Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
1 / 10
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels WA ANGON 4 Maryam Jafar Kaduna HAUSAВООК.СOM WAYE ANGONZMARYAM JA AFAR KADUNA (MTs Khabeer Abdullahi), WAYE ANGON?-4 GODIYA Maryam Jafar Kaduna Ina godiya ga Allah (S.W.T) wanda Ya ba ni damar kirkirar wannan littafi mai suna WAYE ANGON? Tsira da aminci ga shugabanmu Annabi Muhammad (S.A.W) da alayensa da sahabbansa da dukkan mabiyansa. Typesetting:- NURA SADA NASIMAT KT 08131994808 BUGAWA DA YADAWA DANEJI PUBLISHERS 08037968900/08029035187 2 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna ت WAYE ANGON?-4 okacin da Imran din ya shiga Momy na Lzaune falo cikin takaicin wannan abin. Sallama ya yi ya shigo har kasa ya tsugunna ya gaishe ta, fuskarsa ba walwala ba kamar da ba. Bayan sun gaisa ya mike, ta tashi tsaye tare da kiransa. Ya ja ya tsaya tare da juyowa ta ce, "Ka fada min gaskiya, na sanka ba ka min karya, me Mabaruka tai maka?" Ya yi shiru sam ba ya jin zai iya fada mata zancen nan. Ta katsc shi, "Kar ka boye min Imran, ni mahaifiyarka ce, ka kalle ni a haka, kar ka kalle ni matsayin mahaifiyar Mabaruka, ko ma mene ne na san kai ne da gaskiya, amma me ya faru?" Matar tana da matukar girma da kima a idonsa, yana kallonta a matsayin mahaifiyarsa, bai so tona wannan zancen ba, amma ganin sun dade a tsaye tana rokonsa ya sa ya zauna ya fede mata duk gaskiyar abin da ya faru, tun daga kai ta gidansa har jiya cikin dare zuwa yau da safe, da ta nemi ya sake ta. a Kunya ta kama ta, ta gagara haga ido da shi, Mabaruka ta gama ba ta kunya, da kyar ta iya cewa, "Allah yai maka albarka, Ya yi maka zabi mafi alkhairi, Ya zabo maka wata wadda ta fita. Na san ka yi hakuri, amma ka kara hakuri, ina mai rokonka. Ba zan tilasta maka ba, haka ma ya isa, insha Allahu za ka ga sakayya mai girma a wajen Ubangiji". Maryam Jafar Kaduna WAYE ANGON?-4 Sun dade suna tattauna maganar, ya nuna mata bai rike ta da komai ba, da man ta fada ta ce ba ta sonsa, dolc aka mata don haka duk abin da ta yi kar a ga laifinta, bacin rai ne dole sai ya yi shi, amma zai wucc, shi ya ci gaba da kwantar mata da hankali. A firgice ta isa gidan Babanta, sai dai suka ganta kwatsam. Inna na bakin murhu tana kwalkwale gwangwanayen alale ta ganta, ta wuce ta samu kujera 'yar tsugunne ta zauna, tare da rafka tagumi hannu biyu. Inna ta taho tana cewa, "Mabaru lafiya dai ko?" Ta daga kai ta kalle ta, ta watsar ta ce, "Lafiya". Ba ta sake cewa komai ba. Baban ya fito daga daki yana cewa, "Wa nake ji kamar Mabaruka?" Ta ce, "Ni сe". Y a ce, "In ce dai lafiya wannan sammakon?" Ta turo baki tare da cewa, "Yo ya sake ni". A tare suka rafka salati, Inna har kwano na kufce mata, ta ce, "Saki? Y a sake ki?" Ta ce, "Eh mana”. Baban ya yi shiru jim, can ya ce, "Amma ya aka yi haka?" Ta ce, "Ni da man fa ba sonshi nake ba, na gaji shi ya sa kawai ya sake ni". Ya ce, "Au ke ki ka nemi sakin kenan?" Ta ce, "Eh". E WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ya cc, "Amma yau an yi ja'ira, da ma haka ki ke ashc ba ki da wayau don ubanki wa ke kin mai kudi? To kin zo nan in miki mc a nan?" Ta kalle shi cikin jin haushi, ta ce, "Yo ba gidanmu ba nc, ina zan je to?" Ya ce, "Dole ki yo nan kam ‘yar bakin ciki, ki zauna can mu dinga lasar arziki shi ne ki ka kaso auran ki ka dawo min nan ki tsugunna ke babu ni babu? To kin kyauta, ga gidan nan sai ki ci tsiyar da za ki ci a cikinsa, na koko ma yau babu, dan jarin da za a ba ni kin yi bukulu shi kenan, zauna ga gidan nan". Ya shuri takalman ya fice yana bambami duk bakin cikinsa da takaicinsa ta datse masa hanyar samun 'yan sulalla. Inna ta daga murya ta ce, “Yo ka fita ai mijin za ka sa a kira maka ka ji dalili, su sasanta ta koma dakinta in ba uku ba ne". Ta kumbure fuska, ta ce, “Ni ba inda zan je na fito kenan, kar ma ki fada masa haka, uku ya min". Ta zaro ido, "Uku?" Ta cc, "Eh, sai me to?" Ta ce, "Amma Mabaruka ba Babanki kaďai ki kai wa ba, har ni. Ina nan ina shirin zuwa in jc mu dan gaisa, fan jarin alalar ya yi kasa Babanku ya amshe tas sai kamc-kame nake". Ta turo baki tare da mikcwa ta shige tsohon dakinta tana ccwa, "Ku kullum zancenku kudi, Allah sauwakc". WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Lambar Rafi'atu ta kira, ta cc ta zo yanzu-yanzu ga ta a gidan Baba. Ai ko ta taho don jin kiran ba na lafiya ba ne. bayan ta iso ta shigo hankalinta na kan Mabarukar ta shigo dakin, tun kan ta zauna ta ke ccwa, "Wai lafiya ki ka kira ni haka, me ya faru?" Ta tabe baki ta ce, "Um wai Imran ya sake ni". Saboda faduwar gaba ba ta san sanda ta kai kasa ba, tana jan dogon salati kan ta gama ta ce, "Saki? Me ya faru haka har ta kai ga saki?" Та се, "Ke ma kin sani, sau nawa zan fada ba na sonsa, zan bar masa gidansa?" Ta zauna sosai tana kallonta, ta kasa cewa komai, ta ci gaba yayin da idanunta sukai rau-rau, ta се, "Rafi'atu Imran ya cuce ni, ya lalata min rayuwa bà zan taba barinshi ba wallahi, yana sane ni ba matarsa ba cе ya kusance ni jiya, ya keta min haddi". Ta karasa da kuka. Rafi'a ta saki baki tana kallonta, mamakinta ya ishe ta, da kyar ta iya cewa, "Wai me ki ke nufi, kina son ki ce min tunda ki ka je gidan mu'amaler auratayya ba ta hada ku ba har sai jiya?" Ta ce, "Eh, mijina ne shi da zan biye mishi? Me ki ke nufi ne?" Tsaki ta ja tare da cewa, "Ban taba sanin ke bululu ba ce sai yau. Sam ba ki san halacci ba wallahi, Mabaruka ba kya jin magana, kina son zuciyarki, kin ki wa mahaifiyarki biyayya kin runtse ido ba kya ganin 6 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna soyayyar da mijinki ke miki wanda har abada ba za ki taba samun irinsa ba, aurc kuma kin san Imran mijinki ne ba ki da hujjar karyata haka, kin dauki alhakinsa har tsawon wannan lokacin bayan kin sha tsinuwar mala'iku karshc kin 6allo auran. To ni da ki ka kira ni me zan miki bayan kin gama yanke hukunci, in zo in taya ki zaginshi ya yi miki fyade, ko ko in fada miki abin da za ki yi gaba?" Ta dube ta a sanyaye, ta ce, "Ya kamata ki tausaya min Rafi'a, dubi halin da nake ciki, na je gurin Momy ta koro ni, ta yi fushi da ni. Ina cikin musiba fa". Та се, "Ke ki ka sa kanki ciki, ke ki ka sani wallahi ba ruwan Rafi'atu, tuni nake ba ki shawara amma kin yi biris da ni, to tukunna akwai ranar kuka da dana sani”. Ta marairaice ta ce, "Sanadin ciwon yatsa na ma manta da wani ciwon, tuni na neme shi na rasa bala'in da nake ciki Rafi'a ya hana ni nutsuwa, bana son fushin Momyna, me ya sa ba za ta fahimce ni ba?" Tsam ta mike tana cewa, "Kin ga Mabaruka a nan ba mai fahimtarki, hada da ni ba ni da lokacin wannan maganar, kin ga tafiyata. In kina son dariyar Momy ni ma na kasancc da ke, wallahi ki nemi mijinki ku sasanta tun kan ya miki nisa, in kin dauka to kin min waya in samc ki gidanshi". Ta ja tsaki tare da cewa, "Allah ya kyauta! Tir!" WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Та сс, "То shi kenan a sha zama lafiya, sai anjima". Daga haka ta fice da sauri. Ta dago murya tana ccwa, "Ko kowa ya gujc ni bai kamata ke ki barni ba, wallahi ina bukatarki Rafi'a". Haba! Tuni ta fice, gabadaya ta fice mata a rai. A nan ta kife tana kuka tamkar ranta zai fita, wanda ba shi da magani (mu dai sai mu ce Allah ya kyauta). A wannan ranar haka ta kasance cikin kunci, kuka, damuwa ba abin da ta sa a cikinta. A daki ta wuni har dare aka koma 'yar gidan jiya, kannenta suka yayumo tabarmarsu mai cike da zarni saboda ruwan da ta kc sha har kakkaba ta kc. Ta bi su da kallo cikin fargabar ya darenta zai kasance, ba damar hana su, dakinsu ne, nan ta tarar da su. Ta dafe kai cike da takaici, haka dai suka kwana GIDAN INNA Ya fara şamun sauki har yana zancen zai dawo da Nafisa, Inna ta yi tsalle ta dire ta ce, a!Çur'an ba zai yiwu ba, ba inda za ta zauna tunda ta ga hankalinsa ya karkata gurinta ba matar da ya taba aure ta shiga ransa irinta, don haka ta ce ba ta yarda ba, sai dai ya auro wata. Ya ce, "Ni kuma wannan nake so, ba macen da zan sakc aurowa, wannan din ita ce kadai me iya zama da ni, kuma kina nan za ki ga ta dawo". Daga haka ya fice. WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta dago murya a rikice tana cewa, "Sulaiman! Sulaiman!! Kana jina ka fice ko?" Haba turi ya yi nisa, ta cc, "Shi kenan za ka dawo ka sane ni gidan, da ni ka ke zancen". Kwanania hudu kenan da baro gidan Imran, babban abin da ke ci mata tuwo a kwarya fadan Babanta da Inna, kullum da fadan da za su yi harshensu sama ana jiyo su a makota, har da buge-buge kan naira goma sai su tashi kura yanzu-yanzu, dole ta ke raba fadan da biyan wanda aka ci wa ko ba ta yi niyya ba. Gefe ga sauro da dan banzan zarnin fitsarin kannenta duk da yanda ta ke gyarawa, gefe kuma ga fushin Momy, har yanzu ba ta sauko ba, sai na karshen bakin ciki da takaicin, sanin da Imran din ya mata a matsayin 'ya mace. Ta kan yi kuka kamar ba za ta yi shiru ba, idan bakin cikin nan sun mata yawa. Shi ko Imran ya dawo tsohon dakinsa na gida, ba ya jin farin ciki idan ya zauna a wancan gidan duk abin da ya faru za su dinga dawo masa, musamman kwana daya jat! Da ya yi ba tare da Mabarukar ba duk kuncin duaiya ya baibaye shi, kai so masifa ne. Allah ya jarabce shi da son Mabaruka, soyayyarta a cikin jininsa ta ke, da ita aka halicce shi. Ya yi tunanin duk zagi da cin mutuncin da ta masa ya manta da ita, ta fita ransa amma ga mamakinsa kullum da ita yake kwana yake tashi, WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna rashinta kusa da shi masifa ne, yana sonta ainun, anya zai iya hakuri da soyayyarta? Idan ya duba Mabaruka yarinya ce har zuwa yau ba ta san mene ne so ba, haka nan ta ke fadarsa, sannan in ma ta sanshi tuni ta ke fada ba ta sonshi kar a aura mata shi za ta cutu, sannan abin da ya faru da daren zai bakanta mata kamar yanda ta ke cewa ba shi tai wa tanadin kanta ba, dole ne idonta ya rufe ta caka masa son ranta. Ya juya kan gadon da yake kwance, daga shi sai boska a jikinsa, ya fada a fili, "Ina sonki Mabaruka, har gobe ke ce a raina, ba zan iya son wata ba in ba ke ba, sai da ke zan iya rayuwa. Rashinki mutuwa ce gare ni don Allah kar ki guje ni, ki dawo gare ni wallahi zan kare duk hakkinki, zan kula da ke in ririta ki fiye da kowacc mace a duniya. Don Allah kar ki guje ni". Ya sa hannu ya share kwallar da ta fara zubowa. Wayarsa ta dauki kuka, ya jawo ta cikin mutuwar jiki, hoton Mabarukar ne a fuskar wayar tana murmushi, ta yi kyau sosai, ya shafi fuskarta, sannan ya dauka. Daga can akai magana bayar mai wayar ya gaishe shi cikin ladabi da girmamawa, ya cc, "Yallabai sakon nan re ya iso yanun haka muna tare da shi". Ya cc, "Ok, zan turo maka address din da za kai”. Ya rankwafa kamar yana gabansa, ya ce, "Shi kepan Yallabai, an gama, sai na gani". Ba tare da ya ce komai ba ya kashe, tare da tura 14-a address din. Ya dade a kwance yana juyc-juyen 10 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna tunanin Mabaruka, daga bisani ne ya mike ya shiga wanka. Kwalliyarsa kamar kullum mai kyau da daukar hankali, ko ya ya yi ado sai ya haska kuma sai ya burge, sai dai kwalliyar tasa ta yanzu ba walwala a fuskarsa, zuciyarsa a cunkushe ta ke, Mabaruka ta hana masa nutsuwa. Daddy da Mommy suna zaune kan dinning din break fast ya fito, har kasa ya tsugunna yana gaishe su ba annuri a fuskarsa. Bayan sun gaisa Daddy ya dube shi cikin kulawa da dan nasa, ya ce, "Har yanzu damuwar ce?" Ya yi shiru kansa a kasa. Ya mike daga kan kujerar ya nufo shi, ya taso shi daga tsugunnen suka mike cikin kulawa ya ce, "be ginat and patient my son, na san Mabaruka ta shiga rayuwarka, amma ka daure ka cire sonta a ranka idan da alkhairi gaba Allah ya hada ku ko kuma kowa ya masa zabin da ya fi zama alkhairi gare shi". Ya dube shi cike da mutuwar jiki, ya се, "То Daddy". Daga haka bai sake cewa komai ba ya fice daga falon, Mommy da Daddyn suka saki ajiyar zuciya, yayin da ita Momyn ta dafe kai ta tsura wa farantin gabanta ido, shi kuwa Daddy ya bi shi da kallo cike da tausayin dan nasa, har ya fice. Ya dawo ya zauna yana cewa, "Sai addu'a ba damuwa za mu taya shi ba". WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta dago ta kalle shi cike da dauwa har ta fada, ta ee, "Ban san me Mabaruka ta ke nuli ba, taurin kanta yanа ba ni mamaki. Ni yanzu ban isa da ita ba kenan sai abin da zuciyarta ke so?" Ta fada hawaye na son zubowa. Ya dube ta cike da kulawa, ya ce, "Sai yaushe ne wai za ki bar damun kanki ne? Na fada miki duk a nan ban ga laifinta ba, babu masu laifi sai mu da muka nace sai mun aura mata shi alhalin ba ta so. Mun manta sai da soyayya auran zai yi karko ta zauna, ta kyautata masa. Sannan zamanin nan an daina yi a yara auran dole, don samun zaman lafiya da kwanciyar hankali da gudun fitina ba daidai yake da namu zamanin ba. Amma muka dage a kan lallai sai an yi, to an yi din ga shi nan ba wani abu da suka karu da shi sai tashin hankali da rashin nutsuwa, to bare mu kuma. Ita a kuntace shi a kuntace, tunda ya gaza samun soyayyarta, don haka ban matsa ba a kan lallai sai ya dawo da ita ba, su je kowa ya nemi zabin Uhangiji fakat! Magana ta kare. Ke ma na gaya miki ki daina tayar da hankalinki, ki bar komai hannun Allah, Shi ya shirya hakan, kuma Zai kawo mafita". Ta numfasa tare da share hawayen ta ce a sanyayc, "Shi kenan, Allah ya shige mana gaba". Ya ce, "Amin”. Cikin farin cikin saukowarta. Imran din ya shiga mota ya yi shiru, sam ya gagara tashin motar, wai sai yaushe ne zai samu nutsuwartsa? Sai yaushe zai samu soyayyar Mabaruka? Da ma haka soyayya ta ke da daci idan ka rasa masoyinka? Ashe zaman da sukai tare duk da ba sonshi tá ke ba ganin da yake mata ko da 12 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna harararsa ne ashe ya li dadi da farin ciki, da samun nutsuwa? laka Mabaruka ta shiga ransa anya zai iya rayuwa babu ita? Jerin tambayoyin da yai wa kansa, amma amsarsu ta gagara. Kiran Sharifa ya shigo wayarsa ya duba sunan My Sis, ya jawo wayar ya dauka cike da mutuwar jiki ya kai kunne tare da cewa, "Sis ya ki ke?" Da jin maganarsa ta gane ba lafiya ba, kamar yanda ta ke tunani da man, ta ce, "Yes bro how are you?" Ya amsa tare da lumshę idanu yana jingina jikin kujera, "Thank God" Ta ce, "Bigbro da gaske kun rabu da Mabaruka?" Ya yi jim yana jin kamar ta watsa masa ruwan zafi, duk da haka ne amma sai ya ji maganar ta dake shi, wai ya rabu da Mabaruka? Ya jinjina kai cikin takaici ya ce, "Haka ne". Ta yi shiru daga can, ba farin ciki ba, ba bakin ciki ba. Babbar damuwarta Yayanta ta san irin zafin son da yake wa Mabarukar zai shiga mawuyacin hali, ba ta son damuwarsa, ta ce, "Na sanka Bigbro kana nan cikin damuwa, ka bar wa Allah komai, Yana sane, Shi zai kawo maka sauki a cikin lamuranka. Kar kai ta damuwa da tunane-tunane don Allah Bigbro, ni ma zan shiga damuwa na kasa karatu". Ya yi murmushin jin dadin kulawarta gare shi, ya ce, "Shi kenan kada ki damu, ni ma ina nan lafiya ba abin 2 da ke damuna". Ta ce, "Ban yarda ba Bigbro ka dai kiyaye". 13 WAYE ANGON?-4 Ya ce, "Shi kenan zan kula Ta ce, "Promise?" Maryam Jafar Kadunа Ya daga kai kamar tana gabanshi tare da cewa, "Shi kenan na ji. Ta yi dariya daga can, ta ce, "Thank my bro, Allah tsare mu, kai muna exam da zarar mun kammala zan zo". Ya ce, "Shi kenan ki dage ki karatu sosai". Ta juya rigingine cike da jin dadin kasancewarta da dan uwanta, ta ce, "Zan yi Yaya insha Allah, sai ka yi alfahari da result dina". Ya yi murmushi, ya ce, "Ni kuma za ki ga kyautar da zan miki, katotuwa, tuleliya". Ta yi dariya sosai, ta ce, "Shi kenan ka tanadar min tun kan ka gani, na maka alkawarin ba zan ba ka kunya ba. Ya ce, "Shi kenan, ki je ki karatu, zan gani din. Sai anjima Тa сe, "To by my dear bro, love you. Tare da hura masa iska. Ya yi dariya shi ma, ya ce, “Love you too”. Suka kashe wayar. Ta rungume filo tare da lumshe ido tana jin dadin kasancewarta da dan uwanta. Balarabiyar mata ta shigo tare da sallama, ta yane kanta da irin shigarsu ta Larabawan asali, Momy Pateema kenan kanwar Mamansu uwa daya uba daya. Ta zauna tana kallon Sharifar, ta ce, "Manillazi tatakallam fil hatif?" Ta yi murmushi, ta kalle ta, ta ce, "Ana wa aki 14 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna Ta jinjina kai tare da cewa, "A'alam huwallazi takallama wa Anti ariha” Ta yi dariya tare da tasowa ta rungume ta, ta ce, "Haza huwa ya Ummi li anna ni ahabbahu ma ahabbu nafsi". Ta jinjina kai tare da murmushi, ta ce, "Barakallahu fikum fi hayatikum". Ta сe, "Ameen wa fiki barakallah shukran”. Da kyar ya iya jan motar ya fice, kai tsaye gidan su Mabarukar ya nufa. Sabuwar dalleliyar adaidaita sahu ce a kofar gidan an riga an gama hada ta, ja kawai za a yi. Baban Mabarukar ne tsaye jikin motar, sai washe baki yake yana zazzagaya ta tamkar an ce tashi ce, shi dai dan aiken yana kawo wa ya wuce yana cewa, "Maigidana ne ya ce a kawo". Ya fito daga motar, ya iso inda yake. Ai yana ganinshi ya taho yana cewa, "Shi kenan ma ka zo, da ma tun dazų nake jiranka, na ga an kawo motar kabo-kabo in ce dai tawa din ce ta iso?" Ya dan yi murmushi yana kallonsa, ya ce, "Пaka ne Baba, ta sana'ar ce ka fara ja mu ga ya abin zai kasancё". "Yihuhu! Allahu akbar". Ihun da ya buga kenan tare da tsalle ya nufi gurin motar har yana tuntubе ya се, "ka ce tawa din ce? Hamza! Haruna!! Ku zo ku zo da gaske dai tawan ce kamar yanda na tsammata" 15 WAYE ANGON?-4 Magyam JatanKedana Ya kira `yan uwan nasa. Da sauri suka karaso cioke da farin ciki. Ya ce, 'Kun gani ko, da ma na fada muku kila tawa ce, ashe kwa hakan ne. Suka dubi mran suka ce, "Allah saka da alkhairi, Allah kara arziki". Ya ce, "Amin, amn". Sam bai ma tsaya suka gaisa ba yana ta rawar kan motar da kiraye-kirayen abokansa, to bare kuma ya mishi maganar ya aka yi, me ya faru har abu ya kai ga saki, in mai daidaituwa ne a daidaita ta koma dakinta, in babu kuma a san me za a yi, amma sam bai tsaya ba, a tunanin shi kanshi Imran din zai masa magana, amma sai ya ga kamar motar ta fiye mashi komai ma har shi mai kyautar motar. Ya jinjina kai cike da mamakinsa, wannan wane irin uba'ne Mabaruka ta ke da shi? Tunda yake masa rawar kai da maula-maula, roko-roko bai taba ba shi haushi ba sai yau, don me ba zai yi kokarin dawo mishi da matarsa ba, motar ta fi kenan da man don motar yake masa sintiri? Haushi ya kai shi wuya, ya juya kawai zai shige motarshi. Baba Hamza wanda shi ne madaurin auren ya kira shi suka rabe gefe, ya dube shi cikin kamala na dattijai, ya ce, "Na san Mabaruka ba ta jin magana, za ta iya yin komai don son zuciyarta, yarinya ce mai kafiya da taurin kai. Haka aka dinga fama da ita kan auran nan aka samu aka yi da kyar tana ciccijewa, shi kuma Babanta ba girma shi ne babbanmu amma bai maida hankali a kan abin da ya kamata ya yi. Yau kwananta hudu da dawowa gida ta ballo auran ía dawo, amna shi Baban nata bai sanar min ba, sai 16 WAYE ANGON?-4 Maryam Jafar Kaduna dai gurin yara na ji. Jiya nake cewa zan kira ka ka zo in ji me ya faru, sai dazu da safe da ka yo aikc yake cewa ai kai ka aiko masa, kilan ka zo. To sai na jınkirta ka zo din na kuma sa masa ido in ga zai maka magana, ko ko nai ko haka na gani bai yi maganar ba sam. Abiu bai dame shi ba, murnar niotarsa yake abinsa, mutuwar auran 'yarsa ba ya gabansa, don haka na kira ka ina son in ji daga gare ka, me ya faru har aka kai ga saki?" Sosai ya ji dadin abin da mutumin ya yi, hakan ya sa ya kara ganin girmansa da gemansa yana sa rai kila a dawo masa da matarsa tunda manya sun sa baki. Bai yi kauron baki ba ya fada mishi komai, har duk zagi da rashin kunyar da ta ke masa, har na ranar da ya yi sakin. Baban ya dinga fadin, "Subhanallahi! Subhanallahi, assha ba ta kyauta ba, amma ka yi hakuri yaro, zan ci mutuncinta, ba za ta sake ba. Amma yanzu ka jinkirta ka koma ka gaya wa Allah, idan da alkhairi a komenta Allah ya maida auranku ta fahimce ka ku zauna lafiya. Ba zan sake matsa mata ba lallai sai ta koma ba kamar yanda na mata na farko ga abin da ya haifar, kar ta koma ta yi abin da ya fi wannan kyama, abin da za a yi ka kyale ni da ita, zaman da za ta yi gidan musamman nan gidan Baban za ta gane kurenta, sai ta yi kuka da idonta, karshe

Chapter 1 of 10