fasa abin da ya shirya mata ba.
Ya datse kofar tare da sa mata key ya dauki dan key din
ya cillar bayan wordrove.
Ta aje kan table din da ke gefen gadon, ta mike ta wuce
abinta zuwa kofar, ta jawo ta ji ta gam da ta lura da kyau
taga ansa mata key ta ji cak ranta na kara mata daci, to me
yake nufi kenan?
Tamkar ba za ta masa magana ba, amman dai tunda so
take ta fita ya zama dole ta sauke girman kan ta tambaye
shi, ya bude mata.
Shi kuma ya yi zaune kan gadon yana kallonta da son
ganin kokarinta.
Bata juyo ba ta ce "Ka bude min kofar ina son in je in
kwanta dare ya yi."Ya yi mata banza tamkar ba ya dakin.
24
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Ba ta gaji a'afar ba ta sake tambayarsa din, sai sannan ya yi
magana in bacci ki ke son yi ki zo ki kwanta a nan ga gado
nan.
Sai a sannan ta juyo cikin fushi da bala'i zata yi magana,
ganinsa a haka tamkar ba kya jikinsa yasa bakinta ya kulle
ta kasa maganar.
Ta sunkuyar da kai wani tsoro na shigarta ga kofa a rufe
wato dalilinsa kenan na rufe kofa? Tsoro ya kamata, jikinta
ya dauki rawa, idanunta suka yo waje, sam ta gagara daga
ido ta kalle shi.
Sosai ya fahimce ta ya yi dariya ya ce, "Ina jin ki, me za
ki ce da?" Tayi shiru ta kasa magana. Ya sake nanatawa
lokacin da ya mike jikinta ya kara rawa.
Bakinta na rawa ta ce, "Ka..ka...ka bude min...min
kofa bar...barci nake ji."
Ganin ta tsorata ainun yasa ya yi tsaye cak ya ce "Shi ne
na ce ki zo ki kwanta a nan mana ga shimfida nan."
Yana rufe baki ta dauka "Momy zata yi fada ai bai dace
na kwanta a nan bа."
Ya ce, "Waye zai tuhume ki don kin kwana a dakin
mijinki?" Tsoron da ke ranta ne ya hanata ba shi amsa,
25
da
ni
a
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
amman dai ta ce "Kayi hakuri dai don Allah ka bude min."
Ya ce, "A'a ban yarda ba, a nan za ki kwana musamman
da naji labarin duk yau ba ki ci komai ba, shi yasa na ce a ba
ki ki kawo min da kanki, kinga sai muci tare sannan muyi
kwanciyarmu a nan ga gado can.'
Sai sannan ta iya dagowa ta kalle shi a marairaice ta ce,
"A'a ba zan iya ba, don son Annabi ka bar ni na tafi dakina
kar Momy ta jiyo ni a nan dakin."
Tunkarota ya yi yana cewa, "Ba abin da zata ce, nasan
zata yi farin ciki idan ta ji ki a dakin mijinki, kada ki damu
kina tare da Angonki."
Ganin yana tunkarota ne yasa ta kara tsorata, idanunta
suka fito ta faraja da baya har ta dangane da jikin kofa.
Shi kuma bai fasa ba ya ci gaba da tahowa yana dariya,
har ya tsaya gaf da ita suna jin numfashin juna, tayi saurin
sunkuyar da kai jikin nata kuma bai fasa rawa ba.
Ya ce, "Wai meye duk ki ka tsorata, me ki ke tunani? Ta
ce da sauri ba komai. Ya ce, "In ma kina tunanin wani abu
nasha masifarki da ki ka saba min zata kwace ki."
Tayi shiru dai ta gagara hada ido dashi, kamshinsa ya
baibayeta ganin ya daga hannu ne yasa tayi saurin datse
26
WAYE ANGON?
idanunta da kankame jikinta gam.
Maryam Ja'afar
Ya yi dariya yayin da ya ke dora hannunsa, saman kofar
wato bayanta sai ya sata tsakiya tsakanin jikinsa da
hannuwanta jikinsu har yana ta6a juna.
Jikinta ya kara rawa, ya ce yana kallonta "Calm down
my angel, ba zan miki komai ba, kawai da naji baki ci
komai ba ne yasa hankalina ya tashi, naji ba dadi shi yasa
nake son muci abinci in ba ki tunda Momy ta ba ki kin ki ci.
Ba zan iya jurar zamanki haka ba, ba tare da kin ci
komai ba, don nima ba zan iya ci din ba."
Ita dai ta datse idanunta gam bakinta yana ta salati,
jikinta bai fasa rawa ba bayan zufar da ta lullubeta.
Kamar wasa taga ya daga rigarta yana cewa, "In ga
cikin ma?"” Ba shiri ta bude idon tana kallonsa, anya yana
cikin hankalinsa?
Kan ta gama wannan mamakin taji hannunsa saman
cikinta yana shafawa yana cewa "Kin ga ni ko cikinki
shafe yake alamar ba abin da ki ka сі."
a
Ta kalle shi cikin bacin rai ta ce, "Imran!"Ya amsa yana
kallonta. Та се "Ка dauke hannunka daga jikina." Ya
tsareta da ido ya ce "Why?" Ta ce, "Ni matar aure ce matar
27
WAYE ANGON?
wani."
Maryam Ja'afar
Ya yi dariya ya ce, "Ni ba?" Ta ce, "Na dai fada maka ka
cire hannunka a jikina."Ya ce, "Idan ba haka ba..."
Kan ya gama rufe bakinsa a fusace zata ture hannunsa,
caraf taji ya rikota yana kallonta, ta kama kiciniyar kwace
kanta gabadaya ya rikota ya hadata da jikinsa ya riketa
gam.
Tayi iya kokarinta ta kasa, har da cizo ta cije shi ba
iyaka amman ko motsi bata ga ya yi ba bare ya saketa.
Ta hau botsare-botsare, idanunta sun taru da kwalla,
tsawon lokaci tana kokarin kwatar kanta ta kasa, ya rike ta
gam. Sai kawai ta fashe masa da kuka har da shure-shure.
Ya yi tsaye yana kallonta har cikin ransa yake jin
kukanta sam ba ya masa dadi ga wani sonta da ke kara
damunsa, ya ce "Mabaruka wai menene?"
Cikin kuka ta ce, "Ka sake ni in tafi."Ya ce, "Ba zan iya
ba, ina sonki ina son na kasance da ke a yau don Allah
Mabaruka."
Ta kara fashewa da kuka ta ce, "Ni ma ba zan iya ba, ina
da miji kada ka keta min haddi don Allah Imran."
Ya ce, "Ke ba matar wani ba ce matata ce, ni ne Angonki
28
WAYE ANGON?
ba wani ba." Ta ci gaba da kallonsa tana kukan.
Maryam Ja'afar
Ya ci gaba, "Kin san yanda zuciyata take tafarfasa na
sonki Mabaruka son da nake miki wallahi wanda ki ke so
baya miki ba zai baki kulawar da zan ba ki, ba zai tattale ki
ba kamar yanda zan miki ni zan gatanta ni in ba ki farin ciki
da jin dadin rayuwa.
Saboda ni ke sonki tsakani da Allah, kuma na fi shi
sonki, a gidana za ki fi jin dadi. Don Allah ki tausaya min
Mabaruka ki bani hadin kai muyi soyayya me dadi, ba abin
da zan miki a nan har sai kin zo gidana.
Ta kasa cewa komai, illa kukan da take har kanta ya fara
ciwo ta gaji da yi masa bayanin bata sonsa, ta furta masa ta
masa a aikace amman ya gagara fahimta, to me zata ce
masa ya fahimta kuma?
Ta ci gaba da kukan tana kallonsa, ya kalleta cikin
tausayawa ya ce, "Ya isa! Ya isa! Is ok, bana son kukan nan,
kiyi hakuri."
Taki dainawa ta ci gaba da kukan dai tana kallonsa, shi
kuma har lokacin yana rike da ita.
Ya ce, "Kina son nima in yi kukan ko ba kya son farin
cikina ba kya tausayina ko?"Daga kai tayi alamar eh.
29
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Ya yi murmushi ya ce, "Ok, naji zo muci abinci sannan
ki ta fi." Ta tirje ita ba za ta tafi ba, ya ci gaba da lallashinta
da yaga ba za ta je ba, ya jata da karfinsa suka wuce ya
zaunar da ita bakin gadon kusa da jikinsa.
Ta dinga kiciniyar kwace kanta.
Ya dubeta ya ce, "Wallahi idan ba ki tsaya ba a nan za ki
kwana, kinga gadon nan?" Ya nuna mata. Tabi gadon da
kallo.
Ya ce, "To a nan za ki kwanta, ni da ke kuma babu mai
tambayata dalilin hakan, don haka gwanda ki nutsu ki ci
abincin nan sai na bude miki kofa ki fita salin alin abin ki,
kije dakinki ki kwanta."
Tayi narai-narai da ido, kukan ya tsaya cak sai zare
idanu, ganin ta nutsu ne yasa ya saketa yana kallonta.
Ya yi tunanin zata tashi amman sai yaga tayi dai zaune,
don haka ya jawo abincin yana zuba musu shi da ita. Yaje
table din tsakiyarsu ya debo a cokali yana kallonta ya yi
dariya.
Ya ce, "To haa bakin in ba ki." Ta juyo ta galla masa
harara tare da dauke kai tana jin wani takaici a ranta da
karin tsanarsa.
30
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Ya yi dariya ya ce "Sorry my Princess, juyo ki karba ki
ci." Tamkar ba ta gun bare ta amsa, ba yanda ta iya ne yasa
take zaune a dakin, dakin ma akan gado, gadon ma kusa da
shi har tana jin saukar numfashinsa, ta ce a ranta tir!
Ya ce, "Ok, tunda ba za ki yarda in ba ki ba ni ba ni." Ya
juyo da ita ya mika mata cokalin, ba ta da shirin karba.
Ya ce, "To idan har ba ki yarda na ba ki ba, ko ki bani
wallahi a nan za ki kwana kuma abin da ki ke tsoro sai ya
faru."
Hankalinta ya tashi ainun idanunta suka yi rau-rau,
wallahi ita dai an cuce ta tunda aka hadota da shi bayan an
san bata sonsa.
Kawai hawaye suka fara sintiri a kumatunta. Ta jawo
cokalin tana kokarin ba shi, idanunta a rufe taf da kwalla.
Ya fahimceta tabbas ba da son ranta zata yi ba sai don ya
matsa mata, jikinsa ya yi sanyi tausayinta ya kama shi kanta
na kasa ya dan leka fuskarta.
Cikin damuwa ya ce, "Mabaruka!" Tayi shiru tana
shesshekar kuka, ya sake nanatawa a dan rude ya ce,
"Menene Mabaruka?" Kukan ya soma fitowa.
Ya birkice ainun yana cewa, "Ni ne ko ni ne na sa ki
31
WAYE ANGON?
W
Maryam Ja'afar
k
c
2
kuka? Sorry ba zan kuma ba." Ta ci gaba da kukanta tana
Kokarin ba shi hannunta na kusa da bakinshi.
Ya janye hannun yana cewa "Is ok! Is ok! Sorry na fasa
wallahi amjocking, please ki bar kukan kin ji ko?"
Ba ta fasa miko masa ba, sam ya daina sha'awar ta ba shi
din, kukanta ya birkita shi ya tada masa da hankali gefe
kuma tausayinta da ya cika masa rai.
Ya tsugunna gabanta tare da riko hannuwanta bayan ya
cire hannun daga kan abincin ya rike ta cikin kulawa da
damuwa yana cewa.
"Is ok Mabaruka, ki bar kukan na fasa kin ji ko?" Ta
daga kai kurum. Ya dan leko ya ce, "Kin bar kukan ko?" Ta
sake daga kan ya ce, "Promise?"Ta sake daga kanta. Ya ce,
"Ba zan sake miki haka ba, bana son kukanki kin ji my
angel?" ta dai daga kan.
Ya ce, "Please, say something mana am compused."Ta
ce, "To." Kawai ya ce "Thanks my Mabaruka."
Ya koma ya zauna idanunsa still a kanta ya ce, "Za ki
wuce dakinki in buďe miki kofar ko za ki dan ci abincin
sannan.
Ta dan dago ta kalle shi second biyu ta sunkuyar, haka
32
る
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
nan taji gwanda ta ci ko ya ya ne tunda har ya damu taci
kuma ya barta ta tafi din.
Duk da hakan da ya yi ba burgeta ya yi ba, ta ce a can
kasan makoshi “Eh zan ci."Ya ce, "Ok, to ci ki tafi dare ya
yi nisa."
Та се, "Тo." Kawai taja cokalin ta fara kaiwa baki tana
ci don dole, sam abincin bata jin dadinsa ko don shi ya bata
taci kuma a dakinsa.
Yayin da shi kuma ya zuba mata ruwa a cup ya rike mata
yana jiran ta bukace shi ya mika mata idonsa kur a kanta
yana jin matsananciyar kaunarta na karuwa.
Ta mika hannu ta karbi ruwan tasha, zata aje ya yi
saurin amsa yana cewa "Kawo in rike miki." Ba ta cсе
komai ba ta mika masa.
Ta ci abincin sosai da ruwan, dadi ya dinga ratsa shi
gashi gata ina ma a gidansa ne.
Ko da ta gama taja tayi zaune ita bąta tashi ba ita bata ce
komai ba, ya dubeta ya ce "Kin koshi ko?" Ta daga kai
kanta a kasa.
Ya sake cewa "Muje in bude miki ko?" Ta ce, "Um!"
Kawai ta ce tare da mikewa tana gaba yana baya har bakin
33
1
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
kofa, ya duba baiga kayan ba ya tuna ya jefa bayan
wardrove.
Ya jawota ya dauko ya bude mata yana kallonta cikin
fara'a sai da safe ko? Ta ce, "Eh." Ya sake cewa, "Ko in raka
ki?" Ta ce, "A'a" tare da wucewarta.
Ya yi murmushi kawai tare da binta da kallo har ta tura
dakinta ta shige suka yi ido biyu, ya dago mata hannu.
Sunkuyar da kai kurum tayi tare da jan kafarta ta datse.
Kan gado ta fada tare da fashewa da kuka, kukan
alakakan hada ta da shi, kukan takaicin kasancewarta da
shi a dakinsa, yau cikin darennan.
Duk yanda zuciyarta take azalzala akan kiyayyarsa. Ta
ci kuka son ranta daga bisani ta mike ta shige toilet don
wanka, a ganinta akwai datti a jikinta saboda tasata da ya yi
shi kuwa a wannan daran ya yi bacci me matukar dadi da
mafarkin Gimbiyar tasa cikin walwala da annashuwa.
Washegari tunda safe karfe goma ta bar gidan, koda
Momy ta tambayeta ina zata je tunda safe ta ce gidan su
Rafi'atu.
Don haka kai tsaye can ta nufa tun kan nataccanta ya
tashi. Da zuwanta ta fashewa Rafi'ar da kuka tana bata
34
WAYE ANGON?
labarin abin da ya farujiya da kokarin da ya yi.
Maryam Ja'afar far
a
Ta ce, "Na shiga tara ba uku ba Rafi'a, da Imran ya cutar
da ni jiya wallahi da na roki mutuwata a kan na juri
kasancewata da shi, tanadina Sulaiman.
Imran ba shi ba ne Angon bare ya kasance da ni." Ta
dube ta ta ce, "Ni fa ba na son hauka Mabaruka da rashin
hakuri, kan dan wannan abin za ki nemawa kanki mutuwa
don rashin hankali?"
Ta ce tana kallonta a marairaice "Har yanzu ina kara
fada ba ki san kiyayya ba, ba ki san dacinta ba a rai."
Gabadaya za ki rasa me ke miki dadi, musamman idan kina
ganin wanda ba kya son din bare kuyi rayuwar aure tare,
wallahi ba ki san sanda za ki roki mutuwa a kan
kasancewarki dda shi na rantse miki."
Ta tabe baki tare da kauda kai tana cewa, "Ina neman
tsari da wannan tsanar ko wanda ba ya sona ba na fatan na
mishi wannan tsanar."
Ta ce, "Ba wannan ba ma Rafi'a, zullumin gobe nake ya
zan yi idan hukuncin da Alkali ya yanke min wanda bai min
dadi ba."
Ta ce, "Biyayya mana, ki karbi abin da Allah ya zaba
35
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
miki da iyayenki kije ki kyautatawa mijinki, ku zauna
lafiya cikin farin ciki da ganin darajar juna, wannan ita ce
shawarar da zan iya ba ki."
Taja tsaki tare da dauke kanta tana cewa "Ba zan iya ba,
zan nemowa kaina shawarar abin da zan yi wanda ba zai
nakasa rayuwata ba."
Duk yanda Rafi'ar taso ta ganar da ita da tausasarta sam
ta kasa cin nasara a kanta sai dai tasa mata ido.
Suka yi waya da Sulaiman a kan bai zo ya ganta tana ina
sam ba shi da nutsuwa a zamanta gidan Mamanta, ta dawo
gidan Babanta.
Ta dube shi bayan yazo a sanyaye, to ya zan yi Sulaiman
Momyna ba ta min da wasa, ban isa in mata musu a kan abin
da tasa ni ba, ban ma ga fuskar tambayarta ba, bare nazo
nan na tare.
Sannan shi kanshi gidan Baban ba dadinsa nake ji ba,
matsaloli ne dankare cikinsa."
Yaja tsaki tare da rike kugu ya ce "Me ake da wannan
haukan haka nan an hana min nutsuwata, kowa ya sani ya
gani ni ne Angon, amman ana son murkushe zance a bi son
zuciya a ba wani sakarai can."
36
5
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Ta ce, "Ba kai kadai yake wa ciwo ba, Sulaiman na fika
jin ciwo da damuwa ni kadai nasan yanda zuciyata take
min daci da radadi, ba in da nake samun sauki da walwala."
Ya dubeta da kyau yana ganin abin da ta fada a idonta
duk ta rame tayi zuru-zuru, idanuwa ko yaushe a rikide
jajawur kamar ma suna ciwo tayi duhu, kana kallonta kasan
ba ta da sukuni ya dubi mashin dinsa ya ce hau muje. Ta
kalle shi da kyau ta ce "Ina zamuje Sulaiman?"
Ya ce, "Ni mijinki ne kada ki tsorata da ni, ina son yau
kadai ki sami walwala zuciyarki ta saki ki dan ji sanyisanyi kafin zuwa gobe, in dauke ki zuwa gidana."
Ko ba komai taji sanyi-sanyi a ranta duk da a ganinta in
har ba an kawo karshen rikicin ba bata jin akwai abin da zai
sa ta walwala saboda zullumin da yake dankare a ranta,
tsoronta daya.
Ba musu kuwa ta haye ya tada mashin din suka wuce:
Kai tsaye gidansu ya nufa da ita, ta dube shi ido cikin ido
bayan ta sauka ta ce, "Kana nufin nan ka kawo ni?"
Ya dube ta "Eh, wani abun ne?" Ta ce a sanyaye "A'a ba
komai hakan daidai ne."
Duk da tana jin faduwar gaba a tattare da ita, bata nutsu
37
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
da zuwansu ba, amman dai bata nuna masa ba, suka shiga
tare.
Inna na zaune tsakar gida tana dama fura, Samira na
wanke-wanke, yayin da Nafisa na kitchen tana faman aikin
tuwon dare. Inna ta bisu da kallo dai-dai. Ya shige daki ya
dauko tabarma ya shimfida ta zauna cikin jin kunya.
Duk bakin Inna sake shima ya zauna kusa da ita, ta dube
shi da kyau ta ce, "Sulaiman." Ya ce, "Na'am Inna." Та се,
"Ina ka samo wannan yarinyar?"
Ya juyo yana kallon Mabarukar ita ma shi take kallo
idanu sun raina fata, sannan ya dubi Innar, haka nan ya ji
bakinsa ya yi nauyi yana tunanin fada mata ko wacece.
Ta sake fada “kai da kai fa nake, wacece ita wannan din
ka shigo min da ita har da dauko min sabuwar tabarma?"
Ya ce cikin dan tsoro "Inna Mabaruka ce fa."
Ta ce, "Ta ina? Ni nasan wata Mabaruka ne, ina ka samo
ta?" Ya ce da kyar, "Amaryata ce fa."
Tamkar wacce aka watsawa ruwan zafi, ta zabura har
zani na faduwa ta ce, "Amaryarka ta gidan uban wa? Wa ya
bakaiye?"
Da gashi har ita sun tsorata, suka zuba mata ido ya ce,
38
5
WAYE ANGON?
"An fa daura min aurenta kowa ya sani."
Maryam Ja'afar
ifaTa сe, "Haka ka ke cewa, amman kowa yasan ba kai za a
ba ba." Ya turo baki cikin fushi "Ni fa matata ce ba me
kwace min mata."
Ta yunkura ta rarumo kara zata dake shi tana cewa,
"Amarsu ba Amarya ba don ubanka, me na fada maka tun
yaushe nake cewa ka sakar musu 'ya?"
Idanun Mabaruka suka fito, ta juyo tana kallon
Sulaiman din cikin tuhuma daman haka suka yi da Innarsa
amman bai fada mata ba?
Innar ta katseta "Gidan wa kaga ana wannan haukan
auren? Ko a garin Mahaukata ban taßa jin labari ba sai a
nan, shi ne ka ke kokarin kawo mana ita nan gidan ta zama
tarihi a dinga zuwa kallo?"
Ya dinga nuna mata da hannu ta bari tana ba shi kunya,
ta ce "Na ki na bari don ubanka, in kai kana tsoronta ni ba
na tsoronta, da kai da ita sai in hada in zabge ku da wannan
karan don ubanku."
Idanuwansu suka fito suna kallonta baki sake.
Ta ci gaba "To tunda ga ka ga ta sakarta a nan ayi ta ta
kare na fada maka ba kai za a ba ba, wahala kaďai za ka sha
39
lai
E
WAYE ANGON?
sakarai."
Maryam Ja'afar
Daga Samira har Nafisa ido suka sa abu ya zama na
kallo, ya ce "Ba zan iya ba Inna, ina son matata daga na
kawo miki ita ta gaishe ki kafin a kawo ta gobe kin bi kin
rude kina zaginmu."
Tayo kansa "Na zage ku din, sai me? Ko za ku rama
ne?" Suka yi shiru ba amsa. Ta ce, "To wallahi sai ka sake t
na rantse."
Ya ce, "Ba zan iya ba kiyi hakuri na..."kan ya karasa ya
ji saukar karan a jikinsa, abin bai tsaya shi kaďai ba har da
Mabaruka ta dinga jibgarsu.
Da sun yunkura za su gudu dukanta zai maida su, suka
kasa kwatar kansu.
Sai da kyar sannan suka arce ba shiri a wurwurce
takalma a hannu, suka tsaya a waje suna haki da maida
numfashi, suka baro Inna na cizgar fada tana fadin.
"Za ka dawo ka same ni a gidan, sakarai wahalalle, kai
ba ka ma da wayau wa ke shari'a da ma su kudi?"
Samira ta ce "Kin min daidai Inna, ke din ba ta wasa ta
ce." Nafisa ko ba bakin magana, bata isa ta ce wani abu ba,
abu ya dawo kanta sai dai tayi bakin ciki da aka kora su har
40
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
zuciyarta tana son karin aurenshi don samun saukinta.
Mabaruka ta dora hannu saman kai tare da fashewa da
kuka, "Wai wai wai ni Mabaruka na shiga uku, wai ya ake
son nayi da raina?"
Ya rasa ma me zai ce, wannan abin kunyar da Inna taja
masa har ina? Ya dubeta ya ce, "Ya isa Mabaruka, bana son
tashin hankalin nan, ba komai ba ne komai zai daidaita
kada ki damu, nasan yanda zamu yi da ita."
Ta marairaice fuska, kwalla ta cika a idanunta ce "Ko ta
ina akwai matsala, yanzu kana nufin bata son aurenmu har
tana cewa a sake ni Sulaiman?".
Ya ce "Rabu da ita, wannan fadarta ne. Tun yaushe take
fama da ni naki nayi sai dai taji ana shigowa da ke."
Ta zauna dabas kasa ta rafka tagumi ta ce, "Ga shi nan
mun sha duka karo na farko kenan ban san me zai kasance
gaba ba."
Ya ce, "Na fada miki ba abin da zata yi..."Ta katse shi
da'sauri "Don me za ka ce haka? Bayan mahaifiyarka ce ta
isa ta saka ko ta hanaka har sai da yardarta sannan zan shigo
gidanka?'
Ya durkusa gabanta ya ce, "Ni ne mai aurenki ba ita bа,
41
a
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
idan tayi kokarin raba ni da ke zan kaita kara ga
magabatanta."
Tayi jagwam tare da cewa, "Allah yasa to tsorona kar
hukuncin da kotu za ta yi ya ki mana dadi, wallahi ina tsoro
Sulaiman."Ta fada a marairaice tamkar zata yi kuka.
Shi kanshi hakanne a ransa, damuwar kotu tafi ta Inna.
Koda yaushe zuciyarsa na harbawa dankare take da tsoro,
Allah ya sani yana son Mabaruka fiye da duk matan da ya
aura.
Kai yana jin zai iya sadaukar da komai a kan ya sameta
koda 'ya'yansa karshen zance hatta Inna zai iya sadaukar da
ita idan har zai sami Mabaruka bare abin duniya, ko ransa.
Ya kwallafawa ransa ita. Kun ji fa!
A fili ya dubeta ya ce, "Koda kotu ta yanke hukuncin da
bai mana dadi ba, zna iya daga shari'a har sai naje in da za a
bani ke tunda kowa yasan uba shi ke da hakkin aurar da
'yarsa ga wanda yaso ba uwa ba, don haka ina da tabbacin ni
za a ba mata in dai ana bin gaskiya."
Ta kalle shi kurum, ita ba haka ba ne a ranta, tsoronta ya
wuce nasa. Koda ta fada masa ba zai fahimta ba, gwanda
ma kawai ta kyale shi.
42
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
Ta ce, "Mu bar wa Allah Sulaiman, shi zai shige mana
gaba yasan zuciyoyinmu duk wani dabara ko hikima ba zai
fishshemu ba." Ya ce a sanyaye "Haka ne."
Daga bisani ya dauke ta a mashin dinsa suka shiga
yawace-yawace duk don ta saki ranta ta samu nutsuwa.
Ba laifi dai ta dan ji dama-dama, amman da zaran ta
tuno tashin hankalin da ke gaba da idan ta tuna gobe kamar
yanzu an riga an yanke hukunci.
Dayan cikin biyu sai taji komai ya dagule mata, har
goma na dare suna waje.
Tuni take cewa ya maida ta gida amman ya ki, ko da
Momynta ta kirata rikicewa tayi ta rasa me zata ce, sai dai
tayi mata karya ta ce tana gidan Babanta.
Ba ta ce komai ba ta kashe wayar saboda ta yarda da ita
ranta bai kawo komai ba.
Shi kuwa Imran koda ya tashi yake tambayar Momy ina
Mabaruka? Ta ce Taje gidan su Rafi'a. Ya nanata, "Gidan su
Rafi'a kuma?"
"Haka dai ta ce, wai." Ya jinjina kai kawai amman ba
haka yaso ba, yaso ya ganta da safen nan yanda ya tashi da
kwadayin son ganin matar tasa, har ya gama abin da yake
43
WAYE ANGON?
ya fice.
Maryam Ja'afar
Har dare da ya dawo ya sake nemanta bai ganta ba, a
haka dai ya kwanta yana tunaninta.
Sulaiman kuwa gidan abokinsa Mansur ya wuce da ita,
Mansur yana da matarsa da 'yarsu guda daya.
Sun ci sun sha suna ta zolayarsu da sake labarta wannan
rikitaccen auren nasu.
Ya dubi Mansur din ya ce "Mu fa a nan zamu kwana sai
ku bamu daki daya."
Tayi saurin dubansa tare da cewa, "A nan kuma? Wasa
dai ka ke." Ya dubeta ya ce, "Wallahi da gaske nake, yau a
nan zamu kwana."
Ta marairaice fuska ta ce, "Please, kar ka min haka
Sulaiman, wallahi idan Momyna taji sai ta dake ni."
Ya ce, "Ba za ma taji ba, ba kin ce kina gidan Babanki
ba, shi kenan sai ta dauka kina can din, shi kuma daman ya
sakankance kina gun Mamanki.
Sannan ba magana suke ba bare ya tambayeta ke ko ita
ta tambaye shi."
Tayi tsuru-tsuru, sam ba haka taso ba, ta ya ya ma hakan
zai kasance har yana wani cewa a basu daki daya.
44
S
WAYE ANGON? Maryam Ja'afar
ar
1
Masifaffen tsoronta ya taso bata san sanda ta mike ba
tsalam! Sai dai ta ganta tsaye tana wuwwurga idanuwa
suka bi ta da kallo.
Basira matar Mansur din ita ta fahimce ta, tayi dariya
tare da mikewa tana ce musu "Ka bar ni da ita minti biyu."
Da haka taja hannunta zuwa dakinta.
Sulaiman din ya dago murya yana cewa, "Kar fa ki kai
min mata wani gurin." Ba ta saurare shi ba suka shige daki.
Mansur din ya yi dariya ya ce, "Kai mutumina ta zama
matarka kenan har yanzu fa a babin-badinuhu ka ke, ba ka
san tsakaninka da wancan ba,waye me matar?"
Ya dube shi a natse ya ce, "In tambaye ka mana.""Ya ce
"Ina jin ka." Ya ce, "A ganinka ni da wancan din waye
Angon?"
Ya yi dariya sosai ya ce, "My friend kenan, ni ba Alkali
ba ba Lauya ba, ta ya zan san waye Angon?"
Ya ce, "A'a a naka tunanin in za ka bi tsakani da Allah a
hukuncinka wa ka