da farin ciki da rashin tabbas: ko da yake yana cikin gidan mai kuɗi, har yanzu akwai raɗaɗin baya da azabar da ya sha. Amma ganin Raizah na wasa a lambu, da murmushin uncle ɗinsa, sai zuciyarsa ta fara sassautawa.
A kowane dare, Rayyan zai zauna a dakin karatu mai fadi, yana ganin birnin Dubai daga taga. A can ne zai fara tsara yadda zai ci gaba da karatu da horo, kuma zai koyi darussa masu mahimmanci daga uncle ɗinsa:
yadda ake tafiyar da kasuwanci,yadda ake amfani da albarkatun kuɗi don taimaka wa mutane, yadda ake tsayawa da ƙarfi a rayuwa ba tare da barin azaba ta rushe zuciya ba
To be continued.....
Kasan matsayin ka a siyasa yanzu kana neman takarar zama Senator a Majalisar dokoki ta Kaduna State House of Assembly, kai ne kuma Speaker, kana ci gaba da karatu domin cika burinka na zama Gwamnan Kaduna State nan gaba kadan.
A yau, jirgin su Bashir, Daddy, Mommy, Sagir, Muhsin da Khady ya tashi daga Kaduna International Airport da ƙarfe takwas na safe, cikin lokaci kaɗan jirgin ya ɗaga sama cikin sanyi da natsuwa bayan awa ɗaya daidai, sun sauka lafiya a Mallam Aminu Kano International Airport.
Bashir tun a cikin jirgi ya kasa samun nutsuwa — zuciyarsa tana ta bugawa da sauri kamar ana buga gangar alhini da suka sauka, duk da Mommy tana ta masa nasiha da Sagir na ƙoƙarin kwantar masa da hankali, ya kasa zama a mota ko jiran lokaci.
Tuni aka shigo da motoci masu tsaro zuwa filin jirgin, ‘yan sanda da jami’an gwamnati suna nan suna jiran su, saboda tuni aka sanar da su manufar tafiyar. Ba tare da ɓata lokaci ba suka nufi hanyar ƙauyen Rimi, inda komai zai bayyana.
Motoci suka rinka shigowa cikin ƙauyen Rimi a hankali, ƙura na tashi a sama tamkar hadari mai shirin sauka mutane suka fara fitowa daga gidajensu, kowa cikin mamaki da tambaya a fuskarsa.
“Lallai yau akwai wani abu!” cewar wani dattijo yana jingina da sandarsa, yana kallon jerin motocin gwamnati da ke shigowa cikin ƙauyen da ƙarar siren ɗin su ke cika iska. ƴan sanda suna gaba, suna gyara hanya cikin girmamawa, yayin da motar gwamnati ke bi a baya a cikin motar kuwa, Bashir ya zauna a gefe cikin nutsuwa da wani irin yanayi mai cike da tunani kallon da yake yiwa kowace kusurwa na ƙauyen tamkar yana neman wani ɓangare na rayuwarsa da ta ɓace shekaru da suka shuɗe.
A gefensa, Mommy ta dafa hannunsa a hankali, tana ƙoƙarin kwantar masa da hankali “ka kwantar da zuciyarka, Bashir komai da ka rasa a baya, Allah zai mayar maka da shi cikin alheri.”ya jinjina kai kawai, ya kasa magana. Idanunsa sun cika da hawaye da bai so su zubo ba da suka shiga tsakiyar ƙauyen, yara suka fara bin motocin suna ta dariya da ihu. matasa suna tsaye suna ɗaukar hotuna, wasu kuma suna ta kallon wannan shigar da ba a taɓa gani ba a cikin ƙauyen.
Daga nesa, wani tsoho mai farin gemu ya fito daga ɗan ƙaramin gida yana rarrafe da sanda. Kallon motar farko yayi sosai kafin ya furta cikin murya mai rawar sanyi:
“Subhanallah... wannan kam irin wannan rana bata taɓa zo ƙauyen Rimi ba.” a wannan lokacin, Daddy ya ba da umarni, motoci suka tsaya. Ƴan sanda suka zagaye wajen, sannan aka buɗe ƙofar motar da Bashir yake ciki.
yana sauka, iska mai sanyi ta buga masa a fuska, zuciyarsa ta fara bugu da ƙarfi. Kallon ƙauyen yayi da idanu masu ɗauke da hawaye ganuwar ƙasa, bishiyoyi, da ƙofar tsohon gida da ya fara gane ta a hankali.
Mommy ta fita a hankali tana kallon yadda kowa ke rufe baki cikin mamaki. Sai dai Bashir ya tsaya cak, idonsa ya tsaya a kan wani dattijo da yake kusa da wani tsohon gida —
murya ce ta fito daga bakinsa cikin rawar murya:" Babaa"
Dukkan su suka kalli inda yake kallo. Dattijon ya tsaya shiru, yana ƙoƙarin gane muryar. Sai da ya kalli Bashir sosai kafin ya furta da hawaye suna gangarowa “Kai… kai ne Bashir ɗana?!” a hankali suka nufi juna, duniya ta yi musu kamar ta tsaya cak
“Baba… kai ne?”
Dattijon ya ɗago a hankali, idonsa ya tsaya kan Bashir — kyakkyawan saurayi cikin kaya masu tsada, takalminsa ƙirar Louis Vuitton, ƙamshin turarensa yana ratsawa har cikin hancinsa sai Bashir ya matsa dafff, ya durƙusa a gabansa, ya dafa kafaɗarsa cikin rawar hannu da hawaye “Baba… kaine ka dawo haka? me ya sameka? me yasa rayuwa ta juyar da kai haka?”
Kamar a mafarki, Mallam Audu ya tsaya kallonsa da ido mai girgiza, kamar yana son musanta abin da ke gabansa. Sai dai lokacin da ya ji muryar Bashir — muryar da take kama da ta yaron da ya kore daga gida shekaru da suka shuɗe, muryar da ta yi masa barazana da zafin tarihi — sai numfashinsa ya tsaya.
Sandar da yake riƙe da ita ta sulale daga hannunsa ta faɗi ƙasa da ƙarar wargasss!
Idonsa ya faɗa da tsoro da girgiza, jikinsa yana rawa sai ya ja baya da ƙyar yana ƙoƙarin fitar da kalma “Wannan... wannan muryar… ba zai yiwu ba…”Hawaye suka gangaro daga idon Bashir, yana dubansa cikin tausayi da ƙauna:
“Baba... ni ne… Bashir ɗanka ne… wanda ka kori da hannunka...”
Kamar wanda aka jefa cikin wutar zafi, Mallam Audu ya dafe kirji yana kakkarwa. Wani irin zafi ne ya mamaye zuciyarsa — zafin nadama, zafin tarihin da ya shafe shekaru yana ƙoƙarin mantawa da shi.
Sai kawai ya furta da murya mai rawa, kafin idonsa su cika da hawayen da ba su da ƙarewa “Yaron da… na kora kamar kare Allahu Akbar!”
Sai ya zube ƙasa, sandar sa ta narke a gefe, ƙauyen ya ɗauki ihu.
Mommy ta ruga da gudu ta riƙe Bashir, Khady ta kame bakinta da kuka, yayin da Daddy ya tsaya a gefe yana kallon abin da ya faru kamar a fim Bashir ya durƙusa da kuka, yana dafa tsohon da ya faɗi “Baba, ka tashi..."
Sai dai Mallam Audu ya riga ya sulale cikin rashin kuzari, idonsa a buɗe, yana kallon sama kamar yana neman gafarar da bai samu ba shekaru da suka shuɗe…
""""""$$$$$$$$$$$$$$$$$$$$$$$"""""""
Rayyan ya shiga gidan uncle ɗinsa, zuciyarsa cike da mamaki da ɗan tsoro. Falo ya yi girma fiye da tunaninsa; labulen zinariya suna shafa ƙasa, fitilu masu haske kamar tauraruwa na sheƙaɗa kowane kusurwa. A gefe, Raizah, yarinya tilo mai shekaru goma sha ɗaya, tana wasa cikin lambu mai ciyayi kore-kore, murmushi a fuskarta yana kama da haske mai ɗaukar ido. Uncle ɗinsa ya rungume shi da hannu mai ƙarfi, ƙamshi na turare mai daɗi ya lullube dakin, yana cewa:
“Yaron nan, yanzu rayuwarka zata sauya. Ka gama wahala, yanzu lokaci ne ka fara jin daɗin abin da Allah Ya tanada maka.”
Rayyan ya ji wani ƙarfi na natsuwa ya lullube zuciyarsa, amma har yanzu fargaba da mamaki na cikin sa. Duk da alatu da kayan alatu, zuciyarsa tana tuna wahalar baya. Amma ganin Raizah, murmushi a fuskarta, da yadda take kallon sa da ƙauna, sai wani ɗan shauqi mai sanyi ya shiga zuciyarsa.
An shirya masa ɗaki mai fadi, gado mai laushi da auduga mai tsabta, taga tana kallon birnin Dubai mai haske da dare. Kowane dare zai zauna a dakin karatu, yana tunanin yadda zai fara karatu cikin ƙwarewa da natsuwa, da yadda zai zama mutum mai ƙarfi da hikima a rayuwa.
Raizah ta zama wani ɓangare na sabuwar rayuwarsa. Kallo daya kawai daga gare ta, sai zuciyarsa ta tsinke da wani irin jin daɗi, kamar ya dawo gida bayan dogon lokaci. Amma duk da sabuwar rayuwa, Rayyan bai manta da azabar baya ba — waɗanda yanzu za su zama ƙarfi da himma a sabon fara rayuwarsa.
A hankali, murmushi ya bayyana a fuskarsa, ya faɗi:
“Wannan shi ne farkon rayuwata. Zuciyata zata shigo cikin sabuwar duniya, kuma babu wanda zai iya tsayar da ni.”
Rayyan ya juya kallon Raizah, zuciyarsa tana bugawa da sauri. Kyakkyawar fuskar ta, idanuwanta masu sheƙaƙe, da murmushinta mai laushi sun lullube zuciyarsa cikin wani irin shaukin da bai taɓa ji ba.
Raizah kuwa, tana kallon shi da ƙauna da fahimtar juna, ta ji wani ɗanɗano na soyayya mai laushi a zuciyarta, kamar ranar farko da duniya ta bayyana mata da haske. A hankali ta matso kusa da shi, hannayenta sun haɗu da na Rayyan, kuma kallo ya zama kamar harafin zuciya da ke bayyana komai da ba a faɗa ba.
Rayyan ya ɗan ja numfashi, ya ji dumin Raizah yana shiga zuciyarsa. A hankali ya ƙara matsawa, har idanun su suka haɗu, sai zuciyoyinsu suka yi magana fiye da dukkan kalmomi. A wannan lokaci, duk abin da ya faru a baya — wahala, azaba, rashin tsaro — ya zama kamar gajeren mafarki ne kawai, saboda yanzu akwai wannan haske na soyayya da ke ɗaukar su gaba.
Raizah ta ɗan murmusa, ta faɗi cikin muryar sanyi mai shauki “Rayyan… yanzu babu wani abu da zai iya raba mu.”
Rayyan kuwa ya rungume ta da ƙarfi, yana jin zafin zuciyarsa da farin ciki a lokaci guda. Wannan shine farkon labarin soyayya da shauki tsakanin su, inda duk wata tsoro ta baya ta narke a cikin wannan sabon haske ..
“Kasan fa, Daddy, na jirar mu zamu tafi airport yanzu. Dole muyi wani wankan jarabar kananan,” Raizah ta ce da dariya, idanuwanta cike da walwala da shauki Rayyan kuwa ya murmusa, ya janyo ta a hankali zuwa jikinsa, yana jin zafi mai laushi a zuciyarsa “To, menene, baby? Kinsan fa idan kina tare dani, mantawa nake da kaina,” ya ƙara cewa yana kunce mata tawol cikin shauki...
A wannan lokaci wayarsa ta dakkar tar, sai ya ɗaga hannunsa yana murmushi.
“Hello… ehh, Uncle,” ya ce cikin sautin nutsuwa, sannan ya gyara muryarsa:
“By 11 jirgin mu zai tashi, 10:30 me kukiye baku zo airport ba?”
?????????????????
Zuwa ina
to be continued.
An shigo da Mallam Audu cikin gidan a hankali; an ja shi har zuwa zauren inda Baaba ke zaune. Ta jingine bakinta, yawu na zubo da wari mai ƙarfi; a ƙirjinta sai ƙudaje suke bayyana kamar sun fara samun nama — alamar cewa ciwon ya dade kuma ya tsananta.
Ta zauna tana sauraro, idonta a buɗe amma babu yadda za ta iya magana; hawaye na zuba a gefen idanunta kamar ruwan sama. Bashir ya tsaya a gabanta, zuciyarsa cike da nauyi, ba shi da magana; Mommy da Khady suka tsaya a baya, sun dan natsu, sun yi nesa da ita domin gudun ɗaukar cuta gidan ya yi sanyi, shiru na nauyi yana zaune a ko’ina, kowa na kallon Baaba cikin tausayi, yayin da ta ci gaba da sauraron maganganun da ke zagaye da ita, hawaye na zubowa a ƙusuranta.
Chan Mallam Audu dake kallon Mommy, ko ƙiftawar ido bai yi ba.
Babo yace da murya mai sanyi amma cike da iko:“Duk ku zauna… Bashir, tabbas kaine ƙadagaren bakin tulu!”
Wannan kalma ta kada zuciyar kowa dake wurin. Shi ne abinda koyaushe Mallam Sambo ke faɗa — amma yau ne aka tabbatar da ita a fili. Ashe wannan rana ce da za ta tona sirrin shekaru masu tsawo.
Wani shiru mai nauyi ya biyo bayan kalmar.
Sai wata kyakkyawar yarinya ta matso daga bayan jama’a — ƴar shekara goma, idanunta kamar taurari amma cike da tsoro da mamaki.
“Zo nan, ke zauna anan NOOR ,”
in ji Mallam Audu yana nuna mata kujera kusa da shi Ya juyo yana kallon Mommy da Bashir, sannan ya ɗan gyara zama.
“Yau zan faɗi labarin da nasan cewa hakkin wannan labarin shi ne dalilin da yasa har yau ban mutu ba…
Ina ganin rayuwa kalla-kalla, saboda wannan sirri da ke cikin zuciyata.”
Mallam Audu ya dafe ƙirjinsa, zuciyarsa na bugawa da ƙarfin da ya wuce na mutum mai rai. Idanunsa sun cika da hawaye, muryarsa ta yi sanyi amma tana ɓoyar da zafin da shekaru suka tara a ciki ya ɗan kalli Bashir, sannan ya sauke numfashi mai nauyi.
“Bashir… ka saurare ni da kyau, saboda abinda zan faɗa maka yau shi ne abin da nake jira shekaru da dama in faɗa kafin in mutu.
Mamanka, sunanta Ummu Kulsum — mace ce da Allah Ya halitta da ƙima da haƙuri Lokacin da ta zo ƙauyen nan, mutane suka ce ‘yar gudun hijira ce, suka ce ta fito daga arewacin kasar nan saboda yaƙi amma gaskiyar magana ita ce — ta zo ne da wani tsohon makaho, wanda ya ɗauke ta tamkar ‘ya. Mutane suka raina su, suka ɗauka ba su da galihu.
Ni kuma… ni ne bala’in rayuwarta.”
Ya lumshe ido, hawayen da ya dade yana riƙewa suka sauko kamar ruwan sama.
“Na aure ta saboda son zuciya, saboda kishi da ƙeta amma ban aure ta saboda Allah bana zama azzalumi. Na hana ta dariya, na hana ta kwanciyar hankali.
Duk sautin muryarta yana tuna min da hasken da ban taba samu ba.
Na mata duka a bakin murhu, na wulaƙanta ta har ta gaji da numfashi.
Wata rana cikin fushin da ya makantar da zuciyata, na zuba mata ruwan talken towo mai zafi a lokacin ruwan sama.
Ta faɗi, ta mutu a gabana.”
Ya durƙusa yana kuka kamar ƙaramin yaro.
jin irin rawar muryarsa yasa kowa a wajen ya kasa motsi “Tun daga wannan rana, zuciyata ta zama kamar wuta. Amma kafin ta mutu, ta bar kadangare a gidan nan — shi ne kai, Bashir.
Duk da ban san ka ba, ban san lokacin da aka ɗauke ka ba, amma kullum ina jin zuciyata tana tsanar ka, tana tsoran ka, tana son ka lokaci ɗaya ashe wannan yana nufin kai ɗan mamanka ne, kai ne amanar da na watsar.”
Ya share hawayensa da hannun da ke rawa, yana kallon Bashir da idon nadama.
“Rashin addini ya rufe ni, giya ta zama abokiyata, mata suka zama abincina, har na manta da mutuncin rayuwa.
Amma yau na fahimci cewa Allah bai manta da ni ba, saboda har yanzu ina numfashi don in furta wannan gaskiya.”
Sai ya ɗaga kansa sama, yana girgiza kai kamar mai kuka cikin addu’a.
“Ka yafe min, Bashir.
Ka yafe min don mamanka.
Ka yafe min don Allah.
Ka yafe min domin wannan rai da ban cancanci in rayu ba.”
Shiru ya cika wajen, kamar iska ta tsaya.
Sai muryar sa ta katse natsuwar wajen cikin sanyin murya “Bayan mutuwar Malam Sambo, Noor ta ƙi aure kullum maganarta ɗaya ce — ‘zaka dawo kayi alƙawari…’Amma babu labari, babu wasiƙa.Har ƙauyukka ta bi tana nemanka, wancan lokacin.” Mallam ya share hawaye sa, ta ci gaba cikin murya mai motsa zuciya “Lokaci ya ja, ta girma .
Kawayenta sunyi aure, ta ƙi kula da kowa.
Sai wani yaro ya bayyana daga daji — yaro mai kallo kamar aljani, amma idanunsa suna cike da haske da hikima Sunan sa Suhayl.
Shi ne ya kawo mana haske da ilimin sa na Addini Haske da har yanzu ba mu gane ko daga ina yake ba.”
Mallam Audu ya rufe fuskarsa da tafukan hannayensa kukan da ke fitowa daga zuciyarsa bai da sauti, amma ya cika ɗakin da nauyin nadama.
Zuwan Suhayl ya zama tamkar sabon safiya ga ƙauyen un daga lokacin da ya shigo, murmushi ya fara komawa a fuskokin mutane, kuma Noor ta zama kamar sabuwar fure a cikin daji.
Idanunta suna haskawa da farin ciki, zuciyarta ta cika da nutsuwa kamar ta sami abin da take nema shekaru Lokaci bai jima ba, yayan ta ya aurar da ita ga Suhayl, cikin kalmar da ta ce:
“Bangaji da jiran wanda bazai dawo ba ,amman bazan manta da cewa inason Bashir da har abada ba ”
Amma, kaddara ta fi ƙarfin burin ɗan adam.
Noor ta rasu cikin imani, ta koma ga Mahalicci tana riƙe da sunan wanda ta kasa mantawa da shi — Bashir.
Har zuwa mintin ƙarshe na rayuwarta, kalmarta ɗaya ce:
“Zai dawo... zai dawo ne...”
Ta haifi ɗa mace guda ɗaya, mai kamannin ta da kyawunta, mai nutsuwa kamar mahaifiyar ka ta sakawa yarinyar sunan mamanka — Ummu Kulsum,amma kowa a ƙauyen yana kiranta da suna ɗaya kawai: Noor — domin kamar hasken mahaifiyarta take.
Mallam Audu ya ɗan numfasa, yana kallo cikin idon Bashir,muryarsa ta yi sanyi kamar ana furta sirrin da rai ke so ya ɓoye.
“Ga yarinyar nan a gabanka, ita ce amanar da Noor ta bar maka kuma ita ce ‘yar Noor.
Ka sani, tunda Noor ta haifi wannan yarinya, Suhayl ya bar ƙauyen nan..
Ya ce zai dawo, amma har yau bai sake komawa gun yarinyar sa ba,
shekaru na tafiya, lokaci yana shanye mutane, amma har yanzu ana jira.”Ya ɗago da idanu, yana kallon sama kamar yana magana da wata ƙaƙƙarfan zuciya da ta daɗe tana ƙuna.
“Wannan shi ne abinda nake so ka sani, Bashir Amma har yanzu akwai wasu abubuwa da na ajiye, ajiyar mahaifiyarka, da kuma ajiyar Noor tana da imani cewa wata rana,
kai ne zaka dawo gida ka karɓi amanar nan da hannunka.”
Ya yi shiru, ya kalli Noor ƙarama wacce ke tsaye a gefe, idonta yana cike da hawaye amma tana murmushi, kamar zuciyarta ta gane cewa labarin da aka ɗauki shekaru ana jira ya kai ƙarshe.
##$$$$$$$$$$$$$$$#####
A gurguje suka shiga wanka, ruwa mai ɗumi yana zuba musu jin daɗin jiki. Sun shirya cikin abaya irin ta alfarma, mai launin koren zinariya da ja mai haske, an yi ado da ƙyallen ƙasa mai tsada, turare mai ƙamshi na musamman wanda har kewayen gidan ya cika da shi. Hannuwansu da wuya an yi musu ado da ƙaramin zinariya da lu’u-lu’u, fuskar su kuma tana haskakawa da hasken soyayya da farin ciki.
Da sauri suka fito daga gidan, Raizah ta ɗauki kakar akwati guda ɗaya mai daraja, Rayyan kuma ya lumshe ido yana jin dumin zuciyarsa. Sun shiga mota, direban ya danna gaba, ba tare da bata lokaci ba suka tashi kai tsaye airport na Dubai.
A cikin mota, hasken safe ya cika su da kwarin gwiwa, zuciyoyin su cike da bege da shauki. Duk wani damuwa ya narke, yanzu rayuwa ta fara musu sabon babi mai cike da walwala da alfarma.
Daddy ya yi murmushi, ido cike da fahimta, ya ce “Daddy, mun makara ne… we are sorry.”
Rayyan da Raizah suka yi ƙanƙantar murmushi, suna jin sauƙin zuciya saboda Daddy ya fahimce su nan suka shiga jirgi, kowanne na ɗauke da raƙuman tunani da shauki, yayin da jirgin ke tashi daga Dubai zuwa Nigeria, Abuja.
A cikin jirgin, kowane fuska na cike da tsammani da bege, Raizah na kallon Rayyan da wani ɗan murmushi mai taɓa zuciya, yayin da Rayyan yake duba fuskar Raizah cikin shauki. Yanayi na cike da ɗan tsoro amma kuma natsuwa....
A hankali Mallam Audu ya miƙa sandar hannunsa ga Bashir, idanunsa suka kada da hawaye.Bashir kuwa yana kallo little Noor, wacce ta riƙe hannun Mommy tana shiru, kamar zuciyarta na fahimtar nauyin da ke faruwa Duk suka tsaya cikin natsuwa, ƙarar hucin iska kawai ake ji sai Mallam Audu ya zaro wata tsohuwar tsunma daga ƙarƙashin katifa.
Tsumar ta yi duhu saboda tsawon lokaci, amma ana buɗewa sai kamshin turaren da ya tsufa ya cika ɗakin “Wannan ajiyar mamanka ce,”ya ce da muryar da ke rawa.
“Wannan ganye da wannan leda... da takaddar Noor — ita ta ce in ba shi idan ya dawo... idan Kadangaren Bakin Tulu ya dawo gida.”
Bashir ya karɓa da hannunsa, zuciyarsa na tsinkewa kamar ana sare masa numfashi.
Ya buɗe tsumma ɗaya bayan ɗaya…
Sai zoben zinare ya bayyana — zoben da aka rubuta ƙarami a ciki “ Ummukulchum.”
sai kuma hoto guda biyu da aka haɗa cikin takarda mai launin rawaya saboda tsufa.
Ya ɗaga hoton farko...
Sai Mommy ta sake numfashi da ƙarfi, Daddy ya tsaya cak, Sagir da Muhsin suka kalli juna, idanunsu suka cika da tsoro.
“Innalillahi...” kawai aka ji ana furtawa a hankali.
Bashir yana kallon hoton — idonsa ya faɗa, jikin sa ya ɗauki rawa “Wannan... wannan kuwa...?”
Sai kawai ledar ta zame daga hannunsa ta faɗi ƙasa, hoton na biyu ya zame daga ciki...
sai iska ta kaɗa shi a hankali zuwa ƙasan ƙafarsa ya durƙusa yana ɗauka, idanunsa na rawa kamar mai jin kiran da ya ɓace shekaru aru-aru........
A take Mommy ta firgita, hannunta ya saki wayar da ke riƙe da ita, jiki ya yanke mata — ta fadi ƙasa “Mommy!!”
Khady ta kurma ihu tana rarrafe zuwa gare ta, Daddy ya durƙusa yana riƙe ta da rawar hannaye, Bashir kuwa ya tsaya tamkar an soke shi da wuka a ƙirji.
A zuba mata ruwa cikin tashin hankali, sai ta ɗan motsa, ta buɗe idanu cikin hawaye masu zafi.
A hankali ta miƙa hannu ta karɓi hoton daga hannun Bashir, ta dade tana kallonsa kamar wacce ke tafiya cikin wani lokaci daban.
Hawayenta suka zubo a hankali, suna sauka bisa fuskarta kamar ruwan sama mai ɗumi.
Idanunta suka yi haske kamar tauraruwa daga sama, zuciyarta ta kasa ɗaukar nauyin abin da take gani ta furta cikin murya mai sanyi, tana shafa hoton da yatsunta “Subhanallah... wannan hoton... wannan fuskar... ita ce... ita ce Ummu Kulsum.”
A take aka tsaya shiru — iska kawai ake ji tana kaɗawa ta taga.
FLASHBACK 🌙
Bakin dare ne — dare mai tsanani da duhu, kamar sararin samaniya ya ɗaure da damuwa.
Iskar sanyi na busowa a hankali tana rawar da labulen window ɗin da ke gefe.
A cikin ɗaki kuwa, ana iya jin ƙarar ƙaramar fitila mai launin zinariya tana ɗaukar ido da walƙiya mai sanyi.
Ɗakin kuwa cike yake da ƙamshi da tsafta. Katifar gadon farin zane ce, an shimfiɗa ta cikin tsari kamar ɗakin ‘ya mace mai kula da kai.
A kan gadon, yara biyu ne kwance — ba ƙananan yara ba, ɗaya ‘yar shekara ashirin (20) ce, ɗaya kuma tana da shekara goma sha biyar (15) Dukansu cikin kayan bacci ne masu launin ruwan hoda da fari, fuskar su cike da natsuwa da kwanciyar hankali.
‘Yar babba tana kwance da littafi a gefenta, alamar ta dade tana karantawa kafin bacci ya ɗauke ta Kanwarta kuwa ta rungume teddy bear tana baccin zuciya kamar wata ƙarama da bata san komai ba game da abin da ke shirin faruwa.
A hankali wata ta sauko ta haska gefen gadon, hasken nata yana bugawa kai tsaye kan fuskokin su — haske mai kama da annuri.
Wani abu mai nauyi a sararin dare, kamar iska ta ɗauke numfashi na wani abu da ke shirin ɓullo wa cikin rayuwarsuDaren da zai zama farkon wata sabuwar rayuwa.
Sautin bindiga ya fashe cikin dakin malam, ya girgiza duk gidan. Ummu Kulsum ta tashi cikin tsoro, ta kame hannun Maryam, amma kafin su yi wani abu, an ja su cikin sauri — sai dai yaran sun riga sun ɓuya a wajen babban parlour, a bayan wani ɗaki mai zurfi; suna tsare numfashi, idonsu na zurfi suna kalle abinda ke faruwa kamar an dake musu duniya.
Mutanen baki sun faɗo cikin gidan kamar hadari; sun shiga cikin sauri, suna nufi babban tebur. Sun rufe kofa da sauri, suka tilasta iyayen su zauna a wajen parlour, an murƙushe su a wani wuri domin kada su iya motsi — amma yaran suna tsaye ɓoye, suna ganin komai cikin firgigiya da azaba.
Shugaban waɗannan bakaken ya buɗe jakar fata ya zaro wasu takardu. Ya juya ya kalli mahaifin gidan da muryar ƙarfin zuciya:
“Ko ka kawo mana files ɗin? Ka sani — ko da ba mu samu ba, za mu iya ƙaddamar da hukuncin nan — mu kashe iyalanka a nan.”
Kalmar ta fadi kamar wuta a cikin dakin. Ummu Kulsum ta yi ƙoƙarin tsawata, amma an hana ta magana; hawaye sun toshe mata makogwaro. Maryam ta rufe bakin ta da hannunta, zuciyarta na buga kamar za ta fashe.
A ɓoye, Ummu Kulsum da Maryam suka matso kusa da juna, hannayensu na rike da tsananin tsoro. Sun ji dukkan kalmomin, sun ga fuskar mugunta a bakin waɗanda suka shigo — fuskar da ba za su taɓa manta ba.
A gefen duniya kuma sun yi maganganu game da Alhaji Abubakar Imam — shahararren ɗan kasuwa, tsohon gwamna sau biyu, an yi masa fashi da darar miliyoyi a sansanin gidansa a unguwa mai tsada. Amma a nan, abinda ke zamewa shi ne tambaya: menene a cikin waɗannan files? Kuma shin waɗannan masu fashi suna neman su ne, ko suna amfani