Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 10
sai na koma na ci gaba da zawarci, ba lallai kuma na kirki ya zo ya aure ni ba, wani ma in ya ji aurena biyu shekaruna kuma kwana na daya gidan mijin, ba zai yarda ya aure ni ba, don duk me za a ce ni za a ga ban kyauta ba, ni ke da laifi". Ta ce, "Haba! Haba ba ma fata ma, insha Allah ba inda za ki, kina nan gidan Sulaiman tunda yana sonki, ba zan yarda ya yi sakin ba”. Ta dube ta, "Mata nawa ya saka kafin ni, kuma yana sonsu? Ta kasa cewa komai, ta bi ta da ido, haka suka wuni tare, Rafi'ar na kokarin kwantar mata da hankali. Yayin da Sulaiman tun fitarsa bai dawo ba, ya yi nesa da gidan, ya yi wa kansa alkawarin sai dare zai dawo sannan ya san Innar ta yi bacci. Haka kuwa aka yi, goma ta wuce sannan yà shigo gidan. Ya maida kofar gidan ya rufe da sakata, ya cire takalma ya sadada ya shigo, Inaa na kwance tsakar gida tana shan iska da dakun shigowarsa. Ba ta sani ba bacci ya yi awon gaba da ita, zuruf! Ya shige dakin Mabaruka ya yi azamar murza key har da sakata. Firgigi Mabaruka ta bude ido daga wahalallen baccin da ya fara daukarta, ya zauna kusa da ita yana fara'a. "Har kin fara bacci ne Mabaruka?" 83 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta tashi zaune tana murje ido, ta се, "Еh". Ya ce, "Ki yi hakuri don Allah Mabaruka ba haka na so mu kasance ba daren farkonmu, wallahi wata matsala ce ta sha kaina tsakanina da Inna, amma komai ya yi daidai za mu ji dadin aurenmu kin ji ko?" Ta yi kasa da kai kurum tana sauraronsa ba ta се komai ba. Ya leka fuskarta, "Ba ki ce komai ba Mabaru?" Ta ce, "Na ji, shi kenan". Ya yi dariya, "Yauwa amaryar, me ki ka ci ne?" Ya Tada yana waiwaye ko zai ga alamar wani abu. Ta ce, "Ba na jin yunwa, ban ci komai ba". Ya ce, "Haba dai, kin ci dai wani abu ko ya ya ne, ga kazarki ma ban kawo ba, ta jiya matsala aka samu da ila". Та се, "Ва komai”. Inna kuwa a cikin baccinta ta fara mafarki kusan irin na jiya. Mabaruka bakin rijiya tana jan ruwa za ta shiga wanka. Inna na zaune tsakar gida duk tana kallonta, ganin ta sungumi bokitin ne za ta shiga wanka ya sa ta mike ta tare ta tana cewa, "Ke tsaya!" Ta isaya tana kallonta bayan ta aje bokitin, ta ce, "Na tsaya me ye?" Та сс, "Ме ki ke nufi ne? Kin gama tuwo kin kwashe da kanki alhalin kin san ba tsarin gidan nan kenan ba?" 84 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta kalle ta a wulakance, ta ce, "Tsarinki na da kenan, kin wa wasu, amma ni na rantse ba za ki min haka ba" Ta сe, "Karya ki ke, ba mai ikon yin wani abu gidan nan sai da amincewa ta”. Ta ce, "Ai kuwa sai ni Mabaruka, kuma za ki gani" Samira ta shigo tana cewa, "Ya ya dai, me ke faruwa?" yi". Inna ta ce, "Yauwa shigo ki gani, wai dukana za ta Samira ta ce, "Ita din wa? Yo akwai mai taba min ke na kyale shi ko wane ne?" Ta ce, "Sai ni kuwa, matukar ba ta daina shiga abin da babu ruwanta ba". Fada ya kaure tsakanin Samirar da Mabaruka, karshe Mabaruka ta daga bokitin wankanta da nufin ta tsiyaye shi a kan Samira, ba tai aune ba sai a jikin Inna. Ta yi tsamo-tsamo cikin ruwa, dukkansu suka bi ta da kallo. A firgice ta tashi daga baccin tana cewa, "Ina! Kai wallahi 'yar nan kashe ni za ta yi in har ta ci gaba da zama gidan nan, akwai mugun nufi a ranta". Ta sa hannu tana sharce gumin da ta yi, ta saurara da kyau tana jiyo 'yan maganganu a dakin Mabaruka. A firgice ta mike ta nufi dakin tana cewa, "Ba dai yaron nan ya dawo ba ya shiga dakin, ina nan baki hangame ina bacci?" Ta fara dukan kofar iya karfinta. 85 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Dukkansu suka zabura, musamman Sulaiman ita da ma ta san sai an yi haka, sai ta zo. Hai kuwa ta fara fada, Waliahi, wallahi idan ba ku bude kofar nan ba sai na tsine maka albarka". Tsam Mabaruka ta mike ta je ta zare sakatar, shi kuwa zuwa yanzu ya sadakas ya bar wa Allah, Inna ba za ta taba barinshi da Mabaruka ba, in dai yana son zama lafiya. Ya dafe kai yana jimami, ta bi Mabarukar da harara, "Kauce ban wuri munafuka, kin kurmuso min da ciki ko?" Ta kauce a sanyaye. Inna ta wuce ciki, ta tsaya gabanshi tana kallo, shi ma ita yake kallo. Ta miko masa hannu, "Ba zan ce da kai komai ba, ba ni takardarta". Ya kalle ta da mamaki, "Inn..." Ta katsc shi, "Wallahi! Wallahi sai ka sake ta yanzu, ni za ka raina wa wayau Sulaiman, ina kwance hagaga da baki ka safado ka shigo gurinta bayan na yi maka iyaka da ita?" Ya yi shiru dai dafe da kai. Ta ci gaba, "To ida.. har ni na haife ka ka dauke ni uwarka ka sake ta tun kan na tsine maka albarka". Ya dube ta, "Amma Inna..." Saukar mari da ya ji shi ya rufe mishi baki. Ta се, "Bana son jin wata kalma daga bakinka face furta mata saki, in kuwa ba haka ba na ji wata kalmar tsinuwar Allah da ta ma'aikinSa su tabbata a kanka". 86 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Jikinsa ya yi sanyi, zuciyarsa ta karaya, wasu hawaye masu dumi suka zubo masa. Ya jinjina kai alamar gamsuwa da zancen Innar don haka ya mike tsaye, ya tunkari gurin Mabaruka da ke rabе jikin kofar, "Mabaruka?" Ta kalle shi a tsorace idanunta sun sauya zuwa ja, ta ce, "Na'am?" Ya ce, "Ki yi hakuri ya dube ta,, haka Allah ya tsara mana rayuwarmu, za mu yi aure anuna ba za mu kasance tare ba". Ta sunkuyar da kai hawaye na zuba. Ya ce, "Ki je na sake ki saki daya, in kin samu miji ki yi aure". Daga fadin haka ya fice daga dakin da sauri. Mabaruka ta dafe kai tare da runtse ido da karfi hawaye suka zubo. Inna ta matso gabanta tana dariya, "To oya-oya a iattara kayan tsafi a bar mana gida tun kan a fara aiki da su, nan ba a samu wuri ba bare a hallaka ni, tsinanniya". Ta kalle ta kurum tare da dade bakinta saboda tahowar kuka mai sauti. Innar ta fice tana murna. Sakan goma ba ta kara ua ta yayimi wayoyinta da jakarta, ta sanyo hijabinta ta fice daga gidan ba tare da wani ya ga fitarta ba. Ta yi sa'ar samun napep har kofar gidan Momynta. Kasancewar Daddy na garin ya sa ba su yi bacci ba da wuri, tsulum suka ganta ta shigo falon. Ta ja ta tsaya bakin kofa kanta a sunkuye. 87 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Kiaban Momy ya yanke ya fadi, ta kalli agogo, sha daya da rabi, ta ce, "Ke daga ina ki ke ke da wa?" mala. Ba ta ce komai ba sai kukan da ke kokawar kwace Daddy ya ce, "Come on Mabaruka, fada min mana, me ke faruwa? Ke da Sulaiman din ne?" Ta tako ta tsugunna gaban Momy tare da fashewa da kuka mai karfi tana cewa, "Ki yafe min Momy, hakkinki ne ke bina sakamakon saba miki da na yi, don Allah ki yafe min ko na zauna lafiya". Momy ta ce, "Ni na kasa gane me ki ke nufi, wannan zancen ai mun dade da yinshi, na kuma yafe miki to kuma me ya kawo zancen again?" Daddy ya dube ta, "Ke Mabaruka me ya fito da ke daga gidan mijinki a wannan daren, ko kuwa tare ku ke?" Ta kalli Daddy, "A'a, ya sake ni". Suka fada a tare, "Saki?" Ta daga kai, "Eh". Salati Momy ta ke nanatawa in ta sauke wani ta dauki wani. Daddy ya ce, "Saki, kwananki daya? A kan me? Me ki kai masa?" Momy ta ce, "A kan rashin mutunci, halaccin da zai mata kenan?" Mabaruka ta ce, "A'a ba laifinsa ba ne, mahaifiyarsa ce ta tursasa shi". Ta ba su labarin yanda abin ya faru. 88 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Daddy ya sauke ajiyar zuciya ya ce, "Well, Allah kyauta gaba. Kar ki damu, ki kwantar da hankalinki je ki abinki ki kwanta ki huta" Ta mike a sanyaye ta shige ciki. Cikin damuwa Momy ta ce, "Yanzu wannan wane irin aure ne kwana daya? Ka ga abin da na gudar mata kenan, kadan daga cikin halr matar kenan". Ya yi murmushi, ya ce, "Ni wannan ko kadan bai dame ni ba tunda ki ka ga haka akwai abin da Allah ya shirya da hakan, ke ma bai kamata ki damu kanki ba". Ta yi shiru tana kallon Daddy, ta yi dai murmushi, ta ce, "To Allah ya shige mana gaba”. Ya ce, "Shi kenan kuwa". Kafin ka ce me, zance ya bazu ai Mabaruka ta dawo gida, Sulaiman ya sake ta abin mamaki, kowa sai ya ce gwanda haka, babu wanda ya yi bakin ciki, haka ita ma wani farin ciki da walwala ta ke ji a ranta, tana ji kamar ta rabu da kaya. Imran kuwa ya ma fi kowa, jikinshi na rawa ya nufi garin, ko da ya zo Daddy da Momy suka tsayar da shi kar ya sake ya tunkare ta da wata magana, kawai su gaisa akwai abin da suke shiryawa. IHaka kuwa ya shigo har dakinta, sam babu fara'a, ya 6oye murnarsa da zumudin ganinta, ya dube ta, ya ce, "Sannu, ya gida?" A sanyaye cikin rashin jin dadin yanda yai mata, ba ta tsammaci haka ba, da tana murna ga shi ya zo kila ma su 89 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna daidaita, dole murnarta ta koma ciki, ta ce, "Lafiya lau, ashe ka zо?" Cikin ko'in kula ya ce, "Eh, an ce kina gida kin dawo, da zan wuce Momy ta ce in zo mu gaisa". ko?" Ta ce, "Eh haka ne, na gode". Ya ce, "Ba komai, Allah kyauta gaba. Sai anjima Bai saurare ta ba ya fice, da ma a tsaye yake. Ta yi kuka tamkar ranta zai fita, ta yi nadamar da ba ta yi ba a da, sai a ranar ta sake tabbatarwa ta yi babban rashi, Imran yanzu ba nata ba ne. haka Rafi'atu ta zo ta same ta, magana daya ce dai Rafi'ar ta ce, "Me na taba fada miki? Watarana sai kin yi kuka matukar ki ka yarda ya kubuce miki. Ya Imran ba na yarwa ba ne, amma ke a kullum cewa ki ke ba kya sonsa, ba kya sonsa, ke..." "Ina sonsa yanzu". Ta katse ta. Ta bi ta da kallo. Mabaruka ta kara cewa, "Wallahi ina sonsa sosai, ina jin kamar-zan mutu idan na rasa shi, amma shi ya daina sona, na san kila wata yake so Та се, "Ai kuwa don un gaisa ma da matar а waya, ba ki ji ta ba muryarta mai dadi". Ta birkice, ta kasa sarrafa kanta sai kuka. Duk yanda Rafi'ar ta so ta lallashe ta amma ina! Kan dole ta kyale ta a haka ta fita. A falo ta same su dukkansu, Daddy da Momy, Imran din ta shaida musu yanda sukai. Abin yai musu dadi, 90 17 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna musamman Imran wani bangare kuma ya ji tausayinta har abada ne son Mabaruka a ransa. BAYAN WATA DAYA Gidan. Momy kacame yake da 'yan biki, har Sharifa. Su Rafi'atu ba zama, karfe biyu aka daura wa Iran aure da amaryarsa. Hauka, kiris Mabaruka ta kusa yi, ta tsure, ta rame karshe ma ta kulie kanta a daki tana kuka cike da nadama babu wanda ya kula da ita, sai hidimarsu suke. Sai da magriba Imran ya iso a shigarsa ta ango, har dakinta ya shigo tana kwance a gado ta ci kuka har ta gaji ta kode, sai ajiyar zuciya ta lumshe idanu. Babban yatsanta ya ja yana dariya, a firgigi ta bude ido ta tashi zaune. Ta bi shi da kallo cike da mamakin ganinshi a dakin. Za ta yi magana ya katse ta, "Shissss". Dole ta yi shiru ta bi shi da kallo. Hannunta ya jawo yana cewa, "Zo mu je ki raka ni wani wuri". Ba ta yi musu ba ta bi shi suka fita, har ya sa ta a mota, ta dube shi, ta ce, "Ban fada wa Momy ba". Ya ce, "Kar ki damu, ta san da fitarmu". Ita dai abin ya daure mata kai, ta dai shiga ya ja suka tafi. Gidan da ta tsana ta kyamata a da, wato gidan da ta taba zama nan ta ga ya tsaya da mota. Ya fito ya zagayo bangarenta ya miko hannunsa, ya ce, "Zo mu je". 91 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ba ta musa ba ta mika masa ya kamo ta, da za su shiga ya dube ta yana dariya, ya ce, "Ki shiga da kafar dama ki yi bismilla". Ta kalle shi da sauri da mamaki. Ya ce, "Eh, ko ba haka tsofafli ke cewa ba?" Zuwa lokacin ta gama ganewa, don haka ta yi dariya ta yi yanda ya се. A bedroom dinsu suka tsaya ta yi mamakin yanda aka sauya gidan, haka kayan dakin duk an sauya sabbi. Ya zaunar da ita yana cewa, "To Mabaruka, Ya Imran yau ga ki a gidansa a matsayin mijinki karo na biyu”. Kawai sai ta ji hawaye na zuba. A rude ya tsuguna gabanta ya ce, "Kuka kuma Mabaruka? Na mene ne?" Ta ce, "Na dadi Ya Imran, ban cancanci haka ba, kai wane irin mutum ne mai mantuwa da cin fuska da wulakancin da nai maka?" "Mutum kamar kowa sai dai mai tsananin sonki fiye da kowa, ba zan iya daina sonki ba ne Mabaruka bare na kyale ki, shi ya sa na dawo karo na biyu, ban kuma samu matsala da su Momy ba suka goya min baya. Kowa na farin ciki da aurenmu Mabaruka, ya ka:nata mu fi kowa". "Na gode Ya Imran, ni ma ina sonka so mai tsanani, na shiga damuwa da jin wai ka samu wata, bare yau da na tsammaci da wata aka daura maka aure". Ya ce, "Har abada ke ce kadai ba wata, daga mu sai va'yanmu. 92 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Farin ciki ya cikata, da gudu ta fada jikinshi tana dariya. Ya maida hannaycnsa bayanta ya rungume ta kam a kirjinsa. Wani farin ciki ya dinga ratsa kowannensu, a wannan daren sun raya shi da farin ciki cike da kewar junansu, tare da yi wa junansu alkawurruka na har abada. Sun bar su Momy da kowa cikin farin ciki da komawar aurensu, kasancewar babu iddar Sulaiman a kanta ya sa aka maida auren bayan wata daya da fitowarta daga gidansu. *** *** *** Labari sabo mai dadi ya barke tsakanin Rafi'a da Mabarukar da yanda aka daura auren duk ba ta sani ba. BAYAN WATA BIYU. Cikas daya da suke samu shi da Mabaruka da ya yi nisa a Lagos sai lokaci-lokaci yake zuwa, amma dai suna kasancewa a waya koyaushe. Satin da ya zo sun sha bikin Rafi'atu sun gaji, a falo suke kwance yana mammatsa mata jiki har wani zazzabi-zazzabi ta ke ji. A talabijin kamar a mafarki ta ga an nuno Inna ba don ta gane ta ba sai don hotonia da aka nuno, gabadaya halittunta sun sauya. Mai labarin yana cewa, sun samu labarin matar danta ce ta yi yunkurin hallaka ta da ruwan zafi sakamakon takura musu da ta ke, don haka ta gaji ta tanadi hukuncin da za ta mata duk da ita ta sa aka auro ta. Aurer dai bai wucе 93 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna wata daya ba, a yanzu tana cikin wani halin neman taimako ga duk wanda Allah ya hore wa don yi mata aiki. Mabaruka ta sauke ajiyar zuciya, ta dubi Imran, ta cc. "Yanzu me ye ranar wayonta da dabararta na ba za ta bar danta ya zauna da matar da yake so ba? Ga shi dai yanzu ita ta kawo matar. Imran ya ce, "Allah kyauta, izina ne ga masu irin halinta" Ta dube shi a sanyaye. "Please my Imran, inda abin da za ka iya ta Gangarenka ka yi don mu taimake ta ba don halinta ba". Ya nutsu yana kallonta, ya sauke ajiyar zuciya, ya ce, "Well Allah ba ni iko". Ta yi dariya, "Amin, ni kuma ta. bangarena insha Allah sai na yi iya. kokarina na dawo masa da matarsa Nafisa" Mikewa ya yi ya sunkuce ta zuwa bedroom dinsu yana cewa, "Amin to". WASHEGARI Har sha daya na safe ba a tashi ba sabanin da da ta ke riganshi tashi don shirya musu abin kari. Bai damu ba ya fice falo yana kallo, a tsammaninsa gajiya ce. Ganin lokaci ya ja ne ya sa ya mike ya shiga dakin ya ga lafiyarta Da sauri ya karasa gurinta yana cewa, "Lafiya ki ke Mabaruka?" 94 WAYE ANGON?-4 Imran" Maryanı Jafar Kaduna Tana karkarwar sanyi ta ce, "Zazzabi nake ji Ya Ya birkice cikin damuwa, "Zazzabi kuma yanzu da safen nan?" Ta ce, "Eh". Kanta cikin bargo. Da sauri ya fice falo ya dauko wayarsa, ya kira Dr. Faruk. Da jin wannan kiran ya bar abin da yake ya iso gidan da 'yar jakarsa. Ba tare da bata lokacinsa ba ya fara aikinsa duk wani gwaje-gwaje da ya kamata ya mata, musamman zargin da yake. Ya dago yana kallon Imran da ya yi kuri yana kallonsa duk a birkice, kwakkwaran moisi ba ya yi. А kagauce ya ke ya ji me ke damun Mabarukarsa. Dariya ta so kufce masa, ya danne ta don ya san matukar ta fito nausarshi zai yi, don me zai dinga masa dariya, Mabarukarsa ba lafiya, farin ciki ma yake ko abin bai dame shi ba? Don haka ya fauze tare'da saukar da ajiyar zuciya har da yarfe guni, ya rike kugu ya yi shiru. Ya kalle shi a fan firgice bakinsa na rawa ya ce, "Me... me ke damunta?" Gabadaya yanayinsa ya sauya ya birkice, kana ganin kwalla na son taruwa a idonsa. Ya dafa kafadarsa cikin rarrashi ya ce, "Calm dowп my friend ba wani abin tashin hankali ba ne, ka sa Allah a lamuranka zai kawo muku da sauki, amma sai ka fa dage da addu'a". Ya sake rudewa, ya juya yana kallon Mabarukar da ta ke kwance sharaf ba karfi jikinta, baki ya bushe, уa се, 95 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna "To amma me ke damunta, wacce cuta ce ta kama min Mabaruka?" Ya fada kwalla na cikowa ta? Ya kasa cewa komai ya dai tsura masa ido, ya sake rike shi a gigice yana cewa, "Fada min Docter, ina son Mabaruka, bana son na rasa kanta, zan iya ba da komai da na mallaka don lafiyarta raina fansa ne gare ta, amma ka fada min wacce cutar ta kamata?" Ya saki huci ta baki tare da cewa, "Na sani za ka iya komai don ita, kowacce kasa za ka iya zuwa ba wani kasa za ku je ba illa India don su ke da wannan kayan aikin lalurarta, bana son fada maka Imran, don na san kunnenka ba zai iya dauka ba, yanayin da za ka shiga ina tsoro ka kwallafa wa ranka Mabaruka da yawa, ka dinga ragewa saboda irin haka. Hawaye suka zubo masa, ya ce, "Ba zan iya ba, Allah ne ya sa min sonta da kwallafarta, kuma Shi zai ba ta lafiya insha Allah yanzu muka fara rayuwa sai mun jima ni da ita kafin Allah ya dauki ranmu”. Tsoro ya kama likitan, ya baza idanuwa yana kallonsa, can dariyar da yake rikewa ta kwace masa ya fashe da dariya tare da dukewa dafe da ciki. Ya fada kujera ya zauna yana ci gaba da dariyar. Gogan naku ya zo wuya matuka, ya dinga kallonsa kamar zai makure masa ashe akwai mai dariya idan Mabarukarsa ba ta da lafiya? Ya taso yana kallonsa, ya cе, "Haba abokina, haka ka ke son Mabaruka, ba fa mutuwa za ta yi ba. Tabbas na san in ka ji abin da ke faruwa da ita za 96 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna ka shiga wani yanayi, amma me? Sai ka ba ni goron albishir kato kuma". Ya ce, "Look Faruk, bana son wasa, just ka fada min matsalar matata in ba za ka yi ba zan kira wani simple. Ya yi murmushi, ya ce, "Ok, congratulation!" Ya mika masa hannu suka yi musabaha, ya ce, "You'll become father, your Mabaruka she's pregnant 9 weeks". Ya karashe yana kallonsa. Sakin baki ya yi yana kallonsa, ya kasa sakin hannunsa, ya rasa wane yanayi yake ciki, mamaki ko farin ciki? Da kyar cikin nauyin baki ya ce, "You mean my Mabaruka tana dauke da cikin dana?" Ya jinjina kai tare da cewa, "Ofcourse, zan tabbatar maka shi a takarda". Wasu hawayen dadi suka zubo masa, ya lumshe idon yana murmushi. Ya yi godiya ga Allah marar adadi, a ransa shi kadai ya san me ya ce, ya juya yana kallonta, wacce ta ke a kwancen har lokacin, ta lumshe idanu. Ya karaso inda ta ke tare da durkusawa gabanta. Ya yi tsai yana kallouta tamkar ranar ya fara ganinta. Wani sabon sonta na kara shigarshi, tausayinta da kaunarta na kara shigarshi, farin ciki ya cika shi, shin wace murna zai yi a rayuwarsa Allah ya sa masa masifar son yara a ransa, duk inda ya ga yara suna burge shi, to ina ga nashi ne, kuma sun fito daga jikin Mabarukarsa? Wannan wane irin dadi ne? Yana son duk abin da ya shafi Mabaruka to ina ga ita ta haifa masa yaronsa? Hawayen dadi suka zübo 97 WAYE ANGON?-4 Maryamı Jafar Kaduma masa masu dumi, ya sunkuyo daidai labbanta ya sumbace ta, ya yi jim idanunsa a rufe, hawayen na zuba, ya kasa janye bakinsa a kan páta. Ganin haka ya sa Dr. Faruk ya fice yana dariya. Tabude idon a kasalance ta ganshi ta sa hannunta cikin sumarşa, ta ce, "Mene ne?" Ya janye Bakinsa tare da kallonta çikin sabon yanayin soyayyarta, ya ce, "I love you Mabaruka Ta yi murmushi takaitacce, tana kallosa a kullum tana karbar wannan kalmar a gurinsa fiye dr sau dubu, kai ba ma za ta iya lissafawa ba, motsi kadan zai ce ina sonki Mabaruka. Тa сс, "Na sani Ya Imran, kullum haka ka ke fada bayan ka yi shi a aikace ina ganin son a kwayar idonka". Ya sa hannu yana shafa fuskarta, ya ce, "Na yau daban yake Mabaruka, ya fi na kullum, kin sake samun wani gurbin da matsayi a gurina na har abada wanda ba zai taba kankaruwa ba, sonki hade yake da numfashina da raina". Ta sake murmushi, ta ce, "Mene ne ya Imran, me ya sa haka?" Ya tashi daga tsugunnen ya hayo kan gadon tare da tarairayota ya rungume ta jikinsa kam, ya cc, "Mabaruka kina da juna biyu har tsawon sati tara, yanzu Dr. laruk yake shaıda min". Ta dago tana kallonsa tsawon dakiku farin ciki ya cikata, dadi ya hana ta magana kawai sai hawayc 'yan sirara suka sirnano. Ta tsayar da idonta kyam kan nasa lana aasa kallon ina sonka. Ya nutsu shi ma yana kallonta 98 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna tsawon dakiku, ya sa hannuwansa ya tallafo fuskarta ya ce, "Fafa min mene ne ya sa ki kuka?" Bakinta ya fara karkarwar son yin kukam yayin da hawayen ke kara zubowa ta buda baki za ta yi magana, kukan ya ci karfinta ba shiri ta fada jikinsa, tare da fashewa da kukau tana cewa, "I love you Ya Imran". Ya rungume ta sosai jikinsa tare da lumshe idanu yana jin nutsuwa na sake shigarsa da kaunarta, уа сс, "I know love you too my Mabaru'). Ta sake shigewa jikinsa tana cewa, "Ba zan iya rabuwa. da kai ba, kai kadai nake so, ina son danka Ya Imran. Ya dago ta yana share mata hawayen, ya ce, "Is ok, na sani ni ma ina son dan da za ki haifa min, haka ya sa ki ka sake samun wani gurbin a raina. Ke kadai nake so, kin ishe ni har abada ba zan rabu da ke ba, rabuwa da ke tamkar rabuwa da raina ne" Ta sake fadawa jikinsa tana dariya, shi ma ya sa hannuwansa ya rufe ta tsam yana dariyar da jin dadi. Sai daga baya sannan Di. Faruk ya rubuta mata magungunan da za ta yi amfani da su saboda rashin karfin jikin ya sanya mata drip. Sun ci gaba da rainon cikinsu cikin nishadi da walwala, kullum yana tare da ita, yayin da ita tana jikinsa tana sake narke masa, ko ya ta motsa sai ya ce, "Mene ne? Me ki ke so?" 1 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Wani lokaci ta kan yi murmushi ta cc, "I love yor". Hakan ya sa ya dauki hutu gurin aikinsa don samun kula da ita yanda ya kamata. Lokacin da labarin ya je kunnca su Momy ku zo ku ga murna a ranar Daddy kamar ya taka rawa don farin ciki, yau zai dauki jika. Barc Momy har da kukan dadi ganin addu'arta Allah ya karbo anafarkin da ta dade tana yi ya tabbata, tana ganin soyayyar İmraa fin a idanunta. Zamaa lafiya da kwanciyar hankali suke, abin da ta ke so keaan. To yau ga shi har za su samu zuri'a wannan mc ya fi shi dadi? Ta yi sujjada ta gode wa Allah da yi wa Mabaruka fatan samun lafiya da sauka kalau. Ganin yanda ta ke wahala ba ta iya in komai sai ruwa a kwance, duk ta narke ai koke-koke ta ke masa, hakan ya sa Daddy ya tausaya mata matuka, har fuskarta ta nuna ya dubi Imran din ya ce, “Ina ganin za mu tafi da ita gida kamar za ta fi samun kulawa a wajenmu. Ba shi ba hatta Mabarukar suka zaro idanu a gigice suna kallonsa cikin tsoron maganarsa. Bakin İmran ya fara karkarwa da kyar ya iya cewa, "Am... amma Daddy kamar a nan ta fi samun kula, za ta fi son 99 Ban Ya juya a birkice yana kallon Mabarukar ya се, "Ko ba haka ba?" A kwance ta ke amma sai da ta kokarta ta tashi zaune cikin irin yanayinshi, ta ce, "Eh...ch zan fi jin dadi a nan". Ta karashe tana kallon Daddyn. 100 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ya cc, "A'a ki zo mu je gida a nan kina wahala shi kuma ya tattara ya koma aikinsa, in kin ji kwari- kwari sai a dawo da ke. Idanunsu suka kada jajir, ita kuma har da kwalla duk ta birkice, sai ta kalli Dadyn cikin yanayin roko ta kuma dubi Momy ta kasa cewa komai, hankalinta ya tashi sosai don me za a raba ta da Imran, har akwai wanda ya fi shi kula ma? Yayin

Chapter 6 of 10