ya dubi abokansa ya ga yanda suke bin mazaunan Fauziyyah da kallo cike da kwaɗayi da burgewa. Murmushin jin daɗi ya yi sannan ya haɗe fuska ya kalle ta,cike da isa da taƙama ya ce.
"Ki na saka ɗaya ƙafar a ɗaki zaki gamu da ni. Oya maza wuce ki ɗakko waccan tabarmar ki shimfiɗa mana sannan ki kawo wa mutane abinci."
Babu yanda ta iya haka ta juya kamar wadda ƙwai ya fashewa a ciki gudun kar ta yi dogon motsi jikinta ya juya. Sai dai duk da yanda take taka tsantsan hakan bai hana jikin nata juyawa ba,ganin yanda take tafiya bata kaɗa jikinta yanda ta saba ne ya sanya Abbas sake daka mata tsawa ya na faɗin.
"Dalla Malama ki kama jiki ki ɗakkowa mutane wajen zama,shashasha kawai wadda bata san yanda za ta tarbi miji ba idan ya dawo daga wahalar nema mata abinda za ta ci."
Cikin hanzari ta wuce ta ɗakko tabarmar da ta ji jiki,sai dai a wanke take tsaf babu datti,ta shimfiɗa musu. Juyawar nan da za ta yi ta shiga ɗaki zaninta ya kusan kuncewa,da sauri ta kama zanin ta faɗa ɗaki,ta na jin Abbas na masifa ya na faɗin.
"To yanzu Fauziyyah abincin ma sai na roƙa ki kawo mana? Kin san Allah ki dena saka ni yawan magana bana so,idan kuma kika bari na sake yi miki magana na lahira sai ya fiki jin daɗi."
Wani irin dogon tsaki Barirah ta ja a daidai lokacin da take fitowa daga ɗakinta za ta yi alwala,ido suka haɗa da Abbas da abokansa ta kuwa daka musu harara tare da faɗin.
"Me na ci ban bawa mutum ba ake ƙure ni da mugun kallo? Allah dai ya kai mutum lahirar nan ya banbance mana jin daɗin duniyar da na ƙiyama,aikin banza kawai,namiji har namiji amma basirarsa ta kare wajen musgunawa mace mai rauni."
Kallon Abbas abokansa suka yi,wani da ake kira da Salman ne ya ce.
"Tab ! Lallai matar nan ta ci ta ƙoshi,haya fa take a gidanka amma take iya faɗa maka maganganu yanda ranta ke so baka yanka musu tikitin barin gidanka ba."
Abbas bai ce komai ba har sai da Barirah ta shige banɗaki sannan ya yi ƙasa da murya ya ce.
"Idan na kore su ai kaina na cuta,ni kaɗai na san irin amfanin da zaman su yake yi min a cikin gidan nan. Sannan kuma wannan matar da kake gani ta riga ta shanye mijin,kana taɓa ta ko ka faɗa mata baƙar magana ubanka zai ci,ka dai ganta daf da ƙasa ba ta da wani kyan arziƙi,to a wajensa Fauziyyahta mummuna ce."
Nan da nan suka hau musanta kalamansa akan Fauziyyah suka ɗora da yabon shape ɗinta da surar ta tare da muryarta,Fauziyya na ɗaki ta na saka wata jemammiyar doguwar rigarta da ta ji jiki tin ta lefen ta,gashi yanzu auren su ya doshi shekara uku da rabi, ɗankwalin rigar ta ɗaura tare da rufe gashin kanta ta can ƙarshe,hakan sai ya bawa gaban kan nata bayyana kamar tana sane ta yi hakan. Takaicin hirar ta da Abbas yake yi wa abokansa ce ta sanya ta zama a bakin gado ta zabga tagumi,me yasa Abbas yake yi mata haka? Me yasa ba ya iya riƙe sirrin auratayyar su har sai ya sanar da abokansa hankalinsa ke kwanciya? Me yasa kuma baya tashi yabon ta sai abokan sun zo gidan? Meye amfanin yabon da yake yi mata a wajen mutane amma ita ko sau ɗaya bai taɓa yaba ƙoƙarinta ko bajintar da ta yi masa ba? Kiran sunanta da ta jiyo Abbas ya yi a ƙufule ne ya dawo da ita hayyacinta ta miƙe da sauri ta nufi kitchen. A jikinta take jin yanda idanuwansu ke kallon saƙo da lungu na jikinta. Ƙwalla ce ta taru a idanunta,a haka ta duƙa ta ɗakko abincin ta ɗora a babban faranti ta zuba ruwan randa a jug dan tini ya siyar mata da fridge da deep freezer ɗinta manya,wai babu wajen ajiye su,duk lokacin da suka yi gidan da ya fi wannan girma zai siya mata.
Cikin takunta mai cike da natsuwa ta ƙarasa gaban su ta durƙusa ta ajiye abincin,gaishe su ta yi kanta a ƙasa suka amsa sannan ta dafa gini ta miƙe ta koma ɗaki. Ta na shiga Rabi'u ya ce.
"A gaskiya Abbas duk cikin mu kai kaɗai ne ka yi dacen macen nuna wa duniya ba ma sa'a ba kaɗai,ka ga mace kamar ka sace ta ka gudu?."
Dariya suka saka Abbas kuwa ya na jin kansa kamar ya fashe dan girma,Salman ne ya ce.
"Allah sarki Babangida,yanzu da yana nan fa da ya ce,wannan abun da kuke yi haramun ne,Allah ya haramta,kai kuma ka zauna kamar mara kishin iyalinsa wasu na yabon matarka,ni duk wanda ya yaba surar mata ta ba sai na zare takobi na fille wa jahili kai ba."
Dariya suka bushe da ita suka tafa,cikin shaƙiyanci Abbas ya ce.
"Ahhh shikenan Babangida ya tafi,ta wanke ta bashi ya kurɓe."
Salman yana dariya ya hau daidaita fuskarsa ya na kwaikwayar Babangida da baya wajen ya ce.
"Ah ka manta ni na sha abuna a haka? Ai bata wanke ba ta sirka da wani abu, concentrate na sha. Ku fa gani kuke yi yiwa matayen ku mugun hali da musgunawa shi ne yake riƙe muku su ko? Ku sani soyayya ce ke riƙe da su kawai da biyayyar aure,ina jiye muku lokacin da zaku kai su bango su juyo kan ku da tasu kalar azabar ba za ku ji daɗi ba."
Dariya suka sake bushewa da ita,cikin isa da izza Abbas ya ce.
"Ni mace ta isa ta juya ni? Kuna gani fa ana zaune wannan ƙwailar tasa za ta kira shi a waya,jiki na rawa yake tafiya,ni yanzu da nake da mace kamar Fauziyya ta isa ma ta min haka? Kun dai ganta kun shaida yanda take da kyau da duk wani abu da namiji zai nema a wajen mace,amma bata isa ina faɗa tana faɗa ba,ballantana mu yi sa'insa ko ta saɓa umarnina."
Dariya suka kece da ita Rabi'u ya daki kafaɗarsa ya ce.
"Shegen sama,ai nake faɗa maka abokina kai kam ka gama dacewa a duniya,saura ƙiyamar ka kawai. Ka samu mai siffofin hurul'ini tin a duniya."
Buɗe kwanon abincin Abbas ya yi da niyyar su ci idanuwansa suka sauka akan dafaffen waken da ya ji manja da yaji,nan take yawun bakin su ya tsinke,kasancewar abincin manja ya gaji haka. Sai dai girman kai da mugunta irin ta Abbas ta sanya shi rufe kwanon ya na muzurai,sai da ya haɗiye yawun da ya cika masa baki ya daidaita natsuwarsa sannan ya ce........
[20/10, 7:52 am] HAERMEEEBRAERH ✍️✨: MUGUN MIJI.
RUBUTAWA HAMIDAH SANUSI AHMAD HAERMEEBRAERH ✍️✨
PAGE 3.
"Ke zo nan!"
Jiki na rawa Fauziyyah ta miƙe za ta fita,ta na ayyanawa a ranta.
'Na shiga uku ni Fauziyyah me kuma na yi?'
Mamakin yanda har ta ji kiransa ta amsa ne ya kama Salman,cikin yin ƙasa da murya ya ce.
"Wai kana nufin wannan kiran da ka yi mata har ta ji ta amsa kuma ta na nan tafe? Gaskiya abokina kai bala'i ne."
Murmushin mugunta Abbas ya saki sannan ya ce.
"Kar ma ta amsa mana. Ai matsawar ina cikin gidan nan to fa kunnuwanta da zuciyarta a buɗe suke,ta yanda ko da motsi na yi ta san me nake buƙata kafin na furta,kuskure ɗaya za ta yi wajen ƙin fahimtar magana ko motsina jikin jakar ya faɗa mata."
Kalmar jaka da ya kira ta da shi a gaban abokansa ce ta daki zuciyarta,cikin ƙunar rai ta durƙusa a gabansa cike da ladabi ta ce.
"My king gani. Ku na buƙatar wani abun ne?"
Haɗe rai Abbas ya yi ya nuna Fauziyyah da yatsansa manuni, cike da wulaƙanci da izza da isa ya ce mata.
"Ke dan Uban ki wace iriyar shashasha ce? Yanzu ace na fita rana da zafi inuwa da damina na nemo abinda za a ci a gidan nan,amma na kawo baƙina ki haɗa mu da zallan dafaffen wake har da wani manja da yaji a ciki? To ina laifin ma ki dafa wake da shinkafa?"
Zuciyarta na tuƙuƙin baƙin cikin zagar mata mahaifi da ya yi a gaban abokansa,ta daure tare da jurewa kar ya gano halin da take ciki ta ja wa kanta mari ko jibgar wulaƙanci ta ce.
"My king ka yi haƙuri don Allah, nima shinkafa da waken na yi niyyar dafawa sai kuma na tarar da shinkafar ta ƙare shi yasa na yi amfani da iya abinda muke da shi kawai na dafa dan kar ka dawo babu abinci."
Cike da ɓacin ran tona masa asirin bashi da ƙwayar shinkafa a gidansa da ta yi gaban mutanen da yake nuna wa shi wani ne, ya daka mata tsawa tare da faɗin.
"Dalla malama tashi ki bani waje! Daƙiƙiya kawai. Kin duba buhun da na kawo ne jiya? Ki na nan kina jan jiki kamar akan ki aka fara ɗaukan ciki baki san ma akwai abinci a gidan ba. Bari mu gama zan shigo ne mu gauraya da ke. Ware ki bawa mutane waje."
Duk rugugin faɗan da yake yi bai dame ta ba da fari,saboda hankalinta ya yi nisa wajen tunanin yaushe ya shiga da buhu gidan? A ina kuma ya ajiye buhun? To ko dai a store ya ajiye bai sanar da ita ba? Ta na tafe tana tunani ta furta.
"Kai gaskiya ban ga wani buhu ba,saboda yana shigowa gidan na je na tarbe shi kamar yanda na saba yi kullum,da hannuna na karɓi jakarsa na ajiye a inda na saba rataye masa,to wanne buhu yake nufi?"
A bakin gado ta zauna tare da zabga tagumi. Ƙwaƙwalwarta ce ta tina mata kalamansa da ya ce.
'Bari mu gama zan shigo ne mu gauraya.'
Hankalinta ne ya yi mummunan tashi,dan kuwa ta san yau ɗin Allah ne kawai zai ƙwace ta a hannun Abbas. Wasu jijiyoyi ne raɗa-raɗa suka firfito a gaban goshinta,hancinta kuwa har wata zufa yake tsattsafarwa,idanuwanta sun kaɗa sun yi jawur saboda tashin hankali. Ta na nan zaune ta ji fitar su suna sake zuga shi akan ya ci gaba da riƙe wuta,domin kuwa kyawawan mata irin Fauziyyah idan suka samu waje juya miji suke yi,wataƙila ma albashinsa ita ce za ta dinga amshewa sai abinda ta bashi na kashewa a ciki. Idan kuwa ya kuskura ya bari hakan ta kasance,to fa babu shi babu ci gaba da more ƙuruciyarsa da ƴan shila,guzumayen ma ba kula shi za su yi ba. Wata iriyar dariya suka sanya suka tafa,shi kuwa gogan cikin haɗe girar sama da ta ƙasa ya ce.
"A da ne kafin mu yi aure take da wannan farin jinin. A yanzu kuwa ko me sharar kasuwa sai dai ya yi manage da ita,saboda ta zamo marar amfani."
Wasu irin zafafan hawaye ne suka fara gudun tsere a kuncin Fauziyyah da ke sauraron duk wata kalma dake fitowa daga bakin masoyinta,wanda ya kusa rasa ransa saboda tsoro da fargabar rasa ta da ya kusan yi a baya,namijin da ya sadaukar da jin daɗin sa saboda ya mallake ta,shin da gaske ne bata da wani amfani ko a wajen mai sharar kasuwa? Shin da gaske ne babu namijin da za ta burge ballantana har a so ta? Ashe shi yasa Abbas ɗinta abun ƙaunarta ya sauya daga masoyinta ya koma maƙiyinta? Lallai rashin gyara masifa ne,to amma ai laifinsa ne ta lalace har ta zamo marar amfanin da yake yawan kiranta. Tini ya dena sauke duk wani haƙƙinta da ya rataya a wuyansa. Turare wannan shi kaɗai yake siyawa kansa ya ɓoye,ko za ta yi warin bunsuru ne sai dai ta yi,amma bata isa taɓawa ba.Sutura kuwa kamar zata kashe Abbas masu kyau da tsada yake siya,takalman sa kaf babu ƙasa da na dubu goma,amma ita tin na lefe take ta murza ko na sallah baya yi mata ballantana idan ya ɗinka nasa ya tuna da ita. Sabulun wanka yake siyawa kansa mai kyau da tsada,ita kuma sai dai ta yi da na wanki,idan ya ƙare ta yi da omo,idan babu omo ta yi da zallan ruwa,shi yasa lokuta da dama ko ta yi wanka da ta yi aiki kaɗan sai ta fara warin hammata. Man shafawarsa na musamman ne,amma ita ko basilin be siya mata ba,tin mayukan lefenta da suka ƙare be sake sai mata mai ba balle hoda,shi yasa ko tsinke babu a saman mirror ɗinta da ya wuce kwalli da brush ɗin da take taje girar ta da shi. Idan tana son shafa mai sai dai idan ta faki ido ta tatse na leda da ta kan adana idan ta juye man. Lokuta ƙalilan ne take samu Barirah ta sammata mai a duk lokacin da ta sai me kyau na gyaran fata. Ranar da Mahaifiyar Abbas ta kawo mata basilin kuwa ririta shi ta dinga yi ta na adanawa,har sai da ya shekara be ƙare ba. Murmushi ta yi a lokacin da ta tina da mahaifiyarsa,mace ce itanmai mutunci da karamci,takaicin Abbas shi ne ya yi sanadiyyar da ta kamu da mummunan hawan jini. Yawan zuwa gidan ta tarar da Fauziyyah a cikin mawuyacin hali har itama nata ciwon ya tashi ne,ya sanya danginta suka bata shawarar ta rage zuwa gidan nasa,idan yaso duk sanda ta so ganin Fauziyyar ta dinga saka shi yana kai mata ita su gaisa,shi kuma ta dage da yi masa addu'a da fatan shiriya,watarana komai zai zamo labari. Wannan shawarar ce ta sa sai su shafe wata ɗaya zuwa biyu basu haɗu ba,wani sa'in ma har sukan kai wata uku Fauziyyah bata ga surukar tata ba. Sai dai shi yana zuwa kullum yana gaida ita,kasancewar wajen da yake koyarwa babu nisa sosai da gidan nasu.
Zumbur ta miƙe tsaye tare da binsa cikin ɗaki,saboda yanda ya fizgi hannunta na hagu ko tausayin tulelen cikin dake jikinta bai yi ba. Jikinta ne ya ɗauki rawa suna zuwa ƙofar bedroom ɗin su ta riƙe gini ta na yarfe hannunta na dama ta ce.
"My king don Allah ka tausaya min,ka ga halin da nake ciki. Ka yi haƙuri ka yafe min duk wani laifi da na yi maka,na yi alƙawari ba zan sake ba."
Mugun kallon da ya zuba mata da shanyayyun idanuwansa ne suka sanya ta haɗiye wani mugun yawu mai bala'in kauri,busassun laɓɓanta ta lashe ta ɗaga ƙafa da ƙyar ta bi bayansa zuciyarta na lugude kamar ana dakan sakwara.
A zafafe ya yarfe hannunta ya koma saman makeken gadon su mai tsananin kyau da tsada ya zauna. Huci yake yi kamar wani kumurcin maciji. Murya a shaƙe kamar ta ragon layyan da ya ci kuka ya gaji ya ce mata.
"Tuɓe."
Hawayen da suka maƙale suka ƙi fita ne saboda tashin hankali,suka samu damar fitowa daga idanuwanta suka hau kwaranya,cike da mutuwar jiki da saddaƙarwa Fauziyya ta hau warware ɗaurin ɗankwalinta. Ta riga ta sani tinda ya shiga wannan yanayin babu wanda ya isa ya ƙwace ta ko da kuwa mahaifiyarsa ce ta zo. Hannayenta na masifar rawa ta ɗaga rigarta tin daga ƙasa ta hau cirewa. Tsaye ta yi a gabansa kanta duƙe kamar wadda mijinta da surukanta suka kama a ɗakin kwarto. Kallon tsayayyu kuma cikakkun ƙirjinta ya yi ya haɗiyi wani mugun yawu,faffaɗan ƙugunta mai ɗauke da manyan cinyoyi ya koma bi da jajayen idanuwansa yana kallo. Muguntar da ya shirya mata ce ta sanya shi fashewa da dariya kamar wani zararre. Hannu ya sanya ya zaro wayarsa daga aljihunsa ya kunna ya koma ya jingina da allon gadon. Bai sake kallon inda take ba. Ita kuwa jikinta ne ya ɗauki rawa kamar mazari,ji take yi kamar ƙafafuwanta ba za su iya ci gaba da ɗaukar gangar jikinta ba. A gajiye ta hau motsa ƙafafunwanta tana ɗaga su daga wannan zuwa waccan. Sai da Abbas ya gama abinda ya mayar ibada sannan ya ɗaga idanuwansa da suka sake rinewa suka koma jajaye ya ce.
"Zo nan."
Da ƙyar Fauziyyah ta ɗaga ƙafafuwanta ta fara takawa zuwa gabansa,hannayenta sun yi sanyi ƙalau kamar wadda ta taɓa ƙanƙara,sai zufa suke tsiyayarwa,zama ta yi a wajen da ta riga ta saba da zarar ya yi mata irin wannan kiran,hannu na rawa ta hau zare masa safar ƙafarsa,tana gamawa ta cire masa dogon wandonsa da rigarsa ta ninke su ta mayar inda take ajiyewa kafin washegari kuma ta wankesu. Ta na kammalawa ta koma saman gadon ta zauna a gabansa tare da sadda kai ƙasa. A wulaƙance Abbas ke bin surar jikinta da wani malalacin kallo. Hannunsa ya sanya ya ɗaga haɓarta ya na kallo,cikin sauri ta buɗe nata idanuwan ta na bin cikin idanunsa da kallo gudun kar ta sake yin wani laifin. Cike da mugunta Abbas ya hau sarrafa gangar jikinta da ta ya ke kira da 'Marar amfani' a koda yaushe......
[20/10, 7:52 am] HAERMEEEBRAERH ✍️✨: MUGUN MIJI.
RUBUTAWA HAMIDAH SANUSI AHMAD HAERMEEBRAERH ✍️ ✨
PAGE 4.
Kwance ta yi kawai ta na jin duk wani bidiri da Abbas ke yi a kanta cike da mugunta da zalunci da rashin tausayi. Domin jin daɗin sa duk wani abu da zai faranta masa rai ya bashi nishaɗi shi ya dinga yi ko da kuwa ita zai zame mata azaba.Tsananin tausayin kanta ne ya sanya wasu zafafan hawaye gangarowa daga idanuwanta suka sauka a saman pillown da ta ɗora kanta. Kiran sallar magrib ne ya sanya Abbas haƙura ya ƙyale ta,domin kuwa ya tina da bai yi sallar la'asar ba. Kallonta ya yi ya ce mata.
"Ki shirya sauran na dare kuma."
Kuka ne ya kusan ƙwace mata,dan ta san babu abinda zai hana shi yin abinda ya furta sai ikon Allah. Dan haka dole ta yi haƙuri ta danne kukanta kafin ya fara yi mata masifa akan haƙƙinsa,se ka ce ita bata da wani haƙƙi nata da ya rataya a wuyansa.Cike da nishaɗi ya tashi ya zira gajeran wandonsa ya fito tsakar gida ya na miƙa. Barirah ce ta ɗaga labule za ta fita domin yin alwalar sallar magrib, ta na yin arba da Abbas sanye da gajeran wando ta yi saurin sakin labulen ta koma ɗakinta. Zama ta yi a kan kujera tare da zabga tagumi ta na jin tsana da takaicin Abbas na mamaye ranta. Tsaki ta zabga kafin ta ce.
"Jahilin banza da wofi kawai,da ma na sani da na gama girkina nayi wanka alwalar na yi gaba ɗaya,yanzu zai je ya ɓata lokaci nima ya ɓata min."
Ta na nan zaune ta ji ya ɗebi ruwa a bokiti ya shige banɗaki,cikin sauri ta miƙe ta fita da nufin ɗaukar buta ta yi alwalarta a gaggauce kafin ya fito. Fauziyyah ta gani a bakin ƙofar ɗakinta kwance kamar gawa. A guje ta isa wajenta ta na faɗin.
"Ke lafiya? Me ya same ki haka? Ko dai naƙuda kike yi?"
Girgiza kai Fauziyyah ta yi,a wahalce ta ce.
"Ruwa...ruwa zan...shaa Aunty."
Cikin sauri Barirah ta matsa kusa da randar da Fauziyyah ke zuba ruwa,ta ɗebo mata ta kafa mata kofin a bakinta,wani irin sha take yi wa ruwan kamar shi kaɗai ne abu mafi mahimmanci a rayuwarta. Ta na gama sha ta lumshe ido ta koma ƙasan ɗakin ta kwanta ta yi lamo. Tunda Abbas ya tashi daga jikinta take jin ƙishirwa,sai dai ta riga ta san ko mutuwa za ta yi ba zai bata ruwan nan ba,sai dai idan ta isa ƙiyama ta sha. Sanin hakan ne ya sa ta yi shiru har ya saka gajeran wandonsa ya bar ɗakin. Ya na fita ta ja doguwar rigarta ta mayar a jikinta. A hankali ta sauka daga gadon,da rarrafe da jan jiki ta iso bakin ƙofar ɗakin,sai ta fara jin jiri ya na neman ya sanya ta kwantawa a saman cikinta,cikin azama ta yi dabarar kwantawa a gefen ta na dama,ta na nan ta na ambaton sunan mai kowa mai komai ta ji motsin Barirah,farinciki ne ya mamaye zuciyarta,domin ta san ita ba za ta taɓa barinta a wulaƙance ta wuce ta ba.
Alwala Barirah ta yi idanuwanta na zubar da hawaye,ta na idarwa yana fitowa,ko ɗaga kai bata yi ta kalle shi ba ta bar wajen ta shige ɗakinta,sallah ta tada tana ci gaba da sharce hawaye. A sujjadarta ta ƙarshe sai da ta yi wa iyayenta da mijinta addu'a sannan ta yiwa Fauziyyah addu'a da fatan Allah ya kawo ƙarshen wannan zaman nasu ita da Abbas,domin a ganinta babu wani alkhairi da ke cikinsa,ba zai taɓa sauyawa ba.
A yanda ya ganta a sheme a tsakar parlour bai yi wani yunƙurin taimaka mata ba,sai ma ware ƙafafunsa da ya yi ya tsallake ta ya shige ɗaki,kaya ya sanya ya fesa turarukansa sannan ya tada sallah,caccaken kurciya ya yi ya sallame,cike da masifa ya koma parlour ya tsaya a saman kanta ya ce.
"Raguwar banza da wofi kawai. Ke wai yanzu sau biyun ne ya gajiyar dake tsabar rashin amfani? To ki buɗe kunnen ki da kyau ki ji ni,zamu haɗu dake zuwa anjima,dan haka gwanda ma ki miƙe ki ƙwarara jikin ki dan ba wai na samu abinda nake so bane,manage kawai na yi. Ni zan fita,ga wannan ki leƙa ki aiki yaro a siyo kalanzir ki saka a risho tinda dare ya yi kuma na ga itacen har yanzu da jiƙa ba lallai ki gama girkin da wuri ba,ni kuma yunwa nake ji sosai. Maza ki tashi ki dafa mana abinci,kar na dawo baki dafa komai ba."
A rikice ta tattaro ragowar ƙarfin da ya yi mata saura ta kalle shi ta ce.
"My king babu fa ƙwayar hatsi da ta rage a gidan nan,kuma na faɗa maka tin wancan satin abubuwa sun ƙare,ɗazu ma ban ci komai ba ku na juyewa duka."
Ji ya yi kamar ta watsa masa tafasasshen ruwa a fuska,a hasale ya daki ƙafarta tare da wara hannayensa ya yi mata daƙuwa sannan ya ce.
"Dan iyayen ki a gidan uban wa kika sanar dani abubuwa sun ƙare? Ko ni soko ne irin ki da zan manta abu mai mahimmanci irin wannan? Bari na mayar da ɗari biyu na za ta min amfani,kin san yanda zaki yi ki ciyar da kan ki. Ba kuma gwaninta kika yi ba da kika hana kan ki abinci kika bamu ni da abokaina,wannan neman suna da wajen zaman ba zai sauya kallon da nake yi maki ba."
Tsallake ta ya yi ya zari takalminsa ya bar gidan ya na ci gaba da masifa har ta dena jiyo shi. Kasa zubar da ko da hawaye ta yi domin ta ji daɗi a ranta. Wannan shi ne sakamakon soyayyar da ta samu a wajen mutumin da ta ɗauka ya fi kowa sonta da ƙaunarta a duniya. Murmushi ta yi ta yunƙura da ƙyar ta tashi. Ruwa ta ɗiba ta je ta dasa kujera a banɗaki ta yi wanka sannan ta fito. Sallar la'asar da be barsu sun yi ba ta gabatar sannan ta ɗora da magariba. Ta na nan zaune aka yi Isha'i,sai da ta yi Isha'i ta yi shafa'i da wutiri sannan ta kwanta a wajen ta na sauke ajiyar zuciya. Sallamar Barirah ce ta tashe ta zaune. Murmushi ta sakar mata sai ta ga idanuwan Barirah sun kumbura sun yi jawur,kwanon hannunta ta karɓa ta ajiye a gefe ta riƙe hannayenta ta ce.
"Don Allah Aunty ki dena damun kan ki saboda ni,ai bahaushe ya ce duk tsuntsun da ya jawo ruwa shi ruwa zai doka. Ni ce na jawa kaina duk abubuwan da Abbas yake yi min,ba dan komai ba sai dan soyayyar da na nuna masa,wadda har yanzu taƙi barin raina,ina jin son sa a cikin jini na wanda yake zaune a zuciya ta,ta yanda duk wani bugu da za ta yi sai ta harba min dafin soyayyarsa a sassan jikina. Kin ga kuwa dole na jure duk wani tukuici da yake bani."
"Ki gudu wajen ɗan'uwanki Fauziyyah,Abbas kashe ki yake so ya yi,ta ya zai bar mace da tsohon ciki da yunwa? Ga munanan kalamai babu lallashi ko tausayawa? Na gaji da ganin halin da kike ciki,idan har baki ɗauki mataki akan Abbas ba,mu zamu ɗauki matakin raba zuciyoyinmu da damuwa da tashin hankalin da kike ƙunsa a ƙarƙashinsa. Ki tashi ki ci abincin nan a gabana na wuce da kwanona,domin ni ba zan zauna zaman dafawa mara mutunci abinci ba kullum. Idan kika ga na bashi abincina to sai dai bashin zai kare ki daga zaluncinsa."
Murmushi kawai Fauziyyah ta yi,tabbas ta san kalaman Barirah akan gaskiya suke,amma yanayin yanda take aibata mata miji yana sukar ranta. Babu yanda ta iya kan dole ta ci abinci ta sha ruwa,Barirah ta wuce da kwanonta,cikin sauri Fauziyyah
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 12