cak. Saqir ya kalli likitan da mamaki da tsoro suka gauraya a fuskarsa. Likita ya sauke numfashi mai nauyi, ya furzar da iska daga bakin sa yana girgiza kai.
“Na san hakan zata iya faruwa…” ya ce a hankali, yana duban su duka. “Ya bugu sosai a kansa lokacin hatsarin, jini ya zuba da yawa. Wannan ne yasa memory ɗinsa ta samu matsala. Ya manta da kowa, da komai — har da kansa.”
Dakin ya dauki shiru. Zuciyar Muhsin ta buga da ƙarfi, hawaye suka fara taruwa a idonsa.
Likita ya dafa kafaɗar saqir cikin tausayawa ya ƙara da cewa:
“Yanzu hakkin kulawa da shi ya rataya akan wuyanku. Zai iya zama kamar jariri, yana bukatar a koya masa komai daga farko. Ku shirya… tafiya ce mai tsawo.”
Sai ya juya ya fita a hankali, yana barin su cikin dakin da ya cika da shiru — shiru mai nauyin tambayoyi da hawaye.
Saqir ya zuba wa Bashir ido, ya kama hannunsa a hankali, zuciyarsa cike da raɗaɗi da alkawari a hankali ya furta cikin zuciyarsa:
“Ko ka manta da duniya Bashir, ni ba zan manta da kai cewa mune sillar shigar ka wanan yanayi na…”
BAYAN WANI LOKACI KAƊAN...
Shaquwa mai zurfi ta shiga tsakanin Noor da Suhail duk inda ka ga ɗaya, to ka tabbata ɗayan yana kusa. Suhail ya saba da kallon ta tana dariya, yadda take tura gashinta gefe ɗaya idan iska ta ɗauke shi, yadda take girmama shi da kulawa irin ta zuciya mai tausayawa.
A gefe guda Noor ta saba da kiran sa “Suhayl” cikin muryar da take fita da salo mai taushi, kamar kiran da yake ta da ƙauna daga wani ɓangaren zuciya da ba ta san yana akwai ba.
Idan suna aikin gona, Noor ce ke kai masa ruwa. Idan suna hutu, shi ne ke lallaba ta da faɗin,
“Ke dai kin zama kamar hasken safe ko rana bata fito sai na ganki.” zuciyarta kan buga, tana juyar da kai tana murmushi:
“Wannan magana taka ka bari, ba komai bane face wasa.”ya ce cikin murya mai natsuwa:
“Wani wasa ne da yake fito daga zuciyar da ba ta iya ɓoye gaskiya.”
haka shaquwar su ta zurfafa har ta kai ga Noor ta daina jin nauyin zama kusa da shi. duk inda suka je, sai a ce “su biyu nan sun zama kamar ruwa da kankara, ba su rabuwa.”
A ƙauye kuwa, magana ta zama abin ci da sha.
Wasu suna faɗa da murmushi, wasu kuma da haushi “wai Noor wacce ta taɓa yin rantsuwa da sunan Allah cewa zata jira Bashir… yanzu ga ta da sabon saurayi.”maganar ta yawaita har ta kai ga iyayenta, zuciyarsu ta yi nauyi da damuwa.
Amma Noor ba ta da ikon tsayar da abin da yake girma a zuciyarta — wani abu mai kama da tausayawa amma yana sauyawa zuwa so cikin sannu, cikin sirri, kamar yadda iska ke sauka a dare ba tare da sauti ba.
Wani dare tana zaune a bakin tagar ɗaki, tana kallon taurari. Sai ta furta da sanyi a cikin ranta:
“Bashir... ka bar ni cikin duhu da alƙawura. Amma wannan zuciya ta... tana neman wani haske ne daga inda ba ta zata ba.”hawayenta ya sauka a hankali, ta shafi kumatunta tana lumshe ido amma a zuciyar Suhail, soyayyar da ke ci kamar wuta ta gama cinye shirin komawa baya.
A wannan lokaci, kowa a ƙauye ya yarda Noor ta manta da amana, ta manta da Bashir.
Sai dai a zuciyarta, akwai sirrin da ita kaɗai ta sani — soyayya ce mai rikitarwa, tsakanin amanar da ta bari da zuciyar da ta fara jin wani sabon sauti.
* What will happened in the next…
✨🌟 KAƊANGAREN BAKIN TULU 💥✨
BY
NARNAH ƘANWAR SOJA
Follow my Wattsp group 👇👇👇
https://chat.whatsapp.com/LDm6JQR1M3L5dOPu5dB0TM
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚
(🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚)
GARGAƊI
Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba ,
********
PART TWO
PAGE 24/25
BAYAN WASU SHEKARU
Firgit ya farka daga nannauyan baccin da ya ɗauke shi kamar wanda aka nutsar cikin duhu numfashinsa ya yi nauyi, idonsa ya buɗe a hankali kamar wanda ke komawa duniya daga wani wuri mai nisa cikin muryar da ta rikice, sai ya fara maimaita addu’a:
“Innalillahi wa inna ilaihi raji’un…”
Kalmar ta tsaya a kan laɓɓansa, tana fita a hankali, tana haɗuwa da rawar jiki da firgici. gumi mai sanyi ya bayyana a goshinsa, yana gangarowa bisa kyakkyawar fuskarsa wadda ta haɗu da tsananin kamala da kwarjini.
Yana daurewa, amma fargabar mafarkin da ya farka daga gareta ta kasa barin zuciyarsa ta zauna a hankali ya dafa kansa, hannayensa masu tsawo da haske suka motsa a hankali kamar yana neman kwanciyar hankali daga cikin jikinsa.
Sai ya sauke ƙafafunsa — dogaye, masu santsi — daga kan gadon farin zanen da ya lullube shi. Gashin kansa mai laushi ya kwanta luff-luff a kan fatar kansa mai haske, yana ƙara masa wani irin kyau da natsuwa da ba a iya fassara wa.
Ya jingina da katangar gefen gado, yana sauke numfashi a hankali, yana ƙoƙarin tuna... amma babu komai. Abin da ya rage a cikin zuciyarsa shi ne wani abu mai nauyi — tsoro, da tambaya, da shiru mai cike da asiri.
Hannuwansa biyu ya saka cikin gashin kansa, yana ja da su a hankali kamar mai son tabbatarwa da kansa cewa yana cikin duniya. Doguwar ajiyar zuciya ya saki, sautin numfashin sa ya gauraya da shiru mai nauyi.
A wannan karon, mafarkin da yake masa kamar rigar jikinsa yau ya sauya salo — domin komai ya dawo masa bayan dogon lokaci na duhu da rashin sanin kansa, yau ya fara tuna komai yau ne Bashir ya dawo cikakken mutum.
Siraran hawaye masu dumi suka fara gangarowa a fuskar sa, suna haɗuwa da ɗan murmushin da bai cika ba — murmushin wanda yake tsakanin farin ciki da firgici.
Sai kawai aka ji ƙarar ƙofar da aka turo da sallama, cikin taushi da nutsuwa.
Wata yarinya ce ta shigo — kyakkyawa, tsaf cikin doguwar abaya mai kamshi, mayafi mai ɗan haske a kanta zubin ta na nuna tarbiyya da asalin gida mai natsuwa.
Da farko ta tsaya cak, idonta a kansa, ta ɗan firgita ganin yadda yake zaune cikin ruɗani da hawaye da sauri ta matsa kusa da shi tana faɗin “Yayah Bashir, lafiya kuwa? Me yasa kake kuka?”
Muryarta mai sanyi da taushi ta dawo da shi daga zurfin tunanin da ya nuts ahankali ya kalle ta, idonsa cike da mamaki, da tambaya, da tsoron gaskiyar da ta dawo masa.
Ta sunkuya, ta tattara light breakfast ɗin da ta ajiye a kusa da gadon — faranti mai ƙunshe da toast, omelet mai cike da kayan lambu, da kofin warm milk wanda kamshinsa ke tashi cikin ɗakin ta juya a hankali, tana kiran:
“Mommy! Daddy! Ya Bashir ya farka!”
Muryarta ta ɗan sarƙe, tana haɗuwa da rawar jiki da jin daɗin mamaki ta jinjina kai, tana kallon Bashir da idanun da ke cike da tambaya da bakin ciki lokaci guda.
“Yaya na kuka Mommy, wallahi yana kuka!”
muryar Khady ta tsinke cikin dakin da ɗan rawar jiki, tana magana cikin hanzari da tsoron abin da ta gani. Idonta ya kaɗa da hawaye, zuciyarta ta buga da sauri kamar zata fito daga kirjinta.
Mommy, wacce take a falo tare da Daddy, ta ɗago da mamaki da hanzari ta miƙe tana cewa cikin murya mai daure da fargaba “Khady, ki yi shiru mana! kwantar da hankalinki... let’s go and see him.”
Bata ma gama kalmar ba sai ta kama hannun yarinyar, suka nufi ƙofar ɗakin Bashir cikin tsoro da fatan alheri cikin wannan ɗan lokaci ne Sagir da Muhsin ya biyo bayansu, yana riƙe da hankici, fuskarsa cike da damuwa da mamaki.
Suna shiga dakin, sai kallo ɗaya ya wadatar.
Bashir na zaune turƙus a ƙasa, gaban gadonsa, hannayensa biyu sun dafe fuska, ƙirjinsa yana motsi da numfashin kuka.
Kamar ƙaramin yaro da aka wayi gari da tsoron mafarki, yana rawar murya yana maimaita addu’a, hawayensa na bin gefen kumatunsa har zuwa gemu.
Mommy ta tsaya cak a ƙofar, zuciyarta ta buga, hawaye suka cika idonta kafin kalma ta fito.
Daddy kuwa ya kasa motsi, yana kallon ɗan nasa da wata irin shiru mai nauyi — shiru mai cike da tambaya, mamaki, da godiyar Allah.
Sagir ya matso a hankali, muryarsa ta yi rauni:
“Bash... Bashir?”
Amma Bashir bai amsa ba — sai ma ƙara saka hannuwansa cikin gashin kansa, yana jan numfashi mai nauyi kamar wanda yake ƙoƙarin farfaɗowa daga tarihin da ya daɗe yana mafarki daga gare shi, gashi yau Allah ya..
#####
DUBAI
A hankali ta shafa kansa, ƙafafun hannunta sun rungume jikin sa da kulawa mai laushi. Nan ya firgita, zuciyarsa na buga da sauri kamar zata fashe.
“Haba Habibty, wallahi na tsoro ta…” cewar Rayyan, murya cikin kaɗan da rashin tabbaci.
Harara ta buga mai kai, idanunta suna cike da tausayi da damuwa. “Don Allah, Kaye… auren ma ba zaka daina wannan tsoron ba ko?”
Cikin murmushi mai cike da baƙin ciki, ya dawo da hankali a hankali. Murmushin sa ya yi sanyi, cike da wani irin nauyi da ya sha wahala, ya furta, “Habibty … kinan… rayuwa tamkar bani da uba, na azabtu a gidan mahaifina. Wallahi, bazan manta watarana da aka min sharrin sata ba ranar da tafe kowacce rana wahala a guna…”
Ya tsaya, ido na kallon ƙasa, zuciyarsa cike da tsoro da fargaba, amma a lokaci guda, akwai wata ƙaramar haske na farin ciki da ke bayyana a gefen fuskar sa — saboda yanzu, a ƙarƙashin kulawar Rayyan, ya fara jin cewa akwai wani wuri mai aminci a rayuwarsa.
A cikin murya mai rauni, Rayyan ya faɗi, yana kallon matarsa da idanuwa cike da zafi labarin da ya sha kamar wuta a zuciyarsa.
“Sun kawo wani tsohon soja Iri — mutum mai fuska kamar dutse, hannunsa kamar sanda. Sun daure ni a bayan hannu, aka rufe ni a ɗaki mai duhu; babu rana, babu iska, babu ruwa, babu abinci. Rana da dare duk sun tsaya a wuri ɗaya — zafi ya mamaye wajen kamar an jefa ni cikin ƙarfe mai ɗumi, tsawon kwanaki ukku ina azabtuwa
A can ne suka fara ‘horon’ — ba horo na ilimi ba, horon azaba. Sun kunna mini fargaba, suka nuna mini wani abu a matsayin ‘shaidar wuta’ — alamun azaba da nufin tsorata ni. Idona ya yi jaƙeƙe, zuciyata na bugawa kamar kararrawa, a duk lokacin sai na ji ƙamshin hayaki na bakin zuciya.
Hawayen suka fara cika idona; a lokacin Iro ya ƙi tausayi — ya shafa hawayen da hannunsa mai ƙarfi, amma shafinsa ba tausayi bace, sai tambaya mai sanyi: ‘Tabbas ka sha azaba Hayyaty amma me ya ƙubutta da kai a wancan ranar?’
ya sauke ajiyar zuciya, ya amsa cikin murya mai ƙasa, Muryar da na rawa: ‘Na ƙubutta... saboda ba ni da wata hanya tsoro ne ya ja ni, rashin gida ne, da rashin abin dogaro. Amma ba azabar ta zama banza ba; na rike abin da aka bani, na ɓoye amanar da zata ceci wasu.’
A duk lokacin da na tuna, numfashina na faɗuwa da sauri; amma a zuciyata akwai ƙanƙanin haske — sanin cewa duk wannan azaba ba ta ɓace ba, tana da lokaci tsanani baya tabbata haka daɗi baya dawwama ”
A jiyar zuciya na sauke, hawayen na zube kamar ruwan damina — a hankali, numfashin na ya fara rikewa cikin ƙarfi da kuka. Duk da haka, a tsakiyar ƙunci da azaba, sai wani abu ya zo min kamar labari mai dumi a kunne: murya — murya mai ƙamshi na gida, mai cike da tausayawa.
“Yaro na… ka natsu, ka daina kuka,” muriyar ta zo a hankali kamar ta fito daga cikin inuwa. Rayyan ya ɗaga kansa da sauri, idanunsa sunɗan yi jaƙeƙe. Bai yi shakka ba — muriyar mahaifiyarsa ce; ta fito masa fili a zuciya kamar ido yake gani.
A lokacin, sai na tuna da zanruttukannhikima da ƙawata Suwaiba kimin “Ka kasance ƙarfin zuciya, ka jingina da addu’a, kada ka bari tsoro ya mallake ka.” Wannan ƙaramar muryar ce ta sa zuciyarsa ta ɗan natsu.
Ya ɗan yi dariƙa, ya share hawayensa da bayansa na hannu, ya ce cikin rawar murya mai rauni:
“Mom… na tsoro… na sha azaba…”
Muryar mahaifiyarsa ta ƙara taushi, tana ƙoƙarin mika masa kwanciyar hankali:
“Na sani, ɗana. Amma ka ji daɗi — kai ba kaɗai bane. Mun zo tare da kai ka rike wannan ƙarfin zuciyar, mu za mu tafi tare muka samo mafita kada ka manta, hayaniyar duniya ba za ta wuce ba — amma girmanka da kirki zai zauna.”
A hankali, Rayyan ya sami ƙaramin natsuwa. Kukan sa ya ragu, numfashinsa ya koma daidaito yana kallon matarsa da idanu masu ƙara laushi, ya ɗauki hannunta, ya matsa kusa da ita da ƙanƙantar murya:
“Na gode, kin zo min a daidai lokacin da na fi buƙata.”
Ta rungume shi da ƙarfi, kamar tana ƙoƙarin ja masa duka danƙon duniya. suna kallon yadda ƙauna take warkar da raunuka.
To be continued.............
✨🌟 KAƊANGAREN BAKIN TULU 💥✨
BY
NARNAH ƘANWAR SOJA
Follow my Wattsp group 👇👇👇
https://chat.whatsapp.com/LDm6JQR1M3L5dOPu5dB0TM
*https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v
💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️
*(J.W.A)*
_Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️
🦚🦋THE NOBLE WRITER'S TEAM🦋🦚
(🦚✊DEDICATION IS OUR STRONG✊🦚)
GARGAƊI
Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba ,
********
PART TWO
PAGE 26/27
A hankali Bashir ya ɗago kansa daga cikin hannayensa, idonsa ya cika da hawaye, amma a ƙarƙashin su akwai wani sabon haske hasken da ya rasa shekaru da dama, hasken tunawa ya dafa kirjinsa, numfashinsa yana fita da sauri, kafin a hankali ya furta cikin murya mai rawa “Mommy… yau… yau na tuna komai. tabbas, nine Bashir.”
Mommy ta dafe ƙirji, Daddy ya ja numfashi da kyar, Sagir kuwa ya matso kusa, muryarsa cike da ruɗani “waye kai Bashir? wacece Noor da kake faɗa?”
Bashir ya lumshe ido, hawaye na zuba a hankali, yana jin kamar zuciyarsa tana sake rayuwa daga farkon ta ya ɗan murmusa da ciwo a fuskarsa, sannan ya ce:
“Sunana Bashir mahaifiyata ta haife ni cikin kurɓattaccen yanayi — ta mutu tana kuka, tana roƙon Allah ya kare ni daga zalunci na taso cikin wahala, cikin azaba, amma akwai wata rana… wata rana da ta sa rayuwata ta zama haske. ya ɗan yi shiru, numfashi na rawa, sannan ya ci gaba:
“Noor ce — yarinya ce da ta zama hasken rayuwata mun taso tare, mun yi alkawari na ce mata zan dawo garinta, na dawo da amana, saboda soyayyarmu ta yarinta ba ta gushe a raina ba.”
Ya share hawayensa, idonsa ya ƙara ƙyalli kamar wanda yake kallon nisan baya.
“Mallam Sambo… shi ne wanda ya raina mu, kuma shi ne mahaifinta. Shi ya sani yadda nake numfashi da wahala, yadda nake rayuwa da fatan wata rana zan dawo da cikakken ni.”
Shiru mai nauyi ya biyo bayan kalmomin sa. Mommy ta kasa magana, hawaye suka gangaro ta kumatunta Daddy ya dafa kafaɗarsa cikin taushi yana cewa:
“Bashir, tabbas ka zama ƙadangaren bakin tulu — duk wahalar da suka baka tun kafin ka zo duniya, duk ɓacin ran da ka sha, ga shi yau ka fito da haske. Allah ya baka rayuwa mai kyau, da kamala da nagarta. Amma… shin zaka iya tuno gida? kana tuna inda kake fitowa?”
Sagir, wanda har yanzu idonsa cike da hawaye ne, ya ƙarasa cikin rawar murya:
“Yallabai, motarmu ce ta buge shi shekaru da suka wuce a hanyar gaba da ƙauyen Rimi dake Kano mun ta nema — mun nemi danginsa har muka gaji. Likita ya ce brain dinsa ya samu rauni, jinin kansa yana ƙanƙancewa. Ya ce idan Allah ya yarda, lokaci zai gyara komai...”
ya juya yana kallon Bashir da murmushi mai cike da tausayawa:
“Yau lokaci ya yi, Bashir. Ka dawo da kanka da labarinka.”
cikin ɗakin aka ɗauki shiru — shiru mai daɗi, shiru mai cike da hawaye da godiya.
Mommy ta rusuna ta rungume ɗan nata, tana kuka da murmushi lokaci guda.
“Alhamdulillah… ka dawo Bashir… ka dawo daga duhu.”
Nan ya ɗago da jajayen idanu, muryarsa na rawa kamar mai jin sanyi cikin zafi ya ce:
“Tabbas zan gane hanyar daji, zan gane ƙauyenmu.”ya yi shiru na ɗan lokaci, yana kallonsu cikin mamaki da zafin zuciya, sannan ya ci gaba, muryarsa cike da raɗaɗi:
“Amma me yasa kuka riga ni da amana tsakaninku da Allah? me yasa kuka kai ni wannan matakin? Su waye ku a zahiri? Ku mutane ne ko kuwa wata jarabawace da aka aiko min da ita?”
Sai ya dafe kansa da hannayensa biyu, yana girgiza kai a hankali, hawaye na zuba kamar ruwan sama da bai da niyyar tsayawa.
Mommy ta zuba masa ido cikin tausayawa, Khady kuma ta matso da sannu tana ƙoƙarin riƙe hannunsa, amma ya ja hannunsa a hankali, yana cewa“Kada ki taɓa ni yanzu... ban gama fahimtar komai ba.” wannan yanayi ya ɗauki hankali gaba ɗaya, har iska ta ɗauki sassan ɗakin cikin shiru mai cike da nauyi.
Sagir ya matso da nutsuwa a fuskarsa, yana dubansa da idon da ke cike da tausayi, ya ce cikin murya mai laushi:
“Ka kwantar da hankalinka, dan’uwa… babu abin da ya faru da kai da ba Allah ya ƙaddara ba.”Muhsin ma ya gyara zama kusa da shi, yana ɗan lumshe ido kafin ya ce cikin natsuwa:
“Lokacin da muke tafiya da gudu muna shirin shigowa garin Kaduna, a lokacin ne muka buge ka da mota. Mun firgita sosai, hankalinmu ya tashi… muka yi ƙoƙarin taimaka maka. Mun kai ka asibiti, muka bayar da jininmu, da dukiyar mu, har sai da ka warke.”
Ya ɗan yi shiru, sannan ya ci gaba da bayani:
“Mommy da kake gani ita ce mahaifiyarmu, Khady kuma ƙanwarmu ce. Daddy ne ya ɗauke ka tamkar ɗansa, suka ba ka kulawa fiye da yadda kai kanka ka taɓa tsammani. Aka saka ka makaranta, aka koya maka karatu mai zurfi, har ka kai matakin degree na biyu a fannin Political Science.”
Sagir ya ɗan murmusa cikin yanayi na alfahari, sannan ya ce:
“Yanzu kai mutum ne mai burin zama shugaba — Shugaban ƙasa! Wannan shi ne burinka, wannan shi ne abin da kake so ka cimma shin yanzu ka gane waye kai?”
Shiru ya rufe ɗakin, sai numfashinsa da ke fita a hankali ya durƙusa da hawaye a idanu, zuciyarsa cike da godiya da mamaki.
“Na tuna komai…” ya furta a hankali, yana duban Mommy da Daddy da sauran ’yan gidan.“Na gode da kuka bani rayuwa ta biyu.”
sai Daddy ya ɗan yi murmushi cikin natsuwa, yana cewa “Haba Bashir, yanzu ba lokacin kuka bane mu shirya, zamu tafi Kano.”
duk suka amince, fuskokinsu na cike da kwanciyar hankali da sabon fata.
Safe journey Bashir
###################
Ana haka, uncle ɗinsa, wato ƙanin baban sa, ya iso cikin ɗakin horo cikin hanzari, idonsa cike da damuwa da fargaba. Sai Umme ta tsaya a gefensa, ta bayyana masa halin da ake ciki: yadda Rayyan ke cikin ɗakin horo ana azabtar da shi, kuma yadda jinin sa ke zuba saboda sun yi tsammanin zai ɗauki kuɗi mai yawa.
Da wannan bayanin, uncle ɗin ya miƙa hannu, ya ce da ƙarfi:
“Haba, Daddyn Rayyan, kana kallo ne? Ana azabtar da ɗan ka saboda jini da kudi? Ashe menene a zuciyar su? Shin basa ganin cewa babu yadda zai iya ɗauke kuɗin nan? Kowa ya san Abdul ne kadai zai iya kwashe ma kuɗi. Wannan ya ishe!”
Da wannan, ya ɗauki matakin da zai ceci ɗansa. Ya yi saurin buɗe ƙofa, ya shiga ɗakin da zafi da duhun horon ya cika, ya ɗaga Rayyan cikin kulawa, yana yi masa kwantar da hankali:
“Rayyan ɗana, yanzu ka tsaya. Zan kai ka Dubai zaka samu tsaro, za ka zauna lafiya, kuma za ka cigaba da karatunka a can. Anan ba za ka ƙara jin tsoro ba, ba za ka ƙara wahala ba ,tun bayan mutuwar ka mahaifiyar ka nake so na ɗauke amman Daddyn ka ya hana , kasani yau babo wanda ya isa ya rabani da ɗaukar ka ”
Rayyan, cikin shiru da mamaki, ya ji zuciyarsa ta ɗan sassauta. Duk da tsoron da ya sha, ganin uncle ɗinsa da kulawa, da cewa zai samu tsaro da ilimi a Dubai, ya sa ya fara murmushi a hankali, yana jin cewa Allah ya shirya masa hanyar kuɓuta da rayuwa mai kyau.
Bayan uncle ɗinsa ya ɗauke shi, Rayyan ya shiga mota cikin sauƙi, duk da cewa zuciyarsa cike da haɗuwa da tsoro da fargaba. Safiyar nan, motar ta fice daga gidan horon, kuma ya ga duhu da zafi suna rabuwa da nesa da su, kamar duhu da azaba sun tsaya a baya, suna kallon yadda yake barin su.
A hanya, uncle ɗin ya rike hannunsa, yana masa kwantar da hankali:
“Rayyan ɗana, komai da suka yi maka an bar shi a baya. Yanzu za ka fara sabon rayuwa. Za ka samu tsaro, karatu, da damar da ba ka taɓa tunanin samu ba.”
Jirgin sama ya ɗauki su daga filin saukar jirgi na Kano zuwa Dubai. Rayyan yana kallon birnin daga sama, hasken dare da taurari sun yi kamar suna yi masa maraba. Duk fargabar da ya sha a baya ta fara raguwa, zuciyarsa ta ɗan sassauta.
Da suka sauka, aka karɓe su a tashar jirgin da motoci masu tsaro suka zo, suna ɗaukar su zuwa wani hotel mai tsada. A can, Rayyan ya fara fahimtar cewa duniya tana iya canzawa daga mugunta zuwa tsaro, kuma akwai damar da Allah ya tanadar masa cikin gidan su ɗin, ya zauna yana kallon birnin da tsawo, zuciyarsa cike da sabuwar fata:
“Zan yi karatu mai kyau zan zama mutum mai nagarta kuma ba zan taɓa bari mugun zuciya ta dinga rike ni ba.”
A nan ne ya fara sabon babin rayuwa, cike da karatu, tsaro, da damar da zai iya amfani da shi wajen gyara rayuwar kansa da ta waɗanda yake ƙauna. Kuma kowanne dare, kafin ya kwanta, yana tuna duk darasin da ya koya daga wahalarsa a gida — da ƙoƙarin fita daga mugun hali zuwa sabuwar fata.
Rayyan ya iso gidan uncle ɗinsa, wanda shi ne ƙanin mahaifinsa, mutum mai arziki sosai a birnin Dubai. Gidan cike yake da kyakkyawan kayan ado, fitilun zinariya, da kayan alatu — komai na nuna tsari da daraja. A gefen gidan, Raizah, yarinya ɗaya tilo, tana wasa cikin lambu mai tsabta da ciyayi kore-kore, tana dariya mai kayatarwa.
Uncle ɗin ya rungume Rayyan yana cewa “Yaron nan, yanzu rayuwarka zata canza. Ka gama wahala, yanzu lokaci ne ka ji daɗin abin da Allah Ya tanada maka.”
an shirya masa ɗaki mai kyau, gado mai launin zinariya da auduga mai laushi, duk abin jin daɗi yana nan. Rayyan ya ɗan yi mamaki, zuciyarsa cike