Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 10
yi jim tana kallonta tana mamakin yanda Mabaruka ta ke yarinya, sam wasu abubuwan ba ta sansu ba ko don tana 'yar fari, auta kuma gurin Mamanta? Amma 49 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna a ce takamaimai ba la san me ta ke so ba, kuma ta rasa dalilin hakan? Ta kalle ta, ta ce, "Magana ta Kare Mabaruka, an riga an daura a nan ban ga wata shawarar da zan iya ba ki ba face in ce ki saki ranki ki karbi auran tsammanin da aka daura miki, ki zauna lafiya da mijinki abokiyar zamanki, uwa-uba sarakkuwarki. Ki rike addu'a wannan ita ce shawarar da zan iya ba ki, al'amurranki Mabaruka ban san me ya sa suke zuwa haka ba, anya Mabaruka kina kuwa yawaita addu'a komai sai ya zo da matsala?" Ta yi narai-narai da idanu, ta cc, "Ina tsoro Rafi'a, bau san me gaba za ta kasance a rayuwata ba". Ta nisa tare da daſa kafadarta cikin kulawa, ta се, "Kar ki damu Kawata, ki rike Allah ba abin da zai same ki sai alkhairi, za ki yi murna gaba, za ki farin ciki. Idan kin samu sukuni ko a gidanki ne ki shiga islamiyya za ki samu addu'o'in da shawarwari gurin malamanku, ki kuma san yanda rayuwar 'ya mace ta ke a musulunci". Ta dube ta tana fadin, "Ina da karancin ilimin addini ko Rafi'a?" Ta daga kai, "Sosai Mal.a.uka, kina da karancin hakan kin fara ki ka watsar da kin dage kin yi wallahi da abubuwa ba su zo miki haka ba. Kar ki sake Kawata”. Ilawaye suka zubo mata, ta jinjina kai cikin gamsuwa, "Insha Allah na miki alkawari zan shiga, sannan zan je gidan aurena in zauna inda Allah ya kai ni in yi biyayya ga mijina, amma ki taya ni addu'a Allah ya yaye 50 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna min kunci da rikitaccen al'amarin da ke damuna don Allah Rafi'a". Ta riko hannunta daidai sake zubowar wasu hawayen, ta roke ta ita ma, ta ce, "Insha Allah zan taya ki Ta jawo ta jikinta, ita ta san me ke damunta, amma fadin ba shi da mana'a tunda gidan wani za ta je magana ta kare, dole ne ta yi iya bakin kokarinta kan kwantar mata da hankali duk da ba ta so ta yi aure a gidan Inna ba, tana tausaya mata. Ta sososai ta koma gidan Inran, a ganinta shi ne mafi dacewa da rayuwarta, ba za ta taimaka ba wajen tayar mata da hankali ba, kamar yanda Maman ta yi kowa ya san ba ta son ta auri Sulaiman ko da ba za ta koma gidan Imran din ba ita ta san matsalarsa, to amman tunda an daura babu amfanin ta tayar mata da hankali kamar yanda ta tayar da hankalinta. In har tana son farin cikin 'yarta da nutsuwarta to dole sai dai ta goyi bayan Baban don ta sa mata nutsuwa, zance dai ya kare tunda an riga an daura, amma tana bakin cikin auranta gidan Sulaiman. Ranar a nan ta wkana duk da yanda Sulaiman ya so ya ganta saboda azarbabin zuwanta kwana uku ya sa tariyarta, sam ta hana masa ganinta. Jin aa ce nan da kwana uku ya sa ta dinga wa Momyn kuka don me nan da kwana uku, a bari sai bayan sati biyu ita fa ba ta shirya ba. Tа dube ta cikin damuwa ta ce, "Haba Mabaruka me ye kwana uku an fa yi mai wuya, ba ki da wani shiri ki yi hakuri ki tafi gidan mijinki tunda an riga an daura duk wani abu da ya kamata zan miki insha Allah kar ki damu, ke dai ki je ki ta addu'a. 51 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta kwanta jikinta tana cewa, "Shi kenan Momy, Allah ya kai mu Та се, "Amin". Tana shafa kanta, "Allah miki albarka". Baban kam da man tunda ya duba ya ga ba ta nan ya san tana can dòn haka bai damu ya san ina ta tafi ba. Shi ko ango yana can yana ta hidimar tarbar amaryar kamar yanda yake ziyartar Nafisa gidansu ya same ta ya shaida mata batun auransa da Mabaruka. Sosai ta yi murna ta dade tana son auranshi da Mabarukar, ta kara masa kwarin gwiwa, ya shiga fito da duk tarkacen da ke dakin ainahin dakin da aka taba ba Mabarukar. Inna ta ga ana fito da kaya zuwa wani dakin, ta fito fana kallonsa, ta ce, “Sulaiman?" Ya dago yana kallonta tare da amsawa, ta ce, "Ina za ka kai min kaya ka ke ciro min, me za ka yi da dakin?" Ya ci gaba da aikinsa tare da cewa, "Wai dan fenti za a yi muku, duk wannan ya tsufa”. Ta dube shi da kyau, ta ce, "Anya? Na fa sanka kar in ji wani zance can. Ya ce, "Wane zance? Ki yarda da ni mana" Ta rausayar da kai tare da cewa, "To shi kenan, ai za mu ganı Bai ce komai ba ya share ta ya ci gaba da aikinsa. Aka yi wa gida ras! Ana gobe tariyar aka zo jere, sai dai ta ga mala na shigowa da kaya, manyan mata masu ji da naira 'yan gayu. Kaya na lada da ba da labari ba komatsai ba. Bayan sun 52 WAYE ANGON?-4 Maryam Jatar Kaduna gaisa cikin mutunci suka ce, "Mu ne iyayen amaryar, mun zo jere ne, ko ina ne dakin da aka ba ta?" Ta dube su daidai, ta ce, "Amarya? Nan gidan? Anya ba kuskure ku ka yi ba? Ba nan ba ne za a kawо mana amarya ba". Suka hau kallon-kallo suka ce, "Ba nan ba ne gidan Sulaiman ba?" Ta ce, "Tabbas nan ne”. Suka ce, "To ai nan din ne, shi ne mai auran". Ta ce, "Sulaiman shi ne zai yi aure ban sani ba?" Suka yi shiru suna kallonta cike da mamaki, ta ce, "Shi kenan ya kyauta tunda ba ni da wani matsayi da zai fada min sai ya san mai ba shi daki, ba dai a nan gidan ba". Suka ce, "Amma Inna an riga an daura ya za a yi haka? A yi hakuri dai, me yiwuwa da dalilin rashin sanar miki din". Ta taso cikin fada, "Kai kar ku gaya min maganar banza, dalilinsa na banza? Ina uwarsa amma don ubansa ya ki sanar min, wato har an daura aure? To wallahi ba dai a nan ba". Abu fa yana kokarin zama fada, tamkar ta dake su, kamar su suka yi laifin. Samira ta ja hannunta tana cewa, "Zo ki ji Inna". Ta ja ta gefe ta dube ta, ta ce, "Haba Inna ke kuwa sai kin nuna masa halinki a tafi ana yi da ke duk sai bakin mutane ya kama ki?" Ta ce, "Na yi din, su cinye ni. Gaskiya ce nake fada ban yarda da karya ko munafunci". 53 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna a Ta ce, "To ki yi hakuri ba dai sun zo da kaya ba, to ki barsu su jera gida ai namu ne, mun ga yanda za a yi kawo amarya, da guda-guda in dinga dauka iba sayar mana muna cin balangu". Ta washe baki, "Allah 'yar nan?" Ta ce, "Wallahi, to ki kyale su su jera za mu yi maganinsu, kin manta wadancan muka fara saidawa sai daga baya suka zo suka kwashe?" Ta сe, "Пaka ne fa". Та сс, "Тo kyale su su yi, in ya zo ki ci mutuncinsa. Ta ce, "Shi kenan, zai hadu da ni, ni ya maida za a mana fenti wancan ya tsufa, ashe amarya ya yo, zai cі ubansa. ke". Ta yi tafi, "Yauwa Innarmu, Allah bar mana Ta ce, "Amin, ai ke rainona ce, ba mai raina ki ko kin yi aure. Ta ce, "Haka ne kam, mu je kar su ji shiru". Ai ko haka aka yi suka jera daki ras da kaya masu tsada da kyau, tabbas naira ta yi kuka, sai dai kash! Duk kyansu ba su kai wanda aka kai nata gidan Imran ba, wannan ga shi ba shiri, ba kuma murna ake da shi ba sannan ba guri daki daya ja! ko kicin babu. Wannan kenan. Imran ko yana nan kwance lokaci guda duk ya bi ya fige, tamkar wanda ya shekara kwance, to ba ci ba sha, su Momy da Dady suna tsaye kansa gidan koda yaushe cike yake da mutane 'yan dubiya, daga Mommy sai Daddy suka san ciwonsa, gwanin tausayi kai so masifa ne wani lokacin, 54 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Allah ya jarabce shi da soyayyar Mabaruka ta barshi cikin wahala. Dr. Faruk ya zo duba shi, shi ne likitansa yana tsaye yana sa masa drip ya dube shi cikin rashin kuzari ya сe, "Ka daina wahalar da kanka, ka je ka huta wannan duk ba shi zai sa in warke ba, ba ku da maganina. Mabaruka се kadai maganina, in har za ku kawo min ita ni na san zan tashi, kuna wahalar da kanku ne Doctor". Ya zauna gefensa yana kallonsa, ya ce, "Haba Imran, kar ka ce haka. Mabaruka ba ita ba ce maganinka ba, ka sha magani za ka samu sauki. Ka yi kuskure da ka sa soyayyarta a ranka bayan ka san ba ta sonka, yanzu me ye amfanin ci gaba da soyayyarta har kana kokarin rasa lafiyarka alhalin tana matsayin matar wani?" Tamkar ya watsa masa ruwan zafi ya ji, yanzu Mabaruka matar wani ce ba matarsa ba, ta fita sunan matarsa kenan. Ya yi dif takaici ya hana shi magana, likitan ya ci gaba da rarrashinsa, amma sam ba ya jinsa, dole ya gaji ya kyale shi. Ana gobe za ta tare suka fita kunshi da saloon ita da Rafi'a an zuba mata kunshi mai kyau da gyaran kafa. Rafi'a ta dafa ta, ta ce, "Kin yi kyau kawata, kin ganki kuwa?" Ta yi murmushi iyakarsa fuska, ta ce, "Ban manta ba, haka aka yi wancan karon ana min kunshi da gyaran jiki, amma sam ba na cikin farin ciki da murna kamar 55 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna yanda sauran amare ke yi, suna farin ciki da walwala, nishadi saboda za su tafi gidan masoyansu. Wannan karon ma ga shi nan haka ne, ba na farin ciki har yanzu kuma ban san dalilin hakan ba". Ta dago ta kalle ta, "Sai yaushe ne zan yi farin ciki da aurena kamar kowa?" Ta zauna tana kallonta cikin damuwa, "Ilaba Mabaruka, me ya sa ki ke furta haka? Kowa fa da tsarin rayuwarsa ba iri daya ba ce da kowa, mene ne ciki nan to za ki yi farin ciki idan ki ka je, Sulaiman dinki ne fa". A sanyaye ta ce, "To Allah ya sa ina fatan hakan ya kasance". Ta ce, "Insha Allahu kawata kar ki damu, za ki farin ciki a gaba". Sai ranar da za ta tare sannan Sulaiman ya kawo mata kayan sawa, atamfofi biyu, leshi daya sai shadda an dinka biyu da 'yan tsiraran kayan kwalliya. Rafi'atu ta ja ta dakin Imran su gaishe shi da jiki, ta dube ta a marairaice ta ce, "A'a Rafi'a bana son haduwa da shi". Ta dube ta da sauri ta ce, Caboda me?" Ta yi jim sannan ta ce, "Kawai dai ban san dalili ba, ni dai kar mu je". Ta jawo hannunta ta ce, "Kar ki damu Mabaruka, ganinshi za mu yi da jiki, ba za mu jima ba". Kan dole la biyo Rafi'atun har dakinsa, suka kwankwasa. Daga shi sai Dr. Faruk, suka shigo tare da zama a kan kujerar da ke gefe. Rafi'ar la taso har zawa 56 A WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna bakin gadon inda yake cike da tausayi ta dube shi, "Sannu Ya Imran, ya jikin?" Ya dan dago ya kalle ta ya maida kansa tare da cewa, "Alhamdu lillahi". Duk da ta ga alamar sauki a jikinsa ya yi kyau sosai, to amma yanayin yanda ya amsa mata kamar yana jin haushinta. Abin da bai mata dadi ba, ta ji wani iri, ba haka suka saba gaisawa ba, duk sai ya sage mata gwiwa. Ta nisa tare da cewa, "To Allah ya kara sauki". Bai ce komai ba, haka ta dawo jiki a sanyaye ta dubi Mabaruka wacce da ganin fuskarta ka san akwai dumbin damuwa a tattare da ita, kamar har da dan tsorotsoro. Ta ce, "Ki je ku gaisa". Ta kalle ta tare da girgiza kai alamar ba za ta iya ba. Rafi'a ta ce, "Saboda me? Ba gaishe shi ki ka zo yi ba? Ki je ku gaisa bari in fita". Ta yi saurin riko ta alamar rokonta, ta ce, "Mene ne haka Mabaruka? Ki je mana". Ta janye jikinta tare da duban Dr. Faruk ta се, "Mu je waje". Tamkar jira yake tsam ya mike suka fice, ya zamto daga ita sai shi a dakin. Yasan tana dakin amma yai shiru ya share ta, ganin babu amfanin zamanta a gurin ya sa ta mike tsam za ta lita tana cewa, "Da ma na zo na gaishe ka da jiki, Allah ya kara sauki, sai anjima". 57 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Har ta kai bakin kofa ya tsayar da ita, "Na san kina farin cikin kin rabu da ni nanataccenki kamar yanda ki ke cewa, za ki je gidan masoyinki zuciyarki". Ta juyo da sauri cikin marairaicewa, za ta yi magana, "Ba haka ba ne wallahi, ban..." Kan ta karasa ya mike da sauri cikin tsananin tashin hankali da tsawa ya katse ta, "Ba ki da abin da za ki ce, muguwa marar imani da tsoron Allah. Burinki ya cika ni da ba ki so na bar miki rayuwarki, karshe ma bar miki duniyar zan yi ke ko za ki je ki rayuwarki da masoyinki. Na gode Mabaruka, na gode da tsanar da ki ka min". Ya fada daidai zubowar hawaye. Hankalinta ya tashi tunda ta ke ba ta taba ganin babban mutum na kuka gabanta ba, kalaman da ya fada tamkar ba daga bakinsa ba, ya juya sam daga Imran mai hakuri da sanyin hali, har yana kiranta muguwa? Kalaman sun tayar mata da hankali. Ta dube shi ya zauna bakin gado yana kuka, kuka mai karfi da sauti hawaye wasu na tunkudo wasu sai a yau ta ke ganin abin da yake fada a idonsa a yau ta ke jin kwatánkwacin abin da yake ji tsanisár kaunarta ta gani a idonsa. Wannan shi ne karo na farko a rayuwarta da ya fara ba ta tausayi tamkar tai masa kuka, ta fadi gabansa tare da durkusawa hawaye suna zubowa masu zafi da daci, ta kama kunnuwa cikin tsananin nadama da matukar tausayin kanta da nasa. 58 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ya dube ta, ta dube shi dukkansu hawaye na zuba, ita tana yi shi yana yi cikin wani yanayi iri daya da zafi da zukatansu ke musu. Da kyar ta iya buda baki ta ce, "Sorry! Sorry!! Sorry!!!" Ta ci gaba da kukan, "Na yi nadama, na yi nadama Ya Imran, ina cike da dana sani da rashin sanin me zan yi, na cuci kaina Ya Imran, na wulakanta kaina ba kowa ba ce ni face butulu. Na bijire wa kyautar da Allah ya min, mahaifiyata ta min gatan da duk kowacce uwa ta ke son tai wa 'yarta ta ko ina an min gata, an min halacci, amma na kasance butulu na runtse idanuwa, zuciyata ta kurumce baua jin komai, bana ganin komai da kowa sai abin da zuciyata ta ke so". Ta sake fashewa da kukan tana kallonsa, "Sai a yau nake nadarna da dana sani ranar da ba ni da sauran dama, lokacina ya wuce, damata ta kare. Ranar da ba ni da sauran daraja ko kima da zan dawo da su sun guje ni. Ban san da wane ido zan kalle ka ba, ba ni da bakin ba ka hakuri, nadamata ba ia yi amfani ba lokacin da ba zan iya maka maganin abin da ke damunka ba, ni ma yake damuna a yanzu in..." Da sauri ya katse ta yana kallonta da idanunsa da suka sauya, hawaye na zuba. "Ba ki da abin da za ki ce har abada, ba ki da wata magana da za ki in yarda da ke. Ina nan a yanda nake gurinki na san ba zan taba canzawa ba, mutum daya ki ke 59 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna so, kuma bukatarki ta biya shi ke nan ki je ki tashi ki tafi gıdan masoyinki ni ne daman ba ki so Ta kalle shi da hanzari ta ce, "Wallahi ina..." Ya katse ta, "Kina me? Karya ko ko yaudara lokacin da ki ka san ba yanda zan yi na sake takura miki, ba na tunanin haka har abada". Ta ce, "Wallahi Ya Imran ka yarda da ni-na..." Ya katse ta, "Don Allah ki tashi ba na son ganinki, ba zan taba manta ki ba a rayuwata kin min tabon da ba zai taba gogewa ba, ki sa a ranki koda yaushe ina tuna abin da ki ka min da tsanar da kika min, tashi ki je". Z.a ta yi magana ya daka mata tsawa, "Bana son jin komai, tashi ki je”. Ta sake fashewa da kuka tana kallonsa, tana son yi masa magana amma ya hana ta. Karshe ma bandaki ya shige yana cewa, "Idan kin gama ki rufe min kofa". Kai wannan abu na da takaici da bakin ciki, mutumin da da yake rawar jiki da kai yake son koyaushe kana kusa da shi, amma yau wai shi ke korarka? Ta tashi ta fita da gudu íana kuka, ta gaban su Rafi a ta wuce suka bi ta da kallo. Rafi'ar ta kwalo mata kıra ganin ba ta da niyyar amsawa ya sa ta mike ita ma ta bi ta da gudu, dakinta ta shige da zuwa ta fada gado tare da fashewa da kuka mai tsanani. Rafi'ar ta zauna kusa da ita cikin damuwa tana cewa, "Mene ne Mabaruka?" 60 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta dago fuska share-share da hawaye ta ce, "Na shiga uku Rafi'a, Imran ya canza min, ya daina sona, tsanata yake yi Rafi'a ta dube ta tana fadin, "Me ki ke son ce min, kina bukatar son nashi ne da za ki damu kanki?" Ta ce, "Ki fahimce ni Rafi'a ko ba na bukatar ya so ni bai kamata ya tsane ni ba, me ya sa zai ji haushina?" Ta ce, "Kina jin ciwo ke nan?" Ta daga kai alamar eh. Та се, "То kar ki manta wannan shi ne kadan daga cikin abin da yake ji lokacin da ki ka tsane shi". Ta yi jim kanta a kasa, sai can ta dago ta dube ta, ta ce, "Na yi nadama Rafi'a da ina da hanyar da zan gyara kuskurena wallahi da na yi, sai ya yi mamakina da kowa ma, sai dai kash ba ni da wannan damar-nai wa kaina Rafi'a". Ta ce, "Ba komai, Allah ya ga zuciyarki, ki je gidan mijinki ki masa biyayya ku zauna lafiya shi ne babban abin da za ki yi yanzu, kuma shi ne a gabanki". Ta koma ta kwanta lamo tana jin kunci a ranta, hawaye na ci gaba da zuba. Yamma lis aka zo da motar daukar amarya, bayan ta koma gidan Baban ta sha. kuka sanda za ta bar gidan Momy duk abin da ya kamata Momy ta yi ta mata, bayan ta damka mata kudade saboda toshe matsalolin da ko da za su taso tamkar za a cire mata rai ta ke ji. 61 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ga ta a mota zuwa gidan Sulaiman wanda ta nemi farin cikin da ta ke tsammani za ta yi idan aka ce yau ga la za a kai ta gidan masoyinta, kunci ya mamaye ta miyan bakinta ya kafe har daci-daci ta ke ji, har aka iso lokacin da za ta shiga gidan ta runtse ido gam tare da ambaton Allah ta ce a zuciyarta, "Ya Allah ka sa min farin ciki da wałwala а cikin gidan nan da na shigo, Ka yaye min duk wani kunci da damuwa da nake ji. Ka ba ni ikon yi wa mijina biyayya kamar yanda ka umarta". Ta zauna kan tumemen gadonta da ya sha shimfidun alfarma masu tsada da kyau, kanta a lullube. Nan fa aka dinga shigowa ganin amarya, wannan ya shiga, wannan ya fita. Tabbas duk wanda ya shigo sai ya fita da gulma yana jinjina kai, lallai ba 'yar kananan mutane aka auro ba, kusoshi ne kaf kayanta sabbi dal daga waje, ko cokali ba a kawo ta da shi ba tsoho wanda ta yi amfani da shi gidan Imran ba. Sai dai kash duk irin yanda mutane ke zuzutawa har a gaban idonta da irin bajintar da Momynta ta yi, babu daya daga cikin kayan da suka burge ta sam sai a yanzu ta ke ganin duk na gidan Imran sun fi yau da ma su -aka kawo mata, me yiwuwa ma ta fi murna da su. Shi kanshi dakin duk ta ji ya kuntace ta ba wata yalwa da gadon da kujeru duk a daki daya tal komai а kukkutse ba abin da ya wala yanda ya kamata. Ta tuno gidan Imran tamfatsetse mai yalwa, ko ina kal-kal tar gadonta a tsakiyar dakin yake bare kuma girman falon. Idanunta suka ciko kwalkwal, ta dubi Rafi'a ta tura 62 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna hannunta cikin nata, ta ce, "Ki taya ni addu'a kawata Allah ya yaye min masifar da ke damuna”. Saboda mutane ya sa ba ta ce komai ba, ta jinjina mata kai alamar gamsuwa. Ta dora kanta saman kafadarta ta yi lamo. Sai da aka shigo da amaryar sannan Inna ta gane ko wace ce, ta shiga daki ta dinga-cizgar fada inda ta ke shiga ba nan ta ke fita ba, "Ashe wannan yar mahaukatan ya sake aurowa? Sai da ya kashe mata aure kenan saboda naci, ashe bai hakura ba? Sai da ya yi yanda ya yi ya auro ta kenan?" Samira da ke gefe ta ce, "Haba Inna, me ya sa ki ke son damun kanki, me ye ita din? Ta zauna mana da kanta ma za ta gudu, nawa muka fitar bare wannan lakasun ba abin da za ta iya". Та се, "Кс yarinya ce ba ki san komai ba, iyayenta kudi gare su, idan har kana auren 'yar masu kudi kai kana talaka to juya ka za a dinga yi, saboda kudin mai yiwuwa gidansu ake mata komai har kai ka ci albarka, sai ka koma sakarai iyayenta na juya ka, ba ka da iko da ita". Ta ce, "Amma me Yaya Binto ta ce? Mu ma fa za mu lasa" Та се, "Кe banni da zancen nan, ban nutsu da shi ba. Ina nan ina lasa za a lashe min da in zama ba ni iko da shi, ai ta juya min da, abin da kuma ba zan yarda da shi ba ke nan 63 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta ce, "Ni ban ga wani abu nan ba, ki kwantar da hankalinki kawai". Та се, "Кoma dai mene ne ban cancanci ya min haka ba, a dauro masa aure ban sani ba, sannan ban san wace ce amaryar ba? Dole ne in yi fada, wallahi ba za ta sabu ba". Kowa ya daware an bar amarya daga ita sai 'yar wuarta, kawarta kuma aminiyarta Rafi'a suna dakin an gyara shi fes, an saki labulayen masu kyau da kauri an saki turaruka masu rikita kwakwalwa, babu wuta sai dai aka kunna lenter ba laifi dakin ya haske tarr! Duk Rafi'atu ke aikn yayin da ita tana zaune kan kujera ta yi shiru, tunanika kala-kala ba wanda ba ta yi, sai dai ka ji ta saki ajiyar zuciya tare da share kwalla. Har Rafi'atun ta gaji ta dawo kusa da ita ta zauna tare da riko hannunta cikin kulawa ta ce, "Mene ne Mabaruka?" Ta kalle ta tsawon dakiku kwallar na sake ciko idanunta, ta ce, “Ba komai". Tare da dauke kanta gefe. Ta ce, "Amman ba komai ki zauna kina ta ajiyar zuciya?" Ta yi shiru, ta sake cewa, "Haba kawata za ki manta ni ne? Ni ce fa Rafi'atu, ba za ki iya sanar min damuwarki ba matsayina ya canza kenan?" Ta kalle ta da sauri, "A'a har abada kina nan a matsayinki ba za ki taba canzawa ba, ke 'yar uwata ce babu abin da zan boye miki". Ta ce, "To na ji me ye dalilinki na ajiyar zuciyar?" 64 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta kalle ta a marairaice, ta ce, "Ke ma kin sani Rafi'a, har yanzu haushin kaina nake ji. Ban taba ganin marar sala irina ba, mai makauniyar zuciya. Rafi'atu na yi bakin ciki na yi asara tunda har na bari Imran ya kufce min, ina cike da tausayinshi, Rafi'atu ya cutu daga wurina duk lunanina gidan Sulaiman kadai zan samu farin ciki da wałwala a nan nake zaton zan nishadantu hankalina ya kwanta, amma sai na ga akasin haka. Wallahi Rafi'a ranar da na je gidan Imran ina ganin ina cikin kunci, ashe farin ciki ne, ashe walwala nake sabanin nan. Gani nake kamar a birsin nake, an kuntace ni tsananin kunci ya cika min zuciya, kuncin da nake ciki a yau da aka ce an daura min aure da Sulaiman ya lunka ninkin ba ninkin a kan sanda aka cc an daura min aure da ímran. Wallahi na ſi murna da auran Imran a kan na Sulaiman, amma saboda rashin rabo na take na ki karbar kyautar da Allah yai min, na dinga hango nan, ga shi na zo nan din ban ji wani sauyin da nake tsammanin zan samu ba, sai ma bakin ciki da takaici na kasa nutsuwa, ba abin da nake hangowa a yanzu sai Imran". Rafi'a ta ce, "Sai yau ki ke gani, kin manta lokacin da nake gaya miki ina tunasar da ke akwai irin wannan ranar, ki ka nuna min ke kin fi son hakan don kin san za ki farin ciki. Yanzu ga ranar ta zo kin baro gidan da ba ki so kin dawo gidan da ki ke so, amma ba wani nutsuwa me ye ribarki, me ye abin burgewarki a nan?" Ta fada lokacin da hawaye yake zubowa, ta ce, "Babu illa ma bacin rai da hasara, na yi kaico da kaina". 65 Maryam Jafar Kaduna WAYE ANGON?-4 Ta dafa kafadarta cikin kwantar da hankali, "To ya isa, komai ya wuce a duniya ba wanda ba ya kuskure, abin da ake so ga dan Adam da ma ya tuba ya gane abin da ya yi baya kuskure ne ya bari, alhamdu lillahi kin yi wannan, na tabbala gaba za ki kiyaye da duk ma wani wanda ya ji labari. Akwai addu'o'in da zan ba ki ki dinga yinsu insha Allah za ki samu nutsuwa da kwanciyar hankali, duk damuwarki za ta tafi soyayyar Sulaiman kuma za ta dawo sabuwa, ku yi zamanku mai dadi da farin ciki insha Allah”. Ta jinjina

Chapter 4 of 10