Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 10
ita za ta nemi maida auran. Na ji dadi sosai da abin da uwar ta yi ta koro ta gwanda ta dawo nan din ta tantance rayuwa ba kamar can ba. Ina fatan ka fahimce ni?" Ya daga kai alamar gamsuwa. WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ya ci gaba, "To za ta so komawa dakinta, ka ga in ta koma din za a samu abin da ake so ta zauna idan ta tuna zaman da ta yi a gidan nasu". Tabbas ya gamsu da maganarsa, hakan na iya yiwuwa. Amma yanda Mabaruka ta tsane shi anya akwai ranar da za ta so zaman gidanshi, za ta so shi har gidanshi ya fi gidansu? Baban ya fahimci kamar bai gamsu ba, ya ce, "Kada ka damu yaro an yi haka ba sau daya ba, ba sau biyu ba. Matsa mata da za a yi ba zai ba da ma'anar abin da ake so ba, ka bar ni da ita zan yi maganinta. Idanuna za su tsaya kanta, da kaina zan sake daura maka auranta tana farin ciki na fada maka, insha Allahu'. Sosai ya ji dadin zancen har ya samu nutsuwa. Ya yarda da Baban dattijon arziki ne, ya ce, "Shi kenan Baba zan je ni ma in dage da addu'a Allah ya taimaka mana". Ya ce, "Amin. Amin yaro, babban abin da za ka yi kenan. Ni ma zan yi nawa, za ka gani insha Allahu”. Yana murna ya ce, "Allah sa Baba, Allah kara girma". Haka dai suka bar zancen ya masa alkhairi, amma sam Dattijon ya ki karba, dele ya kyale shi suka rabu ya shige motarsa. Yana kallon Baban Mabarukar yana ta dana yara a motar, ya jinjina kai. Inna Binto ko da aka zo mata da labarin motar, ai sai rawa lana juyi kudi sun zo, fada ya kare yau Mabaruka ta huce musu takaicin rashin sana'a sai la yayimi zani sai waje don duba sabuwar motarsu, har da d'ani. 18 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Daidai fitowar Mabaruka daga bayi rike da buta tana fama da atini, gefe kuma duk ta fada, ta yi zuru-zuru iamkar mai azumi. Та се, "Кan uba! Mota? Ka ji dan rainin wayau, dan ubansa cewa muka yiba mu da abin sana'a da zai kawo mana motar haya, wato mu ci abinci ko?" Ta yayimi hijabi ta fita tana bala'I, "To wallahi ba ka isa ba, sai dai ka juya da ita dan rainin wayau". Ta fice sai dai akasin da aka samu tana fita yana jan motar ta kalli motar; ta kalle su yanda suke rawar jikin motar. Ta ja tsaki tare da hararar motar ta ce, Dan iska". Tare da shigewa gida. Ai a ranar bai jira ba ya shiga gari yana cewa Inna Binto, "Ki je ki wanke tukunya kan rana ta yi zafi. zan dawo". Ta yi guda tare da cewa, "Allah tsare ka, Allah dawo da kai lafiya, a samo da yawa". Ya ce, "Amin". Ya ja cike da farin ciki, ai tun kan ya bar unguwarsu ya fara samun. fasinja, har ba wurin sa wasu. Kan ya dawo ta yayimi gyale, farin cikinta bai misaltuwa sai gida gurin Inna. A kofar gida ta hadu da Sulaiman, ta yi guda tare da shewa ta ce, "Albishirinka?" Ya dube ta, ya ce, "Mene ne haka? Sai ihu ki ke saman titi, mene ne ya faru?" Та сс, "Кai dai albishirinka?" Ya ce, "Goro". 19 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta ce, "To Mabaruka ta lito, mijinta ya sake ta". Ya dube ta sake da baki cike da mamaki, ya ce, "Wacce Mabarukar, tawa?" Ta ce, "Taka ko, yau kwananta hudu a gida, yau tunda safe kuma sai ga dalleliyar mota ta kabu-kabu an kawo wa Malam daga mijinta. Ta kaso auran ita lallai kai ta ke so Wani tsalle ya yi tare da fasa ihu tamkar zararre, har da taka rawa, ya cc, "Allah Binto?" Ta ce, "Alkur'an da gaske nake, ka je ka gani, ita lallai sai kai". Ya dinga juyi tamkar zai hau bori, sai da ya nutsu sannan ya dube ta, уa сс, "То bakinki alaikum mu bar maganar nan kar ki sake Inna ta ji zancen nan, sai dai ta ga ana shigowa da amarya". Ta dube shi galala, ta ce, "Kamar ya? Kana nufin ba za ta sani ba?" Ya ce, "Sosai, kin manta yanda aka yi da ita wancan karon? Na santa sarai za ta iya min bakin ciki, sam ba zan sanar mata ba". Ta ce, "Anya ba na zaton haka, saboda ko wancan karon da na sa ta hanya ta gane amfanin abin ina da tabbacin ba za ta ki ba wannan karon". Ya ce, "Oh Binto, na fada miki na fi ki sanin halin Inna, wallahi tamkar birkitatta ce tana iya cewa ina! Ba ta yarda ba, musamman yanda ta ga hankalina yake kan Mabarukar da ma sai' da ta dinga amso min rubutu sannan na dangana, yanzu ga Nafisa nan ta korar min, Ja ga na 20 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna nutsu da ita, ita ma tunda na rasa Mabarukar ta shiga ta fice ta raba ni da matata. To yanzu dama ce ta same ni, da ma ba ni da mata, zan auro Mabaruka sannan in dawo da matata Та се, "Нaka ne kam, na goyi bayanka na yi gum!" Ya ce, "Yauwa, kin ga ni ko mahakurci nawadaci, ga shi nan Allah ya ga zuciyata ya dawo min da 1ta. Ya san ba ni da hakki cutata aka yi, aka nuna min karfin mulkin kudi, ga shi nan za ta dawo hannuna. Allali na gode maKa, yau ina cikin farin ciki har.sadaka sai na yi": Та се, "Ai ko ni ma ina taya ka, ai ina son Mabaryka gwanda ta dawo hannunmu". Ya ce, "Bari ki gani, ai ba zama zan yi ba". Sai ya kwasa da gudu dafe da hula. Ta shigo cikin gidan daidai Inna na cizgar fada da yara, ta shigo tana cewa, "Laſiya tun daga zaure ana jiyo harshenku?" Та се, "Bar ni da su in ci mutuncinsu tun shekaran jiya waccan suka ze suka sayi koko, sai suka bar canjin ashirin ba su zo sun karba ba, ke sai yau wai a bada canjin, ki ji fa rainin wayau da ajiya suka va ni?" Та се, "Кai Inna rigimarki yawa ne da ita, to ba kudinsu bạ ne, don ba su zo sun karba ba sai ya zama laifi? Ke dai tunda ba naki ba ne gurinsu ba shi kenan ba, duk sanda suka shirya sun zo su karba. Nauyi ne ma za ki sauke Ta dawo kanta, "To ba zan bayar ba, sanin kanki ne ba a bar min canji in kana son kudinka ka isaya kı karbа. 21 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna amma in ka nuna min ba ka so sai ni kuma na nuna maka ina so, don haka alkur'an ba zan bayar ba". Ta murtuke fuska, "Kun ji fa karfin hali?) Yaro ya turo baki ya ce, "To ai ta ce in da sauran koko ki zubo mata na ashirin din". Ta ce, "Shi ma ba a bayarwa, daga yau ba za ta sake ba". Ta shige daki abinta. Inna Binto ta dube su, ta ce, "To ku kun ji ba za ta bayar ba, ku yi hakuri da ina da dan canji da na biya, maigidan yau ya fara fita kasuwa” Suka juya suka fice da dan kwanonsu suna gungunai. Innar ta fito tana cewa, "na suke, sun tafi din?" Ta ce, "Sun tafi, amma dai don allah in sun dawo ki ba su kudinsu, alkur'an in ba ki biya a nan ba za ki biya a can Та се, "Ко daya ba zan biya ba, na rantse". Binto ta ce, "To shi kenan, ni dai ba ruwana, kin gan ni na zo da farin cikina in gaya miki Malam an samu sana'a, yau mijin Mabaruka sai ga shi da dalleliyar motar kabu-kabu ya ba shi, ya je ya nemi kudi”. Ta dube ta, "Allah Biniu? Na sanki fa da -shegiyar karya, wa ke iya yin kyauta har haka? Ba na ji an ce kudinta da yawa ba?" Ta harare ta, ta ce, "Lallai to shi an gaya miki matsiyaci ne, mai rowa? Su da kudin yayo su suke". Ta jinjina kai, “Lallai na jinjina masa, kun gode. To na sanki in za ki zo haka ki ke żuwa hannu biyu in na miki magana sai ki ce ina kudin, to yanza miji ya samu abin yi 22 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna ya bar kashe wando, in za ki zo ki dan yo min dage-dagen nan. Ta ce, "Za ki sha ko kin san ni in ina da shi zan yi, ba ni da rowa. Musamman ma na abinci ban sha nono ba" Ta sani sarai da ita ta ke, ta ce, "Za ki ci ubanki yanzun nan, an yi rowar na ji ba ki sha nonon rowa ba, amria dai kin yo gadon tsiya gurin ubanki da mutuwar zuciya". Tsam ta mike tana gyara zani, ba za ta iya zaman fadansu da Inna ba, gwanda ta tafi-ko tukunyar da za tai dage-dagen ta wanke. Ta daga kai tana kallonta, ta ce, "Ko za ki dake ni ne?" Та се, "A'a ban kai wannan matakin ba, amma in dai ana tafiya a haka watarana za a iya jarabta haka". Daga baka ta wuce ta bi ta da kallo, ta ce, "Eh lallai na gani, dote tunda mijinki ya samu sana'a dole ki yi min iskanci za ki sani da ni ki ke zancen". Ta juyo ta kalle ta tare da daga mata kafada, la wuce abinta cikin isa. Baban Mabaruka ko dam ya Jawo da aljihu, ciniki sosai. Sai da ya dangana da kasuwa ya yo cefane ledoji har da kaji ya yo gida jikinsa na rawa. Da guda ta tare shi hannu biyu ta karbi ledojin cewa yake, "Allah ya yi wa Mabaruka albarka da mijinta". Ta ce, "Amin, amin Maiam, dage-dagen za a yi? Ya ce, "Kwarai, a raba biyu rabin a yi farfesu da d'an attarugu, ya yi yaji sosai 23 WAYE ANGON?-4 Ta ce, "An gama Malam Maryam Jafar Kaduna Mabarukar ta fito daga daki fuska a dukunzune tana fushi, ta dube shi, ta ce, "Kai yanzu Baba da gaske ka karbi motar bayan ya sako maka ni?" Ya dube ta galala, ya ce, "Kanbu, amma ke 'yar rainin wayau ce, don ubanki an min kyauta sai in mayar, wato in ci gaba da zama cikin talauci ko? Ke uwarki tana can cikin daula ta canza wannan ta maida wannan tana zaune iska na kadata tana kallon kasashen waje, ni dai da ba ki so in zauna a tsiya? Wallahi Mabaruka sam ba ki Kaunata. Kin fi son uwarki, facaka nawa ki ka yi da kudi kullum sababbi dal! A jaka, amma rana daya ba ki ce bari ki sai min ko mashin ne in dinga haya ko na samar wa Kannenki abinci ba. Shi ne an ba ni ki ke min bakin ciki irin dai na uwarki wanda ki ka sha nono ko?" Ta turo baki tana kumburi, kan me zai dinga zagar mata uwa? Duk sanda ita ta masa laifi in ba yana hake da ita ba. Ya ce, "To wallahi zan ci mutuncinki a gidan nan 'yar bakin ciki, mota na karbe kin ga ni ma daga albarkarta ga kaji can za ai miya, da ke kuma za a shanye ta. Aure kuma ina ruwana yai ta mutuwa tunda kin ce ba ki sonsa kin fito, to ni kam ba zan miki dole ba, da ma ke ce mai zaman, don haka kina gama idda zan aura wa Sulaiman ke, shi ke nan magana ta kare in ce dai shi ki ke so ko?" Ta daga kai alamar ch, ya ce, "To an gama. Ban wuri in wuce. 24 WAYE ANGON?-4 Maryani Jafar Kaduna Татабс уa wuce yana cewa, "Ni dai tunda ya ban abin sana aa ya gama min komai, me ya rage?" Inna na fama da yanka kaji, ta ce, "Babu zance ya Kare". Ko ba komai ranta ya mata dadi tunda ya ce zai aura mata Sulaiman to alhamdu lilla, tabbas tana ji a jikinta ta rabu da Imran kenan har abada, nanatacce kawai za ta je ta yi rayuwarta mai dadi da 'yanci gidan masoyinta Sulaiman, sai dai matsalarta daya fushin Mommynta yana damunta, dole sai ta nemi yafiyarta da amincewarta da auran Sulaiman din, sannan ta lalubo aminiyarta Rafi'a su shirya. Wannan ke nan. BAYAN KWANA ARBA'IN Kadan ya rage ta gama iddarta har zuwa lokacin ba ta samu saukowar Momyn ba, abin yana damunta, yakan hana ta sukuni, ko ya ta ke farin cikin ta bar gidan Imran, shi kanshi imran din ya dauke kafa daf! Tamkar ba a yi shi ba. Yana can yana addu'a duk da har yanzu Mabaruka na ransa, duk bayan second sai ya tuna ia a kullum tamkar ana Kara masa sonta. Jefi-jefi yakan leko Baba Hamza a kasuwarsa su gaisa yana kara ba shi kwarin gwiwa. Yau tana da lecture don haka ta alkawarta wa kanta tana fitowa za ta dangana da gidan Momy kamar yanda ta ke kusan kullum, a yau ta bambanta da sauran żuwan da ta ke, don a yau sai ta baro gidan da yafiyarta. Mamanta ce tana sonta, tana ranta ta tabbata don haka kuka za ta mata 25 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna ba za ta kuma bar gidan ba ko da za ta kore ta, don haka da shirin haka ta fito. Abin ya zame mata biyu, ita kanta Rali`a fushifushi ta ke da ita, sama-sama sukė gaisawa duk da wajen zamansu daya, sai ta kirga maganarta da ita kan su fito school, daga ch, sai a'a. ita ma sai in ita ta tambaye ta, sosai Rafi'a ta yi baya da ita, ta daina sakar mata fuska, wai duk don ta bar gidan Imran, wannan wane irin so suke masa? Rafi'ar da labari gurinsu kamar ba zai kare ba, a da da kyar suke rabuwa, wani lokacin ma sai daya ta bi daya gidansu don su karasa labarinsu, kowa ya sansu ya san kusancinsu, suna ba mutane sha'awa da dama, amma lokaci guda Imran ya shiga tsakaninta da makusantanta wadanda ta fi kowa sonsu, ga Baba Hamza sam ba ya amsa gaisuwarta fushi yake da ita sosai. Ta ja tsaki cike da jin haushin Imran din, tsanarsa na kara karuwa a ranta, ta furta, "Allah ya isa". A fili, yayin da idanunta suka yi kwalkwal har mai adaidaita sahun da ya dauko ta ya juyo ta yi saurin dauke kanta zuwa gefe don ma kar ya lambaye ta dalili. Ta dawo da kudi sosai gida, amma saboda makarantarta 'yan hidimomin abin hawa duk sun kare, sannan in ta dawo gidan ta tarar an yi abincin da bai mata ba, musamman ma Inna Binto ba wani gogewa ta yi da girke-girke ba. Ita ko ta saba cin abinci kala-kala mai dadi, wanda an kashe masa kudade, amma wannan a yi dai en wai nan ma an yo cefane kenan, don haka ta gwammace ta bada a siyo mata ko indomie ce da kwai ko kayan tea. Duk a haka ta karar da kudin, 26 こ WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna yanzun ne da ba ta da su in za ta tafi makaranta Baban ke ba ta naira dari kullum. Sosai yana ganin kokarinsa har naira dari kullum? Don haka ta fara gane kurenta, sai dai in za ta je ta hau adaidaita sahu naira saba'in ba maganar shan cock ko Maltina da ta ke a makaranta, wannan ka'ida ne kafin a tashi ta sha robobi in ta ji yunwa ne sosai ta ci chiefs. Abincinsu kenan ita da Rafi'a, to yanzu ba kudi sai dai ta dinga hade miyau in wasu na sha, ga rashin koshi da ba ta ji ba ta fito haka nan ta ke shan kokon Inna ta hada da alalar ashirin ta fito, har ta koma ba za ta sake cin komai ba, ko za ta kai yamma. Sai in za ta dawo ta hawo bus naira talatin a sauke ta bakin titi can-can nesa da gidansu, sai dai ta tako a kasa, ga rana ga yunwa hade da gajiya. Hakan ya sa duk ta yi baki ta fada zuru-zuru sai dogon hanci kamar an dasa shi, fuskar ta rage kumari da dan taushi-taushin nan, wanka ta koma da sabulun wanka dan ashirin bare a zo ga wanki, sai ga ta da durkuso tana wanki da kyar da kyar a ta gama dafe da kugu, tunda ta ke rayuwarta sai dai ta wanke under wear dinta ta koma ta kwanta tana canza channel gefe ga drinks mai sanyi tana kurbawa. Shara, wanke-wanken Inna da Fan karan wanki duk ya koma kanta. Ta ci wuya da rana, da dare ta kasa bacci saboda sauro ga dankaren zafi, gefe kuma zarnin fitsarin kannenta da tusoshinsu mai kumbura ciki. A haka ta ke bacci mawuyaci, sai ga ta da gyangyadi a school ana tsaka da lecture, ta sha iskan fanka. Gefe kuma Baban da ya shigo korafinshi duk ita ke cin kudinsa, a ce kullum sai ya ba ta har naira dari ga na siyen alalarta naira ashirin, gefe 27 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna ga omo da sabulun wankinta, shin karatun ma dole ne, ba za ta bari ba? Ta kan shiga daki ta ci kuka ba wacce ta ke tunawa ssai Momynta, rana daya ba ta taba gajiyawa da ita ba. In za ta je school kullum sai ta ba ta dari biyar kawai don shan coca cola dinta da ta sanda shi ba don lalurar makaranta ba, ko shan mai ga motarta nan na jira an wanke an goge dal tana dalle ido, idan ko Daddy ne zai mata sallama dubu uku ec zir! Wai ko da wani abu ya taso a kullum kenan. Bayan hidimar makaranta yana yi tun tana nursery, sannan duk wata sai ya aje mata dubu ashirin saboda bukatuwarta a matsayinta na 'ya mace, bayan haka nan ma sai ya ba ta dubu biyar ko goma wai ta sai cakulet, sutura ko sai dai ya dauke ta a mota in yana da lokaci ta yo shopping kowane ta ke so, mai tsada. Zuwa yanzu ga kayan nan duk sun dafe don ba ta iya wanke su su fita. Haka Mommyn kullum da abin da za ta kawo mata, kyalkyal ne ko ko na ci ne, har tambayarta ta ke, ba abin da ta ke bukata ko na makaranta? Rana daya ba ta taba gajiya da ita ba duk da wasu ba hakkinta ba ne na ubanta ne, amma shi don yana ba ta naira dari jal ba ma isarta suke ba, haka nan ta ke jalaulautawa har sai ta hada da Allah ake daukarta, amma gani yake duk ta takure masa, bayan kudin da yake samowa a sanadin motar da aka kawo masa duk sanadinta yakan samo sama da dubu biyar a rana, musamman akwai shi da naci sai ya kai sha daya na dare bai dawo ba, ga shi ba raina fasinja yake ba, ko kudin da za 28 WAYE ANGON?-4 a Maryam Jafar Kaduna ba shi ba su kai sun kawo ba shi dai kar ciniki ya wuce shi, amma yana ganin naira dari ta tsaya masa a rai. Ta sa hijabin jikinta ta goge hawaye tare da cewa, "Allah ka yafe min, ka sa mahaifiyata ta saurare ni ko na samu saukin masifar da nake ciki". Ta dubi kafarta har ta fara kaushi, ga kanta duk ya dankare ya karairaye saboda arshin saloon din da aka sabar masa akai-akai. Bayan sun iso ta fito da kyar ta karaso class saboda azabar ciwon kan da ke damunta na rashin bacci, ga kokekoke. Rafi'atu ta riga ta zuwa don har an fara lecture, ta sani in dai an riga shiga in dai uncle Tukur ne to dole ka !saya waje sai ya ſito, don haka ba ta ma nemi ya yi hakuri ba ta ja baranda ta rakube, hawaye na on zubowa in ta tuno yanda ta ke żuwa da wuri har maigadin da ke bude musu classes ta kan riga shi zuwa, don haka key din class dinsu ya komä hannunta. Duk wani lecturer yà santa da kokari, a nan za a same ta ta kwakkwafe wa books cinta, ita ce ta farko a class din, haka tunda ta zo makarantar har tana shekarar karshe a digirinta ba ta taba samun carry over ba ko test ba ta taba faduwa ba bare a ce ta yi missing dinta, haka assignment amma a yanzu ta kai kan ta iso wani lokacin an gama test ko summiting assignment, saboda in dai ta ce tun a cikin unguwarsu za ta hau adaidaita sai dari amıma, in ta tako zuwa titi sun dauke ta saba in da rokonta kamar la musu kuka. To kan ta iso titin sai ta ci minti ashirin, shi ko Baban tunda asuba ya fice ba ta ma tarar da shi bare ya rage mata hanya. Ilawayen suka ci gaba da 29 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna zuba, Uncle Tukur ganta sosai ya yi mamakin canzawarta test da ašsigment dinsa duk ba ta yi ba zai yi sammako ya yi saboda 'yan latti to duk ba ta a ciki, sabanin da ko ma dai mene ne akwai dalili, ya bar wa kansa. Don haka ya leko ya kira ta. Ta yi saurin goge hawayen, ya ce, ta shigo kawai. Ta masa godiya ta shige da sauri, ta zauna scat dinsu ita da Rafi'a. ta dube ta, ta ce, "Ashe kin zo?" "Um!" Kawai ta ce, tare da maida kanta zuwa window saboda tausayi da ta ke ba ta in har ta kalle ta za ta iya mata kuka. Ba ta ce komai ba sai ta rausayar da kai tare da dauke kanta zuwa jakarta tana lalubo handout idanunta na shirin sake zubo da hawayen na tausayin kanta, ganin yanda Rafi'a ta sauya mata sosai. Har aka gama lecture magana ba ta hada ta da ita ba, sai lokacin da suka samu dan hutu duk aka fita zuwa capteria. Rafi'a ta mike tana cewa, "Matsa na wuce". Ba ta ce komai ba ta rabe ta wuce abinta. Ta yi zaune jugum, yunwa na kwakwalarta, ta san ba ta da ko biyar bare ta iya fita ita ma, sai ta kalli can ta kalli can kwalla na taruwa a idonta. Ta kalli hijabin jikinta duk ta yi yaushi ba wankin kirki bare maganar guga, tuni ta aje gyaluluwa a ganinta ba kwalliya jiki duk rame me za ta sa wa gyale ai mata dariya, ta gwammace ta zura hijabi. Can bayan an daddawo sannan Rafi'ar ta dawo, kan desk ta dire mata robar cock kamar yanda ta sani lana 30 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna sonta. 31 Kallonta ba ta yi ba ta zauna tare da cewa, "Ga shi nan Ta kalli cock din ta kalli Rafi'ar, tabbas tana bukatarta kwananta nawa rabon da ta sha? Tana wkadayinta amma yanda aka mata kyautar ya sa ta fitar mata a rai tamkar ta roka ita da ta ke kusan sayen katan tana rabarwa duk kawayensu, yau ita ce a ke ba a dangware? Ta share hawayen tare da duban Rafi'ar ta ce, "Ban cancanci haka ba Rafi'a, ba Cock nake bukata ba, fuskarki nake so da dariyarki na fi bukatar hakan. Amma Rafi'a duk kin canza min, kin dauke min fara'arki da tausayinki, kin manta ni Mabarukarki aminiyarki, komai na yi ya kamata ki min haka ko kowa ya ki tausaya min ya kamaia ke ki tausaya min, in kin luna soyayyar da ke tsakaninmu. Kar ki manta haka, dubar ni fa, dubi yanda na dawo na lalace na rame, duk sanadin fushinku ke da Momy Ta fashe da kuka, "Wallahi ina bukatarki Rali’a, ina son kulawarki". Ta dora kanta saman kafadar Rafi'ar tana ci gaba da kukan. Tun sanda ta fara maganar Rafi'ar ke kuka, kukan tausayin aminiyarta har ta gagara rike kukan ta fara yi da sauti. Ba Mabarukar ba ita kanta tana bukatarta kusa da ita, ba ta saba da rashinta ba. Ta juyo cike da kukan ta rungume ta Kam tare da cewa, "Ni ma ina sonki, wallahi ina bukatarki kusa da ni Suka rungume juna tare da kukan. 31 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Esawon lokaci ta daga ta tana share mata, liawayen ya isa haka nan Mabaruka, kar kanki yai miki CIWO Ta dube ta da jajayen idanunta, ta ce, "In ba ki son kaina yai ciwo me ya sa ki ka min haka, kin daina damuwa da ai ko?" Ta kamo hannuwanta cikin kulawa ta ce, "Ko kadan kuilum kina raina, ya ki ke, me ki ke yanzu? Abin da ki ka yi ne Mabaruka ban ji dadinsa ba, Imran ya wuce ki masa haka idan ki ka tuno halaccinsa gare ki ko ba ki sonsa kin zauna ko don haka, in ba ki wa Momy biyayya ba. lyayс daraja gare su da girma Mabaruka, ban taba tunanin za ki ki abin da Momy ke so ba har ki fito gidanki duka yaushe ki ka je, kwananki nawa? Kin manta irin wahalhalun da aka sha kafin auran? Ta tsayu a kanki ta dage ba ta huta ba duk don ta kai ki gidan da ba za ki da kin sanin zuwansa ba. Bayan kin je din zagi, rashin tarbiyya, gallazawa da danne hakki ba abin da ba ki ba. Momy ta fada min komai, ki duba irin zagi na rashin tarbiyya da ki ka dinga masa tun daga Mamansa wacce ba ta da rai a halin yanzu, har zuwa gurin Babansa wanda ya miki abin d.. ita kanta Momyn ba ta miki ba, ke ma ba za ki iya wa kanki ba. Ya dago rayuwarki, ya so ki, ya gatanta ki, ya ba ki duk jin dadin rayuwa bayan ya hada ki da `ya'yansa bai bambance ba, amma ki ka zage tas! Kan lallai sai an sake kı, haba Mabaruka ina tarbiyyar da Momy ta dade tana ba kı, kin watsar duk don an daura miki Imran wanda bar yau ban ga 35 3 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna aibunsa ba, ban ga abin kinsa ba, me ya sa haka? Me ya sa? Ko yana da wani aibu?" "A'a". Ta girgiza kai da sauri tana kuka tare da cewa, Та сс, "Тo don me ki ka ki zaman gidansa? Don kin fi son zabin zuciyarki a kan na Momyn?" Nan ma ta girgiza kai, "A'a". Та се, "Don ki bata masa, ki bata mata ko Mabaruka?" Ta kara fashewa da kuka, ta ce, "A'a na tuba Rafi'a, na yi nadama wallahi na yarda zan koma gidansa duk da ba na sonsa ko da zan

Chapter 2 of 10