Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 9
mai godiya ga Allah tare da jin dadin irin taimakon da dattijon Mubashhir yayi masa wand aba don shi ba da tuni ya hallaka a cikin wannan tsibiri da aka kawoshi don ya hallaka. Ya ci gaba da tafiya ya mike hanya kamaryadda aka umarce shi sallah da cin abinci ne kawai ke tsayar da shi sai dai wani lokacin idan yay i matukar gajiya ya yada zango ya kwana da haka har ya shafe tsawon kwanaki uku da yini daya sannan ya isa inda wannan Bukka take a tsakanin wasu manyan tsaunuka kamar yadda Dattijo Mubasshirya sanar da shi. Da isar sa wajen sya karasa kusa da bukkar yay i salama aka amsa masa ba tare da wani jinkiri ba, yana shiga ya tadda wani dattijo zaune akan wata karaga yana jan tasbaha, kamar yadda ya tadda dattijo Mubassshir a cikin kogon dutsen ya sameshi kuma yayi matukar kama da dattijo Mubashhir tamkar wa da kani,sai dai bai kais hi tsufa da yawan shekaru ba, Muzaffar ya matsa kusa da shi ya dauko 57 harafi Tafiyar ajali zoben da dattijo Mubasshir ya bashi ya mika masa ba tare da ya sakeyin Magana ba, Dattijon nan ya karba ya rikezoben a tafin hannunsa yana dubansa har zuwa tsawon wani lokaci sannan ya dago kansa ya dubi Muzaffar y ace da shi. "Yaro nag a sakonk ada kazoo da shi da abin da ya kawo ka gare ni,don na taimakamakana fitar da kai daga wannan tsibiri na maida kaii birninku kamar yadda dan uwana da ya turo ka gare ni ya nemi alfarmar na taimaka maka, kuma ka yi sa'a gobe zanyi tafiya daga wannan tsibiri ya zuwa alkaryar mutane bil'adam har kusa da birninku don haka zan taimaka maka na tafi tare da kai na kaika birninku, idan da ni kadai ne zan yi wannan tafiyar zan gama ta ne baki daya a cikin kwanaki goma, sai dai da yake yanzu zamu yi tafiyar tare d akai sai mun shafe sawon kwanaki saba'in da biyar kafin mu fita daga wannan tsibir mu isa birninku,saboda ba zai yiwu na dauke kaa kaina na fitar da kai daga wannan tsibiri ba, dole ne sai mun yi tafiya da kafa kuma idan mutum bil'adama ne irin ka zaiyi wannan tafiya shi kadai sai ya shafe tsawon shekaru goma akan ingarman doki idan yay i sa'a bai hadu da wani abin cutarwa ya hallakashi a cikin wannan tsabiri ba, sannan ya umarce ni cewa na sanar da kai yadda z aka yi amfani da ita saboda haka z aka zauna a nan tare da ni kafin gari ya waye, mu fara wannan tafiya tae da kai sai dai zan gargadekatare da sanar da kai sharuda da nake so ka kiyaye cikin wannan tafiyada 58 harafi Tafiyar ajali zamu yi tare da kai matukar kana son na taimakamaka na maida kai birninku". Da farko dai ban a son yawan tambaya cikin lamarina duk abin da ka ga na aikata ko kuma na umarce ka da ccewa ka aikata kada ka sake ka tambaye ni, saboda me yasa za a yi haka kuma ka kiyaye kada ka sake ka aikata duk wani abu da ban umarce ka da aikatawa ba, idan ka kiyaye wadannan sharuda da na sanar da kai cikin tafiyar da zamu yi tare da kai ta tsawon kwanaki saba'in da biyar. O kuwa zan taimaka maka na fitar da kai daga cikin wannan tsibiri na maida kai birnin ku idan kuwa ka kuskure ka kasa cika sharudan da na sanar d akai to kuwa zan tafi na rabu da kai ka halaka b azan taimaka maka ba, said aka yi hattara". Da y agama yi masa wannan bayani Muzafar ya amsa da cewa ya amince kuma zai kiyaye da abin da ya sanar da shi, daga nan ya daowa Muzaffar da zobensa gare shi,ya kumasanar da shi sunansu Zarkiyul ambas tare da nuna masa shimfidar da zai kwanta kafin gari ya waye su fara tafiya. Da gar yaw aye, bayan sun kamala shirin tafiya Zarkiyul Ambas ya kawo wani takalmi na gata ya bawa Muzaffar y ace da shi "Ka sanya wannan a kafarka da shi ne za mu yi dukkanin tafiyar da zamu yi har mu isa birninku, kuma kada ka sake ka cire shi daga kafarka idan ba lokacin kwantawa barci ba, ko mu ma wani uziri da ya zama dole ka cire shi ba". Muzaffar ya karbi takalmin ya sanya a kafarsa daga nan sukafita daga cikin bukkar suka kama 59 harafi Tafiyar ajali hanya, suka soma tafiya cikin wannan bakin daji suna keta duhun itatuwa da sarkakiya, kuma tun da suka baro inda wannan bukka take basu hadu da wata halitta da ke da rai ba, daga jinsin dabba kokuma tsuntsu sannan babu wani abu dake tsayar da su ban da sallah da cin abinci, sai dai idan dare yay i Muzaffaryagaji da tafiyar da sukeyi su yada zango don su kwana, kafin gari yaw aye su ci gaba da tafiya. Da haka har sukashafe tsawon kwanaki biyar cikin tafiyar da suka fara ba tare da sun hadu da wani abin cutarwa ba, ko kuma wanda zai tsayar da su akan hanyar su. A rana ta shida cikin ranakun tafiyarsu ne suka iso wani waje a cikin wannan tsibiri mai matukar duhu mafi tsaanin daga yankin duhun dare ga hayaki ya turnuke ko ina daga cikin duhu,da isar su wajen sai Zarkiyu ya dubi Muzaffarya ce da shi. "Kana da masaniyar cewa za u hadu da miyagun halittu a cikin wannan tafiya da muke yi wanda dole sai mun yi yaki da sum un hallaka su kafin mu samu damar wucewa don isa birninku? Kuma daga cikin wannan bakin daji dake gabanmu ne zamu fara haduwa da s har zuwa ranar da zamu fita daga cikin wannan tsibiri mu isa alkaryar mutane bil'adama, kuma ka sani cewa duk halittar da z aka gani a cikin wannan tsibiri ba irin halitun dake cikin mutane bil'adamabane don hakaka kasance cikin shiri kuma ka kiyaye da abin da na sanar da kai." 60 harafi Tafiyar ajali Da y agama yi masa wannan bayani sai ya zaro wata takobi dake daure a damararsa da akwai sauran takobi tare da mashi da kuma ragowar mamai na yin fada a tare da shi Zarkiyu amma bai baw Muzaffar ko daya daga cikin makaman ba, don yay i amfani da shi, wajenkare kansa ko yin artabu da halittun da za su hadu da su a ciikin wannan waje da zasu shiga sai ya tafi jikin wata bishya da ke kusa da su ya sanya takobinsa ya saro reshin biyar ya fekeshi,kamar tsinin mashi sannan ya mikawa Muzaffar yace da shi "Ka rike wannan itace ka yi amfani da shi wajen kare kanka da yin fada da halittun da zamu hadu da su a cikin wannan waje zamu shiga har zuwwa lokacin da zamu isa inda ya kamata na sanar da kai yadda z aka fara amfani da takobin da ke tare da kai". Muzaffar yay i mamakin wannan al'amari ya dubi Zarkiyu y ace da shi "Me yasa ba z aka bani takobi ko kuma daya daga cikin makaman dake tar da kai ba,don na kare kaina sai dai ka bani wannan itace da b azan iya kare kaina da shi ba, kamar yadda zan iya kare kaina da takobi ko kuma daya daga cikin makaman dake tare da kai". Zarkiyu ya juya ya dube shi y ace da shi "Ai dama tun a farkokafin mu ara tafiya na kafa maka sharadi da gargadinka cewa bana son yawan tambaya cikin lamarina ko na umace ka aikata wani abu ka tambaye ni saboda me yasa za a yi haka. Wannan shi ne kuskure na farko da ka fara aikatawa a gare ni, kuma idan baka kiyaye b aka ci gaba da 61 harafi E i E Tafiyar ajali aikata kuskure makamancin wannan to kuwa zan tafi na barka kahallaka b azan taimaka maka ba, don haka ka zama mai aikata abin da na umarce k aba ka zama mai yin tambaya a gare nib a". Da Muzaffar ya ji wannan bayani sai ya karbi wannan sanda ya sunkyar da kai bai sake yin Magana ba, daga nan Zarkiyu ya juya ya wuce gaba, Muzaffar yana biye da shi suka shiga cikin wannan bakin daji dake gabansu, da shigarsu cikin wannan duhun daji sai Muzaffar ya soma jin wani irin gurnani da gunji yana tasowa daga can cikin dajin, ska ci gaba d atafiya suna kara shiga ciki gurnanin yana dada karuwa alamar suna tunkarar wajen da halittar dake yin gurnanin take sai da suka yi tafiya mai nisa a cikin wannan bakin dajin sannan suka iso inda suke jin wannan gurnani da gunji yana tasowa daga cikin : duhun wani kogon dutse da yake gabansu. Da isarsu wajen sai suka ga wasu irin halittu masu matukar munin kama da rashin kyan gani suna ketwa daga cikin kogon dutsen suna fitowa su taho gare su tare da yn wannan gurnani da sukeji tun da farko. Halittun suna da kafafu biyu da hannuwa biyu kuma a tsaye suke tafiya kamar mutane, sai dai suna da wuya irin na kare tare da kaho a tsakiyar goshinsu, jikinsu buzu-buzu da gashi kuma a mimmike kamar kayar beguwa idan suka yi gurnani ko gunjin da suke yi sai ka ga wani farin abu mai matukar yauki da kumfa yana zuba daga bakunansu, Halittun nan suka yi ta fitowa daga cikin kogon 62 harafi Tafiyar ajali dutsen suna zagaye su. Muzaffar tamkar ba za su kare ba, saboda tsananin yawansu suka yiwa Muzaffar kwawanya ta ko ina yadda ba zas iya komawa da baya ko kuma su samu mafita daga barin wajen da wadannan halittun suke, sannan sai halittun suka yyunkura gaba daya suka taso kansu cikin gurnani da gunjin da sukeyi da nufin far usu su hallaka su. Zarkiyu ya fara zare takobinsa yay i yunkuri ya tare su, ya fantsama a tsakaninsu yah au su da sara da kaifin takobinsu, nan take ya fara girbar kawunan da sassan jikin wadannan halittun yana hallakasu duk wanda ya sara da kaifin takobinsa sai ka ji yay i wata kadaitacciyar kara mai kama da haushin kare ya fadi kasa yana shure shure, idan ya hallaka ransaya fita daga cikinsa, sai ka ga yana narkewa ya zama jini. Shima Muzaffar da ya ga yadda Zarkiyu yake hallaka wadannan halittun sai ya yunkura ya tari wadanda suka taso gare shi, duk wanda ya kawo masa sura daga cikin wannan halittu da nufin ya wafce shi ya hallaka shi sai Muzaffar ya tokare shi da tsinin itacen da yak e hannunsa ya caka masa tsinin a wuya ko a kirjinsa ya hallaka shi. Haka su Muzaffar da zarkiyu suka yi ta hallaka wadannan Halittu har sai da suka gama da su baki daya gaba daya kasan wajen yay i jajawu da saboda yadda halittun nan suka rika narkwwa suna zama jini idan su Muzaffar sun hallaka su. Bayan sun gama hallaka wadannan halittu da suka fara haduwa da su suka yi duba da saurare ba 63 harafi Tafiyar ajali tare da sun sake ganin wata halittar ta sake fitowa daga cikin kogon dutsen ba, daa nan sai Zarkiyu ya maida takbinsa cikin kufenta sannan yaumari Muzaffarda cewa su gaba da tafiya ba tare da san yada zango a cikin wannan bakin daji don su kwana ba. ** Al'amarin Waziri Haawaisu kuwa bayan wani lokaci da tsintar gawar Hadiinsa da suka hallaka da maida siffarsa irin ta Muzaffar aka kawo si birnin AMbar akabinne shi amatsayin Muzaffar,sai yay i shiri ya tafi ga Sarki Sa'ad don sake neman auren Gimbiya Zuhuriya ga dansa Najiranu, tunda wanda aka bada aurenta gare shi ya hallaka. Da isar sa fada ya tadda Sarki da sauran yan majalisarsa zaune a fadar anafadanci ya isa ga Sarki ya kai gaisuwa aka amasamasa sannan ya nemi waje ya zaua aka ci gaba da zaman fad tare dashi da lokacin tashi daga zaman fada yay i aka yi addu'a aka tashi sauran yan majalisa suka fita daa fadar Sarki shi kuma aziri Hawaisu sai ya matsa ga Sarki y ace da shi, yana son Magana da shi Sarki Sa'adda ya bashi dama Waziri Hawaisu ya fara da cewa. "Allah ya baka nasara na dawo gare ka ne akan maganar neman auren yar ka Gimbiya ZUhuriya ga dana Najiranu, wanda ya dade yana bege a gareka kasancewar wand aka bada aurenta gare shi Allah ya kaddara ba za ta zama mata a agare shi bay a hallaka, sai dai mu yi masa addu'a Allah yay i masa rahma ya gafarta masa". Da Sarki Sa'ad ya ji wannan bayani sai ya amsa masa da cewa "Hakika na ji abin da yake tafe da kai gare 64 harafi Tafiyar ajali ni kuma ina sane da cewa ka taba neman auren Gimbiya ZUhuriya ga danka Najiranu, tun kafin na bada aurenta ga Muzaffar dan gidan Liman Adnan da ya rasu, sai dai kamar yadda na sanar da kai tun a farko b azan yi saurin yanke hukunci akan taba har sai na ji daga gare ta don haka zan bawa danka damar zuwa gare ta don su fuskanci juna,idan sukasan kansu ta amince da cewa tana kaunarsa t kuwa zan bada aurenta gare shi. Wannan shi ne shawarar da na yanke akan dukkanin mai neman aure Gimbiya Zuhhuriya". Waziri Hawaisu yay i godiya da ya ji wannan bayani na Sarki Sa'ad sannan suka yi sallamaya tashi ya kamahanyar komawa gida da isar su gida yay i kiran dansa Najiranu, ya sanar da shi yadda suka yi da Sarki Sa'adul gamidi akan zai bashi dama ya je su yi hira da Gimbiya ZUhuriya idan sun fuskanci juna ta amice tana kaunarsu to kuwa Sarki Sa'ad yay i alkawarin zai bada aurenta gare shi, Najiranu yay i matukar murna da farin ciki da jin wannan labarin sannan ya kasance cikin sauraren lokacin da za a bashi dama ya fara zuwa gareta don su fahimci una. Shi kuwa Sarki Sa'ad da ya koma gida sai ya sa akakira masa yar sa gimbiya ZUhuriya don ya sanar da ita shawarar da ya yankeakan batun masu neman aurenta da zuhuriya ta samu sakon mahaifinta ta tafi gae shi ta Baishe dashi, bayan Sarki Sa'ad ya amsa ya shaida mata cewa "Na sa an kira ki ne don na sanar da ke shawar da na yanke akan maganar auren ki zan bawa Najiranu dan gidan Waziri Hawaisu damar ya zo hira gare ki don ku fahimci juna, idan Allah ya sa zuciyarki ta amince da shi kin zabe si ya zama madadin masoyinki wanda ya hallaka to kuwa zan bada aurenki gare shi, idan kuwa ba kya 65 harafi Tafiyar ajali ra'ayinsa kina da zabin ki ki fidda duk wanda kike so na bada aurenki gare shi matukar dai bai zamo daga cikin mutanen da shari'a ta haramta aurar da ke a gare sub a, ina sane da halin da kike ciki na mararin rashin masoyinki Muzaffar da ya rasu, sai dai zan so ki kasance mai juriya hakuri da yadda da kaddara ki ci gaba da addu'a Allah yayi masa rahma ya kuma hadaki da wanza zai zama madadinsa gare ki". Da gimbiya zuhuriya ta ji wannan bayani na mahaifinta sai ta ce ta amince da shawarar da ya yanke akan maganar aurenta daga nan sai Sarki Sa'ad y ace da ita "Ta shi ki je Allah yayi miki albarka Gimbiya zuhuriya ta tashi ta koma dakinta ta zauna ta shiga tunani da sake sake a ranta game da abin da yake faruwa cikin rayuwarta, kuma har yanzu ba ta gasgata cewa masoyinta Muzaffar ya hallaka ba, zucyarta na hangen cewa wata rana zai dawo gare ta matukar yana raye a doron kasa don haka ta yanke shawarar ta dauki matakin da zata kauce daga bada auren a wani har masoyinta Muzaffar ya dawo kamar yadda take fata da muradi a cikin zuciyarta. Bayan kwanaki uku aka bawa Najiranu damar zuwa ga Gimbiya ZUhuriya don su fahimci juna a ranar da zzai fara zua Gimiya Zuhirya ta yi ado da kayan adona alfarma irin wanda yayan manyan sarakuna sukekwalliya dashi wancan zamani, ta tafi lambun mahaifinta ta zauna tana jiran isowar Najiranu cikin nuna rashin damuwa da sakiin fuska da cewa bata kaunar Najiranu ko kadan a ranta kuma ta shirya yadda za ta rabu da shi a cikin zuciyarta, can da yammaci bayan rana ta yi sanyi sai ga Najiranu ya iso wannan lambu da gimbiya Zuhuriya takezaune tana jiran iowarsa,ya caba ado da sutura ta 66 harafi Tafiyar ajali alfarmada manyan attajrai da yayan Sarakuna suke sanya aka yi masa iso gare ta ya shiga har nda take zaune yay i mata sallamata amsa masa cikin farin ciki tamkarbabu wani abu a zuiyarta sannanta yi masa izinin zama kan kujerar da ke kusa d aita ya zauna suna fuskantar juna. Bayan Najiranu ya zauna ya dube ta y ace da ita "Ranki ya dade tauraruwar a cikin 'ya'yan Sarakunan duniya na san kin yi sani da dalilin zuwana are ki kamar yadda maaifinki ya sanar d ake, sai dai zan kara yin tahaliki akan hakan don ki fahimci alkiblata, an turo ni gare ne domin mu fahimci juna idan kin amince da ni a matsayin masoyi kamar yadda na dade ina begenki a cikin zuciyata, to kuwa mahaifinki yay i alkawarin zai bada aurenki gare ni, na san kna cikin tsananin kewa da mararin rashin abin begenki da ya hallaka, don haka ina mai fata da muradin na zamo madadinsa a gare ki, na maye gurbinsa da yake a cikin zuciyarki da sannu zaki same ni mutum ne mai kyautata da faranta zuciyarki fiye da duk wani danamiji da za ki so a cikin zuciyarki mene ne makomar zance na?" Gimbiya ZUhuriya ta dubi ajiranu bayan da ta gamajin bayanin sa sannan ta yi ajiyar zuciya ta amsa masa da cewa "Hakika ina cikin kewa da mararin abin begena da na rasa kuma zuciyata na tare da fargabar rashin samun wanda zai zama madadinsa gare ni cikin mazajen da suka kasance masu neman aurena a bayan rashinsa. Najiranu yay i sauri y ace da ita "Me yasa kika ambata wannan Magana baya ga cewa bas hi kadai bane da namiji da ya rage a doron kasa, kuma ya hallaka ba sannan ace irin daraja da martabar Muzaffar ya fi ni da b azan iya zama madadinsa a zciyar ki ba, girman nasa ba ta 67 harafi Tafiyar ajali sarauta ko kuma tarin dukiya, duk da kasancewar mahaifina ba Sarki bane amma shi ne wazirin mahaifinki,don haka na isa girman daraja na aure mace yar Sarki kamar ki. Gimbiya Zuhirya ta yi murmushi ta ce da shi "Dukkanin abin da ka ambata babu wanda Muzaffar ya fi ka girman daraja dukiya da nasaba da saurauta, sai dai Muzaffar yana tare da wata baiwa da na kasa riskarta cikindukkanin mazajen da suka bayyana gare ni da nufin neman aure na, wannan baiwa it ace jarumta da bajintarsa wadda dukkanin jama'ar birnin nan sun tabbatar da haka,ina so na auri namiji jarumi, mai karfin zuciya da rashin tsaro wanda zai yi alfahari da shi a cikin dubban dubatar mazaje kuma na rasa samun kamarsa a cikin mazajen da sukarage suna neman aurena. Najiranu ya fusata dajin maganarta yayi sauri y ace da ita, "Ka da ki zamamai nuna kaskanci ko gazawa ga wanda ya ambata yana kaunarki don kina cikin mararin rashin sabin begenki wa wnda ya hallakaakan shu'umanci da hatsabibancinsa, kuma wace irin jarumta da bajinta Muzaffaryake da ita wadda nib a zan iya aikata kamarta ba". Gimbiya Zuhuriya ta ji zfin maganar ad Najiranu ya ambata akan Muzaffar saboda kaunar da take yimasa, amma sai ta daure ta danne abin a ranta cikin sakin fuska ta ce da shi. "Kada ka zama mai fusatuwa cikin abin da na ambataban zama mai nuna tozarci ko gazawaa gare k aba don na yabi jarumta da bajintar Muzaffar,idan kana soka ka zama madadinsa a gare ni, na amince da maganar aurenka to ka zama jarumikamarsa, ina son ka tafi bayan birnin Anbar ta bangaren kofar dake kudu bayan kwanaki 68 harafi S Tafiyar ajali uku massu zuwa, z aka hadu da wani jarumi mahayin doki sanye da bakaken kaya yana rike da wata takobi abar yiwa marikarta ado da zinare katunkare shi kayi fada da shi idan hark a samu nasara akansa to kuwa nay i maka alkawarin zan aureka". Shaidar da zata tabbatar da hakan it ace ka dauko takobin da ke hannun wannan jarumi kakawo ta gare m,kuma koda ka samu nasara akan wannan Jarumi kada ka hallakashi kamar yadda shimaidan ya samu nasara akanka ba zai hallakaka ba, don haka ina sauraronka daga nan zuwa kwanaki biyar idan hark a kawomin takobin wanan jarumi da na sanar da kai to kuwa nay i alkawarin aurenka". Tana gama fadar wannan maganarta yi masa sallamata tashi daga inda take zaune ta koma cikin kuyanginta suka kamahanyar komawa gida, daga nan shima Najiranu ya tashi ya fita daga cikin lambun ya kamahanyar komawa gida yana mai tunanin maganar da gimbiya ZUhuriya ta sanar da shi, tare da daukar alwashin cewa zai je ya tunkari wannan jarumi da ta sanar da shi don fafatawa dashi ya karbo takobin da take hannunsa ya kawo mata kamar yadda ta bukata, cikin wannan tunanin da yakeyi har ya isa gida yana zuwa ya sanar da mahaifinsa abin da yake faruwa tare da yadda sukayi da gimbiya ZUhuriya da kuma alwashin da ya dauka don tunkarar wannanjarumi ya karbo takobin da take hannunsa ya kawo mata don ta amince da maganar aurensa. ** Al'amarin su Muzaffar da dattijo Zarkiyu kuwa bayan da suka hallakawadannan halittar da suka fara haduwa da su a cikin wannan bakin daji da suka shiga 69 harafi Tafiyar ajali suka ci gaba da tafiya ba tare da sun ya da zango don su kwanta barci ba, sai da suka shafe tsawon kwana daya da wuni daya suna tafiya a cikin wannan daji, sallah da cin abincine kawaiyake tsayar da su, sannan suka isa wani waje a tsakanin wasu manyan tsaunuka guda biyu da saman tsaunukan da yake ci da wuta akwai hanyar wucewa a bangaren dama da kuma bangaren hagu, hanyar da take a bangaren habu babu komai tar da ita sai farin rairayi da fili fetal tun daga farkonta har karshenta, wadda take a bangaren dama kuwa tana tsakan wadannan tsaunuka ne guda biyu da samansu yake ci da wuta, idan iska ta kada da karfi sai ka ga brbudin wuta yana zubowa kan hanyar daga saman wannan tsaunuka haka kuma idan wutar ta yi huci da ruri mai karfi da take yi sai ka ga harshen wutar ya taho har kasa ya lullube hanyar baki daya. Da isar su wannan waje suka ja suka tsaya Zarkiyu ya dubi Muzaffar y ace da shi "Babu wata hanyar wucewa sai ta cikin wannan hanyoyi guda biyu dake gabanmu, kuma ta cikin wannan hanya dake bangaren dama da wuta take zubuwa akanta zamu bi u wuce ba zamu bi hanyar dake bangaren hagu ba". Da jin wannan magan ata zarkiyu sai Muzaffar yayi sauri y ace da shi "Saboda me za mu bi ta kan wannan hanya da wuta take zuba a kanta mu kai kanmu ga hallaka tare da cewa ga hanya a bangaren hagu wadda ba ta tare da wata musiba,kokuma abin cutarwa da zai iya kai mu ga hallaka". Zarkiyu ya juyo cikin sauri y ace da si "Umarni nake baka kana bin da na ambata ba ina neman shawarar a gare k aba,kuma na hane ka da yin tambaya a gare nit un a farkon marra kafin mu fara yin wannan tafiya a 70 harafi Tafiyar ajali tsakanina da kai, sai dai b aka zama mai kiyaye abin da na hane ka da aaikatawa baka kasance mai wofinta da maganata da yin tambaya cikin lamarina, wannan shi ne kuskure na biyu da ka aikata a gare ni cikin wannan tafiya, kuma idan baka zama mai kiyayewa ba, ka nisanta ga barin wannan hali n aka to kuwa zan tfi na bar ka a cikin wannan tsibiri ka hallaka b azan taimaka maka ba". Da jin wannan Magana ta Zarkiyu sai Muzaffarya sunkuyar da kai kasa yay i shiru bai sake cewa komai ba, zZarkiyu ya ci gaba dacewa da shi "Za mu bi ta kan hanyar dake bangaren dama mu wuce idan mun isa inda wutar take zubowa daga sama n wadannan tsanuka kada kaji tsoron koka razana ka bi ta cikinta mu wuce sai dai id aka ji wutar tayi ruri da huci mai karfi ka dakata da tafiyar da kakeyi ka tsaya har sai wutar ta gama hucinta, karhshen wutar da yakerufe hanyar ya koma sama sannan ka ci gaba da tafiya, idan kuwa bakakiyaye ba, ka ci gaba da tafiya a sanda wutar takeui da ruri to kuwa harshen wutar zai konaka kahallaka kakonekurmus baki daya sai ka yi hattara". Zarkiyu yana gamafadar wannan Magana sai ya juya ya wuce gaba ya nufi hanyar da wutar take zubowa akanta, Muzaffar ya bi bayansa ba tare da ya sake zubowa akanta, Muzaffar ya bi bayansa ba tare da ya sake ambaon wata Magana ba har suka isa inda hanyar take,suka somatafiya akan wannan hanya dake tsakanin manyan tsaunuka,idan suka ji hucin wutar dake saman wadannan tsunuka sai su dakata da tafiyarar da suke yi har sai harshen wutar y agama rufe kan hanyar ya komasama sannan su ci gaba da tafia da haka har suka wuce wannan hanya ba tare da wani abu ya faru gare sub a,da suka ga sun wuce wannan hanya lafiya sai sukayi 71 harafi Tafiyar ajali goddiya ga Allah sannan sukaci aba da tafiya acikin wannan daji. Bayan sun yi tafiyar kwanaki biyu daga inda suka wuce wannan hanya suka sake isowa wani keweaye a tsakiyar wannan daji,Zarkiyu ya ja ya tsaya ya zare takobinsa dake tare da shi,sannanya dubi Muzaffarya се da shi, "Ka kasance cikin shiri domin za mu sake haduwa da wasu miyagun halittun a cikin wannan kewaye da zamu shiga kuma sai mun yi yaki da sum un samu nasarar hallakasu kafin mu samu damar wucewa daga cikin wannan da ira dondon haka ka yi amfani da wannan it ace da nab aka don kare kanka da kuma hallaka wadannan halittu da zamu hadu da su a ciki wannan da ira. Muzaffarya amsaba tare da yay i masa tambaya ba don kiyaye abin da ya umarci kada ya sakeaikata kuskutedaga nan Zarkiy ya wuce gaba Muzaffaryabi bayansa sukashiga wannan kewaye da kegabansa.da shigarsu cikin wannan kewaye sai sukasomahangen wasu irin halittu masu kama da siffar mutane amma girmansu ya ta'azzara fiye da girman dan adam suna dadoro a tsakiyar bayansu kamar tozon rakumi tare da kahonni guda biyu a tsakiyar kansu, idanunsu guda daya ne a tsakiyar goshin kuma suna da wasu dogayen hakura guda biyu da sukafito daga cikin bakinsu zaro zaro kamar hauren gawa, kuma halittun bas a Magana ko

Chapter 5 of 9