Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 10
ke gani shi ke da mata?" Ya nutsu tsawon dakiku.sannan ya ce "Kai! I can't, ban san wa zan ce shi ne angon ba, wannan sai mai shari'a." Ya yi jim sannan ya ce "Ka taya ni addu'a abokina a bani 45 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar matata, zan iya mutuwa idan a ka ba wancan, ko kuma na kashe shi wallahi." Ya buda baki yana salati, cikin tsorata da mamaki yake kallonsa. Ya ce, "A'a kar ka fara wannan tunanin, ka bar wa Allah komai kar ka bi son zuciyarka, Allah shi zai ba mai mata matarsa." Bai iya cewa komai ba, ya yi daijim yana sauraronsa. Koda suka shiga daki ta zaunar da ita bakin gado tana dubanta. Ta сe, "Me ki ke tsoro ne?" Tayi shiru tana kallonta ba amsa. Tayi murmushi ta ce; "Na fahimce ki abin da ki ke tunani ba haka ba ne. Ki kwantar da hankalinki, Sulaiman dai mijinki ne ba komai yasa ya bukaci haka ba sai don samun nutsuwarki da tasa, don farin cikinku. Don kin kwana a nan ba wani abu ba ne, kowa yasan kina tare da mijinki ne bare ba wanda yasan kina nan..." Ta katseta a sanyaye "Amman wannan ha'inci ne bai kamata na ha'inci Mahaifiyata ba. Sannan ba ni da tabbacin waye mijina tsakaninsu. Ina tsoron sabawa Mahaliccina, haka nan idan 46 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar far a Mamana taji ina tare da Sulaiman bare na kwana da shi na rantse sai ta karya ni." Ta zauna tare da dafa kafadarta cikin lallashi. "Ba abin da zai faru da ke, kiyi tunani tun yaushe ku ke cikin rashin nutsuwa da fargaba? Yau kadai idan ku ka wuni da juna ku ka kwana za ku sami nutsuwa ku shiryawa tanadin gobe. Ki nutsu da kyau hakan babu aibu, don shi mijinki ne ya bada sadakinki an kuma daura muku aure yana da ikon fita da ke duk in da ya so." Tayi shiru tana tunanin maganarta, wani gefe na zuciyarta yana son amince mata wani gefen kuma yana hanata. Da dadin bakin Basira da lallashi ta shawo kanta a kan eh zata kwana din amman a kan sharadi. Ta dubeta ta ce, "Wane sharadin kenan?" Ta ce tana kallonta "Ba zan kwana tare da shi ba a daki daya, sai dai su kwanta da mijinki ni kuma na kwana tare da ke." Tayi dariya ta ce, "Wayo ko Mabaruka?" Murmusawa kawai tayi ta sunkuyar da kai ta ce, "Shi kenan kada kiji komai hakan za a yi, amman muje muci abinci muyi hira 47 WAYE ANGON? yau sai mun kái dayan dare muna hira." Maryam Ja'afar Haka kuwa ta kasancen, sun dade a falo suna labari gefe kuma da dan abin sa wa a baki. Bai ce komai ba suka shige shi da Mansur din wani dakin su kuma suka shige dakinta. Can ma suka dasa da ita, musamman hirarmu ta mata da Karin shawarwari. Taji dadi kam da sukuni ta dinga nishadi musamman kasancewarta da masoyinta ga abokanan hira masu mutunci da ban dariya. Sun ba su shawarwari a kan addu'a ce kadai mafita gare su. Ta kwnata tana nishadi tana cewa a ranta me ake da wnai Imran can! Ina! Ai sai Sulaiman. Haka zalika ta tashi da farin ciki, sai dai kash! Tuna yau za ayi ta ta kare yasajikinta ya yi sanyi kalau. Fargabarta ta dawo sabuwa, addu'ar da su Mansur suka bata ita take ta nanatawa a baki, har suka baro gidan karfe goma. A hanya Momy ke kiranta ta ce tana kan hanya. Can nesa da gidan ya ajeta a kan sai sun hadu a kotu, ya juya ya wuce. 48 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar ifA harabar gidan suka hadu da Imran. Ya yi kyau sosai yasha dream yard ya yi matual dress, fuskarsa manne da glass fari yana kokarin shiga motarsa wacce a ka wanke masa tana ta sheki. Suka hada ido biyu ya sakar mata murmushinsa mai kyau. Yayin da tayi saurin dauke kanta ba ta dai harare shi ba ta shige ciki da sauri tamkar wacce a ka ce a kamo. Ya yi siririyar dariya tare da fadawa mota yana ambaton sunan Allah, ya ja motar ya fice zuciyarsa cike da tunanin 'yar Mabarukarsa. la112 1Karshen tika-tika-tik! ** A KOTU Kamar yanda Alkali ya ce a yau zai yanke shari'a, zai ba mai mata matarsa a yau dinnan. Kuma koda aka fara tasu ce kan gaba ya kara jaddadawa lallai a yau zai yanke hukunci. 'Yan cikin Mabaruka suka hautsina, zufa ta keto mata, 49 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar jikinta ya yi sanyi kalau, gabanta ya dinga dukan tara-tara, fargaba ta cikata dam. Har sai da Rafi'a dake gefenta ta riko hannunta tana cewa, "Ki nutsu Mabaruka ki ta ambaton sunan Allah, za ki samu nutsuwa." Ba ta iya amsawa ba sai dai ta daga kai saboda yanda bakinta yai nauyi ta baza kunnuwa da idanu tana kallon Alkali. Imran kuwa da Sulaiman ban san wa ya fi shiga fargaba da zullumi ba, sai kallon kallo suke. Ita kanta Momy a zulumce take, tana tsoron kar 'yarta ta shiga gidan Sulaiman ko ba lallai Imran ba tana tsoron matsalar gidansa, sabanin Babanta da fargabarsa ba wata ba ce. Da farko Alkali ya faro da nasiha da wa'azi, ya kawo ayoyi da hadisai a kan yanda aka ce mu Musulmai muyi aure. Maza an ce su aura daga bibbiyu zuwa uku har hupu, idan sun ji tsoron ba za su yi adalci ba to su tsaya ga daya. Babu wata aya ko hadisi da aka ce mace ta auri fiye da miji daya, sai dai ko in auren ya mutu ko mutuwa ko 50 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar rabuwar aure shi ne mace zata sake auren wani namijin. Ba don komai ba kuma sai don adalci ne hakan. Kai kanka ka nutsu kayi tunani a kan abu daya ma kawai mu dauke shi dangane da daukar ciki. Yau in tana dakin wannan gobe tana dakinw anna sai ta sami ciki, to ta ya ya za a gane cikin wannan ne 'ya'yan wannan ne? Ba yanda za a yi hakan ta faru. Don Allah bai ce ayi haka ba, ba wata dabara ko hikima da zai sa mace ta auri maza biyi, yin hakan kuma babban zunubi ne, rashin tsoron Allah ya shigo da rashin tsoran azabarsa. Duk wanda ya yi haka kuma ya sabawa Allah da Manzonsa, sannan akwai tsantsar jahilci da isa, don sai jahili zai yi haka, kai ko jahili in dai ba mahaukaci ba ne ba zai yi irin haka ba. Babu inda ake auren maza biyu, mace namiji daya take aure, don haka iyayen wannan yarinyar sun aikata babban sabo da zunubi, dole ne su nemi gafarar Ubangiji suyi ta istigfari. Idan rashin jituwa ce su sasanta kansu, an haramtawa Musulmi gaba da junansu, an fi so su kasance ma su yafiya 51 afar la Li a 1 WAYE ANGON? da hakuri ga dan uwansu. Maryam Ja'afar In ita mahaifiyarta tana jin haushinsa ta rike abin da ya mata sai tayi hakuri ta dubi matsayin da Allah ya bata а yanzu ba don yinta ba shi ma yasa wa kansa dangana. Su daidaita da junansu don zaman lafiyarsu da kwanciyar hankalin yarinyar da suka haifa, don a kullum da ba shi da kwanciyar hankali matukar iyayensa ba sa jituwa, ya kan rasa nutsuwarsa. Sannan duk wannan abin da ya faru rashinjituwarsu da hadin kansu ne ya jawo haka, in akwai jituwa da kyakkyawar fahimta sai su tattauna su shawarta a kan wa ya fi cancanta su ba auren 'yarsu? Sai su tantance su aura mata a nutse da aiki da ilimi amman a haka kowa yana ji da kansa shi fa ya haifi 'yarsa don haka shi zai aurar da ita ga wanda yaso, shi yasa hakan ta faru." Alkalin ya dan tsahirta tare da yin wasu rubuce-rubuce sannan ya ci gaba. "Don haka zamu yanke hukunci mu ba mai mata matarsa." Dukkansu suka kwalalo idanuwa da kunnuwa, yayin da 52 C WAYE ANGON? ita kuma faduwar gabanta ya karu. Maryam Ja'afar Ya dubi takardun da ke gabansa sannan ya dago ya cсе, "Imrana Umar shi ne a ka fara daura mata aure da shi a kan sadakin da ya bayar lakadan, shaidu sun shaida an yi addu'a kuma kanin Babanta wanda suke Ummi wa Abba shi ya daura mataa matsayin waliyyinta tare da nashi. Don haka ya tabbata lallai babu mai mata face shi, kasancewar shi aka riga aka daura kafin wancan." "Innalillahi wa'inna ilair'raji'un! Hasbunallahu wani'imal wakil! La'haula wala kuwwata illa billah!" Abin da take nanatawa kenan, ta dora hannu saman kai. Alkali ya ci gaba. "Daurin auren da ya biyo baya ya zama shirme, harbin iska ba shi da mata saboda akwai mai matar an riga an kuma daura din. Don haka sai ya nemi wata. A yau muka kawo karshen wannan shari'a, idan kuma akwai mai son daukakata yana iya daukakata daga nan kotun Musuluncin zuwa wata kotun ta gaba." Wannan kenan. Tsalam! Ta mike ta dubi Alkali fuskarta da niyyar kuka 53 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar ta ce, "Babana shi ya daurawa Sulaiman aurena, kuma ya ce shi yaba kowa kuma ya san uwa ba ta daura aure, ya za a yi a ba shi?" Ya kalle ta tsaf ya ce, "Yarinya na riga na yanke hukunci, ga mijinki nan." Ya nuna Imran. "Saboda kanin mahaifinki zai iya daura miki aure kuma kasancewar shi ya daura yasa a ka ba Imran din. Kamar kuma yanda na ce idan bai yi muku ba za ku iya daukakawa." Ta fashe da kuka ta haďa hannuwa tare da cewa "Don son Annabi don iyayenka ka canza ka ba Sulaiman, wallahi ba na son Imran din." Bai saurareta ba ya buga abin da ke gabansa alamar ya tashi, duk a ka mike ana amsa masa daga nan ya wuce abinsa. Dogaransa suka bi shi da takaddun da ya bari. Ai fa nan kotu ta hau kace-nace, ayarin Sulaiman da shi kanshi Sulaiman din sai bala'i suke, yayin da shi gogan ya yi tsaye ya kasa cewa komai. Sam bai yi tunanin haka zata kasance ba, tuni ya barwa kansa shi za a ba mata saboda uba ke daura aure. Imran kuwa da ayarinsa sai murna da farin ciki, bakinsa 54 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar ya kasa kullewa, hatta Momy tana cikin farin ciki sabanin Sharifat. Daddy da Rafi'a ma ba a bar su a baya ba. Ita kuwa ta juya nan ta juya can, duk ta kidime ta rasa a ina take, ta manta komai. Jiri ya dinga kwasarta, ta dinga yi luu-luu ana juyata idanunta suka rufe, kafafunta suka kasa daukarta. Sai dai aka ji rijib ta zube a nan. Nan fa aka yo kanta a rude, musamman Imran din shi kanshi Sulaiman ya runtumo da gudu da Momy da Rafi'a ke mata fifita. Cak! Imran ya daukota tamkar jinjira a gigice ya nufi waje da ita zuwa mota, sauran kuma suka rufa masa baya. Wani abu ya tokare makogwaron Sulaiman, ransa ya baci ya dinga huci tamkar kumurci, idanunsa suka kada jajir. Ya yunkura zai bi shi ya kai masa duka, abokansa suka rike shi tare da tunasar da shi wancan dukan abin da ya jawo masa. Sam ba ya jin su ba ta wannan yake ba, ya dinga kokarin kwace kansa, ko da ya kwace din yana zuwa suna barin 55 WAYE ANGON? wurin da motarsu, suka Ôace masa 6at! Maryam Ja'afar Ya dinga kuka yana dake-daken duk abin da ya tari gabansa, tamkar zai cinye mutanen da ke gurin, idan kaga yadda yake yi kamarwani sabon hauka. Asibitin suka nufa da ita, da zuwansu a ka ba su gado, ba da jimawa ba ta farfado kasancewar bata yi nisa ba a sumar. Ba kowa dakin sai Rafi'a ta shiga wuwwurga idanu don son gano a ina take, ta daga kai ta kalli karin ruwan da ake sa mata, ta gane a asibiti take sai a sannan komai ya dawo mata. Ta dubi Rafi'ar cikin yanayin mutuwa jiki. "Ba da gaske ba ne ko Rafi'a?" Ta ce, "Ba da gaske ba me?" Ta ce, "Sulaiman shi a ka ba ni ko ba Imran ba ne?" Tayi shiru. Sam ta kasa cewa komai bata san me hakan zai jawo ba, idan ta fada. Kafin ta ce komai Momy da Sharifa suka shigo suka hau mata sannu, binsu da ido dai take tana son karyata abinda zuciyarta ke son tuna mata. Kamar hadin baki Daddy da Imran suka shigo suma. Da zuwansa ya hayo kan gadon a dan birkice yana mata 56 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar rsannu ta bishi dai da ido ta kasa amsa masa, so take a bata amsar abind atake zargi. Ya hau rawarjiki da ita me take so me zata ci ba dai in da ke mata ciwo? Sam taji bakinta ya kulle, sannan idonta ya kasa daukewa daga kansa. Likita ya shigo ya duddubata tare da tambayoyi gareta, jikin ba wata matsala, amman ya ce tana bukatar hutu sai. gobe zai sallame ta. Ya rubuto wasu magunguna da za su sa ta kuzari da karin lafiyarta. Imran din ya fita don nemo su. Dady ya dubeta ya ce, "Sannu my doughter ta daga kai ta kalle shi tare da amsawa a hankali." Ya ce, "Kin tabbata ba wani abu da yake damunki ko?" A can kasan makoshi ta ce, "Eh Daddy." Ya ce "Good, idan kina bukatar wani abu ki sanar da ni kin ji ko?" Та daga kai alamar 'To.' Ya ce, "To zan wuce sai anjima zan dawo." Ta се, "To a dawo lafiya." Ya dubi Momy yana cewa "Zan je wani guri دو idan na dawo zan biyo ta nan." Ta ce, "To shi kenan a dawo lafiya."Ya amsa amin. Sharifa ta mike tana cewa "Nima zan bika Daddy." 57 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Yanayin fuskarta ba annuri, ya ce "Don me ke da za ki zauna kuyi jinya. Ta yatsina fuska tare da turo baki ba tare da ya ce komai ba. Mommy ta riga ta gama fahimtarta, sam ba son auran take ba da Yayanta, duk saboda yanda Mabarukar take nuna kiyayyarsa a zahiri kuma bata da laifi, waye zai so dan uwansa ya cutu? Tayi murmushi ta ce, "Me yiwuwa ta gaji ne tun safe fa." Ya ce, "Amman ai dole ce zata sa ta tsaya din." Ta ce, "Ka barta dai taje din da dare ta dawo." Ya yijim sannan ya ce "Shi kenan muje." Tayi dariya ta dubi Mommyn ta ce, "Thanks Momy."Ta rufawa Daddyn baya. Ita ma tayi dariya ta fita don raka su. Dakin ya rage daga Rafi'a sai Mabarukar ta juyo ta kalli Rafi'ar, ta ce "Fada min gaskiya Rafi'a, waye Angon? Wa kotu ta ba?" Tayi jim tana kallonta, dole ne ma ta sani yau ba sai gobe ba, ta kamo hannunta cikin kulawa ta ce, "Komai ki ka ga ya faru ga dan Adam daga Allah ne, Mabaruka me 58 WAYE ANGON? kyau ko akasinsa. Maryam Ja'afar ar Ba kuma don ba ya sonka ba sai don ya jarabaka kuma me yiwuwa shi ne mafi alkhairi gare ka...' Ta katseta "Ki fada min kawai bana son sharar fage, duk nasan wannan, ki fada min waye mijina?" Ta kalleta da kyau, ido cikin ido ta ce, "Mabaruka Allah ya yi miki baiwa, ya zabe ki a cikin dubban mata, ya azurta ki da miji na kwarai mai addini da kamala. Ba kowacce mace ba ce take samun irin mijin da ke ki ka samu ba, kin yi miji ba ki da bakin cikin gidan aure, za ki yi rayuwamai kyau da dadi." Ta dai tsura mata ido tana kallo, ta kasa cewa komai. Ta ci gaba da magana a tausashe, duk a kokarinta na kwantar wa kawar tata hankali don ta nutsu ta gane abin da take fada mata gaskiya ne. "Mabaruka! Imran shi ne Angonki, shi ne kotu ta ba." Tamkar wacce a ka dasa, ta zamo a kan gadon tare da kurawa Rafi'ar ido tamkar yau ta fara ganinta. Ita ba tunani ba ita ba kallonta ba, ba ta ce kuma komai ba. Har sai da ta taba ta, amman ko motsi. Sai da ta jijjigata daidai zubowar wasu hawaye masu 59 1 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar dumi daga idanunta wadanda ba su nuna alamar zuwansu ba. Ta ee, "Mabaruka kuka kuma?" Tà kalle ta ta ce, "A tunaninki dariya zan yi ko shi yasa har ki ka yi mamakin ganin hawayena?" Ta ce, "In ba ki dariya ba kuka bai kamace ki ba, godiya za ki yi wa Allah, don hakan ya fi dacewa." Ta ce, "Dag ayau na fara kuka a rayuwata Rafi'a, har daukewar numfashina na har abada. Kukan zahiri kukan zuci wanda za a gan shi ko ba za a ganshi ba." Ta ce, "Don me Mabaruka? Sai ka ce wacce a ka hadata da mugun abu?" Ta ce yayin sakkowar wasu hawayen. "Ai wannan yafi mugun abu a guna, gwanda a hada ni da mutuwata a kan nayi rayuwa da shi saboda ba na sonsa! Ba na sonsa!!."Ta fada tare da fashewa da kuka, sannan ta kife a nan tana rizgar kukan. Hankalin Rafi'ar ya tashi, ta birkice ta dinga kokarin dagota. "Haba Mabaruka, kina son jefa kanki a tashin hankali? Duk fa abin bai kai haka ba. Meye laifin Imran da har za ki 60 WAYE ANGON? bakin ciki da auransa?" Maryam Ja'afar Tan dago ta dubeta fuska share-share da hawaye, "Gwanda a hada ni da mutuwata yafi min farin ciki da nutsuwa, koda kullum tana daukar numfashina. Na fada miki ba na sonsa Rafí'a, amman kińn kasa ganewa, wallahi mutuwa zan yi." Kasa furta komai tayi sai dai ta bi ta da kallo, abin nata ya fara wuce misali sai kallo. Kan ta ce wani abu taga mikewarta, tana kokarin sa takalma idonta a rufe. "Mabaruka ina za ki je?" Rafi'a ta tambayeta a hanzarce. Ba ta jin za ta iya bata amsa, ta wuce ta gabanta da sauri. Ba ta tsaya ba itama ta rufa mata baya. A baranda ta samu cimmata, ta juyo da ita da karfi tana cewa "Wai lafiyarki, ina za ki je?" Yanayinta ya sauya gabadaya. Ba abin da ka ke gani a idonta sai bakin ciki, idanun nata sun sauya launi, hatta fuskarta ta sauya. Ta tsura mata ido cikin tsananin fushi tana kallo, uffan taki cewa. Ita ma ta kura mata idon tana jiran amsarta. 61 E WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Tsawon dakiku suna haka, kawai sai ta sake juyawa tayi gaba a hanzarce. Ita ma Rafi'ar ta sake binta. Wani mai adaidaita sahu yana sauke wata mata da sauri ta shige cikinsa, ganin yana kokarin jan mashin din ya tafi Rafi'a tayi saurin shigewa itama. Mai Adaidaita sahun ya ce, "Ina za ku je?" Rafi'ar ta bita da kallo don son jin ina zata je. Ta yi masa shiru. יי Ya sake nanatawa, ta ce "Kai ni ko'ina ma." Ya juyo yana kallonta cikin mamaki, "In kai ki ko ina? Lafiya ki ke?" Ta ce, "Lafiya nake, ka kai ni duk in da ya maka." Rafi'a ta dube shi ta ce, "Yi hakuri Mallam, bari mu sauka bata da lafiya."Yaja ya tsaya. Ta jawo ta da karfi ta fito. Suka yi cirko-cirko suna kallon-kallo a tsakaninsu. Tsaki kawai taja tare da wucewa. Tamkar za su tashi sama tana tafe tana biye da ita suna fada, ta ce "Wai har ina za ki je Mabaruka? Ya kamata ki saurare ni." Ta tsaya tare da juyowa a fusace ta ce "Ai bina ki ke, ki sa ido ki gani." Daga haka ta juya ta ci gaba da tafiya abinta. 62 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar ar Abin da ta gani ne ya girgizata, idanunta suka fito, tsoro ya bayyana tattare da ita. Ganin Mabarukar tayi tsakiyar titi, manya-manyan motoci da mashina sun sa ta tsakiya sai faman horn suke mata. Ta hada go slow, amman ko a jikinta taja tayi tsaye tamkar mahaukaciya. Da wani irin gudu ta falla wanda ba ta san tana da shi ba, da zuwa ta fincikota da wani irin karfi suka dawo bakin titin, mutane daga ma su zaginta sai masu tir da ita. Ita kuwa Rafi'ar saboda tsabar haushi ji take tamkar tai ta falla mata mari. Ta dubeta cikin fushi ta ce da ita. "Ba ki da hankali ko kina hauka? Auren dole hauka ne ko kanki aka fara? Kina son ki kashe kanki ko Mabaruka?" Tanke ta kasa cewa komai, illa wani takaici da take ji a ranta, me yasa Rafi'atu take son zama matsalarta? Ta ci gaba "Wallahi na kusa raba hanya dake tunda kin canja kin juya halinki, kawai don an aura miki wanda ba kya so, meye laifin mahaifiyarki har za ki ga laifinta? Bа zan iya hada hanya da marar biyayya da da'a ba." Dòn fadin wannan maganar kawai sai ta fashe da kuka, taja da baya ta fadi kasa tim! tamkar karamar yarinya 63 WAYE ANGON? yayayyiya. Maryam Ja'afar Nan ta hau shure-shure tana kuka, abin ya daina ba Rafi'atu haushi illa takaici da jin haushi. Wai me Mabaruka take son zama? Tsakiyar titi cikin mutane take nuna halinta? Momy kuwa tunda ta fita sai kawai ta hau motarta ta wuce gida, a kokarinta na ta dan samawa Mabarukan wani abu don jin dadinta, musamman abin da tasan zata bukata a asibitin, ba da jimawa ba tajuyo. Zata shiga dakin suka hadu da Imran da ledar magungunansa, sai wata ledar shake da su fruits jikinsa har rawa yake yi. Suka tura kofar dakin da Mabaruka ta ke suka shiga a tare, amma suna shiga suka ga wayam! Dakin babu kowa. Suka bi junansu da kallo cike da mamaki, kowa so yake ya tambayi dan'uwansa ina Mabarukar? Wata Nurse ta shigo ganin shigowarsu, ta ce "Marar lafiyar nan ku ke nema?" Suka hada baki da sauri suka ce "Eh." Ta ce, "Yanzunnan naga sun yi na ita da wacce ku ka zo tare, har sun shiga mota naga sun sauka sun wuce 64 WAYE ANGON? kuma." Maryam Ja'afar aBai san sanda ya saki ledar ba ya runtuma a guje har yana ture Nurse din. Mamaki ya cika Momy, tayi sake da baki tana tambayar kanta ta fita ina to za ta je? Su kuwa suna can tana ta bige-bige da ihu saman titi, mutane sun mata caa kowa na kallonta, wasu na tambayar Rafi'ar me ya faru? Ba ta jin za ta iya ba daya daga cikinsu amsa, takaici ya cika zuciyarta, ta dinga zubar da hawaye tana gogewa, saboda abin da Mabaruka take ja musu saboda shegiyar kafiyarta. Ta tsaida Adaidaita sahu, da kyar ta samu ta tura ta ciki ta rirrike ta tamkar hauka sabon kamu, a kan ita wallahi ba in da zata je sai ta kyaleta an kasheta a wannan titin. Gidan Momyn suka sauka, ta jata suka shige ciki. Still dai ba ta fasa shure-shuren ba, ita a lallai sai ta mutu. Koda ta shigar da ita dakinta bata fasa ba, taja ta jingina da bango ta dubeta ta ce, "To ci gaba da yi har ki kashe kan naki don Allah." Karshe ma fitowa tayi ta dawo falo tayi zamanta tare da 65 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar rafka tagumi tamkar tana jira, tana fita ta maida kofa ta бame бam! Ta ci gaba da buge-buge duk abin da ya tari gabanta sai ta kai masa duka. Hankalin Rafi'ar ya tashi, tsoro ya kama ta kar fa ta kashe kanta kamar yanda take bukata, tayo dakin tana bubbuga mata ta bude, tamkar ba ta dakin bare ta amsa. Tana jin ta tana kashe glass din mirror da na drower, 'yan kwalaban turaranta su Humra ta dinga kashe su. Ta ci gaba da rokonta a kan ta bude don son Annabi, ganin ba za ta bude ba yasa a rikice jikinta har rawa yake ta lalubo lambar Imran. Shi kuma a lokacin ya fito sai wiage-waige yake, ya yi nan ya yi can yana son gano ina suke? Sam babu nutsuwa a tare da shi. Kiran da Rafi'ar tayi masa ne a waya yasa da sauri ya dauka ya kai kunne don yasan suna tare da Mabarukar. Ta fashe da kuka tana cewa "Ka zo ga Mabaruka nan a daki ta rufe kanta tana ta buge-buge, wai sai ta kashe 66 . WAYE ANGON? kanta." arMaryam Ja'afar Ya kara rudewa, jikinsa ya hau rawa ya ce "A wane gidan?" Ta ce, "A nan gidanku." Bai sake cewa komai ba ya tura wayar aljihu ba tare da ya ko katse kiran ba saboda tsananin firgita da tashin hankali, da gudu ya shige mota ya jata a guje. Mintuna kadan suka kai shi gidan, Momy ta fito kenan taga jan motarsa. Tabbas tasan ba lafiya ba, hankalinta ya kara tashi. Cewa ta ke "Oh ni! Me ke faruwa kuma ina zan yi?" Duk ta birkice ta rasa me zata yi. Shi kuwa Imran ya isa gidan a gaggauce ya shige falon. Yana shiga ya kwankwasa mata kofar tare da cewa "Bude دو mana Mabaruka ni ne." Tana jin muryarsa, sai ta kara wuta a kan abin da take yi. Ya sake cewa, "In dai ni ke şa ki wannan tashin hankalin zan kyale ki Mabaruka, ba na son kiyi asarar ranki, ki yiwa mahaifiyarki ke kadai ke gareta, ki tausaya mata ko don ita kadai ki bari kada ki kashe kanki. Ba zan zama masifa a rayuwarki ba, amman ki bude zan miki duk abin da ki ke so. Iya nacin ya yi mata amman ta ki sauraronsa, ji yake 67 E i WAYE ANGON? Maryam Ja'afar kamar ya fasa bangon ya shiga ya daukota, har cikin ransa yake jin kukanta wanda da jinsa ta gaji da yinsa, ga fashefashen abubuwa da take idan ta fasa wani abu har sai ya razana, ji yake kamar a jikinta take fasawa. Ya ci gaba da dukan kofar yana mata magiya, ya damu kwarai duk a kansa take wannan haukan, har take kokarin rasa ranta, meye laifinsa? Meye illarsa? Ko dai yana da wani abu ne na aibu wanda ba kowa ke gani ba sai ita? Rafi'atu ma bata gaza ba, wajan bata hakuri da lallashi. Tun suna jin motsinta da gunjin kukan har suka ji dif! Hankalinsa ya kara tashi, tsoro ya bayyana a tare da shi, zufa ta keto masa, ya hau tambayar kansa meye ma'anar shirun da tayi? Tsawon awa kenan ana abu guda. Kai da yaga abin ya wuce misali, ficewa ya yi da sauri ya nemo masu kwance kofa. Nan da nan kuwa aka kwance kofar, har yana buge mai aikin ya fada dakin a rikice. Kwance ya ganta saman tayils, gabansa ya yanke ya fadi. Ya hau jijjigata. Can ta bude ido a wahalce, idanun nata sun rine sun kankance saboda kuka, muryarta ta dishe ta kasa tsayar da idonta. 68 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar a A rude yake cewa, "Lafiya Mabaruka menene?” Ba ta iya ba shi amsa ba, yum! yum! haka take jin kanta wani iri. Rafi'atu ta fashe da kuka tayi tsaye ta kasa karasawa kusa da ita, tsoronta kar dai wani abu taci ko ta sha. Shi ma haka ne a ransa, a tsorace ya ce "Me ki ka ci Mabaruka?" Ta kasa ba shi amsa bata san ma da wa take magana ba. Ya sake nanatawa

Chapter 3 of 10