Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 9
kuma ambata wani abu sai gurnani kamar karnuka, muni da rashin kyawun surarsu ya ta'aza ga idanunsu wanda bai zamo daga cikin jinsinsu don kuwa halittun su kasancе ababen ban tsoro da firgitarwa ga dukanin bil'adama da ya gansu,kuma halittun baki daya suna tafe akan wasu dabbobi ne masu kama da kura, sai dai girmansu ya wuce 72 harafi Tafiyar ajali na ingarman doki abin har ba zai misaltuwa ba, kowacce dabba daga cikin wadannan dabobibi mahayin ta ya sanya mata linzami kamaryadda akeiwa doki wasu daga cikinsu dabbobin mahaya biyu ne akansu wasu kuwa har uku, kuma hannayensu rike da wasu irin bakaken takubba wasu daga cikinsu mashi wasu sasari ko al'amudu da sauna kayan fadatamkar rundaunar baradanu da zasu tafi fafata yaki a fagen fama. Da ganin su Muzaffar sun shigo cikin wannan da'ira sai halittun nan suka karkata gare su baki daya sukayi gunji da gurnanin da sukeyi suka tasokansu a harzuke tamkar daman su sukejira su fito yaki ne saboda su hallakasu. A ganin haka sai zarkiyu ya daga takobin a take hannunsa ya tare su cikin karaji dagunji irin najarumta da sadaukantakayafara tafiyar ruwa da kawunan wadanda suka fara tunkarar sa a karon farko sannan ya fantsama a tsakaninsu ya farmusu da sara da kaifin takobinsababu kakkautaa, duk inda ya ratsa a tsakanin adan nan halittu sai dai ka ga gawarwakinsu da na dabbobin da suke kai suna zuba kasa matattu tamkar busasshen ganyen bishiya da iskatake kadowa daga jikin reshin bishiya, shimaMuzaffar da ganin yadda Zarkiyu yakehallaka wadan nan halittu sai daga wannan fekeken işace dake hannunsa ya karkata gare su cikin karfin zuciya da jarumta irin ta neman tsira daga hallaka, dukwanda ya tasogare shi daga cikin halittun nan sai ya fara sanya tsinin itacen dake hannunsa ya soke wuyan dabbar da yakekanta ta fadi kasa sannan ya sake sanya tsinin itacen ya halakashi,hakasukayi ta dauki ba dadi da bakin gumurzu mai tsananin a tsakaninsu, da wadannan halittu har suka samu nasarar hallakamafi daga cikinsu. 73 harafi Tafiyar ajali Suna cikin kafsawa newani daga cikin halittun ya kaiwa Muzaffar duka da sararin bakin karfen dakehannunsa Muzaffar ya goce sasarin ya samu jikin wata bishiya dake bayansa nan take bishiyar ta ratattake ta zube kasa tamkar wadda aradu ta fada a kanta, saboda musiba ya sakekaiwa Muzaffar duka da sararin Muzaffarya kare itacen dake hannunsa nan take ita cen ya kubce daga hannunsa ya fadi kasa can gefe guda shi kuma yayi baya taga-taga kamarzai fadi kasa saboda karfin bugun da wannan halitta ya kawomasa da nufin hallakashi, halittar nan ya sake tasowa kansa a fusace yana jan sararin dake hannunsa a kasa, duk ciyawar da sasarin yabi ta kanta ta kama da wuta ta kone kurmus saboda musiba da take tare da sasarin wajen ya yi bakikkirin yana karasowa inda Muzaffaryake ya kai masa duka da sararin Muzaffar yayi sauri ya goce sararin ya samu wani daga cikin wadannan halittu dake kusa da ajen nan take suka yi sama akan iska daga shi har dabbar da yake kanta sannan suka fado kasa a can gefe suka kama da wuta suka kone kurmus. Da Muzaffar ya ga haka sai yayi sauri ya tafi ga inda itacen da yake yin amfani dashi ajen yin fada ya fadi kasa, ya sa ahannu ya dauka ya tari wannan halitta cikin hikimadakwarewa ta salon iya fada, suka ska yi karon battar karfe da kazamar haduwa maimuni halittar nan yana kai masa sura da nufin waftarsa ya hallakashi shi kuma Muzaffarsai ya sunkuyar daya sanya itacen da ke hannunsa ya harde kafafun dabbar da yakekanta ta durkushe ta fadi kasa tare da wanda yakekanta, kafin ya yunkura ya tashi Muzaffar ya isa gare shi yayi tsalle da majaujawa cikin azama da zafin namayasokamasa tsinin itacen dake hannunsa har sai da ya huda kan makoshinsa 3 74 harafi Tafiyar ajali ya fito ta baya,jini yay i tsartuwa sama ya watsu akan fuskar Muzaffar halittar nan yayi atakadairacciyar kara mai tsananin karfi irin ta azabar fitar rai gaba daya da irirar wajen ta yi amsa kuwa da amo mai hauhaa da ya garaye koina sasarin da yake hannunsa da ya daga shi da niyar kai bugu ya dao kansa, nan take ya kama da wwuta ya konekurmus ya hallaka Muzaffar yana gamahallaka wannan halittadaya da ya taso masa shima Zarkiyu yana gamakarasa hallakahalittun da suka yi saura yana fafatawa da su, suka tsaya suna duban halittun nan babu sauran wani mai rai a cikinsu kuma basu sake ganin wasu sun tunkaro inda suke ba daga nan sai suka yi godiya ga Allah a bisa nasarar da suka samu na hallaka wadannan halittu da suka taso gare su baki daya sannan zarkiyuu ya maida takobinsa cikin kubenta ya umarci Muzaffar da cewa su ci gaba da tafiya don su fita daga cikin wannan da'ira da za su tafiya Muzaffar yay i nufin ya dauki daya daga cikin makaman wadannanhalitu da suka hallaka,amma sai Zarkiyu ya hane shi da daukar kowane irin makami ko taba waní abu a cikin wannan da'ira har su fita daga cikinta, tare da gargadinsa cewa babu wani makami da zai iya amfani dashi acikinwannn tsibiri ban da fekeken tacen da ya bashi har sai sun isa inda zai sanar da shi yadda zai yi amfani da takobin dake tare da shi wannda dattijoMubasshiru ya bashi,hakaMuzaffar ya hakura bai dauki komai daga cikin makaman wadannan halittun duk da cewa zuciyarsa tana so. suka ci gaba datafiyadon su fita daga cikin wannan da'irada suke cikinta. 75 ** harafi Tafiyar ajali Can kuwa a birnin AMbar bayan kanaki uku da zuwan Najiranu wajen gimbiya Zuhuirya ta shaida masa ya fita bayan gari zai hadu da wani jarumi da zai yi fada da shi ya karbo mata takobin da take hannun wannan jarumi idan yana so ta amince da maganar aure a tsakaninsa da ita. Da ranaku sukacikakwanaki uku Najiranu ya yi shirin yaki ya dauki duk wani makamida yake amfani da shi a wajen yin fada ya shirya dokinsa ya kama yah au ya fita ya kama hanyar fita daga birnin ta kofar dake bangaren kudu kamar yadda gimbiya Zuhuriya ta umarce shidan ka ga Najiranu cikin shirin yakin da yay i a lokacin da ya fito zaka yi zaton wani hamshakinjarumine kokuma gawurtaccen sadauki ya fito cikin shirin yaki da nufin zuwa ya yaki jama'ar wani birni shi kadai ba tare da masu taimaka masa ba. Ita kuwa Gimbiya Zhuriya tun kafin Najiranu y agama nasa shirin ya fito daga gida tuni ta gama shiryawa da shirin yaki ta sanya sulke da hular karfea kanta (Kwalkwali) adda ta rufr mata fuska,ba da idanunta babu abin da ake iya gani yadda ba za a iya gane cewa mace ce ba, kamar yadda ta yi a sanda za ta jarraba jarumta, da bajintar Muzaffar, ta tafi ta kama dokinta ta hau ta fita ta kofar bayan gida, ba tare da kowa ya sani ba, ta nufi wajen da ta kwantataa Nairanu cewa zai hadu da wannan jarumi da zai yi fada da shi ya karbo takobin da take hannunsa ya kawo mata, idan yana so ta amince da magarsa aure a tsakaninsa d aita, tana zuwa daidai wajen ta samu wani duhun itatuwa ta shiga ta labe tana jiran isowar Najiranu. Bayan wani lokaci da zuwanta wannan waje sai ga Najiranu tafe akan dokinsa yana sasarfa ya nufo wajen da gimbiya ZUhuriya take boye cikin duhun itatuwa tana jiran isowarsa da zuwansa daidai wajen sai ya jalinzamin dokinsa ya tsaya yana huci da cka irin na fusatattu tamkar wanda ya fito neman abokin gabar da ya kashe masa mahaifiya don daukar fansa akansa ita kuma gimbiya ZUhuriya da ta gay a iso wajen 76 harafi Tafiyar ajali sai ta fito daga cikin duhun itatuwan da ta labe a cikinsu ta bayyana a gabansa. Na jiranu ya dubi wannan mahayin dokin da ya bayyana gare shi cikin shirin yaki ba tare da ya gane cewa gimbiya Zuhirya ce ba, ya dubi takobin da take tare da shi ya ga tana sheki da haske kasancewar anyi marikarya ado da zinare nan take ya gane cewawannan shi nejarumin da gimbiya Zuhuriya ta shaida masa cewa zai hadu da shi idan ya iso wannan waje wanda zai iya fada da shi ya karbi takobin da take hannunsa ya kai mata idan yana so ta amince da maganar aurensa da ita, don haka ya dubi annan mahayin da ke gabansa yace da shi. "Kai bajirarre, fandararrre,gafalalle makaskancin bawa, na fito ne domin nemankakuma na zo gare ka ne saboda na yake kana karbi takobin da takehannunka wadda zata zama shaidar yadda da amincewar abar begena cikin lamarin wanzuwar are a tsakaninmu don haka zan afku a kanka na karbi wannan takobin dake tare da kai ta karfin jarumta da bajinta don samun biyarn bukatata na auri gimbiya Zuhuriya, ko kuma ka bani takoin cikin lumana ba tare da na afku akanka ba, don kaucewa ukuba da azabar kaifin takobina a gare ka". Gimbiya ZUhuriya ta yi shiru tana sauraronsa bata tanka mas aba, ko ta maida masa da Magana shi kuwa Najiranu da ya ga haka sai ya fusata ya zare takobinsa cikin karaji da gunjin fusatuwa ya sake linzamin dokinsa ya taso kan mahayin da nufin gamawa da shi ya karbi takobin daga hannunsa, Gimbiya ZUhuriya ta yi sauri ta zare wannan takobi da ke tare da ita, ta tare shi cikin karumta da kwarewa ta sakon iya fada, suka hadu a tsakanin kaiwa juna sara alokaci guda, kaifin takubbansu ya hadu akan iska karfin haduar takubban da kwarewa a kai sara irin na gimbiya Zuhuriya y sa takobin da take hannun Najirannu ta kusa kufcewa ta fadi kasa yay i kokarin ya riketa da kyar ba tare da ta subuce daga 77 harafi Tafiyar ajali hannunsa ba sukawuce ba tare da wani ya samu abokin karawarsa ba daga cikinsu. Suka sake juyoa suka maida kai hari ga juna, da kaifin takubbansu nan take artabu ya rincabe a tsakaninsu aka soma zamiya da kai bara akan juna cikin salon nuna kwarewa da jarumta ga mamakin Najiranu sai ga wannan Jarumi da suke kafsawa da shi ya fi shi tsananin zafin namada saurin kai sara akansa,kuma salon fadan da jarumin yake amfani da shi Najiranu bai taba ganin makamancinsa ba a tsawon rayuwarsa, tun yana kokarin kare sara da maida martani har ya gaza kai sara sai dai kokarin kare kansa, ga Gimbiya Zuhirya ta ga haka sai ta himmatu wajen nusar da shi kuskurensa da tabbatar da gazawarsa a fagen jarumta da rashin kwarwa ta salon iya fada. Ta yunkura ta kai masa wani gawurtacce sara da takobinta Najiranu ya kasa karewa da takobinsa sai da ya sanya garkuwar dake rike a hannunsa na hagu yak are garkuwar tayi wata irin kara mai tsananin karfi saboda karfin saran da ta kai masa tartsatsin wuya ya tashi sama daga jikin garkuwa, shi kuma Najiranu yayi baya taba taga-taga kamar zai fado daga kan dokinsa saboda karfin sara. Kafin ya warware daga firgicin saran da ta kai masa ya maida kai hari ta sae jau dayju are sgu cujub azana da zafub banam ta jau nasa wabu sarab a daudau jafadarsa tana da daar da za a ta same shi idan ta so amma da ta gay a kasa kaucewa ko yak are saran kuma ba ta da niyar cutar da shi ko ta hallakashi sai ta kauda kaifin takobinta daga kansa ta sarai jikin garkuwa dake hannunsa. Najiranu yayi baya ya tntsiro daga kan dokinsa ya fado kasa, kansa ya bugi jikin wani kututture itace dake kusa da wajen ya ji masa ciwo a goshi. Garkuwar da takobin da suke rike a hannunsa suka fadi kasa gefe daban, kafin ya yunkura ya tashi gimbiya Zuhuriya ta dao kansa ta sake kai masa sara sai da takobin ta kusa sauka a kansa sai ta ja linzamin dokinta ta tsaya batare da ta sauke kaifin takobin a kansa ba. Najiranu ya rintse idanunsa yana jira ya ji saukar kaifintakobin a kansa ya hallaka sanda ya ga wannan jarumi da suke 78 harafi Tafiyar ajali kafsawa da shi ya kawomasa sara bayan faduwarsa kasa daga kan dokinsa ammasai ya jib a a saukekaifin takobin a kansa ba, ya bude idanunsa domin ya ga abin da yake faruwa sai ya ga wannan jarumi bai dauke kaifin takobinsa daga daidai kansa ba, nan take ya saduda ya tabbatar da cewa wannan jarumi ya samu nasara akansa, saboda yana bukatar ya hallakashi da tuni ya mika ruhinsa barzau ta sa ta kare, daga nan sai ya ga jarummin nan ya dauke takobin daga daidai kansa ya maida ita cikin kubenta sannan ya kadaliinzamin dokinsa ya iuya ya bar wajen ya nufi cikin dhun itatuwan da ya fito daga cikinsa da farko. Najiranu ya bi shi da kallo har ya shige cikin duhu itatuwan a bacemasaya tafi ya bar shi anan alamarya samu nasara akansa. Bayan tafiyar annan mahayi Najiranu yay i ajiyar zuciya sannan ya yunkura ya tashi ya dauki takobi da garkuwarsa dake a yashe a kasa ya tafi ya kama dokinsa yah au ya juya ya kama hanyar komawa gida zuciyarsa cike da bakin ciki na kasa samun nasara akan wannan jarumi da ya zo gare shi, domin ya karbi takobin da take hannunsa, ya kaiwa gimbiya Zuhuriya don samun amincewarta akan maganar aure tsakaninsa da ita, kamar yadda ta sharadanta masa. Da isarsa gidan mahaifinsa Waziri Hawaisu ya ganshi cikin matukar jigata da galabaita alamar bai ji dadin karawar da suka yi da jarumin da ya tafi don karbo takobin da take tare da shi ba, bare tunanin samun nasarar a kansa, cikin sauri Waziri Hawaisu ya tare shi ya kama masa ya sauko daga kan dokinsa sannan ya tambaye shi abin da yake faruwa. Najiranu bai boye masa komai bay a bayyana masa irin a rangama da artabu da sukayi da wannan jarumi kuma ya kasa samun nasara akansa ya karbo takobin da take hannunsa. Waziri Hawaisu yayi matukar bakin ciki da jin wannan labari na dansa Najiranu ya sunkuyar da kai kasa yay i shiru yana tunanin bayan wani lokaci ya dago kans aya dubi Najranu ya ce da shi. 'Dukda kasancewar baka samu nasara akan jarumi ba, ka sake komawaw wajen gimbiya Zuhuriya ka nemi amincewarta akan ta sake baka dam aka koma wajen wannan jarumi don karbo takobin da take hannunsa, idan har ta amince maka da cewa ka sake komawa gare shi don karbo takobin to kuwa zan nemi taimako daga Boka Musailamatu don kasamu nasara akan wannan jarumi ta hanyar alkaluman sihiri komai tsananin jarumta da sadaukatakar da yakeda ita koma ko wanene shi a doron kasa. 79 harafi Tafiyar ajali Da Najiranu ya ji wannan bayani sai ya samu karfin zuciya da himmatuwa ta ya koma ga gimbiya Zuhuriya don sake neman amincewarta ta bashi damar ya sake komawa don karbo takobin da take hannun wannan jarumi. Ita kuwa Gimbiya Zuhuriya bayan da ta samu nasara akan Najiranu ta tafi ta barshi a wajen da suka fafata da ta shige cikin duhu itauwa ta bace masa sai ta zagaye ta kama hanyar komawa gida da isarta gida ta cite kayan dake jikinta ta koma dakinta ta zauna ta ci gaba da gudanar da al'amuranta kamar yadda ta sab aba tare da wani daga cikin jama'ar dake gidan ya san abin da yake faruwa ba, da gari yaw aye yamma ta karato daidai lokacin tafiyarta lambun mahaifiinta tare da kuyanginta, kamar yadda ta saba ta zauna tana jiran isowar Najiranu domin ta ji abin da zai zoya ambata a gare ta tunda ya kasa samun asara akanta bare ya karbi takobin dake hannunta ya kawo mata don ta amince da maganar aurensa kamar yadda suka yi yarjejeniya da shi. Bayan zuwanta lambun ba da dadewa ba sai ga Najiranu ya iso ya nemi iso daga gare ta akan bahi damar shigowa cikin lambu, ya karasa inda take a a zaune Gimbiya Zuhuriya ta taryeshi cikin wawala da sakin fuska tana mai yi masa murmushi da nuna rashin damuwa da lamarinsa tamkar ba it ace tatare shi a daji suka fafata ba, bayan Najiranu ya zauna daga gefe suna fuskantar juna gimbiya ZUhuriya ta dube shit ace da shi. "Yau dai nag a tamkar baka tare da walwala cikin lamarinka kuma ban ga takobin da muka yi alkawarin zakakarbo daga hannun jarumin da na sanar da kai ba, domin na amince da maganar aure a tsakaninmu, ko kuma ba kasamu nasara akansa b aka dawogare ni bayan ambaton jarumta da bajinta da kakeikirarin kana tare da ita". Najranu ya amsa da karfin zuciya yana mai fadin cewa "Lamarin ya taʼazzara a gare nia farkon marra ban samu nasara akan wannan jarumi da na je domin na karbo takobin da take annunsa ba, a karawar da muka yi da shi kamar yadda ki ka umarce ni na kasance cikin halin rashin lafiya a wannan rana wadda ta tsananta gare ni amma saboda irin kaunar da nake yi a gare ki ya sa ban kauda kai ga barin alwakrin da muka yi dake ba, na tafi ga annan jarumi domin karbo takobin da take hannunsa, wannan shiyasa ban samu nasara akansa ba balle na karbo takobin da na kawo ta gare ki, saidai wannan ba yana nufin nuna gazawa ko kuma rashinjaruta a gare nib a face dai wanzuwar akasi don haka na sake dawowa a gare ki ina 80 harafi Tafiyar ajali mai neman izini da yardarki akan ki sake bani daman a koma ga wannan jarumi na karbo takobin da ke hannunsa, ni kuma nayi miki alkawarin zan koma gare shin a karbo wannan takobin na kawo ta gare ki,kamar yadda kika kubata matukar za ki amince d amaganar aure a tsakaninmu". Gimbiya Zuhuriyata yi shiru tana saurare da tunanin akan maganar da ya ambata duk da ta san cewa babu gaskiya cikin lamarin da zancen da ya ambata a gare ta da yake ta san cewa koda ta sake bashi dam aba zai iya samun nasara akanta ba, saboda karancin kwarewa ta salon iya fada kuma ta fishi jarumta da dabara na iya fada da kowane irin makami sai zuciyarta ta amince da cewa ta sake bashi dama ya koma ga wannan jarumi kamar yadda ya bukata. Bayan wani lokaci ta dago kai ta ce da shi "Zan sake baka dama a koma ga wannan jarumi don karbo takobin da take hannunsa kamar yadda ka bukata, amma sai ka amince da shauradan da zan sanar da kai guda biyu a yanzu. Sharadi na farko shi ne ba z aka sake neman watabukata a gare nib a matukar b aka samu nasara akan jarumi da z aka tafi gare shi domin karbo takobin da ke hannunsa, ba tare da ka sake dawowa gare ni akan maganar aure, sharadi na biyu kuma shi ne za ka sanar da mahaifinka ya koma ga mahaifina ya sanar da shi ka janye akan maganar neman aurena, idan kaamince da wannan sharuda to kuwa na baka dama bayan kwana biyar ka sake komawa ga wannan jarumi don karbo takobin da take hannunsa, kuma idan hark a samu nasara akansa zan amince da maganar aure a tsakanina da kai". Najiranu ya ji wannan bayani sai y ace ya amince da sharudan data ambata agare shii daganan suka yi sallama ya tashi ya kamahanyar komawagida cikin murna da farin ciki, cikin samun amincewarta ita ma gimbiya Zuhuirya ta tashi suka fita daga lambun tare da kuyanginta suka kam hanyar komawa gida. Da zuwan Najiranu gida ya sanar da mahaifinsa yadda sukayi da gimbiya zuhuriya mahaifinsa Hawaisu yay i matukar murna da farin ciki samun amincewarta sannan ya sanar da Najirannu cewaidan gari yaw aye tunda farkon safiya zai tafiya ga boka Musailamatu domin neman taimako a gare shi cikin dalasumai na aikin sihiri don samun nasara akan wannan jarumi komai tsananin jarumta da sadaukatarkasa a doron kasa. ** 81 harafi Tafiyar ajali Su kuwa su Muzaffar da dattijo Zarkiyu bayan da suka gama hallaka wadannan halittu da suka hadu da su a cikin wannan da'ira da suka shiga cikinta, suka ci gaba da tafiya tare da sun yada zango a ko in aba har suka yi kwana suka wuni suna tafiya acikin wannan da'ira Muzaffar yayi matukar gajiya da galabaita sabida arabun da suka yi da wannan halittu suka hallaka su sannan basu zauna sun hut aba suka ci gaba da tafiya. Suna cikin wannan tafiya e sai suk ji wata irin tsawa da rugugin aradu mai tsananin karfi da ban firgici sun gauraye dajin baki daya, har sai da suka daina jin komai ban da wannan rugugi da tsawar da suka dauki lokaci mai tsawo suna amsa kuwa da amomaihauhawa, iska mai karfi ta biyo baya tare da wata irin bakar guguwa da ke cudanye da wani haske mai kama da hasken walkiya a tsakiyar ta, bayan lafawar iskar da tsawa da rugugin da sukeji sai suka ga wandasu irin manyan mikiya masu matukar girma da ban tsoro da Muzaffar bait aba ganin nau'in tsuntsu mai irmansa ba, idan sukai wani irin kuka mai kama da kakari sai ka ga wuta tana fesowa daga bakinsu, duk abin da wutar ta zuba a kansa sai ka gay a kone kurmus cikin dankankanin lokaci ya zamatolka. Da Zarkiyu ya ga wannan al'amari da yake tare da wadannan mikiyoyi da sukatunkaro inda suke sai yay i sauri ya nemi wani kogon dutse dake kusa da wajen da suke y ace da Muzaffar su yi sauri su shiga cikin kogon dutsen su buya kafin wadannan mikiyoyi su karaso inda suke suka shiga cikin kogon dutsen suka zauna sai suka rikajin tsawa da rugugin da suke jinn a dada kauwa da hauhawa har dusten da suke ciki yay a soma girgiza da raurawa tamkar zai fashe ya rufto kansu su hallaka, bayan wani lokaci yana kara tsananta da munana a agare su suka rika jin wata irin zazzafariskamaikamada tiririn ruwan zafi tana ketowa tana shigowa cikin wannan kogon dutsen haka suka dauki lokaci numfashi sai ya ji tamkar zai kama da wuya yak one kurmus saboda musiba. Da rana ta gama faduwa tare da yay i su Muzaffar suna zaune cikin wannanmummunan yanayi da suka riski kansu a ciki sai Zarkiyu ya tashi ya dubi Muzaffarya ce da shi "Zan fita na yaki wadannan halittu har sai na hallaka su baki dayansu, domin mu samu damar ci gaba da tafiya mu fita daga cikin wannan da'ira kazauna a cikin kogon dutsen nan har na dawo kada ka sake kace zaka fita daga cikinsa idan ban i na umarce ka da cewa ka fito ba, kuma babu wani abin cutar da zai iya shigowa cikin wannan kogon 82 harafi Tafiyar ajali dutse ya cutar da kai matukar kana cikinsa baka fto ba, idan na samu nasarar akan wadannanhalittun zan hallaka sun a dawo gare ka kafin ketowar alfijir". Da y agama masa wannan bayani sai ya zare takobinsa ya juya ya fita daga cikin kogon dutsen don zuwa yaki wadannan mikiyoyin dake waje tun da zarkiyu ya fita sai Muzaffar ya soma jin kakari da kuka wadannan mikiyoyin ya sake gauraye dajin baki daya, wani lokaci yak an hango irin feshin wutar da wannan mikiyoyin suke fitarwa daga bakinsu idan ya zubo kasa daga cikin ogon dutsen da yake boye, haka a ka shafe tsawon daren wannan rana har gari yaw aye Zarkiyu bai dawo ba, kuma Muzaffar bai daina jin kuka da kakarin wadannan halittu ba, aka sake shafe tsawon yini ranar har dare yayi ana cikin wannan yanayi ba rae da Zarkiyu ya dawo ba hankalin Muzaffar yay i matukar tashi yashiga fargaba da rashin tabbas akanhalin da Zarkiyu yake ciki ganin cewa y ace zai dawo kafin ketowar alfijir gas hi har ya kwana ya wuni bai dawo ba. Cikin wannan dare sai Muzaffar ya rikajin kakari da kukanwadannan mikiyoyi ya dada karuwa fiye da yadda yakejinsa afarkon mara, hankalinsa ya kara tashi ya soma tunanin ko Zarkiyu ya hadu da wani abin cutarwa da yay i masa illa a bayan ftarsa, don haka yay i tunanin cewa idan har gari ya sake wayewa Zarkiyu bai dawo ba to kuwa zai fita don ganin abin da ya faru a gare shi ya kuma san halin da yake ciki. Da gari yaw aye Zarkiyu bai dawo ba bayan Muzaffar ya idar da sallar asubahi sai ya yanke shawarar fita daga kogon dutsen domin ya ga halin da yake ciki ya dauki fekakken itacen nan da Zarkiyu ya tashi don ya rika yin amfani da shi wajen yn fada ya nufi kofar fita daga kogon dutse, ya fara lekawaaaa waje a hankali ya ga babu komai a wajen ban da gawarwakin wadannan mikiyoyin gasu nan birjik a kasa tamkarbusassun ganyayyakin bishiya da iska ta zubo da su kasa kuma gaba daya kasar wajen ta kone ta yi baki saboda feshin wutar da wannan mikiyoyin suke yi. Bishiyin da ke kusa da wajen sun kone sun yi baki busasssun iatuwa kuwa sun zama toka. Muzaffar ya duba bai ga dattijon Zarkiyu a kusa da wajen ba, don haka ya fito daga kogon dutsen domin neman inda zai ganshi da fitowarsa daga cikin kogon dutsen sai ya ji wata irin iska mai karfi ta taso kansa, ya juyo da sauri domin ya a abin da ya taso masa kafin ya lura da abin da ya taho gare shi tuni ya ji an sure shi an yi sama da 83 harafi Tafiyar ajali shi a cikin wannan iska, sannan ya ji kuka da kakari wanda wannan mikiyoyi suke yi tun a farkon sanda suka fara hangensu karfin sura da daukar da akayi masa ta gigita da firgita shi, sannan ya ji wani abu mai kama da tsinin mashi ya kama jikinsa sosai ga tsininzafi yana ratsa jikinta tamkar ana sukansa da kibiyar da aka zaro ta daga wtar makera soma saboda musiba, nan take ya soma fita daga hayyacinsa ya sarkewa. Muzaffar ya ji an ci gaba da tafiya da shi akan iskacikin wannan hali na kunci da musiba da yake ciki yun bayan da ya ji an asure shi an tashi da sama akan iska yay i duba ya zuwa ga abin da yake rike da shi sai yaga daya daga cikin mikiyoyin nan ce ta sure shi ta tashi sama da shi akan iska, yayi kokarin ya kufce daga rikon da ta yi masa don ya kwace kansa daga gare ta amma sai ya ji ya kasa, koda zare faratan da ta kafa masa a jikinsa bare

Chapter 6 of 9