfad daga suman da yayi, a lokacin rana ta fito haskenta ya gauraye ko ina, ya yunkura da kyar ya tashi saboda tsananin yunwa da kishirwa ga kuma galabaita da yayi, ya tashi ya soma takawa da kyar yana rangaji saboda jigata. Can daga gabansa sai ya ji wat airin tsawa tare da rugugi mai tsananin karfi da ya gauraye dukkanin dajin tamkar tasowar hadari, wata irin bakar iskadake cudanyeda guguwa mai karfi suka tasu suka rufe dukkanin wajen duhu ya gauraye ko'ina mafi tsananin daga yankin duhu dare sannan sai Muzaffar ya ji kasa ta somagirgiza da raurawa tamkar zata tsage ya nutse a cikinta. Daga nan kuwa sai ya ga wani irin bakin ififiitu ya bayyana a gabansa yana da matukar girma da muni na firgita,duk wani bil'adama da ya ganshi hannunsa rike da wani almudi nab akin karfe jajawur da shi tamkar karfan da aka ciro daga wutar makera. Ifiritun nan ya dubi Muaffar yana wani irin huci da gunji irin na fusatuwa, iska mai zafi tana fitowa daga cikin hucin da yake yi tana bugun jikin Muzafffar yana jin tamkar ana kona shi da wuta, sannan ya daga kansa sama yayi karaji da kururuwa mai tsananin karfida ban firgici da ta yi masa kuwa da amo mai hauhawa da ya gauraye dukkanin dajin, ya daga almudin da ke hannunsa y ataso kan Muzaffar a fusace yana wannan karaji da gunji wuta daga bakinsa ya nufe shi da 40 Tafiyar ajali nufin narka masa bugu da wannan almudu da ke hannunsa ya hallaka shi. TAFIYAR AJALI @ Muzaffar yay i maukar gigita da razaa da ganin wannan ifiritu da ya taso gareshi a fusace da nufin hallaka si, gas hi baya tare da wani makami da zai iya tunkarar wannan ifiritu da shi bare yayi kokarin karr kansa, yay i nufin juyawa ya gudu daa inda yake amma sai ya ji ya kasa koda motsi bare ya sami damar guduwa tamkar wanda kasa ta rike, da ya ga babu mafita cikin lamarinsa hallaka na shirin tabbata a gare shi sai yay i Kalmar shahada ya mikalamarinsa ga ubangiji yana mai saurare da jiran abin da zai wanzu gare shi, na hallaka da yak e tunanin zai ta kasnace a kansa cikin wannan lokaci. Ifiritun yana isa gareshi ya kai masa bugu da al'amudun bakin karfen da ke rike a hannunsa, kafin al'admun ya sauka a kan Muzfffar sai wani farin haske ya keto daga tskanin duhun itatuwan da ke kusa da wajen cikin tsananin sauri mafi sauri daga tafiyar harbin kibiya,ya bugi jikin ifiritun nan d akarfi tamkar jifa da mashi, Ifiritun yayi wata kadaitacciyar kara mai tsananin karfi da ban firgici da tayi amsa kuwa da amo mai hauhawa, gaba daya dajin ya amsa sannan karfin bugun da hasken yayi masa ya daga shi sama akan Iska ya jefar da shi gefe, karfin karar da ifiritun yayi ta sanya shima Muzafar ya yanke jiki ya fadi kasa sumamme. suman da Bayan wani lokaci Muzaffar ya farfado daga yayi tamkar wanda aka shafawa ruwa ya duba jikin rigarsa ya ganta a jike alamar an zuba masa ruwa a lokacin da yake cikin halin suma. Ya dubi wajen da yake sashi szuwa sashi bai ji koda motsi ba, bare yay i tunain wani ne ya kawo dauki gare shi, ya taimaka masa. Ya dubi bangaren da Ifiritun nan ya fadi ya gay a kama da wuta yak one kurmus ya zama tka, hatta da al'amudin bakin karfen da yake haunsa ya narke babu shi, ya duba bangaren da hasken nan ya keto ya bugi jikin Ifiritu ya ga babu wata alama da zai iya tantance abin da ya hallaka 41 harafi Tafiyar ajali wannan Ifiitu, yayi godiya ga Allah da ya kubatar da shi,daga hallaka duk bai san abin da ya hallaka wannan Ifiritu ba. Ya juya zai tashi ya ci gaba da tafiya sai ya ji hannunsa ya taba wani abu a agefensa na dama ya duba wajen sai ya ga wani karamin akushi tare da salkar ruwa a ajiye a kusa da shi, mamaki ya wanzu cikin zuciyarsa mafi girman mamaki ya sa hannu ya bude akushin sai ya ganshi makare da abinci yana tiriri alamar ba a dade da gama dafashi ba, mamaki yya sake karuwa a gare shi ya duba dukkan wajen bai ga koda sahun mutum ba bare yay i tunanin wani bil'adama ne ya gabato da wannan abinci a gareshi da yake Muzaffar yana cikin halin jin matsananciyar yunwa da take addabarsa, sai kawai yay i bismillah ya sa hannu ya soma cin abinci ba tare da wani tsoro ko fargaba ba. Ya ci gaba da dibar abincin yana ci amma har sai da ya koshi, ba tare da abincin ya ragu ba, bare alamar zai kare, ya dauki salkar ruwa ya shay a koshi itama yana dauketa daga bakinsa sai ya ga ruwan ya sake cikowa tamkar ba daga cikinta ya sha ruwan ba, mamaki ya karu gareshi cikin wannan al'amari yayi ta tunani da sake-sake cikin zuciyarsa. Bayan wani wa'adi mai tsawo da gama cin wannan abinci ya huta sosai ya samu nutsuwa sai ya yanke shawarar ya tashi ya ci gaba da tafiya cikin wannan daji ko zai riski wata alkarya a gabansa ko kuma ya hadu da wasu jama'amatafiya yayi tambaya a gare su koza a samu wanda ya san hanyar da zai bi ya koma birninnsu da zai ci gaba da tafiya sai ya dauki akushin abinci tare da wannan salkar ruwa dan yin guzuri da su tunda abincin da ke ciki tare da ruwan basu kare ba, kuma gas hi baai san inda zai sake samun wani abincin ba a cikin wannan dajin. Ya ci gaba da tafiya yana keta duhun itatuwa tsaunuka da kwazazzabai a cikin wannan bakin daji ba tare daya hadu da wata halitta dake da rai ba koda dabba bare ya ga mutum bil'adama a cikin sa da rana ta yi zafi sosai Muzaffar ya sake jin yunwa ya tsaya a bude akushin nan ya ci abinci ya koshi ba 42 harafi W d Q O Z t Tafiyar ajali wannan Ifiitu, yayi godiya ga Allah da ya kubatar da shi,daga hallaka duk bai san abin da ya hallaka wannan Ifiritu ba. Ya juya zai tashi ya ci gaba da tafiya sai ya ji hannunsa ya taba wani abu a agefensa na dama ya duba wajen sai ya ga wani karamin akushi tare da salkar ruwa a ajiye a kusa da shi, mamaki ya wanzu cikin zuciyarsa mafi girman mamaki ya sa hannu ya bude akushin sai ya ganshi makare da abinci yana tiriri alamar ba a dade da gama dafashi ba, mamaki yya sake karuwa a gare shi ya duba dukkan wajen bai ga koda sahun mutum ba bare yay i tunanin wani bil'adama ne ya gabato da wannan abinci a gareshi da yake Muzaffar yana cikin halin jin matsananciyar yunwa da take addabarsa, sai kawai yay i bismillah ya sa hannu ya soma cin abinci ba tare da wani tsoro ko fargaba ba. Ya ci gaba da dibar abincin yana ci amma har sai da ya koshi, ba tare da abincin ya ragu ba, bare alamar zai kare, ya dauki salkar ruwa ya shay a koshi itama yana dauketa daga bakinsa sai ya ga ruwan ya sake cikowa tamkar ba daga cikinta ya sha ruwan ba, mamaki ya karu gareshi cikin wannan al'amari yayi ta tunani da sake-sake cikin zuciyarsa. Bayan wani wa'adi mai tsawo da gama cin wannan abinci ya huta sosai ya samu nutsuwa sai ya yanke shawarar ya tashi ya ci gaba da tafiya cikin wannan daji ko zai riski wata alkarya a gabansa ko

Chapter 3 of 9