take sai kumbure-kumbure tana turo baki
91
WAYE ANGON?
motsi kadan taja tsaki.
Maryam Ja'afar
A ganinta suna 6ata lokacinsu ne da asara bata jin zata
yarda ya ganta da kwalliyar bare ya ji dadi.
Sannan duk yanda aka yi da ita sai tayi musu kamar dai
yanda aka yi da ita wancan karon, dole a haka ake mata
kwalliyar.
Aka ciro mata rantsattsen leshi din da zata saka jikinsa
har rawa yake saboda tsada ga kyalkyali yana kashe ido,
tsadarsa ya kai.
Komai sabo aka ciro mata, duk kayansa ne tun da aka
fara bikin sai yau zata sa kayansa, don ya gani ya ji dadi.
Nan fa aka dinga yi ta ce ita atafau ba za ta saka ba,
wallahi kyamarsu take tir ta sa su, har ya mutse fuska take
wai zuciyarta na tashi saboda ganin kayansa, har tana
tsirtar da yawu.
A ka taru kanta ana abu daya, amman ta ki sauraron
kowa, ga motar daukarta tazo ita kadai ake jira.
Momy bata gun sai da aka je aka fada mata tare da dan
aiken suka shigo.
Koda taji ga Momyn nan zuwa gabanta ya fadi, ta
tsorata. Nan da nan kwalla ta taru a idonta taf! Ta riga ta
92
WAYE ANGON?
sani dole sai tasa kayan tunda Momy taji labari.
Maryam Ja'afar
Tasan Momynta sarai, tana masifar tsoronta, sam ta
canza mata tunda aka fara maganar aurannan ta sauya.
A da tamkar ba Mamanta ba, mai sakar mata fuska suyi
wasa suyi dariya tayi mata rigima da shagwabarta son
ranta.
Ko dunguri bata taba mata ba sai a kan Imran, har ta kai
jiya da duka da dorina.
Don Allah me zai sa ba z ata kara tsanarsa ba? Duk shi
yaja mata haka. Me ake dashi? Tasa hannu ta goge kwallar
daidai shigowar Momyn.
Ta dubeta fuska a hade babu alamar dariya ta ce, "Me
yasa ba za ki sa kayan ba?" Tayi shiru tana kallonta ba
amsa.
Ta sake nanata mata "Da ke nake, me yasa ba za ki saka
kayan ba, bayan kin san tun dazun ake jiranki, ko a kanki za
su kare?"
Ta girgiza kai "A'a." Ta ce, "To dauki ki sa minti biyar
ina jiranki." Ta juya hawaye suka dinga kokarin zubowa
saboda takaici.
Zata yi magana "Momy ni..." kan ta karasa ta juyo a
93
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
fusace ta ce, "Kin san Allah Mabaruka ko ki kiyaye ni, ko
ko kafin ki bar gidannan in miki karo na biyu, na rantse."
Ta sauko daga kan gadon a marairaice ta durkusa
gabanta tana rokonta.
"Don son Annabi ki min afuwa kar ki tursasa ni sa
kayan nan, ki bari nasa daga cikin wadanda ki ka dinka
min, don Allah Momy."
Ta ce, "Wallahi ba za ki saka ba, wadannan za ki saka
kuma kije da su har gidansa, kuma ya gan ki da su.
Idan kuma har ba ki yi haka ba Allah ya isa. Kin nuna
min ban isa da ke ba, ba ni da wata kima da muhimmanci a
gurinki, sannan ki sa ni yin kaffara."
Daga haka ba ta sauke saurararta ba, ta juya a binta a
fusace ta bar dakin. Ta dafe kai tare da zubowar hawaye ta
ce, "Na shiga ukuna!Wayyo Allahna!"
Ita kanta Rafi'a abin ya bata haushi, taja tsaki tare da
dubanta ta ce, "Wallahi ba ki jin magana Mabaruka, kin
cika kafiya.
Sa kayan kawai sai an ta fama da ke kina sa ta rantsuwa,
meye wuyar a ciki?"
Ta dawo ta zauna bakin gadon tana cewa, "Imran!
94
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Imran!! Wallahi ka shiga uku a hannuna, sai ka gwammace
ba ka kawo ni gidanka ba, dan iska kawai mugu."
Kwaraf! Taji an buge mata baki, ta daga kai tana kallon
aikin waye wannan?
Anti Karima ce ta gani a tsaye tana huci ranta a басе,
tana kallonta ta ce "Ke dai 'yar wulakanci ce wallahi,
fitsararra marar kunya. Don ubanki mijin naki ki ke cewa
haka?"
Tayi shiru tana zumburo baki, ta ci gaba da cewa "To
don Allah mu zo mu tarar da gawarsa tunda ba kya sonsa,
sakarya mararwayau."
Ta juya ta fice ita ma rai a bace tana fada.
Rafi'a ta kalleta cikin fushi ta ce, "Gaskiya ina ganin zan
tafi gida ni ma, na gaji da ganin wannan fitsarar taki
wallahi.
Tunda ba ki jin magana nayi iya bakin kokarina kin ki
ji, gara in je gida in huta da bakina."
Ita ma ta kalleta tare da harararta ta watsar ta ce, "Ki tafi
mana sai me? Tunda daman ba goyon bayana ki ke ba,
bakinku daya."
Abin ya ba Rafi'a mamaki, bata yi zaton zata fada mata
95
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
haka ba. Taji haushi sosai, don haka ta zuciya sosai.
Ta mike tana cewa "Haka ki ka ce ko?" Mabaruka ta cе,
"Haka na ce'mana, ai ba tsoronki nake ba, na fada
dukkanku a bayanshi ku ke ba kwa sona, sai me kuma don
kin yi tafiyarki?"
Ta kara zuciyà, ta wuce a fusace ta figi gyalanta ta fice
cikin fushi. Tabi ta da harara tana tabe baki.
Mai yi mata kwalliya ta ce, "To yi maza ki sa kayan in
karasa miki kwalliyar."
Tamkar ba zata tanka ba ta ce, "Je ki ba sai kin karasa
ba, wannan ma ta isa." Zata yi magana ta dakatar da ita,
"Kije don Allah bana so."
Ganin kanta na rawa tana yi wa kowa rashin kunya tayi
wa wadancan to ina ga ita! Don haka da sauri ta bar dakin
kartayi mata tata rabon.
Taja tsaki tare da fadawa gadon tana gunjin kuka.
Koda Rafi'a ta fita a falo suka ci karo da Momy, ta
fahimceta sosai saboda bayyanar fushinta a fili.
Ta ce, "Rafi'atu lafiya, me ya faru?" Ta dan kakalo
murmushi ta ce "Ba komai."
Daidai fitowar mai yi wa Mabaruka kwalliya, ta ce "A'a
96
WAYE ANGON?
tsakaninta ne da kawar tata."
Maryam Ja'afar
Momy ta ce, "Me ya faru?" Ta fada mata duk abin da ya
faru. Ran Momy ya kara бaci.
Mabaruka ba ta jin magana, kan aurannan duk ta fitsare.
Taja hannun Rafi'a ta ce, "Yi hakuri 'yata kar kiyi fushi,
zata gane muhimmancinki, ki dan saurara ki rakata gidan
mijin." Ta ce, "Shi kenan Momy, ya wuce."
Tayi murmushi ta ce, "Na gode." Suka wuce cikin
dakunan, kan hakan sai da Momyn ta ci mutuncinta ta
zazzageta.
Mabaruka tasha kuka, don dole ta shirya cikin kayan
makiyinta tunda take ma a rayuwarta bata taba kyau irin na
yau ba.
Kayan sun zauna mata, sun karbeta sosai kowa sai
yabawa yake yana daukarta hoto, tana ta walwali.
Ita kuwa sai botsare-botsare take tana turo baki,
gabadaya kyamar kanta take kamar tasa kayan da suka taба
kaşhi, ta tara miyau bakinta taf!
Aka yi mata kwalliya mai gigita mai kallo, gabadaya ta
sauya tamkar ba ita ba.
Masha'Allah kawai ake cewa. Aka shiga da ita gun
97
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Momyn don suyi bankwana, tasa mata albarka sosai tare da
yafe mata duk abin da tayi mata.
Ta kara ja mata kunne sosai da sosai. Tun a nan ta fara
kuka tan'aihu bare da taga an fito da ita an sakata a motarta
wacce ya bata a lefenta.
Ta dinga shure-shure tana kuka tamkar zata buge
mutane ta fito.
Abokanan Ango suka dauka irin kukannan ne na barin
gida, a haka dai aka dauki hanya da ita zuwa rantsattsen
gidansa inda ya tamfatsa mata don ita kawai.
Har suka iso tana kuka, musamman da taga an tsaya
bakin gate a na yi wa Maigadi horn wanda ya fara aikinsa
tun bayan gama ginin.
A ka shiga da ita cikin motarta. Runtse idonta tayi gam!
Don kar taga gidan, aka fito da ita tamkar makauniya.
Anti Karima ta ce lokacin da za su shiga falon "Ki
ambaci sunan Allah don shiga gidanki."
Tsaki taja a ranta, bata jin zata iya don ba alkhairi take
nema ba cikin gidan.
Aka shiga da ita falon wanda sassanyar iska da kamshi
ke bankadowa mai dadi da sa nutsuwa, dole in ka shake shi
98
WAYE ANGON?
ka lumshe idanuwa, aka wuce da ita dakinta.
Maryam Ja'afar
A dosane ta zauna kan tafkeken gadon nata wanda ya
dago yasha lallausar katifa tumemiya, ga shimfidu na
alfarma.
Shi kanshi kamshi ba iyaka, kayanta wayyo Allah! Sun
dauki hankalin kowa, kamar kayi ta zama cikinsa.
Komai yayi cas-cas wallahi, yayi kyau. Lallai Momy
tayi kokari, kuma dai Daddy shi ya bada kudin komai, sai
dai ita ta shige gaba kan shigowar kayan.
Kowa yana cikin farin ciki saboda shigowar wannan
kerarren gidan da dakuna kamar a kasar Turai, ga kamshin
gidan na dukan hancinansu.
Amman ita sam haushi, bakin ciki da takaici sun cika
mata rai, tayi tsuruu, bakin ciki ya hanata magana. Wai yau
ita a gidan Imran? Kai jama'a wannan wane irin bakin ciki
ne?
'Yan rakiyar duk na gida ne, sun saba da angon. Shi ma
haka cikinsu ba wacce yake jin kunyarta, haka suma.
Don haka da shi aka shigo dakin da abokanansa. Suna ta
tsokanar juna. Ya shigo kansa ba hula, hannunsa rike da
waya da charger yana cewa, "To-to-to a tashi a tafi gida
99
WAYE ANGON?
haka nan mun gode."
Maryam Ja'afar
Samira daga cikinsu ta ce, "Lallai ma! A nan za mu
kwana ba ka san in an kawo amarya ana kwana tare da ita
ba?"
Ya zaro ido yana cewa, "Wallahi ba zai yiwu ba, ba mai
kwanar min gida tunda dai kun kawo min ita to kuje na
gode zan neme ku."
Aka yi dariya.
Anti Karima ta ce, "Ai ko ba ka isa ba sai mun huta
gajiyarmu a wannan lallausan gadon dukkanmu."
Ibrahim daya daga cikin abokansa ya ce, "In kuma ki ka
ce haka Gwaggo ba ki tausaya ba, tun yaushe yake tsaye ita
kanta Amaryar ya kamata a bar su su huta su san sun
angwance.
Duk maganganun saman kanta suke yi, fuskarta a rufe
da mayafi. Haushi ya cikata, sai jan kananan tsaki take tana
harare-harare cikin gyale ba wanda ke ganin me take yi.
Don me zai shigo mata har nan yazo suna mata rashin
kunya saman kai? Taja tsaki tare da dauke kanta, dan iska
kawai! Ta fada a ranta.
Anti ta ce, "Kai-kai-kai kalle ni da kyau Anti ce ba
100
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Gwaggo ba, baka ganni ba ne ban yi kama da Gwaggo ba da
saurana?"
Dukkansu suka yi dariya, Imran ya ce "To sorry Anti, ni
dai bari in sa chaji kafin ku tafi."Ya wuce yana jonawa.
Rafi'a ta ce, "Duk ba in de za ka sa sai a nan?" Ya ce,
"Wallahi socket din duk basa aiki sai an duba min su, na
nan ne kawai ban san ya aka yi ba."
Dayan abokin ya ce, "Ai ba laifi tunda dakin Amarya
yana yi, ai faduwa tazo daidai da zama, kaga shi kenan."
Ficewa ya yi yana dariya, suma abokan suka rufa masa
baya suna dariya, ba don komai ya yi haka ba sai don lura da
ya yi da Gimbiyar tasa maganganunsu sun isheta, tsoron
kar ta ba shi kunya ne yasa ya fice.
Sauran 'yan kawo Amarya duk sun tafi sai su Anti
Karima da Anti Luba, sai kuma Rafi'a.
Sai da suka yi sallar Isha'i sannan suka yi shirin tafiya,
bayan sun gama santin gidan suna ta zuzuta shi, ina ma su
ne.
Ita kuwa Gimbiyar ba abin da take yi sai gatsine-gatsine
a cikin lullubi babu mai ganin abin da take yi.
Da taga za su tafi da gasken, idanunta suka yo
101
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Kwalkwal, ta tuno inda take gidan Imran daga ita sai shi, a
wannan makeken gidan.
Hankalinta ya tashi, kuka ya dawo sabo. Ta dube su ta
ce, "Anti Luba don Allah kada ku tafi, ku zauna tare da ni."
Suka yi dariya ta ce, "Lallai Mabaruka! Har yanzu
yarinya ce ke, yaushe za mu zauna nan godai-godai da mu,
Allah ya tsare.
Anti Karima ta ce, "Ai ko dubi tun dazu yake cewa mu
barmasa gida, ina ga yazo ya tarar da mu a nan?"
Ta mike tsaye hawayen suna fara zuba ta ce a
marairaice "Wallahi Imran zai cutar da ni in dai daga ni sai
shi ne, don Allah Anti ku..."
Anti ta katse ta, "Mabaruka ki cire komai a ranki, ya
riga ya zama mijinki ba zai taba cutar da ke ba saboda yana
sonki.
Ya sha wuya kan ya same ki, kin ga ko ba zai yi wasa da
יי
ke ba, zai rike ki da kyau.'
Ta ce, "To amman kin san bana sonsa Anti, ya zan zauna
da shi?" Ta ce, "Wannan mai sauki ne, ni nasan Imran
Jarumi ne tsayayye, za ki sha mamakin yanda za ki fara
sonsa, ke dai kiyi biyayya."
102
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Ta ce, "Ba zan iya ba Anti, ina ji kamar zan mutu."
"Za ki iya Mabaruka, kowa da haka ya faro, kuma ya
saba, kema hakan zai kasance a gare ki, za ki gani. Mu da
zamu dawo nan da wata tara daukar baby." Ta fada tana
dariya..
Ta dauke kanta daga gareta cikin jin haushin
maganarta.
Duk suka yafa mayafansu, suka ce "To sai gobe zamu
dawo, a aje mana kazar nan mai maiko-maiko, wallahi kar
ki yarda ki cinye in ba haka ba ranki zai 6aci." Cewar Anti
Luba tana dariya.
Anti Karima ta ce, "Haba kema da wani zance a ganinki
Imran zai kawo kaza daya ne, ai yasan zamu dawo zai
tanade su don mu."
Sam! Labarinsu ba ya mata dadi, sai ma karin takaici da
bakin ciki." Ta katse su "Don Allah Anti ki fahimce ni ku
zauna."
Anti Luba ta ce, "Ke kina da isasshen lokaci, mu gaba
muka yi ba mu da lokacin sauraron shirmenki." Tayi gaba.
Da sauri ta riko Rafi'a tana kuka, ta ce "Nasan ko kowa
ya guje ni ke ba za ki iya ba, kin san komai kawata don son
103
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Annabi kada ki tafi, ki zauna tare da ni don Allah Rafi'a."
-Rafi'a ta zaro ido tare da cewa "Ni? Ba ruwana, so ki ke
yazo yasa a fitar da ni da tsiya? Wallahi ba ruwana, kiyi
hakuri dai gobe insha'Allahu zna dawo kar ki damu."
Ta kara fashewa da kuka tare da kankame Rafi'a, a lallai
ba ża ta tafi.ta barta ba.
Ita ma Rafi'ar sai kuka, aure ne ya rabata da kawarta, su
kan kwana tare suyi yawo tare, makarantarsu daya, seat
daya.
Kowa ya sansu tare, amma yau aure ya nisanta su, me
yasa ba za ta yi kukan rabuwa da aminiyarta ba?
Ta ce cikin kuka "Rafi'a ki zauna da ni kada ki manta
baya muna kwana tare mu wuni tare, me yasa yau za ki guje
ni? Kema ba za ki iya zama a wannan Kuntataccen gidan ba
amman ni ku ka kawo ni cikinsa kuma kitafi ki bar ni?"
Ta ce, "Da da yanzu ba daya ba Mabaruka, yau Imran ya
kwace min ke, ya raba kwana da nake tare da ke, babu wata
ranar da zamu kwana tare saboda shi.
Shi zai zama madadina, wanda kuma yafi ni. Na tabbata
za ki fi samun farin ciki da walwala a kan ni, za ki saba da
hakan ba da dadewa ba, sannan gidan mai yalwa ne ba
104
WAYE ANGON?
Kuntatacce ba, kada ki manta da haka."
Maryam Ja'afar
Ta rasa inda zata sa ranta, duk in da ta bullo musu sai
sun zame, me yasa wai ba a sonta?
Imran ya leko yana cewa, "Wai me ku ke ba ku fito ba?
Kar na fito muku da halina fa?"
Suka yi dariya tare da wucewa suna cewa "Sorry ango,
kar muyi laifi har a wajen Allah."
Ta rikice ganin za su tafi ta yunkuro zata biyo su, yana
daidai bakin kofa zata wuce ta gabansa kenan.
Yasa hannu ya dakatar dan ita ta hanyar rike mata hannu
gam yana dariya.
Taja tayi tsaye cak! Tana kallonsa, tamkar an dasata
gun. Ya lakuce mata kumatu tare da cewa, "Sorry, kije ki
jira ni zan raka su in dawo, ba nisa zan yi ba."
a
Daga haka ya wuce da sauri, ta bishi da kallo cikin
kunar ran taba ta da ya yi da dakatar da ita da ya yi.
Haka nan kuma taji ta kasa fita din, taji ta fasa fita din.
Ta rasa dalilin hakan.
Da gudu ta koma ta fada gado tare da fashewa da kuka
mai karfi.
105
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Sai da yaga shigarsu mota har ihsani ya yi musu, sannan
ya dawo zuciyarsa cike da farin cikin zai kasance da
amaryarsa a yau.
Ga ta a gidansa a matsayin tasa, mallakinsa daga shi sai
ita a gidan.
Ita kuma a can tana zaune sai ta tuna ta bar kofarta a
bude yasa da sauri ta mike tana kokarin rufewa.
A iya bincikenta bata ga key ba, tayi mamakin rashinsa.
In dai ba an shirya haka ba me yasa za a dauke shi? Bayan a
jikin kofa aka saba barin key kowane gida?
Tayi kwafa tare da komawa tsakiyar gadon tana share
hawaye wasu kuma suna yunkurin zubowa, duk takaicinta
na kasancewarta ne a gidan makiyinta.
Imran ya shigo da sallama idonsa a kanta yana fara'a.
Ya tunkarota har kan gadon in da ta kifa kanta a kan gadon
tayi ruf da ciki.
Da zuwansa ya ja mata yatsan kafa, cikin wata irin
fusata ta juyo da bala'i yanda ka san da ta juyo zata kife shi
da mari.
Sai kuma tayi sororo tana kallonsa, ba abin da ya fado
mata sai maganar Momy. Tayi sukut tare da sunkuyar da
106
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
kai kasa bayan ta janye kafafunta har da nade su cikin zani.
Sarai! Ya fahimce ta. Ya yi murmushi yana kallonta
daidai sanda ya zauna bakin gadon kusa da ita.
Da sauri taja baya ta kauda kanta daga gefen da yake
tana jin bakin cikin zama kusa da ita da ya yi.
Ya kirata "Mabaruka!" Tayi masa banza tamkar ba ta
gurin sai bakin rai. Ya sake nanatawa, nan ma shiru.
Ya ce, "Shi kenan tunda ba za ki amsa ba, ko sai na kira
ki da matar?" Ya fada yana dariyar tsokanarsa.
Haushi da takaici suka kara turnike ta, ji take da ma tayi
tsuntsuwa ta 6ace a dakin.
Tun shigowarsa ta gagari maida numfashi mai. kyau.
Tana jin duk ya cika dakin da kamshinsa mai sa ta tashin
zuciya da gagara maida miyau, ta tara miyana bakinta fam,
bayan ta dan kara hannunta a hanci.
Ya ce, "Idan ba ki amsa ba zan hayo gadon sosai in ga
dalilin rufe bakin."
Taja tsaki a ranta tana harararsa ta wutsiyar ido. Ya ce
"Mabaruka!"Jin abin da ya fada ne yasa ta amsa can kasan
makoshi "Uhum!"
Ya ce, "Har yanzun fushin ne ba ki bari ba?" Tayi masa
107
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
banza dai, ya sake cewa "Zuwa yanzu ya kamata ace kin
saki ranki kin yi farin ciki tunda dai fushin bai miki magani
ba, ga ki dai a gidana."
A ranta ta ce, "Yanzu na fara, ba ka ga komai ba wallahi
tunda har ka nace sai ka zauna da ni."
Ganin dai ba za ta tankan ba shi kadai ke surutunsa yasa
ya ce bayan ya maida numfashi.
“Well, bari in kyale ki mai yiwuwa har da gajiya, in kin
huta sai muyi labarin ko?"
Ba ta da shirin amsa masa, don haka ya mike still idonsa
na kanta, haka nan ba ya gajiya da kallonta ko yaushe
amarmarce yake da ita.
In zai kalleta sai yaga kamar yau ne ya fara ganinta, ya
gagara dauke kansa daga gareta.
Ya ce yana kallonta "Na tafi." Ci kanka ba ta ce ba. Ya
kada kai kawai ya wuce har ya kai bakin kofa ya juyo yana
kallonta, ya ce "Kada ki sa ran ba zan dawo ba, zan dawo."
Daga haka ya wuce a binsa.
Yana fita ta juyo tana hararar kofar tare da jan dogon
tsaki, 'Dan iska kawai, mugu. Naga gidan da za ka dawo,
wallahi Allah sai ya nuna min karshenka azzalumi." Ta
108
WAYE ANGON?
sake jan tsakin.
Maryam Ja'afar
Da fitarsa dakinsa ya zarce, inda shi ma haduwarsa ta
wuce kwatance, kayan da ya sha tamkar ya so yafi nata.
Ya cire kayansa ya fada wanka don ya ji sanyi-sanyi, ga
gajiya har da alwala yayo ya maida jallabiya fara sol ya
feshe jikinsa da nau'ikan turarensa yajawo kofar ya fito.
Dakinta ya tunkaro, a rufe ya ganshi. Ya tura da niyyar
budewa, kofar dai gata a bude amman da alama an tokareta
da wani abu.
Ya leko yana cewa "Me ya sami kofar ne Mabaruka?"
Tayi masa banza tana harararsa.
Ya fahimci aikinta ne, don kar ya dawo kenan? Ya yi
dariya ya turo hannunsa ya janye abin da ta tokare din yä
shigo.
Tana zaune a kasan tayils ya nufota, tsugunnawa ya yi
gabanta idonsa kur a kanta ya ce, "Wai menene Mabaruka?
Ba kya son na dawo ne?"
Tayi shiru dai, ya ce "Ba kya son angon naki ya taya ki
bacci yau?" Dagowa tayi ta harare shi son ranta sannan tà
sake durkusar da kanta tana kokowa da zuciyarta.
Ya ce, "Sorry, ban cancanci wannan kallon ba amin
109
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
uzuri, ba daga ni ba ne laifin zuciyata ce mai naci."
Ba ta dai tanka din ba.
Ya ce, "To zo muje kiyi alwala muyi sallah mu yi wa
Allah godiya da ya kawo mu wannan ranar, nasan ba ki ci
abinci ba, in ki ka dan ci wani abin sai ki kwanta ki huta
gabadaya."
Kala! Ba ta ce ba. Ya sake cewa, "Mabaruka wai
menene haka? In ta yi ko, ni mahaukaci?"
Ta dago ta harare shi ta mayar.
Ba ta yi tsammani ba taji ya riko hannunta daf! Ta bishi
da kallo masifa na cinta.
Zata yi magana yasa yatsa bakinsa tare da cewa
“Shihh!” alamar tayi shiru, sai kuma ta gagara cewa wani
abun, ta ci gaba da kallonsa din kawai.
Mikar da ita ya yi tsam! Yana cewa "Taso muje in raka
ki." Ta fara botsare-botsare tana ture hannunsa, bakin yayi
tsini saboda zumbure-zumbure.
.Shi kuwa ya rike ta gam ta gagara kwace kanta, sai
guna-guni.
Ya turata bandakin ya aje mata buta gabanta.
Mikewa tayi ita ba za ta yi ba, ya sake durkusar da ita ta
110
愛
2
WAYE ANGON?
sake mikewa. Sun yi haka ya kai sau bakwai.
Maryam Ja'afar
Ya dubeta ya ce, "Wai me ke damunki, lafiyarki kuwa?
Ba kya jin magana ko?" Tayi tsaye tana turo baki.
Ya sake ta yana cewa, "Shi kenan kada kiyi din fito."Ya
juya ya fice. Taja tsaki tare da harararsa.
Ba wai don ya bata ransa yasa tayi alwalar ba, sai don
Momynta kawai, musamman da ta tuna bata yi sallar Isha'i
ba, tayo ta fito tana zumbure-zumburen baki.
Zaune yake bakin gado hannunsa rike da waya yana
dannawa, wucewa tayi ta dauko Darduma ta shimfida ba ta
ce komai ba ta zura hijabinta ta kabbara sallar.
Bin ta ya yi da kallo yana mamakin taurin kanta, ta cika
kafiya. Yajinjina kai kurum. Haka nan ransa ya ba shi Isha
zata yi, don haka ya kyaleta har ta idar.
Ya mike tare da shimfida wata Dardumar gabanta yana
cewa "To tashi muyi nafilar ko raka'a biyu ne."
Ba ta dago ta kalle shi ba, bare ta ba shi amsa. Har ta idar
da lazimin ta mike.
Ganin ta mike ne yasa ya kabbara sallar a zatonsa ita ma
ta kabbarar, amma ita kowama tayi ta zauna abinta bayan ta
cire hijabin.
111
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Har ya idar ya hau jero addu'o'in zaman lafiya da zuri'a
dayyaba, duk idan ya fada zata ce a'a Ya Allah! Har ya idar
yajuyo.
Ganinta ya yi zaune ta mike kafafuwa tana danna waya.
Ya ce "Mabaruka!" Tayi mishi banza, ya sake kiranta. Ta
dago kawai ta kalle shi ta watsar.
Ya ce, "Ba ki sallar ba ko?" Tayi shiru. Ya sake
nanatawa can cikin makoshi. Ta ce "Eh." Ya ce "Saboda
me?" Tayi shiru.
b1 50 Ya gaji da maganar, don haka ya ce "Shi kenan za ki yi
watarana." Ya matso kusa da ita har jikinsu na goguwa da
juna. Tayi saurin matsawa, ya bita da kallo tsawon dakiku.
Ya numfasa ya ce, "Ok! Akwai wata addu'a da Manzon
Allah (S.A.W) ya umarta ga duk wanda ya yi sabon aure,
ko ya sayı abin hawa.
Saboda samun alkhairinsa da nisanta daga sharrinsa,
kuma an so ga wanda ya yi sabon aure ya sanarwa amaryar
da yin addu'ar saboda an so ya kama kanta ya yi addu'ar.
sm Faidar hakan kuwa don kar kawai taga ya tunkarota
kwatsam! Amman idan da bayanin zata fahimce shi ta ba
shi hadin kai, kamar yanda muka yi sallar nan muyi
112
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
addu'o'i mu nemi rahamar Allah da tsarinshi da alkairin da
ke cikinsa.
Bayan haka sai wannan addu'ar da na fada miki." Ya
tsaya yana kallonta kanta na kasa kan waya tana dannawa
tayi kunnan uwar shegu da shi, shi kadai ke surutunsa.
Ya ci gaba "Sannan an so Angon ya gabatar musu da
dan abin tabawa a baki da abin sha daidai karfinsa.
Bayan haka a wannan daren ana bukatar su raya shi da
sunnar Annabi (S.A.W) saboda dare ne mai rahama,
albarka da daraja gare su.
Kar su bari wannan daren ya wuce haka nan."Ya kalleta
da kyau "Ina fatan kin fahimci me nake nufi?"
Ta dago kawai ta kalle shi ta watsar. Ya ci gaba da
magana.
"To idan kin fahimce ni ina son wannan daren
abubuwan da na lissafo miki muyi su a aikace don samun
ladar sunnar.
Na sanki ba yau na sanki ba, tun kina yarinyarki. Nasan
gwargwadon ilimin da ki ka yi na Islama, kin san komai,
kin san aure kin san me ake nufi da shi da kuma
hakkokinsa, haka ne?"
113
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Tayi masa banza. Ya sake nanatawa. Don ya kyaleta ne
yasa tadaga kai kawai. Ya ce "Alhamdulillah."
Ya mike tsaye ya tunkarota yana cewa "Bari in yi
addu'ar." Kafin ta yunkura taji ya rike mata kai.
Da wani azama ta mike ta tunkude shi, idanunta sun
kada jajir saboda 6acin rai tana harararsa.
Yaja baya hannu da baki a sagale yana kallonta cikin
mamaki, da kyar ya iya cewa "Meye haka?" Ta harare shi
tare dajan tsaki ta durkusa ta dauki dankwalin da ya cire ta
koma kan gado ta zauna tana fushi.
Ya dan tako gabanta kadan idonsa a kanta ya ce, "Anya
lafiya ki ke?" Ta dago ta harare shi son ranta, ta kawai tana
kara jin tsanarsa a ranta da takaicin kasancewarta a
gidansa.
Tsugunnawa ya yi tare da dora hannunsa saman
wuyanta yana cewa, "Ina ga ba ki da lafiya don..."
Kafin ya karasa ta mike da sauri tare da janye jikinta
cikin masifa take cewa.
"Wallahi kada ka kara taba min jiki."Ya kalleta da kyau
ya'ce, "Don me?" Taja tsaki tare da rike kugu tana harareharare.
114
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Ya ce, "Tunda ba ki da dalili ni kuma ba zan fasa ba, ke
matata ce ya zama dole