Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 10
a wahalce da gajiya ta ce, "Ba komai ban ci komai ba, na gaji yunwa nake ji, ku bani abinci naci yau kwanana biyu ban ci abinci ba." Ya juyo yana kallon Rafi'a cikin farin ciki. "Ba ta ci komai ba, ina ga kukan da ta dade tana yi ne yas ata gaji, ba ta ma cikin hayyacinta." In ji Imran. Ita ma farin ciki ya bayyana a fuskarta, ta durkuso tana cewa, "Mabaruka!" Ta dago tana kallonta a wahalce, ta ce a hankali "Rafi'a, Rafi'atu ba ni abinci." Ta ce, "Yunwa ki ke ji?" Ta ce, "Eh." Da kanshi ya hado mata tea ya dagata ya jinginar da ita jikinsa kanta saman kafadarshi, a hankali yake bata tea din. Ta ci gaba da sha, ta sha sosai har sai da yaga ta koshi sannan ya kwantar da ita. 69 E1 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Duk dakin ta birkita shi, duk wani abun fashewa ta fashe shi tas! Koda Momy ta dawo taga abin da ya faru har da kwance kofa. Rafi'a ta ba ta labarin yanda abin ya faru. Ranta ya 6aci sosai, ta inda take shiga ba ta nan take fita ba. Ta dinga wa Imran fada sosai, kan me zai biye mata ya kyaleta mana taje ta kashe kanta mana, wa ta yi wa? Ta san dai hukuncinta, shi dai ya dinga bata hakuri, hankalinsa na kan matarsa wacce take barci bata san me ake ba. Ta shige dakinta tana fada, "Za ki tashi ki same ni, fitsararriyar yarinya kawai marar jin magana." ** ** Sulaiman kuwa wannan ihu da ya dinga yi ba arziki aka sa shi a mota, amman duk da haka kokari yake ya fito shi sai an ba shi matarsa. Gidan Inna aka kai shi, bai fasa ihun ba. Sai da aka banka masa magunguna don ya samu bacci ko ya lafa. Baccin kuwa ya dauke shi, nan da nan yana sambatu. Inna ta numfasa tare da cewa "Dankari! Nan fa ake 70 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar aryinta, so ake a zauta min da kenan? To ba zai yiwu ba." Ita kuwa Mabaruka sai dare sannan ta farka, tun baccin da ya dauke ta. Sayau ta tashi, sai dai damuwarta wuni daya duk ta fada tayi zuru-zuru tayi jugum tunanika kala-kala marassa dadi suka dameta, sai dai zaryar hawaye. Rafi'a na gefenta duk yanda taso tajata da labari amman sam ta kasa shawo kanta, ita kadai ce ke labarinta. Dole ta yankewa kanta shawarar ta kwana a nan tare da ita. Suka tsayar da magana tsakanin Momy da Daddy sai uban gayya Imran, akan tarewar matarsa gobe insha'Allahu. Ya yi jim! Yana jin damuwa a ransa da tsoron abu daya game da hakan, Daddy ya lura da shi ya ce "Akwai matsala ne?" Ya ce, "Um to! Akwai Daddy."Ya ce, "Me kenan?" Ya ce cikin damuwa yana kallonsu. "Ban san ya zamanmu zai kasance da ita ba. Ina tsoron kar ta hallakar da kanta a kaina kamar yanda take fada. Na lura har zuwa yanzu bata sona ko kadan, ko ganina bata son yi. 171 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar A duniya bata da makiyi kamata, dubi fa irin haukan da tayi yau duk don an tabbatar mata da ni ne mijinta? To yanzu kenan muna nesa da juna, ina ga muna tare da juna? Zamu yi rayuwa da ita ta kusanci kuma har abada." Yana magana abin tausayi. Da Daddy da Momy suka tausaya masa.Amman Daddy ya ce "Kai namiji ne Imran me karfin zuciya, kada ganin haka yasa ka sare. Mabaruka matarka ce an riga an daura baka da zabi a yanzu zama da ita dole ne, sai kayi hakuri da juriya zaka ci nasara, za ka samu abin da ka ke so daga gareta. Batun tsoro duk ka aje shi a gefe, ka sa a ranka zaka iya duk kurari ne ita kuma ba za ta kashe kanta ba kasa ido kuma ka gani." Ya yi jim har yanzu dai yana jin shakku a ransa, soyayyar nan fa ba dole zai iya hakuri da ita koda hakan shi ne ajalinsa ya gwammace farin cikinta a kan nasa, gwanda ita taji dadi a kansa. Daddy ya katse Imran. "Calm down my son, ka zamajarumi mana ba komai ba ne hakan anyi ba iyaka, kuma abu ya zama tarihi." 72 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar ar Kafin ya ce wani abu Momy ta ce, "Kada ka ce haka mana Imran, tunda har an zo wannan matakin kar ka sare ka ci gaba da hakuri nayi maka alkawarin Mabaruka zata zama yanda kake sonta. Maganar hakuri ma bata taso ba a יל nan. Duk yanda za su kwantar masa da hankali da ba shi kwarin gwiwa sun yi har ya ji kwarin gwiwar yasa a ranshi yanzu ma ya fara sonta da nacin zama tare da ita har abada. TO MU SAI DAI MU CE MUJE ZUWA, MUGA WANNE IRIN ZAMAN ZAAYI? A haka dai suka tsayar da maganar gobe za a kai masa matarsa, don ma rikicin da aka samu ai da ta dade a gidanta, Yanzu kuma tunda abu yazo karshe ba wani 6ata lokaci gobe a tattarata akai masa shi kenan, don ma tsiyar da tayi ai da yau za a kaita daga kotun direct. Dare har ya fara, Momy ta shigo dakin ta dubeta fuska a daure ta ce, "Ki biyo ni dakina." Daga haka ta ficewarta. Ta tashi zaune tana turo baki cikin fushi da kumburi, sai da ta gama jan jiki sannan ta mike ta fice. Rafi'a ta bita da kallo. Momyn na zaune bakin gado ta shigo ba tare da ta 73 E WAYE ANGON? Maryam Ja'afar kalleta ba ta ce "Rufe kofar ki shigo." Ta tura kofar tare da Karasowa, taja ta zauna dosane bakin gadon ta sunkuyar da kai, can kasan makoshi ta ce cikin fushi "Ga ni." Ta kalleta da kyau ta ce, "Aina ganki maganar ke banga damar yi miki ba, yanda ki ke jin kin isa da kanki nima haka nake jin na isa da kaina, bare gidana ki ka same ni gidan mijina, karkashin mijina wanda karkashinsa nake sa ran samun Aljannata. Ko nan gidanku ne ke?" Ta dago tana kallonta da sake nanata maganar a ranta, ta katseta "Da ke nake nan gidan ubanki ne?" Tayi jim sannan יי ta ce "A'a gidanki ne ba gidanmu ba ne." Ta harareta sannan ta ce, "To kin san gidana ne ki ke min iko da isa kina nuna min tamkar gidan ubanki ne nan?" Ta dago da sauri tana kallonta cike da mamaki, anya Momynta се? Ta ce, "Kalle ni mana! Na fada nan ba gidanku ba ne kara ki akai har ki ke zaune cikinsa kici abinci mai kyau wanda ki ka zaba, ki sa tufafi mai kyau da tsada irin wanda ki ke so, duk kuma ba gumin Babanki ba, ko nasa ne?" Ta ce, "Mom..."Ta katseta "Ba ni amsa kawai." Ta ce, "A'a ba nasa ba ne." Ta ce, "Da kyau! Kin ga 74 WAYE ANGON? ANGON Maryam Ja'afar kenan a matsayin agola ki ke ba 'yar gida ba ce kara ki aka yi." Maganganun sun mata zafi matuka, amman kasancewar mai fada mata ba ta wasa ba ce ko musu bata isa tayi mata ba, dole taja tayi shiru zuciyarta tana mata zafin maganganun. Momy ta ci gaba da cewa, "Shi ne kin san hakan har ki ke iskancinki son ranki ba inda iskancinki ya tsaya sai ga masu gidan, duk halaccin da suka miki da gatan da suka miki, don kin samu ko? Ki dube ki ki gan ki, kin san matsayinku ba daya ba da su bare shi makiyin naki, gabansa gaban mahaifinsa gaban 'yar uwarsa da shi ne mafi soyuwa a gurinsu sun gwammace su rasa komai a kan su rasa shi, amman ke shi ne abin wulakantawarki. To dubi kanki ba ki fi shi komai ba, kyau, asali, ilimi da kudi sai ma shi ya fiki duka hudun bare ki masa isgili, har yana bin ki shi yana sonki da kyautatawa amman ke kina nuna masa tsana saboda iskanci da rashin hankali har da kidahumanci. Sam ba ki da godewa Allah a rayuwarki, ba ki san baiwa 75 3 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar da kyautar da ya miki ba, kin watsar. Shi wanda ki ke wa ba shi da wani dalili da za ki nace masa face matsaloli dankare a gidansa. Sannan ni kin manta wacece a gurinki, kin manta matsayinki kin fifita ra'ayinki a kan nawa, kin zabi farin cikinki a kan nawa. Kin fi son saurayi a kan uwarki, wacce ta sha fadi-tashi da ke har kawo girmanki. Ko irin sadaukarwar nan ke ba za ki iya ba saboda ni kawai don na ce ki aure shi ba don yana da illa ba, sai ma ingancinsa da na ganar miki da irin farin cikin da za ki samu a gidansa. Saboda son da yake miki wanda ko rabin rabi bai kai wanda ki ke wa wancan ba, amma kin rufe idonki kina ta yin rashin mutunci ko a jikinki. Tun farkon maganar nan nake fama da ke da lallashi da ban baki amma har a ka daura aurennan ba ki ji za ki iya min biyayya ba, sai rashin kunya da ba ni kunya gaban mutane. Har yau ki ka fito fili a kotu ki ka yi magana son ranki, an kai ki asibiti ki ka baro ki ka zo tsakiyar titi ke za ki kashe kanki saboda an hada ki da mai yankar naman jikinki 76 WAYE ANGON? kullum, abin cutarwa gare ki. Maryam Ja'afar fara Kina son ki kashe kanki ki mutu kafura, kije gaban Ubangijinki wuta ta kasance makomarki, tun a nan kin sabawa Mahaifiyarki kin sabawa Mahaliccinki, kin ki karbar zabin da ya miki har ki ka kashe kanki. Ba ki ma tsaya a nan ba, ki ka dawo bakin titi ki ka dinga ihu kina kururuwa a cikin dubban mutane, saboda ki tozarta ni ki wulakanta ni. Bayan an saka ki a mota da kyar kin dawo gida kina hauka da kashe-kashen abubuwa wanda ba ubanki ya sai min su ba, ni nasa kudina na saya miki don jin dadinki, ki ka kulle kanki ke za ki kashe kanki, har ta kai ga karshe aka Balle kofar aka fito da ke..." Ta tsagaita tare da mikewa ta durkusa ta dauki dorinar dake gabanta ta nufota tana cewa. "To sai kin fada min kwakkwaran dalilinki na aikata wadannan, da kuma dalilinki na tsanarsa. Yau na gaji da iskancinki don ubanki." Idanuwanta suka fito, tsoro ya bayyana a tare da ita saboda ganin wannan sharbebiyar bulalar, jikinta ya hau rawa ta faraja da baya a tsorace. 77 1 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Ba ta fasa biyo ta ba har sai da suka dangane da bango, ba shiri taji saukar bulalar nan mai azabar zafi har cikin Kwakwalwa. Ta fasa wani ihu mai gigitarwa, a rayuwarta wannan shi ne karo na farko da ta taba dukanta da bulala a rayuwarta. Tamkar ba ita ta haifeta ba, ta dinga dukanta ba ji ba gani iya karfinta, sai da tayi mata lilis duk ta fasa mata jiki, jini ya kwakkwanta, hatta motsi ta bari bulalar duk ta ciccire. Ta dinga kuka kanta na masifar ciwo. Ta jawo kunnenta ta matse tana cewa. "To bari kiji in gaya miki, duk asarar da ki ka sa nayi yau na kayan da ki ka fasa sai kin biya su tas! Sannan duk abincin da ki ka ci da suturar da ki ka sa har karatun da ki ka yi sai kin biyawa ubansa kudinsa, tunda ba na ubanki ba ne. Me za ki yi da kayan uban makiyinki? Sakarya marar mutunci." Ta dinga kuka tana bata hakuri, hankalinta ya tashi. Tunda take bata taba ganin fushin mahaifiyarta ba har da dukanta. Mabaruka yarinya ce 'yar fari, kuma 'yar auta. Ba ta san 78 WAYE ANGON? FaMaryam Ja'afar a wani abin ba maganganun Maman suka bata tsoro, a ganinta da gaske take don haka ta rude taci gaba da bata hakuri kamar ranta. Momyn ta ci gaba da cewa, "Auran an fasa, amma duk abin da na lissafo miki sai kin biya su kayansu. Ba za ki more su a banza ba, ke a ki morarki. Sannan ni kaina daga yau ki sa a ranki ba ki da uwa, uba kadai ke gare ki. Za ki tattara komai naki ki koma gunsa can ku karata da kannanki ba ruwana da ke zan manta da ke a rayuwata, kije can ubanki ya aura miki Sulaiman din da ya fini." Ai fa hankalin Mabaruka ya kara tashi, ta gigice ta dinga gurza kuka tana rokonta tayi hakuri. Ta durkusa gabanta hannu biyu tana rokonta. "Don Allah don girmansa da zatinsa kar kiyi fushi da ni, wallahi zan yi abin da ki ke so, na tuba wallahi zan aure shi. Ba ni da kowa sai ke, ba ni da gatan kowa sai ke, don Allah kar ki rabu da ni zan aure shin wallahi na yarda." Sam taki sauraronta don ta kara tsoratata, daman tasan za ayi haka, tasan Mabaruka da tsoro sam bata san barazana ba. i1 179 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Duk don ta rikitata yasa ta ce ta tashi ta bata guri ta gama magana, tunda safe ta bar musu gidansu. Kuma ta biya su kayansu. Mabaruka ta ki tashi tana kukan tare da bata hakuri. Ta ce, "Ki tashi ki ba ni guri na gama magana, tunda dai ba kya sonsa zan nemo masa mata ya aura wacce ta fi ki, ke kuma kije can gidan Sulaiman dinki." Ta ce, "A'a Momy, na tuba wallahi na fasa na hakura zan zauna da shi, kiyi hakuri in zauna da ke in na rasa ki na rasa komai na duniya." Haka dai ta dinga magiyar nan, karshe dai turata waje tayi ta datse kofarta tana dariya. Ta dinga dukan kofar tana rokonta, tsawon lokaci da ta gaji da jan gwiwa ta nufi dakinta tana gunjin kuka. Rafi'atu ta tashi a rikice ta rikota. "Lafiya Mabaruka, me ya faru?" Kuka ya ci karfinta, ta kasa fada mata. Da kyar ta iya cewa "Na shiga uku! Rafi'a Momyna tayi fushi da ni. Ta ce ta rabu da ni in bar mata gidanta kuma sai na biya su komai da naci. Wai in koma gidan Babana, na ba ni Rafi'a ba zan iya 80 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Farhakuri da Momyna ba, ina son Mamana. Ki taimaka min a Rafi'a." Duk cikin kukan take fada, tana ji tana yarfa hannuwa. Dariya ta kusan kwace wa Rafi'ar, saboda jin shirmen da take karanto mata, an linketa baibai kuma ta linku duk don a tsoratata. Itama ta biye mata. Sai kawai ta hade rai ta ce, "Mun shiga uku Mabaruka! Ya zamu yi idan Momy ta cire hannunta a kanmu? Uwa fa ba abar wasa ba ce, ba abar yarwa ba се." Ta kara rikicewa ta ce, "Wallahi zan mata duk abin da take so, ina tsoron kar ta rabu da ni ita ce gatana." Tayi jim sannan ta ce "Gaskiya ni kaina na tsorata Mabaruka, kan namiji ki rabu da mahaifiyarki, wacce tun kafin ki zo duniya take dawainiya da ke? Take tattalinki har zuwanki duniya, har yanzu ma rana daya ki ka yarda namiji ya raba ku kin shiga uku, zai iya wulakantaki ya juya ki son ransa. Don ganin har ki ka iya rabuwa da ita don son da ki ke mishi, ki rasa inda za ki sa ranki kiji sanyi ko ma ya sakoki ki rasa in da za ki zauna ma. 81 i 1 1 1 1 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Yanzu ma to ina za ki samu kudin da za ki biya ta, tunda dai Sulaiman ki ke so? Kin ga sai a biya su sai kije ki auri Sulaiman din." Ta fadi kan gado zaune jagwab tare da rafka tagumi hawaye na tsiyaya, ta kasa cewa komai. Rafi'ar ta zauna tare da dafa kafadarta ta ce, "To me ki ka ce?" Ta juyo ta kalleta a natse tsawon dakiku. Sannan ta share hawayen taja majina ta ce, "Shi kenan na yarda." Ta fito da idanuwa "Kin yarda da me? Kin yarda ki auri Sulaiman din ki rabu da Momyn?" Ta kalleta ta ce, "A'a na yarda zan zauna da Imran, zan دو je gidansa a kan na rabu da Mamana." Farin ciki ya sauka a zuciyar Rafi'a bata taba zaton haka daga wurinta ba. Ta jinjinawa Momy da wannan hikima tata, kafin ta ce wani abu ta ce "Amman da sharadi." Tayi saurin kallonta "Wanne sharadin?" Ta ce, "Ba zai taba samun farin ciki na rana daya ba tare da ni, da yin auransa da rashinsa daya ne, ba zai ga amfanin auransa ba. 82 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Nayi alkawarin ba zan taßa ba shi farin ciki ba wallahi." Ta fada cikin kakkausar murya, idanunta sun rikide. Bin ta take da kallo kawai, abin ya wuce maganarta, ta nisa can ta ce, "Amman Mabaru..." Ta dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu "Bana son cewa komai dinki, amincewata ake bukata kuma nayi ba wani abu da za kuma ku ce." Zata sake magana kenan ta mike tare da ficewa daga dakin cikin sauri don kar taji wata maganar. A haka suka kwana wannan ranar, tun kuwa da asuba ta tafi dakin Momyn a marairaice ta durkusa gabanta inda ta sallame sallah. Ta ce, "Don Allah Momy ki janye maganarki, wallahi na yarda na amince da auransa, ina sonki bana son rabuwa da ke." Matuka taji dadin hakan, amman a fili sai ta ce, "Ni na riga na gama maganata, ba neman amincewarki nake ba, hukunci ne na riga na yanke. Lokaci ya kure miki, lokacin da nake son amincewar taki ai wulakanta ni ki kayi. Imran dai ba zai rasa matar aure ba kusa-kusa ba da nisa 83 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar ba a satinnan. Ke kuma kije ki auri Sulaiman dinki." Ta fara rudewa, ta fashe da kuka tana rokonta. Sam! Momy ta ki saurarenta, sai da taga da gaske har a ranta ta amince da auran sannan ta ce da ita. "To shi kenan, na yarda amman akwai sharadi." T се, "Na menene?"Momy ta ce da ita. "Zan fada miki amman sai kin je yanzu da kanki wajen Imran din kin fada masa kin amince da auransa har zuciyarki ba don an tilasta miki ba, kuma ba cikin fushi ba." Tayi dif! Tana jin nauyin hakan. Ta sake cewa "Ko ba za ki je ba kin fasa?" Ta girgiza kai "A'a." Ta fada da sauri, sannan Momy ta ce, "To mike kije." Ta mike jiki a mace, zuciyarta cike da takaicin hakan. Kan dole ta doshi dakin nasa. Ta shiga yin knocking. Shi kuwa ya koma bacci kenan ya dauke shi, ya ji dukan kofar. Daga kwancen ya ce "Waye?" Ta ce, "Ni ce." Ya yi matukar mamakin jin muryarta, amman ya sake cewa "Ke ce wa?" Ta zumburo baki tare da hararar kofar tamkar shi ne a 84 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar tsaye a gun. Ta ce cikin kufula "Ni ce Mabaruka." Ya yi murmushi tare da dirowa daga gadon ya tunkarota. Yana bude kofar ta wuto ciki da sauri, ya maida ya kulle yana mamakin zuwanta da sanyin safiyar nan. Ya zauna bakin gado yana kallonta, ya ce "Lafiya Mabaruka na ganki yanzu?" Tayi shiru kanta a kasa, sai kuma ta ce "Daman Momy..." sai kuma ta fasa cewa daga Momyn tuna yanda suka yi da ita. Tayi cak! Tana tunanin ta ya za ta faro maganar? Ya ce, "Ina jin ki, menene?" Ta dan dago ta kalle shi, kiftawar ido ta kuma dauke kanta ta ce. "Daman nazo in fada maka na amince." Ya ce "Kin amince da me kenan?" Haushi yazo mata wuya, don me yake son kureta? Ta dai daure da kyar ta ce "Da aurenka." Abin yazo masa kamar daga sama, ya aka yi haka to?Ya dubeta ya ce, "Me yasa ki ka amince? Ko an tursasa miki ne?" Tayi saurin cewa, "A'a, don kaina ne kawai.” Sam bai yarda ba, duk yanda aka yi aikin Momyn ne, 85 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar amma shi ya sani ba don son kanta ba ne, amman sai ya ce da ita. "Nayi mamakin hakan, idan na fahimce ki, kina sona kenan?" Sam bata da amsar da zata ba shi, ba za ta ce eh ba, ba zata ce a'a ba kuma. Ya sake nanatawa. Tayi mai banza kanta na kasa. Ya yi murmushi iya fuska ya ce, "Shi kenan na gode." Daga fadin haka tsam! Ta mike tare da cewa "Na tafi." Ya daga kai yana kallonta tare da cewa, "To sai anjima." Ba ta ce komai ba ta wuce da sauri. Ya girgiza kai tare da komawa kan gadonsa abinsa. Koda taje gun Momy ta fada mata yanda suka yi ta ce, "Shi kenan, in ma ba haka ba ne zan tambaye shi, kuma zai gaya min komai."Ta ce, "Eh na yarda." Ta ce, "To sharadin da zan kafa miki ba wani abu ba ne mai wuya, tunda har ki ka amince da auransa ya zama dole ki siffantu da matarsa. Ki masa aikin da duk mata take wa mijinta, ki ba shi farin ciki ban ce ki bakanta masa ba. Dole ne ki girmama shi da biyayya, yi masa da'a da 86 WAYE ANGON? ganin girmansa,ban da rashin kunya. Maryam Ja'afar Duk abin da ya bukata kiyi masa ba cikin fushi ba, ba kuma cikin bacin rai ba. Duk abin da yake so daga gare ki ki ba shi, ba tare da ya 6ata rai ba. Ko ya sake nanata miki, ai kin fahimce ni?" Ta daga kai kurum tana kallonta. Ta ce, "Kije ki rike wadannan, sauran kuma zan fada miki idan naga yanayin zaman naki, da kaina zan zo." Та се, "Тo." Can cikin makoshi. Ta gama jaddada mata da ja mata kunne, daga bisani ta ce "Tashi ki bani guri ki shirya duk abin da ki ke bukata da yamma za a tafi dake." Ta mike ta fice tana ji tamkar ta fasa ihu. Ta bude kofar ta shigo a sanyaye ta maida kofar ta datse. Ta jingina jikinta tare da daga kai sama tana jin wani daci-daci a ranta, miyan bakinta ya bushe kam! Hawaye masu dumi suka gangaro kumatunta, ta ce "Ya Allah! Allah ka san zuciyata, ka san bana son mijin da aka daura min aure da shi. Allah ka san wanda zuciyata take so, Ya Allah ka kawo min agaji cikin gaggawa kafin zuwa yamma. Allah kada ka 87 WAYE ANGON? bari a kai ni gidansa, zan cutu wallahi zan cutu. Maryam Ja'afar Ba na sonsa, ko kadan ba zan yi farin ciki da auransa ba, shima ba zai yi farin ciki da aurena ba, illa 6acin rai da takaici. Bana son na dauki zunubi Ya Allah ka gaggauta canza min da Sulaiman Ya Allah. Wallahi bana sonshi." Ta fada tare da fashewa da kuka mai karfi tare da durkushewa a Kasa tana ci gaba da gunjin kukanta. Duk Rafi'atu tana jin ta ta idar da sallah kenan ta koma ta kwanta, ba ta san ma me zata ce mata ba in ma za ta ce din ba zai wuce lallashi ba da ban hakuri. Ita kuwa a wannan lokacin ba zata ji hakuri ba bare lallashi, mafita take nema. Don haka babu amfanin ba da hakurin. Tayi kwanciyarta kawai ita kuwa tana ci gaba da kukan tayi goho har tana hadawa da dukan tayils din. Ganin kukan nata ya ki karewa ne yasa ta sauko daga gadon cikin damuwa. Ta dagota ba tare da ta ce da ita komai ba, suka zauna tare a kan gadon. Idanunta taf da hawaye, sun yi jajur. Hawayen na zubowa ta dubi Rafi'ar zata yi magana ta 88 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar tare ta "Ya isa, ya isa na sani nasan matsalarki ba sai kin fada ba." Ta ci gaba da kallonta tana rera kukan. Ta ce, "Imran ko?" Ta ďaga kai da sauri "Eh." Tayi shiru ta rasa ma me zata ce, tajawota jikinta ta dora kanta saman kafada cikin lallashi tare da sa hannu tana share mata hawayen. "Ya isa haka nan Mabaruka, kukan nan ba shi da dadi, kuma ba magani zai miki ba. Addu'ar dai da ki ka yi ita ce mafitar tunda kin gaya wa Allah ki sa ido ki gani." Ta dago ta dubeta ta ce, "Ina jin tsoro Rafi'a bana son zuwa gidansa, me yasa ya ki hakura da ni ya kyale ni ya nemi wata? Har sai da ya shiga tsakanina da mahaifiyata har tana Kokarin fushi da ni don dole tasa na amince da auransa. Wanne irin bala'i ne wannan? Me yasa dole sai ni?" Ta Karasa da kukan tana kallonta. Ta ce, "Wannan ba ni za ki tambaya ba Mabaruka, shi za ki tambaya. Ya san me yasa ya nace sai ke din. Wallahi Mabaruka ina yo miki wani hange a gidansa 89 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar abinda nake hasashe irin yanda zaman naku zai kasance da shi yakan ba ni sha'awa da marmarin lokacin. Na kan ji na kagara lokacin ya yi, ke kanki sai kin yi دو mamakin yanda ki ka zama haka a kansa, bare mu kuma... Ta katseta "Kina ganin har zan je gidansa ne ki ke min wannan mugun fatan?" Tayi murmushi tana kallonta ta ce, "Shi kenan, ba za ki taba ganewa ba a wannan lokacin za ki same ni ni na sani..." Ta ce, "Ya isa Rafi'a, bana son maganar nan ki bani mafita da shawara." Ta ce, "Ai tuni kin ba kanki tunda kin amsawa Momy to ni wace mafitar zan ba ki ko shawara?" Tayi jim sannan ta nisa tare da share hawayen ta ce, "Shi kenan nasan me zan yi."Ta ce tana kallonta. "Me za ki yi kenan?" Ta ce, "Za ki gani." Ta ce, "Shi kenan Allah yasa in ga alkhairi abin da nake zato."יי Ta ce, "Wai shi ne har Momy take cewa in hada abin da zan bukata har wnai shiri zan yi a yanda nake kawai su zo su tafi da ni." Ta ce, "Sosai ma shirye-shirye ga ma magungunanki 90 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar can da Mama ta dafa miki suna jiranki, jiya naji ta ce yau ko gobe za ta dafa 'yan shilan da ciccibi." Wani abu ya tokare a ranta, jin wannan zancan da Rafi'a take yi mata a yanzu. Wallahi ba abin da zata ci ko tasha, tunda ba wannan ya kai ta ba gidan, tir! Allah ya tsare. Mikewa tayi tsam! Ba tare da ta ce komai ba ta shiga bayi don zubar da miyan da ya taru a bakinta. Dariya kawai Rafi'a tayi ta bita da kallo. ** KARFE 4:07 NA DARE Su Anti Karima tuni suka hallara a wannan ranar tare da wasu dangin Momy ba daya daga dangin Babanta. Tunda safe mai gyarata tazo, tun safen take tsaye kanta na gyaran jiki, ta zuba mata lalle aka gyara mata gashin kanta, wanda aka nannade shi ya yi kyau sai tashin kamshi yake. Ballantana kuma jikinta tamkar an zubar da turaruka, jikinta ya yi kyau jikin har wani sulbi yake. Ba abin da

Chapter 4 of 10