tana a bakin ƙasa, garin Kano — babban masarauta mai madogara, gadoji masu faɗi, da zauren sarauta mai kololuwa. A zahiri ana girmama mai gidan: jaka mai daraja, masarautar ta yi suna cikin kwarjini. A zahiri kuma, talakawa na fama da haraji mai nauyi, jami’ai masu karfi suna yi wa mutane zalunci, kuma an rufe bakin masu adawa.
IYALI: GIDAJEN MASARAUTAR SULAIMANU (Roster)
. Emir Sulaimanu, mai karfin mulki, sarauta ta gargajiya, yana da ƙarfin son mulki. A fili yana nuna girma, amma a bayan fage yana da tsananin kishin iko da kishi.
Yana dafawa neman karuwar iko ta kowanne hali; yana ƙyama ga duk wanda zai kawo ƙarƙashin sa.
. Hajiya Binta (Uwargidan Emir)
Kyakkyawa, mai tausayi,Rike da sirrin rayuwa:.
. Crown Prince Idris, Ƙara mai takobi — son karɓar mulki da sauri. Yana da kishiya ga duk wani sabon haihuwa da zai iya rage matsayinsa makirci: Zai yi komai don hana wani gado ya ci nasara.
Princess Amina, Tausayi, ilimi, abokiyar talakawa — ta fara jin rashin daidaito na masarauta.
Waziri Musa (Babban Waziri Mai kutse, mai riba daga haraji, yana gudanar da ayyukan asiri Shi ne babban dafa makirci a masarauta; yana sarrafa jami’an tsaro.
. Dogo Ibro (Kaptin na ‘Yan Tsaro,Jabɓa, mai bin umarni, tsanani: Aiki da Wazirin Musa; shi ke jagorantar hukunci.
Maid (Ungozoma) Mai kirki, sanin sirri; ita kadai ke da ilmin haihuwa na sarauta.
***********
BASHIR
Fara Tafiyar Bashir
Bashir ya tsaya bakin ƙauyen, iska tana kadawa a sannu kamar tana rera masa waƙar ban kwana. Ya runtse idonsa, zuciyarsa na bugawa da ƙarfi, zuciyar da ke cike da tambayoyi marasa amsa.
“Ina zan dosa?” ya tambayi kansa a hankali, murya na rawa kamar mai shirin fashewa da kuka. Amma babu wanda zai ba shi amsa, sai shiru da ƙarar tsuntsaye na sama.
Ya dube hanya ta gaba, babu alamar gari, babu alamar mutum, sai wani ƙasa mai fadi da dogayen bishiyoyi suna karkarwa kamar masu ɓoye wani sirri. Ya yi nufin komawa baya, amma zuciyarsa ta tuna masa da kalaman Mallam Sambo:
“Kai ka zama tamkar mai tafiya a sahara — ba komai ya kamata ya mayar da kai baya. Ka je, Allah yana tare da mai gaskiya.”
Wani irin zafi ya mamaye zuciyarsa, amma sai ya daura hannu a ƙirjinsa ya ce da kansa:
“Na amince da kaddara. Na amince da tafiya. Idan mutuwa ce, to a hanya zan riske ta, amma ba zan tsaya nan da tsoro ba.”
Ya ɗora ƙafafunsa a hanya. Ƙafar farko ta ji kamar tana sauka a kan duwatsu masu zafi, ƙafar biyu ta zama kamar tana nutsewa cikin rairayi. Amma ya dage. Kowane mataki da ya ɗauka yana jin kamar yana raba kansa da tsohon rayuwarsa.
Wani hadari ya fara kunno kai daga nesa, gajimare sun rufe rana, iska ta fara busa ƙarfi kamar tana gwada jarumtarsa. Sai ya ɗaga kai ya dubi sama cikin ƙarfi ya ce:
“Ya Allah, idan wannan hanya ce da za ta kai ni ga alkhairi, ka bani ƙarfin zuciya. Idan kuma bala’i ne, ka bani juriya.”
Sai ya cigaba da tafiya, cikin tsoro da ƙarfin hali a lokaci guda — zuciya ɗaya tana kuka, zuciya ɗaya tana addu’a.
Bayan wasu kwanaki Bashir ya ci gaba da tafiya a kan hanya, zuciyarsa cike da tunani da rashin tabbaci. Rana ta yi zafi, ƙasa ta yi dumi kamar za ta ƙone ƙafafunsa, amma bai tsaya ba — ya ci gaba da tafi.
Ba zato ba tsammani, a nesa sai ya hango wata mota mai sauri tana taho kamar iska. Kansa ya ɗauki hankali — amma mota ta ratsa masa a gefen hanya! Direban bai lura da shi ba; motar ta ja sanyi, ta yi ƙusoshi, ta juya sai ta buge shi da ƙarfi.
Fannin ƙasa ya yi ƙasa da ƙasa: ƙarfe ya buga ƙashin ƙafarsa, jikin sa ya jujjuya kamar kayan da aka murƙushe. Sai ƙara mai ƙarfi — ƙarar ƙarfen mota, ihu na mutane, murmushi na girgiza. Bashir ya faɗi kamar mattace; numfashinsa ya yi rauni, zuciyarsa na gudu kamar za ta ƙare.
Hannayensa suka yi laushi, ya ji zafin jini a fuska. Idonsa ya yi ja sai ƙaran hayaniya ya rufe duk abin da ke kusa. A ransa ya yi tunanin Noor, maganar Mallam Sambo, alkawarin da ya ɗauka — duk sun ratsa a ciki kamar ƙunci. Ya yi ƙoƙarin yin magana, amma murya ba ta fita.
Motar ta tsaya a tsakiyar hanya, sai ƙarar ƙafafun maza biyu suka yi kamar mai bacci ya tashi. Sun fito daga gefe — matakan su masu hanzari, sun tsaya kusa da Bashir. Fuskar su kyakkyawa ce, kamar samari na birni, amma idanunsu sun nuna mamaki da tashin hankali.
Daya daga cikinsu ya tsaya a ƙafa, ya kalli Bashir da dare-daren rai. Jinin ya yi ta zubo daga jikinsa, ya manne kafafunsa da ƙasa. Bashir kuwa — ba ya iya motsawa, idonsa na kallon sararin sama kamar wanda baya ganewa. Gaba ɗaya jikinsa ya yi sanyi kamar an kurɓaɗe masa ruwan rai.
Sauran saurayi ya yi sauri ya cire riga, ya matse ƙirjinsa da lumshe ido — a hankali ya binciki bugun zuciyarsa, yana jin numfashi. Amma har yanzu Bashir ya kasa tashi, bakinsa na ƙoƙarin magana, sai sunansa ya fita ne kawai:
“Noor… Mallam Sambo…”
Wani daga cikin matafiya ya danna mahaɗin wayar sa, yana ƙoƙarin kira wani mai motar daka, amma a wannan hanya babu wayar hannu mai karɓa sai a duk wani latse ne. Saurayin da ke duba Bashir ya mike ya kalli saman motar, sai ya juya ya ce da sautin damuwa:
“Ka dawo nan! Mu ɗauke shi mu kai shi asibitin gari — ko kuma mu samu abin ɗaukar sa!”
A lokacin, fuskar daya daga cikin maza biyu ta sauya — a cikinta akwai ƙarfin halin kai da tausayi. Ya timid da cewa ba za su iya barsa a nan ba. Ya kawo hannunsa ya rufe idon Bashir da sauri, yana duba idonsa, sannan ya rufe hancinsa domin ya ji numfashin sa. Sai ya juye ya kalli abokin sa yana cewa:bl
“Yaro ne daga wani ƙauye? Ko ɗan wani malami? Mu ɗauke shi cikin mota. Ni zan zauna a gaba in duba hanyar.”
Sun ɗaga Bashir cikin ƙoƙari, jini na zuba a kafadarsu, sai ragargazawa ta yi mana. Bashir ya ji ruwan ƙafa yana zame masa, sai zuciyarsa ta yi wasu ƙananan bugun da suka soma dawo masa hankali. Ya ji kamar wani yana rike hannunsa — sautin ƙwallon zuciyarsa ya koma kadan; amma bai iya tsayawa ba tukuna.
Ɗaya daga cikin matasan ya lanƙwasa kansa ya yi addu’a cikin ransa; ya jefa Bashir a motar da saurin gaske. Motar ta tashi, ƙaurace-ƙaurace ta bar ƙasa tana fasa ƙura. cikin mota, Bashir ya fara motsawa kankane, idonsa na buɗewa a hankali — yana ganin fuskar wanda ya aje hannunsa kusa da nasa, idon sa cike da tausayawa, yana jin muryar mai kuka cikin rassan magana:
“Ka tsaya! Ka kwanta! Ka yi haƙuri! Mu ke tare da kai, ba za mu bar ka ba…”
Amma zuciyar sa ta na sake raguwa; duniya ta fara ninkuwa. Kuma a lokacin da motar ta yi hanzari ta shiga cikin karkara, Bashir ya sake faɗin sunansa da ƙarfi:
“Noor… Mallam Sambo… kada ku bar ni…”
Sannan duhu ya rufe idonsa numfashi sa ya tsaya chakk idon sa suka kafe a sama.....
Abubuwan tambaya
Shin suwaye suka kaɗe Bashir da mota ?
ina suka dosa ?
Shin zai rayu ko zai fita cikin wannan lamari na labarin mu ?
Waye SUHAYL?
ina kaina tambaya nan idan na zauna shin waye shi?
ya zai kuɓuta daga wannan dajin ?
shin ma zai rayu yakai ga matakin ko nasara ?
Gidan sarauta ya shigo cikin lamarin mu ya zata kaya?
ina labarin Rayyan da Abdul ?
Chakwakiya iya chakwakiya salo iya salo, tafiya ta fara tafiya wanan amsasoshin suna nan a tare da wanan littafin in Sha Allah
mujeee zuwa.
to be continued
🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎
BY
NARNAH ƘANWAR SOJA
Follow my Wattsp group 👇👇👇
https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t
GARGAƊI
Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba ,
********
بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️
PAGE 16/17
08101235739
KANO
Daren Kano ya yi nisa, fitilun masarautar suna kyalli tamkar taurari, amma a cikin ɗaki mai ɗauke da ƙanshin turaren wuta, Hajiya Binta ta naɗe jikinta da farin lulluɓi tana barci. Sai dai barcin ya koma azaba.
A mafarkin da take ciki, ta ga yaro mai shekara kusan goma sha biyar hannunsa rike da makami mai zafi, yana ta ƙoƙarin shanƙo ta da shi. Idonsa jajir kamar wuta, muryarsa ta daki kunnenta “Zan dawo! zuciyar ki za ta tsage da azabar gaskiya!”
tayi ƙoƙarin gudu cikin mafarki, amma ƙafafunta sun makale a cikin ƙasa mai jini. Gidan sarauta ya koma wuta, kuma daga saman wutar ta hango fuskar mace da aka taɓa sani…
Hajiya Hafsah.
Wacce ta kasance tsohuwar kishiyarta, wadda aka zarge ta da ɗauke ciki namiji shekaru da suka shuɗe, amma aka kashe ta da makirci don kar ta haifi ɗan gado. Fuskar Hafsah ta bayyana cikin hayaki tana dariya mai ban tsoro, ta na kallon Binta da ido biyu masu cin rai “Binta! kin yi zalunci! Kin ɗauke rayuwata, amma ba zaki iya hana zuriyata dawowa ba. Jinin jaririn da aka kashe zai dawo ne da ƙarfin sarauta!”
Cikin tsananin tsoro, Hajiya Binta ta yi ihu — sai ta farke da gumi ya jika lulluɓinta. Numfashinta ya yi nauyi kamar wanda aka tsere da shi. Ta ɗaga kanta sama tana hawaye, zuciyarta cike da rawar jiki anan take, ta hango cikin ɗakinta Hajiya Maryam, wacce ta shigo da sauri da riga mai duhu. Fuskar Maryam ta sha bamban: daɗin rai da makirci suka gauraye, idanunta sun yi ƙyalli.
“Lafiya, Hajiya? Kin yi ihu kamar wacce aka kunna da wuta.”
Hajiya Binta ta farka daga mummunar mafarki da ta ƙona mata zuciya. Numfashinta na fita da sauri, zufa na zuba kamar an tsoma ta cikin ruwan zafi, ta kasa ɓoye firgicinta “na ga Hafsah…! na ga jinin da muka ɓoye yana dawowa! wataƙila cikin nan nata zai kawo abin da zai ruɗe mu…”
Maryam ta yi dariya mai taurin zuciya, ta matsa kusa da ita tana shafo fuskarta da yatsa: “Ke dai ki daina damuwa mun riga mun mallaki sarauta. Duk wanda ya tsaya mana a gaba, sai mu sarrafa shi da dabararmu.”
Hajiya Binta ta girgiza kai, hawaye na sauka:
“Amma mafarkin nan ba alheri ba ne, Maryam Ina jin kamar masarautar nan za ta shiga bala’i.”
Maryam ta kaɗa hannu da izza, ta miƙe tsaye:
“Bala’i kuwa sai dai idan mu ne muka ƙirƙira shi, kuma mu ke tafiyar da shi. Ki kwanta ki huta, Binta. Rana ta gabbas ke fitowa ba kuɗi ba kuma yauwa ce ta gari ba ta bari kishiya ta ɗauki matsayi.”
Ta fice daga ɗakin da ƙafar ta ta buga ƙasa tamkar aljana. Hajiya Binta ta ci gaba da kuka cikin zuciyarta, tana rike cikinta da hannaye biyu awaje kuwa, iska ta taso daga gefen masarauta, tsuntsaye suka tashi sama suna yi kamar ƙararrawa. Wani fari na wata ya kakkarya cikin duhu, ya haska bangon fada.
Sai wata murya daga zuciyar dare ta faɗo cikin kunnenta:
“Wanda aka kashe ba ya mutu… Jinin gaskiya zai taso daga ƙasa kamar Kaɗangare.”
*******************
Gidan Sarautar Zazzau Alqamar 🌙👑
Masarautar da aka kafa tun ƙarni na da, tana alfahari da tambarinta na “Zanen Wutar Alqamar” – wato wata cike da walƙiya da wuta a jikinsa, wanda ke nuna cewa hasken su ba ya gushewa ko da aka rufe rana. Wannan tambari ana ƙulla shi a kirjin duk wani ɗan sarauta, musamman maza da ake kallo a matsayin garkuwa.
A wannan masarauta aka haifi Prince Idris, wanda aka fi kira Idrisul Kawthar, mai ɗimbin kwarjini a idon jama’a. Shi kaɗai ne ɗa namiji da ya rage a gidan sarautar bayan shekaru na asara da makircin mata da kishiyoyi. A idanun duniya, shi ne madubin masarauta.
Wannan tunanin ya fi mata duka wani bala’i. Cikin firgici ta kira mai gadin ɗaki:
"Ku kira min Idris! Prince Idris yanzu-yanzu ya zo wurina!" cewar Hajiya Binta .
Shigowar Prince Idris
Sai ga shi ya shigo da ƙamshi da ƙarsashi. Dogo, kyakkyawa, farin kaya ya lullube shi, tambarin Wutar Alqamar na kyalli a ƙirjinsa.
Ya kalli mahaifiyarsa cikin damuwa:
"Ummah, me ya same ki haka? kin kira ni cikin tashin hankali…"
Hajiya Binta ta yi shiru tana huci, daga bisani ta ce da rawar murya:
"Idris, al’amura sun fara dawowa garemu. Na hango Hafsah, wacce muka binne tare da asirinmu. Tana dawowa cikin mafarkina, tana riƙe da ɗa namiji! Wannan alama ce cewa zaluncin baya zai dawo ya tarwatsa masarautar mu… Idris! Kai kaɗai ne hasken da ya rage a wannan gida. Kada ka bari wuta ta cinye mu."
✦
Idris ya yi dariya mai ƙanƙanar sanyi, fuskar sa ta kwantar da murya kamar wanda yă san ransa babu matuƙar damuwa. Ya ɗaga hannu ya gyara rawanin ajalin da ke ƙirjinsa — tambarin Wutar Alqamar ya walƙace ƙasa da rana.
“Mom,” ya ce cikin sassanyar muryar da ba ta da tausayi, “mafarki ƙarya ne, mafarki ya kan rarrashi zuciya. Kina ƙoƙarin hana mini natsuwa. Ki kwantar da hankalinki — ba za mu sake barin waɗansu su kawo mana matsala ba. Ki faɗa mini, wacece Hafsah game da mu? Ashe kin yi bacci da tunanin haɗari ne?”
Ya matsa gabansa ya yi murmushi mai ɗaci. “Ki tuna dai, yayin da muke zaune cikin ƙarfi, mun shirya komai.” Ya sauke murya zuwa ƙasa kamar maganar asiri. “Mun kai ta kogi a dajin nan, an harbe ta sau biyu — ban manta ba. Mun buɗe ƙofa ga barazanar gado, amma mun rufe ta da ƙarfi. Ba wanda zai iya tayar da ita yanzu.”
Hajiya Binta ta fasa numfashi, kyallin mafarkin ya riƙe mata tunani. Idanunta sun cika da damuwa, amma da fargaba ta gaɗa baki ta yi ƙoƙarin ƙara haske a murya. “Idris… Allah ya sa mu yi gaskiya. Wannan mafarki… ya na nuna mana wani abu — kamar faɗakarwa. Ka ji muryar ta ce ‘jinin da aka kashe zai dawo’… Me idan akwai gaskiya a cikin wannan mafarki?”
Idris ya matso kai ya kusance ta da sauri, idonsa sun yi ƙyalli. “Mom, ki ɗauki hankali. Ba mu da lokaci na hira da jarabar mafarki. Mun riga mun yi abin da ya dace. Duniya za ta zauna, kuma mu za mu ci gaba. Ki rufe bakinki ki huta — zan tsara komai.”
Sai ya juya ya nufi ƙofar zaure, ƙafar sa ta doke ƙasa da sautin hukunci. Amma kafin ya fita, ya juya ya ƙara faɗa:
“Ki sani, idan har wani yaro zai fito daga cikin ikilisiyar da kuka ɓoye, to zan yi masa abinda ya dace domin kare madafun iko na. Wannan gida ba fili bane na tausayi.”
Hajiya Binta ta zauna gaba ɗaya cikin tsananin firgici, zuciyarta na bhaƙa. A waje, iska ta yi ƙarfi, tsuntsaye sun yi kauri, kuma wani ƙaho mai nisa ya bushe kamar sanarwar wani abu mai zuwa.
— Zarah, ungozoma — na tsaye a bakin ƙofa, idonta na rikitattu. Ta kalle su da idanun da suka san sirri da yawa, sai ta motsa jikinta ta yi shiru. A zuciyarta ta san cewa mafarkin Hajiya Binta ba zai zama abin banza ba — akwai wata ƙasa ta gaskiya da za ta so ta rufe.
Kai a kai labarin ya tsaya, murya na ƙasa ta faɗi cikin duhu:
“Wutar Alqamar ba ta faɗi fage da sauƙi. Wani abu mai tsarki zai fito daga cikin ruwan da kuka ɓoye…”
*********
SUHAYL – Kaɗangaren Tsibiri
Bayan wani lokaci mai tsawo da Suhayl ya ɗauka yana tafiya ta gabashi ba tare da guzuri ko tsoro ba ya kwana a daji yaci ganye yayi sutura da ganye da ya samu, a chan ƙifin hanyar bishiyoyi da ya dosa nan ya fara jin hayaniya ta mutane da dabbobi da bai saba jin su ba , cikin hanzarin ya ƙara kaimi burin sa bai wuce samun abinci ba , yana isowa bai ankara ba yana ganin wasu halittu na mutane da sutura ta jikin su..
Da zarar ƙauyen suka taru a kansa, idanunsu suka fara yawo a jikin Suhayl. Ba rigar mutane yake sanye da ita ba, sai sunaye da ganyaye da ya zagaye jikinsa, tamkar wani ɗan tsibirin almara.
Nan da nan yara suka fara tsokana da ihu:
“Wayyo, ga ɗan tsibiri! Ga mai ganye , "Sauran manya kuma suka tsaya suna yi masa sambatu, wasu dariya, wasu kuma tamkar suna jin tsoro. Suhayl kuwa sai zuciyarsa ta buga da ƙarfi, tsoro ya kama shi, jikinsa ya fara rawa. Wannan shi ne karo na farko da ya hango irin wannan taro na mutane, kuma bai san ko da gaske su ’yan adam ne ba.
Amma kafin ya iya cewa komai, gawata kyakkyawar yarinya ta bayyana daga gefe. Fuskar ta cike da walwala, kyawunta ya tsaya tamkar hasken alfijir. Ta yi dariya mai taushi, ta rufe shi da mayafin da ke jikinta don ya daina jin kunya.
Yaran suka yi shiru suna kallon ikon Allah. Ita kuma cikin nutsuwa ta ce:
“Suna na NOOR… kai fa?”
What the F****k
Mujeeee zuwa
*****
BASHIR
Motar na gudu kamar za ta tashi sama, ƙurar hanya ta mamaye musu baya. Sagir ya riƙe hannun Bashir da jini ke fita ba ƙaƙautawa, yana toshe gurin da ya fi zubarwa da riga. Muhsin kuwa ya riƙe sitiyari da duk ƙarfin zuciyarsa, yana tsalle da hanzari a kan ramuka da gangaren hanya.
“Ka tsare shi kada ya mutu min, Sagir! Kada ka bari ya mutu kafin mu kai Kaduna!” Muhsin ya huro, idonsa na zubar da hawaye amma yana ƙoƙarin boyewa.
“Wallahi jinin nan ya fi ƙarfin rigata! Ya zuba sosai!” Sagir ya yi ihu, yana tura riga a wurin raunin. Idonsa ya koma ja, zuciyarsa na bugawa kamar ana dukan ganga.
Motar ta nufi Kaduna cikin saurin da babu tunani, ƙarar horn na ta fasa iska. Har suka shiga cikin birnin Kaduna, mutane suna kallonsu cikin mamaki.
Da suka ƙaraso bakin wani asibiti mai taken “Garkuwa Specialist Hospital Kaduna”, Muhsin ya yi tsayawar gaggawa har tayoyi suka yi ƙara. Nan take ya fito da gudu tare da Sagir suka ɗaga Bashir da aka kusa tsinke masa rai.
“Help! Help! Doctor! Yana mutuwa ne! Please ku taimaka min!” Muhsin ya fasa ihu da harshen Turanci da Hausa a haɗe.
Cikin hanzari ma’aikatan asibiti suka fito da gadon turawa. Suka kwashe Bashir, jini na riga musu hannaye da kaya. Nurse ɗaya ta danna wayar gaggawa tana kira “Emergency theatre! Prepare for surgery! yaron nan zai mutu idan aka bari haka!”
Sai suka zuba gudu da shi zuwa ɗakin tiyata. Likitoci biyu suka shigo da sauri cikin farin kaya, ɗaya daga cikinsu ya yi magana da ƙarfi:
“Ku cire masa kaya nan take! Ku danna drip ɗin gaggawa, ku kawo oxygen!”
Sagir ya tsaya a bakin ƙofa, zuciyarsa na tsalle-tsalle, jikinsa na rawa. Muhsin ya rungume kansa da hannu biyu yana maimaita:
“Ya Allah, ka tsare shi… kada ya mutu a hannuna… Allah ka ba shi rai…”
Cikin mintuna aka fara ƙarar kayan tiyata — scissors, scalpel, clamps — an rufe ƙofar operation room. Nurse ɗin ta tsaya a bakin ƙofa ta ce musu:
“Ku jira a waje. Ko da nawa ne, sai an yi masa treatment. Amma ku sani… rayuwarsa tana hannun Allah yanzu.”
Sagir ya ji jikinsa ya saki, ya durƙusa ƙasa da hawaye. Muhsin kuwa ya jingina da bango yana kallon ƙofar da aka rufe, zuciyarsa cike da tashin hankali.
Sai suka fara kiran sunan Allah a bakunan su duka biyu, saboda rayuwar Bashir yanzu ta rataya a tsakanin numfashi guda da mutuwa.
Labari na tafiya
Something big is ........ g
Narnah ƙanwar soja ✍️ ✍️ ✍️
🦎🦎 KAƊANGAREN BAKIN TULU 🦎 🦎
BY
NARNAH ƘANWAR SOJA
Follow my Wattsp group 👇👇👇
https://chat.whatsapp.com/C1fwfKiUPGgJQTONvJGjqN?mode=ac_t
GARGAƊI
Ban yarda ba , kuma ban amince a juya min labari ko a sauya ta zuwa audio ba tare da amincewa ta ba ,
********
بسم الله الرحمن الرحيم اللهم صل على سيدنا محمد وعلى اله وصحبه اجمعين والحمد لله رب العالمين ♥️
PAGE 18 / 19
08101235739
Bishiyar Ƙauyen Rimi
Suhayl ya zauna a ƙasan bishiyar, idonsa na kallon ƙasan ƙasa tamkar yana jin tsoron kallon fuskarta. Amma sautin muryarta ya tsinke shi tamkar iska mai sanyi da ta ratsa zuciya.
“Noor… sunan ki Noor? Kin ce a nan aka haife ki, Mallam Sambo shine mahaifinki, Allah ya mai rahma…” sai ta kalle shi a hankali, tana ɗan murmushi da ƙarfin hali:
“Eh, haka ne. Amma kai fa? waye kai da baka da kamanni irin namu? kamar baka saba ganin bil’adama ba me sunanka?”
Shiru ya biyo baya. Kukan tsuntsaye ne kawai ke cika sararin bishiyar. Suhayl ya ɗaga kai a hankali, idanunsa manya suna ɗauke da wani irin sirri.
“Ni… suna na Suhayl ban taɓa sanin gida ba, ban san uban da ya haife ni ba, ban san uwa ba. na taso ne a cikin daji, da namun daji, da ruwa. Tsohuwa ce ta rene ni, ita ce ta rasu ta barni da wannan zoben…”
Ya zaro zoben daga hannun sa ya nuna mata yana rawar hannu.
“Ta ce idan nabi zoben zai kai ne ga makomata.” Noor ta kalle shi da mamaki, zuciyarta ta buga. Kamar ba a duniya yake ba. Ta sauke ajiyar zuciya tana ɗan girgiza kai.
“Subhanallah… toh, Suhayl, wannan ƙauye ne. A nan mutane suke rayuwa, wasu da wahala, wasu da farin ciki. Idan ka yarda, zan nuna maka hanyar gida. Amma ina tsoron yayana idan ya dawo daga gona, saboda shi ba ya son baƙi.”
Suhayl ya runtse idanu, yana jin muryarta kamar wacce ta kira shi tun shekaru masu yawa. Ya ɗaga kai ya ce a hankali:
“Noor… zan iya zama kusa dake? Ko da a ƙarƙashin bishiyar nan kawai…”
-
Suhail da Noor suka ci gaba da tafiya a cikin hanyar ƙauyen, cike da nutsuwa. Hira suke yi tana ta ba shi labarin soyayyarta da Bashir, irin alƙawarin da suka sha yi lokacin ƙuruciyarsu. Muryarta ta yi rauni, tana haɗa dariya da hawaye.
Sai Suhail ya kalleta cikin mamaki ya ce: “Mene ne soyayya, Noor? na ji ki kina ta maganarta kamar wani abu ne mai ƙarfi.”
Noor ta tsaya cak, ta dubeshi da ido cikin rashin tsoro, ta fashe da dariya tana girgiza kanta.
“Kai fa ba ka san komai ba! ashe ba ka taɓa ji ba? Soyayya ita ce abin da ke sa mutum ya yi dariya da hawaye lokaci guda, itacce mai sa kamanta da mugun hali ,ko wulakanci tsakanin ka da abin sonka , ittace garkuwa zuciya mai sanya tsinkewar zuciya a bazara da da damina da rani , ittace Allah ya fasa a zuciyoyyin mutum biyu , ita soyayya gaskiya ce mai yinta baya mantatta ko daɗin ta ko azabar ta , Ita ce abin da ya haɗa ni da Bashir har yanzu, ko da ya barni, har yanzu ina jin shi a zuciyata. Amma kai sai ka ce jaririn da bai taɓa dandana rayuwa ba.”
Suhail ya yi murmushi ya ɗan sunkuyar da kansa ya ce:
“To idan haka ne, za ki koya min? ko kuwa sai dai ki ci gaba da dariya?”Noor ta sake dariya, ta share hawayen da ke gefen idanunta.
“Kai kaɗai ne ka san yadda zaka koya wa kanka. Ni fa yanzu kawai bari mu tafi gida, Yaya ya hana ni yin yawo nesa da gida.”
Ta juya cikin ɗan tsoro da fargaba, zuciyarta tana harbawa saboda ta manta kanta har ta tsaya