Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
9 / 10
се, "Ва уа ce kar a gaya mata ba?" Та сe, "Au haka ne? Mu dai mun san sunanta, amma Little za mu riga ce mata". Ta zauna dabas ranta ya fara baci, ta се, "То amma me ya sa ni yake boyc min bayan ni na fi cancanta 137 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna da na sani kan kowa, ni na sha wuyar cikinta na haife ta, don me ba za a sanar min ba, akwai wanda ya haifar min ita, ko shi ya haifar min bare ya ki fada min sunanta?" Rafi'atu ta ce, "Ya yi kyau, dole ki fada mana kin haihu. Kan wani suna can za ki runtse ido kina fada masa maganganu haka? In ya dawo za ki masa kiri-kiri ba za ki lallaba shi ba?" Ta ja tsaki tare da cewa, "Kar ya fada mana, ya je ya yi ta riko. Suna dai dole a kira ta da sunanta, in kuma ba ya sonta ba zai iya sa mata ba. Ni ina son 'yata, zan sa mata sunan, ba shi kenan ba?" Ta dauki 'yar da wayarta ta fice cikin bacin rai. Dakinta ta shige ta haye kan gado, sai kumburi ta ke. Tsam Rafi'atu ta mike ta biyo ta, ta shigo ta zauna kusa da ita tana kallo. Ta kama 'yar ta kankame kam, Rafi'a ta ce, "Me ke damunki Mabaruka? Kin san me ki ka ce kuwa?" Ta dago ta kalle ta, ta dauke kai tare da cewa, "Na sani mana, sai me? Na fada, karya na yi?" Ta ce, "Ina ga kin samu matsa! wajen haihuwar nan, har za ki iya cewa Ya Imran ba ya son 'yar nan duk kin manta baya, kin manta dawainiya da wahalhalun da ya sha a kanki wajen rainon cikinki? Kin manta yanda ya aje komai yana kula da kc, akwai imagine kan ya boye sunan 'yar bai gaya miki ba, wasu sun sani me ke damunki Mabaruka? Har ashe za ki iya fada masa 138 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna maganganu irin haka ko kunya ba ki ji ba, kin manta irin soyayyarsa a gare ki?" Hawaye suka zubo, ta dube ta a marairaice, ta ce, "To amma me ya sa ya min haka Rafi'a? Ya daina sona kenan?" Ta ce, "Ni kau haushi ki ke ba ni wallahi, kin manta halinsa ne?" Ta ce, "A'a". A sanyaye. Та се, "То ki sa ido ki gani mana". Ko da ya kira ta tamkar ta masa kuka a kan ya fada mata sunan. Ya yi dariya, ya ce, "To mene ne na damuwar za ki ji mana, ke da 'yarki? Kada ki damu kin ji ko my Mabaru, gobe kamar yanzu muna tare". Kwana biyu da haihuwar ya dawo. Tun a airport suke waya, ku zo ku ga kwalliya tamkar ranar ne suna ita da Baby sun cancada ado, kowa yabawa yake. Ya shigo gidan a kagauce da nufin tunkarar dakinta, jikinsa na rawa. Aunty Luba ta tare shi, ta ce, "To tsaya azarbabi, surukanka na ciki, wallahi in kuma a ka nuna musu halinka to". Ya yi turus ransa ya baci, ya ce, "Su waye su din?" Ta ce, "Yan uwan Babanta mana". Bai ce komai ba ya yi kwana, tare da cire hula ya wurgar. Ba haka ya so ba, first Mabarukarsa ya so ya fara gani sannan 'yarsa, 'Little Mabaruka'. Ya fada kan gadonsa tare da lalubo lambarta. Mutane na zazzaune ta 139 WAYE ANGON?-4 Maryanı Jafar Kaduna yanko da gudu, jikinta na rawa da doki ta iso. Ya bi ta da kallo, lokaci guda ta canza masa. Ta kara kyau duk ta sabe. Da zuwa ta fada jikinsa, shi kuma ya rufe ta da hannuwansa yana murnar ganinta. Ya dago ta yana cewa, "Fada min lafiyarki kalau, ba abin da ke damunki?" Ta daga kai tare da cewa, "Lafiya ta lau". Ya če, "Ina 'yata?" Ta ce, "Tana can wajen su Rafi'atu". Ya koma ya zauna tare da cewa, "Maza dauko min abata". Ta yi dariya tare da juyawa ta dauko masa din. Ya tsura wa yarinyar ido a nutse yake kallonta, wata soyayyarta ya ji tana shigarsa a hankali. Ba zai iya misalta shi ba, gefe kuma mamaki ya hana shi magana inda yake tambayar kansa, shin wannan 'yata cе Mabaruka ta haifa min? Allah ya ba ni, ni ne babanta?" A hankali ya sulale ya zauna bakin gado, kwalla na taruwa a idonsa na farin ciki. Ya kankame yarinyar a kirjinsa har da lumshe ido, yana cewa, "Allah na gode maKa". Mabaruka wacce ke tsaye kyam tana kallonshi, fuskarta dauke da murmushi, dadi da zakwadinshi ya hana ta magana, gefe kuma soyayyarshi da ta 'yarsa na kara shigarta Ta tsugunno gabansa taro da dora hannuwanta kan pwiwarsa, har lokacin idonsa a lumshe yake. 140 WAYE ANGON?-4 Ta ce, "Y a Imran?" Maryam Jafar Kaduna Ya bude idon kyam a kan nata, ya amsa, "Na'am". Ta ce, "Kai ma kana sonta?" Tambayar dariya ta ba shi, ya kalli babyn da ta ke nade cikin shawul tana baccinta a nutse, sai kamshi da yake tashi jikinta mai nutsuwa. Ya dago ya kalli Mabaruka, ya ce, "Why not Mabaruka?" Ba ta iya amsawa ba, sai dai dariya. Ya dago habarta tare da cewa, "Yes I love her alots, and you?" Ya tambaye ta yana kallonta. Та сс, "Саb! Sosai ma, ka ji yanda nake jinta a raina kuwa?" Ya yi dariya sosai, ya ce, "I know, mamaki ya ishe ni Mabaruka, dubi fuskarta, idonta, hancinta da bakinta duk irin na Mabaruka ta ne ba bambanci". Ta ji dadi sosai, ta yi dariya tare da leka fuskarta, ta ce, "Kowa haka yake cewa, amma me ya sa haka?" Ya yi murmushi, ya ce, "Ikon Allah tamkar ke kina yarinya. Mun yi waya da Mommy ta ce haka ta haife ki, sam babu bambanci, kamannin ma har ya baci. Ban taba ganin kamanceceniya irin wannan ba, sak! Ke се. Cikin doki tana dariya ta ce, "Dadi nake ji Ya Imran, ban san me ya sa ba". 141 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ya nutsu yana kallon yarinyar, ya ce, "Dole ne, na san za ki ji. Ni ma haka ne a gurina". Ta sake cewa, "Amma na so a ce da kai ta yi kama Ya Imran". Ya-aje yarinyar tare da kamo. ta zuwa jikinsa kan cinyarsa suka kura wa juna ido tsawon dakiku kowa da yanayin da yake ji game da dan uwansa. Ya ce a hankali, "Me ya sa Mabaruka?" A sanyaye ta ce kwalla na cika idonta, "Saboda ina sonka Ya Imran, zaan so a ce na haifi mai kama da kai, don koyaushe in dinga kallonta ina jin dadi". Ya nutsu yana kallonta, can ya tallafo fuskarta da hannuwansa biyu yana jin saukar numfashinta, ya ce, "Na fi sonki Mabaruka, hakan ya sa na fi farin ciki da haihuwar;ya mace, kuma copy din Mabaruka ta". Ta yi dariya sosai, har sai da hakoranta suka fito, ta ce a marairaice, "Amma me ya sa ka ki fada min sunanta Ya Imran? Ka daina sona ko?" Ya yi murmushi tare da shafar gefen fuskarta, ya ce, "Wai da ba na son sanar miki ne 2 yi laifi?" Haushin da ya dawo mata ta hade fuska, ta ce, "Saboda ban kamata na sani ba ko ba ni da muhimmancin sanin?" Ya yi shiru yana kallonta ba amsa. Aunty Luba ta kwala mata kira, "Ki fito ga baki nan sun zo sauri kuma suke za su tafi”. 142 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta yi saurin mikewa daga jikinsa tare da ture hannunsa. Cikin haushi ta ce, "Kar ka ſada, ka yi ta riko bana so". Daga haka ta juya, ya kwalo mata kira, "Z.o mana". Dode kunnuwanta ta yi tare da wucewa da sauri ta bude kofar ta fice tare da banko masa. Murmushi kurum ya yi, tare da cewa, "Allah raya mana ke my Mabaru". Ya fada yana kallon 'yar. Rafi'atu ta ci karo da ita ta debo kunu, ta bi ta da kallo bayan ta wuce ta gabanta fuu zuwa dakinta. Da sauri ta sha gabanta tana cewa, "To me kuma ya faru?" Ta ja ta tsaya tare da sakin tsaki, ta hararo dakinshi ta ce, "Ni da wancan mutumin mana". Kunun ya kusan biyo wa Rafi'ar ta hanci don razana, ta samu ta hade shi da kyar, ta ce, "Waye mutumin can Ya Imran din?" Ta ce tana harararta, "To da wa nake in ba shi ba? Ni son ma sai na fasa gabadaya, 'yata ishe ni". Ta jinjina kai, ta ce, "Da kyau, gaskiya dole ki ce haka tunda ya taimaka miki kin samu 'yar son kuma ki bar yi masa sai me kuma, shi ma Mabarukar ta ishe shi, ba ke kadai ki ka haife ta ba". Ta saki baki tana kallonta, ta ce, "Wacce Mabarukar ni kuwa?" 143 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta kurbi kunun, sannan ta ce, "Yarsa mana, wacce ki ke fada kan bai gaya miki sunanta ba". A dan tsorace ta ce, "Su... su... sunanta kenan?" Ta ce, "Kwarai sunan da ya sa mata kenan tun ranar da aka haife ta. Ba don komai ba sai don son da yake miki". Daga fadin haka ta juya ta wuce kununta a hannu. Gabadaya ta birkice ta rasa wane tunanin za ta yi, wani tsoro da firgici ya kamata, da dafe kai tana salati tare da tambayar kanta, "Me kenan na yi ni Mabaruka? Butulci ko gajen hakuri?" Ta ba kanta amsa. Ta juya tana kallon dakinsa, wata kunya ta kamata. Ta yi saurin juyowa tamkar yana gabanta, ta ce, "Ba ka cancanci halaccin nan ba Ya Imran, ka so ni, kana sona, soyayyarka daban ce. Ta bambanta da ta kowa don me na maka haka? Me yasa?" Hawaye suka zubo mata na bakin ciki. Ganin tahowar Aunty Luba ya sa ta yi saurin juyawa da gogewa. Ya zama dole ta koma gurinsa ta ba shi hakuri, ba za ta iya fushi da shi ba, don haka ta juya tare da tunkarar dakinsa. Suka ci karò da Auntyn har ta wuce idonta a rufe ba ta ko ganin hanya, ta jawo ta ta dawo ta baya. Ta tsura mata ido tana kallo, sai can ta ce, "Me ke damunki idonki ya rufe ko?" 144 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta dauke kai lokacin da hawayen da ta ke makalewa suna shirin zubowa, ta sake cewa, "Lafiyarki kuwa ina miki magana?" Ta juyo a marairaice ta ce, "Please Aunty kar ki tsayar da ni, gurin Ya Imran zan je". Та сe, "Ya Imran kuma, ba yanzu na kira ki ba daga gurinsa kin je ma gurin bakin ko ko, kin nace gurinsa?" Ta ce, "Ban je ba, amma ki bari na koma gurinsa ina zuwa". Daga haka ta wuce da sauri ta barta sake da baki tana kallonta. Sai da ta ga shigarta sannan ta jinjina kai, ta ce, "Turkashi! Kuna da abin kallo". Yana nan dai zaune makale da 'yarsa jikinsa yana kallo, ya ga ta shigo ta ja ta tsaya bakin kofar tana kallonsa. Nan da nan kwalla ta ciko idonta taf, ta kasa motsi sai dai kallon da ta ke masa, sonsa na kara karuwa a ranta. Ya nutsu yana kallon yanayinta, ya ce, "Mene ne?" Shiru ba magana. Ya aje 'yar tare da mikewa yanayinsa ya sauya, ya sake cewa, "Lafiya kuwa, me ya same ki?" A hankali ta fara takowa ta kasa dauke idonta a kansa, shi kuma ya yi tsaye yana kallonta bar ta karaso. 145 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Gaf da shi ta tsaya idanunta na kara cikowa da hawayc, ya dafa kafadunta cikin kulawa, ya ce, "Fada min mene ne?" Bakinta ya fara rawa, tana son cewa wani abu kukan da yake kokarin zubowa ya hana ta. Ya sake cewa a dan rikice, "Why Mabaruka, tell me woo. Kukan ya kufce mata, taffada jikinsa tana kukan mai sauti. Ya sa hannuwansaya rike ta sosai yana lallashinta, ta kasa barin kukan sai kara karuwa yake. Ya yi kokarin dago ta, amma ta rike shi gam. Ya sa hannu yana shafa bayanta, tare da cewa, "Is ok, is ok Mabaruka, please stop cry am with you. Ba ta fasa ba ta ci gaba da kukan. Ya dago ta tare da tsura mata ido, ya ce, "Kin ganki kuwa?" Cikin kukan ta girgiza kai alamar a'a. Ya ce, "Ban taba ganin mummuna ba irinki tamkar biranya, kin ga yanda ki ke?" Ya kwabe fuska gwanin tsoro yana nuna mata. Ba ta san sanda dariya ta kufce mata ba, a fada jikinsa. Shi ma ya yi dariyar ya ce, "Is ok Ya Imran dinki ne mai ya rage kuma?" Ya ja ta suka zauna bakin gadon tana dai jikinsa, ya ce, "Fada min wa ya sa min ke kuka?" Ta marairaice fuska tana kallonsa, ta ce, "Ni kaina na ba kaina haushi". Ya zaro ido ya ce, "Saboda me?" 146 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta ce, "Gajen hakurina mana, na manta waye kai da soyayyarka har na runtse ido na gaya maka magana son raina tun bayan idonka don shirmena. Tambayar ni mana don me na aikata haka?" Ta langwabe kai tana kallonsa. Abin dariya ya ba shi, ya ce, "Ya isa kowa ma zai yi haka ba ke kadai ba, ke ya kamata ki sani kan kowa". Та се, "А'a kar ka ce haka, ka yi haka ne don kana sona, soyayyata ce ta sa haka, ni kuma na maka יי butulci, na... Ya yi saurin sa yatsansa kan la66anta tare da cewa, "Shisssh! Kar ki sake cewa haka, ba ki laifi ba. Yes ina sonki hakan ne ya sa na zabi sunanki tunda na samu copynki ai sai na sa sunanki na kara tabbatarwa kaina yes you are my own'. Dadi ya kamata, ta ce tana kallonsa, "Ni ma ina sonka Ya Imran, ba zan daina sonka ba har abada, har bayan raina kai kadai nake so, I am really love you. Ya kai bakinsa kan nata yana ba ta wani sako. "Rufe idonku!" *** *** Ranar sunan Little Mabaru ku zo ku ga yanda ake wadaka da abinci, kaji bankararru sai tafiya suke da kafafunsu. Gida makil da jama'a don ma akwai yalwa, masu hotuna da bidiyo sai haska su suke. Ku zo ku ga mai jego, wayyo! Masha Allah! Abin da kowa ke cewa 147 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna kenan, ta sha lasa-lasai ubansun da manyan atamfofi, shaddoji ko ba a magana an zuba mata surfani, sai walainiya ta ke cikin gwalagwalai zobba da awarwaro. Tabbas Imran na son Mabaruka duniya ta shaida, haka masu karatu sun shaida don ya fito da ita da dukiyarsa, ya cancade ta. Hakà zalika 'yarsa Little Mabaruka ta sha kwalliya da irin kayanta manya masu tsada da daukar ido, duk wanda ya dauke ta kamar kar ya aje. Ta ci sunan mamanta saboda soyayyar Babanta ga mamanta. Shi kanshi ku zo ku ganshi. Abin ba ya kwatantuwa naira ta yi kuka, duk inda ya yi ana cewa, jarumin Mabaruka, Baban Mabaruka. Tabbas ya burge kowa. Kowa ya tafi da sam-barka, jakarsa dam da kayan suna aka bar Little da iyayenta suka sa ta gaba, wannan ya dauka, wannan ya aje. Ikon Allah aka ce a tafi da ita gida ta huta ko ya ya ne, sai ta sa kuka ta fadi kasa tana rokon ita a barta don Allah, a nan ma za ta huta tunda ga Umma nan, bare shi gogan fada ya kama, wai don me ake son fauke min mata ina sonta fa sai na zauna ni kadai, ta je can ta yi me? Tunda ta haihu lafiya to a bar min abata". Simi-simi aka daye aka barsu, ba wanda ya sake tada zancen. 148 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Sai da ya dauke hutun sati biyu gurin aiki, shi ma da ya cika da kyar da kyar ya koma ya tafi da kewar Mabarukarsa da Little. Haka abubuwa suka ci gaba da tafiya, Mabaruka na rainon 'yarta sun yi kyau sosai da kiba, sumulmul abinsu. Kamarsu kuwa kullum kara fitowa ta ke, har abin ya koma ba mutane mamaki, sak! Mabaruka ba maraba. Lokacin da ta fara zama idan tana wasa ko tana dariya abin har kada Momy yake, ta kan ce, "Wallahi da dariyar da kukanta duk na mamanta ne, ita gani ta ke ma tamkar Mabarukar ce ta dawo yarinya. Shi kam gogan hakan wani farin ciki yake sa shi da karuwar śoyayyarsu, mai kama da Mabarukarsa sak! Tana da wata shida Nafisa matar Sulaiman ta haihu, ta samu 'yarta mace. Komai ya wuce don haka Mabaruka kullum tana can sai yamma ta dawo gida har ranar suna. Ita da inna ko abin kamar a mafarki sai su wuni suna hira, Little Mabaru na hannunta. Ranar suna tana shigowa tun kan ta shigo dakin suan da ta ji yara na fada na yarinyar ya kidima ta, Samira ta tare ta da murna ta dauki Little da ke wasa a hannunta an mata kwalliya da riga da siket short, pink colour an sa mata socks da takalma cover. Gashinta kuma an mata kitso kanana, an sa mata beat yarinyar mai fara'a ba kwiya akwai son wasa. Sai zuba kamshi ta ke na turaukanta. 149 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta dubi Samirar cikin wani yanayi, ta ce, "Da gaske sunan yarinyar Mabaruka?" Ta yi dariya ta cc, "Sosai, kin yi mamaki ne?" Kada kai ta yi alamar aja a sanyayc, samirar ta wuce da Little hannunta, yara suka bi ta yuu don Allah ta ba su ita, yayin da ita kuma sai wangale musu baki ta ke tana dariya, gani ta ke abin wasa ne. ko ba komai ta biyo mahaifinta fara'a, son mutane gabadaya halinsa ne kamar kuma na mamanta. Ta shiga dakin Nafeen ta sha kwalliyar suna ta zauna bakin gadon tana kallonta, ta ce, "Wai sunanta Mabaruka?" Murmushi ta yi ta ce, "Ba gaisuwa abin da ya dame ki kenan?" Ta ce, "Ina mamaki ne me ya sa Sulaiman zai sa sunana?" Ta ce, "Saboda yana sonki har gobe, ba don za ki dawo masa ba sai don kawai son daga Allah ne. Ni ma na karfafa masa gwiwa saboda matsayinki gurina, ke се sanadin dawowata gidan nan, ga shi har na haife ta, me zai sa ki yi mamaki to don mun sa sunanki?"" Kwalla ta ciko idonta, ta ce, "Haka ne, na gode Yaya Nafee, Allah raya mana takwara ta". Mutanen dakin suka bi ta da kallo suka ce, "Da man wannan ce mai sunan?" Nafeen ta ba su amsa, "Ita ce kuwa". 150 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Jinjina kai kurum suka yi ba magana saboda naira da suka gani jikinta, uwa-uba kyau wanda ya sake nuna ta. A gaida 'yar gidan Y a Imran Baban Littlc. Ba da dadewa ba iţa ma Rafi'atu ta sunkuto da nata dan, hula tsakanin dankwali. Abin da kowa ke cewa ya aka yi ya yarda matan suka riga shi zuwa? Kam Mabaruka ta rungume shi, soyayyarsa na shigarta, yau ga dan Rafi'a a hannunta, me zai sa ba za ta so shi ba? Ya ci sunan Alhajin su Dr. Faruk Usman, don haka suka nada masa Ameer. Ba ta huta ba, kullum tana zarya gidan Rafi'ar, har sai da aka gama suna. Da rana da su Momý suka zo da Sharifa ita ma ta zo tun bayan kammala karatunta, don haka Little ta makale musu har da kuka da za su tafi, dole suka tafi da ita tana rungume jikin Sharifa. Ranar asabar ne Imran yana gari, don haka sai can dare ya zo daukarta. Ta fito da tarkacen kayansu ita da Little ta zuba a mota, lokacin yana waya hankalinsa na kau wayar har ta gama ta shiga ya ja suka efi. Har suka shigo harabar gidan sannan ya gama, ya gama yin parking ya juyo yana kallonta lokacin da ta ke kokarin fita. Cak! Ya ja ya tsaya tare da sakin baki ya bi cinyarta da kallo, bai ga Little ba ya kalli bayanta, nan ma. Ya juya da sauri baya ko tana baya. Ya juyo da sauri zai mata magana ya ga ta fice. A gaggauce ya fito tare da 151 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna rufa mata baya. A falo ya cimmata ya juyo da ita da karfi yana cewa, "Ina Littic?" Ta yi taga-taga za ta fadi, ya tarbe ta tare da kura. mata ido, ta ce, "Shi ne za ka kada ni don ba ka ganta ba?" Ya ce, "Sorry, amma tana ina?" Ta ce cikin ko'in kula, "Na baro ta gurin Rafi'atu" Ya rike baki a tsorace da zaro ido, ya ce, "Kut..." Maganar ta koma masa ganin yanda ta zaro ido tana kallonsa, ta ce, "Zagi kuma Ya Imran?" Ya canza maganar da cewa a zafafe, "Kin baro ta gurin Rafi'atu ta yi musu me? Ni na kwana haka babu ita?" Ta ce a marairaice, "Haba my Imran, kwana daya fa kadai, Rafi'ar ta nuna tana so a bar mata don Allah sai na hana ta?" Ya ce, "Yes". Yana zaro mata ido tamkar zai dake ta, "Ba zan iya bacci ba sai da 'yata, ban yarda ta rabu da jikina ba, ba zan taba bari ta kwana a veni wuri ba, ki zo mu koma mu dauko ta?" Ta ce da sauri, "Ina? Gurin Rafi'ar?" Ya yi kicin-kicin da rai, "Eh ko ma ina ne dauko yata zan yi, don me ki ka barta bayan kin san ba zan iya ba?" 152 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta ce, "Rafi'atu fa na ce ba wata ba, yanzu har za mu iya wa Rafi'a haka? Ka manta halaccinta a gurinmu da soyayyarta?" Ya fada cikin tabbaci, "Ko ma wace ce na fada miki wallahi sai na dauko 'yata, ki zo mu je". Ta juya za ta shige daki tana cewa, "To ba da ni ba, kai ka je ba zan iya ba". Cak ta ji ya kamo ta tare da janta. Ta hau tirjewa da kwakule hannunta daga nashi, ko motsi hannunsa bai yi ba bare ta iya kwacewa. Ransa ya gama baci har huci yake, idonsa ya rufe shi dai 'yarsa kawai, ikon Allah. Ya tura ta mota tare da zagayawa ya shiga ya ba ta wuta tare da janta da karfi suka wuce. Ta ce tana kallonsa, "Ikon Allah, tafi da mu a hankali ba bacewa za ta yi ba". Bai saurare ta ba ya ci gaba da tukinsa. Sai da ta ga sun kusa gidan sannan ta ce, "Na manta ba gidan Rafi'a ba ne, Momy ne suka tafi da ita". Ya ci uban birkin da bai yi niyya ba, ya ja ya tsaya cak! Tare da kallonta. Ta dauke kai tare da hade rai. Ya ce, "Wai me ke damunki, lafiya ki ke?" Ta ce, "Oho". Kanta a window. Ya jinjina kai tarc da cewa, "Ok za ki sani". Daga haka ya juya a fusace ya tunkari gidan Momy, ta bi shi 153 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna da kallo ta sa zai hakura, ta cc, "Au ba za ka barta ba har gurin Momy haka za ka ce a ba ka 'yar?" Kansa na kan titi cikin masifa ya cc, "Ko ma wane gida ne dauko 'yata zan yi". Ba ta ce komai ba ta dauke kai ita ma. Ita kuma lokacin Momy tana ta jaje da fada cewa ta ke, amma yarinyar nan akwai mara hankali, cowa nake ta biyo ta tafi da ita in za ta tafi gida, ina ga wucewarta ta yı. Yarinya mai shan Mama yaushe za ta kwana wani guri?" Rufe bakinta kenan ta gansu a hargitse, bare shi ya sha kunu ya ce wa Momyn, "Ina Little". Ta bi shi da kallo, ta ce, "Hala da ba ta yi niyyar zuwa daukarta ba?" "Eh". Kawai ya ce a takaice. Ta ce, "Allah shirya ki Mabaruka, to ga ta can gurin Antynta har sun kwanta ita atafau in barta ta kwana, wai Mabarukar ta ce mata cikin dare ba ta neman Mama". Fit! Ya wuce zuwa dakin Sharfar. Suna kwance tsakiyar gadon sun rungume juna, bacci ya fara daukarsu ta ji ya sa hannu ya zare 'yarsa. Ta tashi cikin bacci, ta ce, "Please Bigbro ka bar min ita mu kwana tare, ka ga har mun yi baссi". Ya watso mata harara tarc da rike 'yarsa gam wacce ta ke bacci, ya ce, "Gwanda ki ce ni na kwana a nan a kan na bar miki ita". 154 WAYE ANGUON?-4 Daga haka ya wuce a fusace. Maryam Jafar Kaduna Ba ta taba ganin fushinsa ba irin yau, duk kan 'yarsa. Ta saki baki har ya fice, ta ce, "Cab! Lallai Little har ta fi ni kenan?" Ko sallama bai yi wa Momy ba ya fice ya barsu tsaye ita da Mabarukar da ta ke turo baki. Momy ta kalle ta ta ce, "Kin ga daga yau kar ki sake bar masa 'ya wani gu in ba iaka ba za ki ja mana har ni, ki duba ki ga fuskarsa ba haka yake ba, amma kan 'yarsa ya birkice ba ta ce komai ba". Ta juya ta fice tana turo baki. Momy ta bi ta da kallo tana cewa, "Haka ita ma 'yarki ta ke ta yo gadonki, tun kina yarinya ki ke da dabi'ar turo baki, ga ta nan ita ma in an mata laifi ta turo baki tana fushi, ku ku ka sani kar ku sake kawo min ita nan". A mota ya sha fama da ita atafau ba za ta dauke ta ba. Ta yi fushi ya je yai ta riko shi mai diya, shi kuma so yake ta rike ta ya yi tukin. Ya tsgunna gabanta tare da cewa, "Please my Mabaru, am very sorry, ba zan sake ba. Wallahi soyayyarki ce ta sa min haka, don ina sonki da yawa ya sa nake son takwararki, har ba na iya hakuri da rashinta". Ta turo baki tana cewa, "Ni ina ruwana? Ka rike kayanka bana so, na bar maka". 155 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ya yi dariya ya ce, "Dole sai da ke gwanda na rasa ta a kan na rasa ki, you know, am rcally really love you Mabaruka". Ya fada kwalla na taruwa a idonsa. Tsakanin mata da miji sai Allah, tausayinsa ya kamata wani sabon sonshi ya rinjaye ta, ita ma kwalla ta taru idonta. Ta sani duk saboda ita ne yake son 'yarta, Imran mutum ne cikakke har da rabi, yana sonta fiye da kansa, shin me zai sa za ta yi fushi da kayanta? Ba ta san sanda ta jawo shi ba, ya fado jikinta ta rungume shi kyam tare da cewa, "Love you too my Imran, you are my world'. Ya rike ta sosai, soyayyarta na kara zafi a ransa fiye da na 'yarsa Little. Abubuwa sun ta tafiya, soyayya kullum karuwa ta ke da 'yarsu da suke ji da ita kamar ransu ba ma su kadai ba, kowa ma. Soyayyar Little ta darsu a zuciyar Momy kamar me, in suka je wuni kamar kar ta barsu su

Chapter 9 of 10