Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
9 / 10
tsoka abar tayar da husuma da shasha shai 'wadanda basu san ciwon kansu ba in.... kan ya karasa yaji sauar kulki saman kansa ta bayansa wanda ke hade da saukar gigitaccen mari a kunne ba shiri ya dafe kai yayi luu yafadi anan yana shure shren kafato tamkar ransa zai fita saboda yanda yake jin azabar dukan har a kwakwalwar sa kan ya dawo hayyacinsa ya sake jin saukar wani, wani irn ihu ya saki tamkar zararre suka cigaba da dukansa ta ko ina ajikin sa kafafunsa da hannuwa gwiwo duk suka sagar masa kafafuwa suka kuma dinga sararsa da wukansu masu tsananin kaifi da tsafi, ya dinga ihu yana kiran sunan allah.Cikin baccinta ta dinga jin ihu da hayaniya ga alamar ana dukan wani abu sai taji tim a rikice cikin tsananin tsoro ta mike sai sannan ta tuna bayi take ta fito daki jikinta narawa ta sadado tad an leko ta kofa ganin ma'aikatan tayi daddaure a kasa sunyi plate ta saki kofa tare da bude baki idanuwa suka fito jinta ya kara rawa ta dafe kai tare fashewa d kuka tace na shiga uku ba dai yan fashi b? Saukar wani dukan da taji ne yasa ta firgita ta koma a guje fitsari na son zubawa ta hau karkarwa ta rasa me zatayi 180 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar sai sintiri a daki tabbas ta gane muryar wake ihu makiyin ta ne imran Sai da suka tabbatar baya motsi ya mutu sannan suka kyale shi yayi jina jina da jinni kwance suka bincuka dakin tas suka dauki abinda suka dauka suka fito da sauri ta leko kenan tad an hudar kofar ta hangosu suna fitowa da sauri su da yawansu, Tasa hannu tad ode baki gam kar wani sautin ta ya fito tare da runtse idanuwa gam tana kiran sunan allah tuni fistarin dake kokawar zubowa ya fito, said a taji tashin motarsu sannan ta dafe kirji tare da silalewa kasa saman tails ta kifa kanta jikin kofa ta fashe da kuka oh ni mabaruka da zuwana gidannan wallahi sam nan gidan ba alkhairi bane gidanmu zan tafi bazan iyaba azo a kasheni a banza haka kawai ya jawo minmasifa.Shi kam yana can kwance baisan inda yake ba cikin jinni shin a mace ko araye? A wannan daran batayi bacci ba, kuma taji bazata iya duba shiba taga yana lafiya ba mussamman da taji shiru tun bayan fitarsu, tayi zaune gari ya karasa wayewa ta ware gida, sai gaf da asuba sannan bacci ya dauketa dukn da tsoron da ta ke yi. Jin ana dukan kofa tane yasa tashi a hanzarce jiki na rawa ciki tsoro a tunaninta ko sune suka dawo taja da baya tana cewa waye? A storace akace mune 181 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar hajiya ma'aikatan ki bata dai gamsu bat ace ya akayi ne? sukace alhaji ne fa ba lafiya kamar ma ya mutu dn baya motsi "yan fashinnan sun dakeshi sosai yana can kwance cikin jini ta nanata cikin mamaki tace ya mutu? Suka ce eh bude kigani. Wani tunanin ta shiga kar dai sakayyar da take nema ce tun yau allah ya saka mata ya dauki ran imran, kenan zata sakata ta wala ta samu sukuni? Tayi wani murmushi tace shikenan ina zuwa ta wuce ta bude kofar sun dauko shi daga dakinsa sun kwantar dashi a falo har yanzu baya motsi tabi jikinshi da kallo yanda suka raunaka shi sosai gashinan dai bako matsi anya ma yana da rai kuwa? Gabanta ya yanke ya fadi hakannan tajijikin ta ya mata sanyi ta gaza daga kafa sai dai ta sulale ta zauna tana innalillahi wa inna ilaihirrajiun. Tsawon dakiku tana kallon sata rasa wane tunanin zatayi murna ko bakinciki jiya jiya fa suka rabu me hakan ke nufi ya mutu kenan abinda takeso? Daya ya katseta muyi gaggawa madam yana neman taimako idan yanada rai kar mu jnikirta tace to a sanyaye ta mike ba jiki ba kwari waya ta dakko ta rasa ama zata kira da wannan mummunar labara. Mommy tabbas itace mafi kusanci gareta gwanda ita akan ta kira 'yan 182 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar uwansa don haka nambobinta ta daddana ta kira. Ta dade tana ringing sannan ta shiga cikin muryar son kuka tace mommy imran ya mutu? Wayar saida kusa faduwa a hannu mommyn a kidime tace lafiya kike kuwa ko kina mafarki ne? Tace wallahi da gaske mommy 'yan fashi ne suka shigo jiya suke kasha shi gashi can a kwance a mace, zufa ta keto wa mommy jikin ta yah au rawa ta gigice rasa me zatayi tayi sai subhanallah take daddy ya shigo dakin ya dawo daga masallaci ya yajiyo salatinta yace lafiya me ya faru ne? hankalinta ya kara tashi ta rasa mezata ce masa yayinda ta manta da wata waya ya sake nanatawa ki nutsu ki min bayani me ya faru da kyar dai bakinta na rawa ta fada masa ya zauna baking ado yayi shiru yana tunani tsawon lokaci ya mike ya dubeta tare da cewa zo muje da sauri ya fice don fito da motor. Ta jajumo hijabin tad a ta idar da sallah ta fi fito kafar ta sanye da silifas sharifa tana dakinta bata san me ake ba suka shiga motar a rikice, tan agama wayar ta dawo farkur ta tsirawa gawansa ido, mahakacin gudu daddy yayo nan da nan sai gasu a bakin gate ya aje motar suke shigo.Da zuwansu suka nufi inda yake daddy ya daga hannunsa sharaf ya sakihannun ya dago yana kallonsu musamman 183 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar mommy da tafi kowa rikicewa itako mabaruka tana kan kujera tana kallonsu dai dai ita ba murnaba ita ba bakinciki ba Yacewa mommy inaga zamu je asibiti tace to to to amman lafuya ko? Yace ina sa ran haka. Haka suke kinkimeshi zuwa motar. Itama ta sanyo hijabinta ta biyosu. Nan da nan suka iso asibiti ingantacce lafiyayye me kyau da kulawa sai dai akwai bayanin kwandala, emergency aka nufa dashi likitoci suka taru kansa sunyi nasara kam don an same shi da sauran numfashi sai dai ba yanda ake sonsa ba yafita sannan raunukan dake jikinsa abin y abaci anyi sa'ama ba karaya tabbas sun so daukar ransa allah bai basu nasara ba, sai dai aka sa masa odygen don ya taimaka masa duk wani treatment an masa aka sashi special room, likitoci sun tabbatar musu da zai sami lafiya su kwantar da hankalinsu insha allah. Daddy ya samu nutsuwa sosai amma mommy still bata nutsuba ita ko gimbiya ko a jikinta wani gefen zuciyarta bata so bayanin likitaba ba haka taso jiba suka tsura masa ido. Ahankali ya fara samun sauki amman dai bai farfadoba mommy ta kira sharifa tana fada mata tazo asibitin amma bata sanar mata me ya faru ba don tazo a nutse tace amman mommy waye a 184 1 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar asibitin tace kizodai tace asanyaye to shikenan mota ta dauko ta taho, mabaruka kuwa ta basu labarin iya abinda ta sani lokacin da tai so idonta kan gadon dan son ganin gano waye wani ihu ta sulale anan ganin dan uwanta mutu kwa kwai rai kwakwai. Da daddy da mommy ke bata hakuri amman sam taki nutsuwa tana cewa na shiga uku meka tarewa wasu da suke shirin daukar mana kai waHahi muna sonka kada ka tafi ka barmu bazan iya jure rashinka ba don allah ka tashi big bro, A wannan ranar haka suka kasan ce cikin tashin hankali da damuwa kowa jugum jugum. Sunyi waya da rafi'a take fada mataa suna asibiti ga abinda yafaru. Ba shiri ta nufo asibitin ita da mamanta maman ta jajanta ainun ya basu tausayi matuka. Haka mutane suka mutane suka dinga turereniyar zuwa ganinsa duk wanda yayi labarin abin nan take zai saki abinda yake ya taho a rikice. Hana shiga akeyi dinga yi sai dai majinya tansa asibitin makil da jama'a yan dubiya, sai dare sannan daddy da mummy suka tafi da sharifa damuwa dam aransu bad an sunzo bad an dole ka'I dar asibince mutum daya zai kwana dashi itace kuma mabaruka. Ranta ya. sake baci saboda barinta de akaji dashi meyasa ba;a bar sharifa ba kamar 185 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar yanda taso daddy yace a'a ita yafi cancanta saboda itace matarsa. Sai washe gari sannan ya fara dawowa hayyacinsa lokacin da taga yana motsa kafarsa ne ta fita ta sanar da likita tare suka shigo. Alhamdulillah jiki yayi kyau sosai nunfashinsa ya daidaita har likita ya daga masa odygen din sai dai tsami da jikinsa yake ga kansa har yanzu bayajin dadinsa ya bude ido yana kallon inda yake asibitin yayi shiru yana tunano abinda ya faru da sauri ya juya kansa wajen mabaruka ya dubeta cikin murya can kasa yace basu miki komai ba mabaruka ko sun tabaki? Ta murtuke fuska tare da cewa a'a can ciki ya lumshe idanuwa yana jin wani dadi tare da hamdala likita ya leko fuskarsa yace to kakejin jikinka yanzu? Yayi murmushi yace lafiya lau ba wani abu kainane kawai ya jinjina kai cikin gamsuwa that's good zai saki insh allah sannu ko, ya daga kai alamar amsawa ya juya yana kallon mabarukar yace idan wani abu ya faru ki nemeni tace to ya juya ya fice yana cewa allah ya sawake tace amen can ciki: Ya juyo yana kallon ta fuskarsa da murmushi yace sannu mabaruka tayi masa banza tana turo baki ya sake 186 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar cewa ba dai abinda abinda suka miki ko? Tace eh cikin gajiyawa yace ka basu gankiba ta sake cewa eh, yayi shiru yana kallonta ganin yanda take fushi bayansa yayi duk ya sandare yana son ya dan tashi zaune ya yunkura zai tashin duk jikin ya masa nauyi yayi yayi ya tashi ta kasa tashi, tana kallonsa sai ma ta juya kanta ta zaro waya tana game ya dan dubeta a sanyaye yace kidan taimamin inshi na gaji da kwanjiyar, tamkar ta kwadeshi da mari don me wai yake son takurawa rayuwarta? Taki ta matsa. Ya sake nanatawa don allah ki taimaken na tashi ta wuce fou tana turo baki ta nufoshi ya dubeta da kyau yace bashshi kawai kije ki kira min nurse inaga akwai matsala ko? Banza tayi masa tana kokarin dagashi din ta taimaka masa din tad an dungurar dashi don ba zaunar dashi tayiba yasa filo ya dan jingina yana lumshe ido cikin jin jikinsa, ya dubeta yace dan snmin ruwain kuskure baki.Tayi kyam cikin takaicinsa wallahi fa tagaji bazata iya da dawainiyarsa ba don ba dolensa bace ya bari wadanda suka zama dolensa suzo su masa yasake cewa kiyi hakuri daga wannan shikenan ta wuce ta dauko ruwa tare da dungura masa ya bude bakin ya kurba yana kuskurawa ta dauko container ta tare masa tare da kauda 187 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar kanta tana yastina fuska tamkar me shirin amai. Ya zubar ya sake kuskurar wani ya zuba yace shikenan na gama nagode, ta wuce ta zubar harda toshe hanci ta dawo ta aje ta koma inda ta tashi taci gaba da gaba game din fuskar babu annuri, sai can sannan su mommy suka zo hade da nau'ikan abinci kala kala da kayan fruit.Suka tambayeta me jiki a can makosh ta basu amsa sunyi murna sosai da ganin tashinshi, sharifa ta dan hada masa tea ta bashi ya shad a danwani abu marar nauyi, har hira akai dashi aranar da labarin abinda abinda ya faru daddy yace wallahi bazan yar daba sai na dauki hakuri zan hada shi da commissioner yan sanda don gobe ko hanyar gidan bazai biyo ba bare yasa a shigo gidan dukkansu sun gamsu da hakan. Gabadaya asibitin ya gundureta ga jikinta baya mata dadi inda son samu ne tad an yi wanka, wajen yamma ta dubi mommy tace in son naje gida indanyi wanka tayi shirutana kallonta can tace a'a wane waka ki jira dai, tahade rai tamkar ta fasa kuka ya dubeta ya dubi mommy yace kibarta taje din nasan mabaruka tana da jumirin wanka bata zama haka a rana nasan ta kanyi har uku to bare kuma batayiba zataji jikinta ba dadi.Tayi jimm sannan tace yo shikenan kije amman 188 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar 1 a a n awa biyu na baki kije kidawo kafin magriba, batare da amsa ba tawuce tana kumburi mommy ta bita da kallo hart a fice tace allah ya shirya, madadin tawuce gidanta sai tawuce gidan mommy ma'aikatan gidan suka bita da kallo basu gabanta ta wuce tsohon dakinta ta nufa ansa masa key, keyn na jikinsa ta murza ta bude tashiga kan gado ta fada tayi lamoo gaba daya rayuwarta bata mata dadi wallahi da tayi farinciki amman ya akayi sulaiman ya samo wadannan yan daban suka shigo gidan imran da gaske neman ransa sukayi koko suzo su dakeshine? Tace ina sulaiman bazai hakaba ninasan sulaiman dina bame kisa bane, karshe dai bayi ta fada tayo wanka tare da sallar da batayiba gado ta fada da tawul din jikinta bacci me matukar dadi ya dauketa. Bangaren sulaiman kuwa suka koma masa washegari suka tabbatar masa da lalle ya mutu don sun baro shi kwance babu rai, yayi farin ciki sosai ya kawo saran kudinsu yabi yasu suka wuce abinsu. Awannan daren yayi farin ciki sosai don gani yake mata ta zama tasa lallai mabaruka tashice ya godewa yayar sad a ta kawo masa wannan shawarar da bebiba da yanzu yana nan cikin bakincikin karshe ya mutu ahaka haka washegari ya saurara yaji anzo masa da labarin 189 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar jan'izar imran din, amma har rana ta take bai ji kishin kishin bay a shiga kokonto kwatam yaje gidansu mabaruka, inn ace ke cewa wai sulaiman wana irin ganganci kay me nace maka ba cewa nayi kasa asace imran dinba shine suka dake shi suka baroshi kwance? Yace eh wani abnne ya kikaji? Taja tsaki tare dawcewa kai dai wallahi baka jin shawara sam way ace maka ya mutu? Yayi wuri wuri da idanuwa yace wayanda nasa mana sun tabbatar min da cewa ya mutu dan baya motsi tace to bai mutu ba yana nan da ransa yana gado asibiti saidai bamusan ko zai tashiba ko ba zai tashiba don baisan indaa kansa yake ba tunada aka kaishi, zufa taketo masa ya ciro hankachief yana share gumin hankalinsa ya tashi tsoransa daya kada a damkoshi musamman da said a ska sanarwa imran din daga gareshi ne shi ya turosu. Yace na shiga uku kada fa su kamani tace su sun fada masa kai ka turosu?, yace sosaima mdanhar fada na musu kan katobarar da sukayi yanzu gashi sun sani a masifa. Tace ah to kai ka sani ai kin bin shawara ta yajawo maka gaka ba mata ba biyan bukata saima jefa kanka dakayi a bala'I, mikewa yayi yana cewa ina zuwa Sai da tasha baccinta ta matse sosai sannan ta tashi ta dauko daga 190 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar kayan data bari nata ta saka tare da dako hijabi ta fito, a hanya rafi'a ke kirana zantafibaki dawoba tace ina kan hanya ki jirani tace to saikin iso ta hau adaidaita sahu har asibitin ta sallameshi tashiga mommy ta dubeta tace sai yanzu kika dawo? Batace komai bat a nemi wui ta zauna shikuwa idonsa a kanta yana jin dadin ganinta musamman da tayi wankannan duk dab a wata kwaliya me zafi tayiba suka rabe ita da rafi'atu tana cewa banson zaman asibitin na rafi'a duk ya gundureni, ta dubeta tace toya zakiyi mabaruka ya zama dolene ki jure mijinkine dolenkine kima godewa allah da ba kashe shi sukayi bad a yanzu anski takaba tsaki taja tare か da dauke kai tace da kasheshi sukayi BUIH! ISWS134 da naïf farinciki 15 wallahi da sauri ta rufe mata baki kar ajita, ta mike da jan hannunta suka fita zuwa baranda ta dubeta tace baki bari bako mabaruka har yanzu kina nan akan bakanki dukda kin aureshi a yanzu kina matsayin matar fa? 25D Tace dam dan wannan ne kika fito dani to bari kiji so daya ne haka kiyayya daya cee ba wata tunda ina kinsa baШОК abinda В КОШЕ 19 zai canza da kiyayyarsa aka halicceni don haka har gobe ban sansa bazan taba sonsa ba hakan yasa na gwammace mutuwar sa akan rayuwarsa. Tace wallahi kiji storon allah 191 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar mabaruka ki san me kie yanzu ba lokacin cigabda sakarcin nan bane dole kisan me kikeyi ki tallafi aurenki ki rumgumi mijinki don shine tsirarki kar kice zaki ja da ikon allah kinutsu mabaruka ina fada miki tun kina dadama kar tazo ta wucemiki kizo ranar dazaki fara kuka da idon ki imran ba kamar kowa bane baa bin yarwa bane idan kika yarda kika rasashi har abada bazaki samu kamarsa ba wallahi wallahi, Taja tsaki tareda wucewa tana cewa saiki tayi na fada bana sonsa saime ya mutu ma meye ruwana.Binta da kallo tayi ta rasa me zatace al amarin mabaruka ya fara bata tsoro tafaje kafiyada naci. Wucewa kawai tayi ta hau mota ta tafi gida tunda ta riga tagama bata mata rai. Haka dai suka kasance a asibinn ahankali yana samun sauki sosai saboda kulawar likitoci ga ingantacan magunguna abinci sai wanda likita tace abashi don hake ya samu kafiya sosai da rana zai wuni dasu momy da sharifa sai daddy sannan gimbiya mabaruka yan dubiya suna ta zuwa ganinshi. In dare yayi abarshi daga shi sai mabarakar ta koma gefe ti kyaleki tana kumburi komai ya mata kunci in zai ta Magana bazata amsa masa ba sai dai ya giji ya hakura. Satinshi biyu asibitin aka sallame shi ba abinda ke damunsa ya warware sosai. Sulaiman 192 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar kuwa aranar da akayi sallama. A ranar ake damkeshi inna ta fito waje tana ta bala'i da basase zaga wai sharri akawa danta akalin taji maganar abakin inna aka sashi mota suka tafi. Inna ta bisu da dawatsu tana jifa tamkar mahaukiya tana allah ya isa shegu masu bakaken fuska da zuciyoyi masifa da bala'i ya sauka kanku tunda kun daukar min da.... Ku biyo ni a 3 za ku ji duk yanda hakan zata kasance, karan batta tsakanin Inna da Mabaruka, haka nan soyayyarta da Imran duk ta ya ya? Ku biyo ni za kuji, akwai labari. Kuyi hakuri mu tara a cikin littafi na uku (3) da yardar. Allah, zai fito nan ba da jimawa ba, na gode sosai Makaranta. Sai mun hadu a (3) 193 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar DANDANO DAGA 'WAYE ANGON?' (Kashi Na Uku) Tunda ta gama abin da take ta shiga wanka, bayan ta turara duk gidan da nau'in turarukansa, tun daga dakuna, toilet har da harabar gidan. Sannan ta hada na wankanta wanda yasha turarukansa masu kama jiki, ta fito. Ta dade gaban mirror tana lindar jikinta da nau'ikan mayukanta masu daddadan kamshi da sa nutsuwa. Fatarta har sheki take, tayi laushi jajir tamkar jini zai fito, musamman diga-digan. Ta nade gashinta bayan ta turara shi da turarukansa, ya yi baki wuluk da laushi sai Kamshi ke tasowa, ta sake shi baya yana reto. Fuskarta tasha kwalliya me kyau da tsari, sai walwali take irin kwalliyarsu ta matan zamani, ko ina ta gyara shi na jikinta. (2) subari minisa Tayi tsaye gaban wordrove tana tantance kayan da ya kamata ta saka, duk kayan da ta daga sai taga sun kaskanta tasawa Imran dinta, darajarshi ta wuce haka. Da kyar dai ta zamo wasu wadanda tasan sune yafi son tayi masa kwalliya da su, yakan rude ya rikice ya yi ta sabbatu, yana cewa "Kin min kyau my Mabaru." 194 WAYE.ANGON? Maryam Ja'afar Tayi murmushi ta dauko su tare da shinshina kamshin turaransa wanda suke amfani da shi, ita da shi. Ta lumshe ido tana jin wani dadi da farin ciki ta ce "Ina sonka my Imran, Allah dawo min da kai lafiya." Tasa kayan ta tsaya gaban mirror a kullum idan ta sa su takan tambayi kanta anya ita ce ba canzata aka yi ba? Tamkar 'yar baby kayan suna karfarta wando baki shortniker. Ko cibiya bata rufe mata ba. Ta saki gashin a baya yana reto, tayi murmushi ta ce, "Nasan za ka yi farin ciki da ganina, haka nima ina tayaka." Ta Kara turare jikinta da nau'ikan turaran daidai sanda take jin hon dinsa. Da sauri ta aje abin da ke hannunta tana murna ta fallo da gudu cikin kuruciyarta 'yar shalau-shalau marar nauyi kamar budurwar Turawa,a kagare take ta ganshi tana masifar kewarsa. Yayin da shi ma bangarensa kamar ya fita jikinsa har rawa yake kasa rufe motar ya yi don son ganin Mabarukarsa da tun a jirgi take matsa masa da kira. Na gaji da jira fa my, na kusan kuka fa? Cikin shagwabarta me rikita shi. Ya taho da hanzari a daidai kofar suka ci karo, kowannensu bakinsa ya kasa rufuwa don jin 195 1 1 t j k t t S WAYE ANGON? dadin ganin dan'uwansa. Maryam Ja'afar Da zuwansa ya buda mata hannuwansa don fadawa kirjinsa, kamar yanda suka saba. Ta fallo a guje tana zuwa tayi tsalle ta fada jikinsa tana cewa. "Welcome back my desire." Cak ya dauketa ya rufe ta da hannuwansa yana jin wani nishadin jin dumin jikin matarsa da ya yi kewarsa kwana biyu. Suka lumshe idanuwa a haka kowa yana jin nutsuwa na shigarsa da nishadin, kasancewa da juna. Sannan ta diro bakinta washe tana dariya ta kasa cewa komai, sai tsalle-tsalle take. Shi ma dariyar yake yana kallon yanda take zumudi, sai ya ce yana kallonta bayan ya dan rankwafo. “Fadi mana menene?" Tayi dariya ta ce "Ina murna my one, naji dadin ganinka." Ya ce yana dariya "Ke kadai ko?" Ba amsa sai dariya kina jin dadin ganin Imran din ki ko?" ta daga kai tana kallonsa. Ya ce, "Good! Zo muje ciki yau zamu sha hira ko?" Та ce, "Eh." lokacin da take tura hannunta cikin nasa "Eh mana, na tanadar maka labarai masu zaki da dadi." Yace, "Allah?"Ta ce, "Allah my." Ta langabar da kanta 196 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar jikinsa suna karasa shiga zuwa dakinsu, tana jin wani farin ciki da walwala, Imran dinta ya dawo daga tafiyar da ya yi kwana uku. Shima bangarensa yana jin dadin dawowarsa gareta, wacce ya yi missing ta na kwana uku sai dai waya. WANI BANGAREN Tun safe take tsaye ba ta huta ba saboda aikin kasancewar ranar girkinta ne, ta gama kwashe tuwon dare a flask dinta masu kyau da tsada ta juye miyar a flask ta aje a kitchen. Wajen rijiya ta nufa don ta debi ruwan wanka ta sirka da na zafin da ta dafa, bayan ta dauro zani da tawul wajen Magriba kenan don har an fara kiran sallah. Inna na zaune tsakar gida duk tana kallonta ganin ta sungumi bokitin ne zata shiga bandakin yasa ta mike ta tarė ta tana cewa ke tsaya! Taja ta tšaya tana kallonta, bayan ta aje bokitin tana cewa, "Na tsaya, meye?" Ta dubeta ta ce, "Me ki ke nufi ne? kin gama tuwo kin kwashe da kanki alhalin kin san ba tsarin gidannan kenan ba?" Ta kalleta a wulakance ta ce, "Tsarinki na da kenan, kin wa wasu amman ni Mabaruka na rantse ba za ki min haka ba. 197 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Ni nayi girki kuma ni zan raba in ba kowa, yanda naga dama kuma ba wanda ya isa ya hana ni, ehe! Ta dube ta da kyau ta ce, "Ai ko za ki ci ubanki wallahi, ba ki isa ba ba tsarin gidana ba kenan. Yau kwananki tara gidannan amman har kina wani gadara, sai nasa ya sake ki walłahi shegiya 'yar gidan mahaukata wacce ake aura mata maza biyu." Ranta ya bace sosai, ta ce "Tsohuwa ki iya bakinki, ki san me ki ke fada, na rantse zan daka ki a gidannan ba a min wasa fa!" Samirá ta shigo jin hayaniyarsu tana cewa "Meye? Meye nake jin hayaniya?" Mabarukar ta juya tana kallonta ta ce, "Ki shigo kiga da دو wa ake yi mana.’ Ranta ya baci itama ta ce, "Au! Da ke ne kenan tun zuwanki gidannan ki ka fitine mu." Inna ta ce, "Wai dukana zata yi." Samira ta zabura "Me? Ita din banza, yo akwai me taba min ke in kyale shi, ko shi dan gidan uban waye?" Ta ce, "Ai ko za ki gani matukar ba ki gargade ta ba a kan karambaninta gare ni." Inna ta ce, "Sannan kin san ba a wankan dare gidannan amman ke naga kina son ki raina min wayo ko?" 198 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Tayi dariya ytare da dukan cinya ta ce, “Wallahi har na cikin dare za ki gani ba ma na dare ba, tunda kin san auro ni aka yi." Ta ce, "Da kyau fitsararra! Zan yi maganinki." Та се tana zaro mata idanu "Sai dai muyi maganin juna tsohuwa." Ran Samira ya 6aci ta daga hannu zata kai mata duka, caraf! Ta rike hannunta tana kallonta ta ce, "Karya ki ke 'yar marassa kunya, kin yi kadan ki dake ni, dubi fatata da kyau." Ta ce, "Za ki gani kuwa na rantse." Ta fincike hannunta ta sake dagawa zata mareta, kan ta sauke hannunta jikinta ita ta kai mata nata gigitaccen marin. Ai fa kan ka ce me? Fada ya kaure tsakaninsu, dan bokitin wankan aka daga sai jikin Inna aka watsa mata shi tas, tayi jagab. A wannan halin ne Sulaiman ya shigo, idonsa ya sauka kansu, ya zaro ido ganin faruwar abin yayin da Nafisa tana daki abinta ranta kwal. Tana godewa Allah da ya kawo musu Mabaruka gidannan, damuwarta tazo karshe ko ba komai dai ta koshi. 199 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar TSOKACI A cikin wari dare, lokaci daya ba zato babu tsammani, wata Kasaitacciyar gobara ta tashi a wasu gidaje uku, wutar da ke ci ta samu makamashi mai girma wanda yasa ta bunkasa. Tun kafin zuwan 'yan kwana-kwana, hasashe ya tabbatar da cewa koda ruwan KOGI ba za su iya kashe wutar ba, to ballantana kuma ruwan RIJIYA. Duk a cikin littafin WAYEANGON? Tirkashi! Labarin BABANA DAMIJINA ya zamo tauraron fito da wani salo mai matukar ban sha'awa da birgewa. Makaranta sun yaba, sun kuma jinjinawa Marubuciya MARYAM JA'AFAR. Na tabbatar wasu za su yi tunanin daga shi ba za ta iya rubuta littafin da ya kai shi dadi ba, wasu kuma za su yi tunanin ta juye dukkan basirarta a cikinsa. To amma lokaci daya sai ga shi ta faso da babban labari, littafin da ya ce wa BABANA DAMIJINA kauce ba ni wuri. 'WAYE ANGON?'. Labarin ya yi matukar kayatar da ni, don kuwa basirarta ta kara bayyana a cikin labarin mutane hudu da suka zamo taurari mafi shahara a cikin labarin, wato MABARUKA, IMRAN da SULAIMAN, a gefe kuma ga babbar kawa RAFI'ATU. WAYE ANGON? Ya fito da sabon salo na daukar hankali, akwai babban darasi a cikinsa. A gaida 'yar JA'AFAR (Maryamu) -NAFI'U SALISU (Marubuci/Manazarci) 200 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na

Chapter 9 of 10