Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
9 / 11
zaizo gurinki sai ki yayyarfa turaren nan a dakinki ki zuba a inda kika san yana zama, to da ya zo ya shaki kamshin turaren to duk abinda kika yi masa umurnin ya yi shi zai yi babu makawa”. Ya kare bayaninsa yana duban Goggo sannan ya koma da bayaninsa kan Haj. Harira. "Ke kuma 'yarki zaki ba turaren ta sa a jikinta duk ranar da kika tabbata zai zo gurinta idan har ya shaki kamshin farin turaren nan to aikin gama ya gama, amma fa ku sani matarsa da iyayenta suna tsaye a kan 'yarsu da addu'o'I, 163 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria saboda haka sai mun hada kai mun yi musu tsaye in ba haka ba za ku dinga tufka ne su na warwarewa, da kunga aikinmu ta a baya sai ku garzayo a sake sabon shiri ina fatan kun gane". Suka ce "Eh, mun gane". Ya ce, Idan maganar aure ta taso to kafin ayi sai an yi wani sabon aikin don yana son matarsa sosai yana jin maganarta baya son ranta ya 6асі, sai na dage sosai". Sai na bashi dubu ashirin, sai kuma sun dawo za su sake kawo wasu kudin na sabon aiki. Sun dawo Dukku cike da murna tare da dokin ganin zuwan Mujceb garin, domin samu nasarar aikinsu yana da nasaba ne da zuwan Mujeeb Dukku. Anyi ta samun tsaikon zuwanshi garin sabida yanayin aikinsa har sai da ya shafe sati hudu sannan ya zo Goggo ta aikata abinda boka tsidigu yace ta aikata, kuma Allah ya yi mata ta talala taci nasara don kuwa tana yi masa umurnin auren Suwaiba ya amshi maganar har ya kara da cewa, "Ni dama ba wai na ki bin umurninki ba ne so nake in kammala shirye-shirye na kuma na kamala, yanzu yaushe kike ganin ya dace a yi bikin". Goggo cike da murna ta sake yi masa wani umurni don ta dada tabbatar la aikin boka tsidugu taсe, 164 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria “Za mu yi shawara amma ya kamata ka je yanzu ku gana da Suwaibar ku fahimci juna, tunda ku ne za ku zauna da juna ba mu ba, ko tadinma mu zamu yi muku?" Ya yi murmushi ya ce, "zan je yanzu in Shaa Allah". Ko ruwa bai tsaya ya sha a gidan Goggon ba ya nufi gidan Haj. Harira don cika umurnin mahaifiyarsa, yana fita Goggo ta yi saurin kiran wayar Haj. Hariran tace mata "Aminiya albishir?" tace, "Goro sahiba ya iso garin ne?' ta ce, "Ai na gaya miki yau zai zo, to har ya zo mun gama komai bukata ta biya, gashi nan na turoshi gurin Suwaibar sai ki yi, azama kafin isowarsa ki aiwatar da umurnin tsidugu don kada a sami mishkila mu ga tangara”. Haj. Harira ta rangwada mashahuriyar guda a wayar har sai da kunen Goggo ya so ya dode tace, "Godiya ta tabbata ga tsidugu (wa'iyazubillah)) yau bukatarmu ta biya, da ya zo za a tsaida magana kin san ba za a ja lokaci ba, tunda tsidugu ya ce aikinmu zai dunga sanyi, kinga gara ayi abin wuta-wuta ko?" Тасс, "Hakan ya yi daidai ke dai je ku yi shiri". Ta katse wayar. Suwaiban na kwance bisa gado Haj. harira ta sameta tace, "Ke tashi maza ki shirya dama kinyi wanka ga mutuminki nan zuwa nan 165 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria gidan yau bukatarmu ta biya aikin boka tsidugu ya ci". Suwaiba ta mike tare da doka tsallc ta dire cike da murna tace, "Mujeeb din ne da kansa zai zo gidan nan yau?" tace, "Shine mana, maza ki yi ki canza kaya, bari in dauko tiraren nan da na gaya miki ki yi maza ki sa kafin ya iso". Kwalliya mai sunan kwalliya Suwaiba ta cancada, Haj. Harira ta kawo mata turaren nan ta gumbuda shi a jikinta, ita kanta Suwaiban karfin turaren ya bi ya dame ta irin turaren nan ne na 'yan bori me hawa ka in banda suna neman cin galaba a kan Mujeebu da ba bu abin da zai sa ya sa wannan turaren da ya kusa sanya haraswa. Gama sa turaren ya yi dai dai da jin dirin tsayuwar mota a kofar gidansu, hakan ya ba su tabbacin Mujeeb ya iso kenan. Wani yaro ya samu a kofar gidan yace ya shiga ya gayawa Нај. ga Mujeeb ya zo. Yaron yana gaya mata sakon tace ya je ya gaya masa ya shigo. A falo ya yi sallama ya sami Haj. a zaune ya risina suka gaisa ta tambaye shi ya aiki da mutanen Gombe yace, "Duk lafiya lau”. Sun yi shiru na 'yan sakonni sannan ya cc, "Gurin Suwaiba na zo tana nan ko?" Haj. tace, "Eh, tana ciki" ta kwalawa Suwaiban kira, ta fito tana rangwada, ya bita da kallo shi kam har ga Allah 166 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria bai ga abinso ga Suwaibar ba don shi ba ya son mace mai kiba sannan kibar mara fasali irin jikin zaki daga sama kiba kasa kuma kamar kwankwason zaki a tsuke ba duwawu, sannan yana auren ta idan ta ji dadin cima mai kyau dada habakewa zata yi ta cika tayi dam, ya fi son jikin matarsa ba rama sannan bata cika kibaba 'yar daidai da ita, ga komai nata mai kyau mai birgewa. Ta nemi kujera ta zauna, sannan ta gaishe shi, Haj. tace, "Tashi ki kawo masa abin sha". Та tashi ta fita itama Haj. ta fita ta yi, tare da Haj. suka shirya mishi juice a jug sannan aka juye wani garin magani me kama da busasshen jinni, wai maganin mallaka ne Haj. Harira ta yi bibaya ita kadai bayan zuwansu da Goggo ta amso, don a mallake musu Mujeeb din ya kasance idan an yjauren za su mallake ragamar rayuwarsa ta yadda ba zai ga kowa da gashi ba ko da uwarsa ce sai Suwaiba da Haj. Suwaibar ta shigo da tiren ta aje a gabansa, ta dauki kofį ta tsiyaya ta mika masa ya amsa ya yi bisimilla sannan ya sona sha, ita kuwa ta koma ta zauna tana kallonsa tare da yaba kyawu irin na Mujecb wanda yike cikin flanin ma sai an tona, ga kyau ga kyan kwalliya ga ilimi ga kudi ga kuruciya, ko da can idan ta je 167 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria gidansu sam bata gajiya da kallon Mujceb, balle yanzu da ya dada hadewa, tamkar ka surc shi ka saka a jaka ka boye saboda kyau, ga kayan da ya sa sun amshi jikinsa shadda ce Galila 'yar asalin, an yi masa dinkin boda me kalar kunun kanwa. Ya dube ta ya cc "ya karatu ance kin gama bana ko?" ta cc, "Eh, na gama", yace, "kin dai cinye ko, kinga sai ki fara jami'a tare da Munceba ita ta sami Nine credit". Cike da bakin ciki da wai Muneeba ta sami nine crcadit ta ce "ni ban je an duba ba, amma zan je". Ta fadl haka ne don ba zata iya gaya masa 3 credit ta samu ba kuma ba maths ba English kenan bata da shiga jami'a a wannan shekarar. Suka ci gaba da hira amma zance daya biyu sai ya sako sunan Munceba, haushi duk ya isheta na yadda ba ya iya wata maganar arziki in bai hado da sunan matarsa ba, yana koda ta yana yabon halayenta sai kace ita ce macen farko mai kyautata wa miji a duniya. A zuciyarta ta sha alwashin sai ta raba harshensa da Ambato sunan Muneeba, za ta maye gurbinta da nata sunan a bakinsa dama zuciyarsa Bai dade sosai ba ya yi sallama da su ya tafi bayan ya yi musu yayyafin naira, Haj. Harira da yarta aka dunga murna har da tsalle saboda burinsu na shckara da shekaru a cikin Mujeeb WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria yau ya cika. Koda ya koma gidan Goggo bata barshi ya tafi ba sai da ta tabbatar sun tsayar da maganar biki da shi ana da wata biyu za ayi zai turo da kudi su baffaninsa tunda kuma su ne 'yan uwan ubansa sai su kai kudin duk da ake kaiwa na neman aure Daga gidan Goggo gidan yayarsa Adda Fadıma ya wuce ya labarta mata komai dangane da maganar aurensa da Suwaiba Fadima ta jinjina maganar tace, "yanzu Goggo dai ta dage lallai-lallai sai sun hadaka da Suwaiban nan, yarinyar da bata da kirki bata ganin mutuncin mutane, sannan kowa ya san Haj. Harira da bin malaman tsubbu, kai kanka na san sunanka aka kai aka yi tsubbu har ka amince tunda da ai baka son auren shine ta san yadda tayi ta shiga ta fita sai da ka amince me ake da irinsu Haj. Harira (FA DALLU WA ADAL) ne, su bata kuma su 6atar, mu dai kada ta koyawa Goggonmu bin bokaye don zata iya tunda ta fata itama ta batar da ita". (Allah sarki ba su san aikin gama ya gama ba) Mujeeb yace, "Wallahi ni kaina ba son yarinyar nake ba, don dai in farantawa Goggo ranta ne ya sa na amine, ni dai ku taya ni da addu'a Allah ya sa alheri za su kulla in kuma ba alheri to Allah ya tarwatsa al'amarin". Adda Fadima ta ce, "Tunda ka ce har 169 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria an tsaida wata biyu, to sai ka gayawa Munccba don ta san halin da ake ciki". Yace, "Gaskiya saboda gudun tashin hankali Goggo tace kada in gaya mata don ba a san ya zata kaаrбі abinba, idan biki ya matso sosai sannan zan gaya mata". Adda Fadima tace, "in kuwa ka yi haka ka ci amanar zumunci kuma ka munafinci matarka, saboda ai ba zama munafinci kuke yi ba da zaka 6oye mata abinda yake faruwa kuma irin wannan halayyar da maza ke nunawa su ki gayawa matarsu zasu kara aure har sai abu ya zo daf su gaya mata, shi yake kawo rigima a tsakanin ma'aurata har a dinga zagin matar ace ta cika kishi tana hauka don mijinta zai kara aure alhalin munafincin 6oye mata da ya yi nc ya kawo musu sabani, amma da tun farko ya gaya mata cikin lallashi da lumana da hakan bata faru ba. Saboda haka yau kana komawa ka gaya mata sannan ka lallasheta, nima bayan ka gaya matan zan kirata in kara lallashinta". Ya yi na'am da shawarar Addanshi, shi yasa ma da ya shiga garin Gombe kai tsaye ya zarce wani katafaren super market ya zabgowa Munecban sayayya ta ban mamaki sannan ya isa gida. Gidan sai zuba kamshin turaruka yakc yi shi kam hakan ya na masa dadi, yadda Muneeba take dadada musu gida da dakuna da Kamshi don 170 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria babu yadda za a yi ka zo gidansu ka tarar baya kamshi, har suna ya rada mata 'yar kamshi. A falo suka hade zata fita tarbo shi sai gashi har ya shigo. Ya jata jikinsa ya rungume yana aika mata da sumba a jikinta ta ſan janye kadan ta се, "Ка dawo lafiya ko?" ya su Goggo da sauran jama'ar Dukku?" yace, "kowa lafiya suna gaishe ki". Sai suka ji sallamar yaron da ke musu hidimar gida Jume". Suka amsa sallamarsa tare da yi masa izinin shigowa ya shigo niki-niki da kaya a hannunsa yace ya kwaso a mota, ya ajiye sannan ya yi musu sai da safe. Mujeeb ya dakatar da shi ya sa hannu a aljihu ya ciro gudar dubu daya ya bashi ya yi godiya ya juya ya tafi, a ransa yana yaba kyawawan halin iyayen gidan na sa na kyauta da alheri da sanin darajar dan adam, har ya kan rasa wa ya fi wani kirki cikinsu, sai dai kawai ya yi musu kudin goro halinsu iri daya ne shi yasa suke zaune lafiya cikin so da kauna,bai taba jin kansu ba. Kai tsayc bayi suka wuce, ruwan wankansa na jiransa, duk da irin kwalliyar da tayi, bai sa ta yi tunanin kayanta za su baci ba, ita ta yi masa wankan suka fito ya gabatar da Sallar Isha'l sannan ya sa 'yar rigar shan iska suka dawo falonta bisa dinning tablc don c.n abinci. Ka'ida a dakinsa suke kwana, sai sunyi WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria nishadi ne suka kwana a dakinta. Sun ciyar da junansu abincin da ta shirya kusan kala biyar har da abubuwa sha, suna ta hirarsu cikin nishadI, sai dai shi da yakc kawai yake yake yi don magana na tsikarinsa amma ya kasa yadda zaiyi ya gaya mata, yana tsoron kada ya ruguza wannan nishadi da farin ciki da ciki yanzu saboda al'amar kishi ga mata hakika babban abu ne, maza yaki shine jihadinsu mata kuma kishi shine jihadinsu, idan mace ta yi hakuri ta iya yin jihadin kishin da ya tunkuro ta to za ta iya samun aljanna. Ita kanta Muneeba ta lura da yanayin nishadin mijinta ya sauya a daren yau, saboda in har zata fita ta dawo sai ta iske shi cikin zurfin tunani har ta yi ta damunsa da tambaya yana ce mata babu komai, duk yana kaucewa fada mata babu komai duk yana kaucewa fada mata nc don ba ya son abin da zai dagula zuciyarta alhalin shi kullum burinta ta gata faranta masa, ko da za ta takura kanta ne, shi kam in banda Addanshi tace idan yaki gaya mata ya munafinceta hakika da ya boye mata don ya samawa kansa farin ciki, shi kam baima san yadda aka yi kaddara ta kwasheshi ya amsawa Goggo cewa zai auri Suwaiban ba. Ko wane namiji yana da hujja kwakkwara idan kaga zai kara aure, to shi kam WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria bai ga wannan hujjar ba, don Muneeba bata rageshi da komai ba, bata da bashinsa in dai gurin kyautata nasa ne, ita kanta Goggon shaida ce akan haka, sai dai ta ki fadan gaskiya, ta fake da cewa don ya sami zuri'a takc son ya kara aure, wai ba zai yiwu Allah ya azurta shi ba ta ko wane fanni amma ace baya da arzikin 'ya'ya, ai arziki bai yi ba, tunda Muneebar ba mai haihuwa ba ce gara ya auro wata kila ita ta haihu, ya yi wa Goggon bayanin da ake musu a asibiti idan sun je cewa lafiyarta lau lokači ne kawai bai yi ba, amma Goggo ta sa kafa ta yi fatali da bayaninsa tace karya ne, boye mata ya ke yi kila ma ance har abada ba zata haihu ba, dole yake hakura da bayaninsa ya kyale Goggon tunda ba zata yarda ta gane ba. Sukan kwana cikin farin ciki da annashuwa, har yake, tunannin shifa zai je kawai a sami Goggo yace mata su yi hakuri ya fasa auren don matarsa babu abin da bata yi masa, kada ya zo ya auro wadda zata wargaza musu zaman lafiyarsu, amma da garin Allah ya waye sai ya ji son auren ya sakc tasiri a zuciyarsa ya ji ba zai iya tinkarar Goggo ya ce ya fasa ba, idan ya yi haka tamkar ya tozartata ne, duk da ba wani son Suwaibar yake ba, zai dai aureta ne 173 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria saboda Goggon ta matsa masa, kuma don ya faranta mata rai. Sai da ya yi shirinsa tsaf na zuwa ofis, sannan ne ya kira Munceba suka zauna a falonsa yace, "Munceba ina son mu yi wata magana, amma ina son ki yi wa maganar kyakkyawar fahimta, kuma wallai ba da son raina hakan za ta faru ba na yi ne don bin umürnin su Goggo, kuma ina ganin ni da ke mun zama jinni da tsoka don idan aka tsaga jiki na za a ga irin jininki, ke ma idan aka tsaga jikinki za aga irin jinina, ina son mu ci gaba da hada kanmu ta yadda ko wani ya shigo tsakanin zaman mu ba zai ga wata faraka a tsakanin mu ba balle ya sami kofar da zai ci gaba da haifar mana da wata 6arakar". Zuciyar Munecba ta soma, bugawa fat! Fat!! Fat!!! ta soma karyata żuciyarta na irin abinda take kitsa mata shine zai faru, kafin ta yi yunkurin cewa wani abbu har ya ci gaba da cewa "kin riga kin san Goggo ta na son hada ni aure da 'yar aminiyarta Haj. Hariria, wato Suwaiba, to sunci galaba a kaina don ban san yadda aka yi ba na amince wa Goggo zan auri Suwaiba, har an tsaida lokaci jiya an aje wata biyu masu zuwa za a yi auren, shine na ke son ki kwantar da hankalinki ki bani hadin kai, mu ci gaba da zaman lafiyar mu,'na yi miki alkawarin in sha 174 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Allah ba za ki ga wani sauyi daga gareni ba, zan ci gaba da sonki da tattalinki har abada ba zan juya miki baya ba don na yi aure, za ki ci gaba da zama tauraruwar zuciyata". Hawayc ne kawai ya kc ambaliya a kuncin Munceba, ta kasa cewa komai, saboda jin wannan bala'I da ya rufto mata, kwarai auren Suwaiba ita bala'I ne a gareta domin ko kankani Suwaiba bata da kunya sannan ba sa shiri ko kadan, don idan ta zo gidan gurin Goggo ita kadai ko da Hajiya Harira harara ce kawai za ta dinga ballawa Munceba, bata yi mata magana sai idan ita ta yi mata, kuma ko ta yi mata ma bata cika amsawa ba, sannan acc ita ce za su yi zaman kishi, sannan ga tarihin rayuwar auren Hajiya Harira da kowa ya sani a Dukku, har ubansu Suwaiba ya mutu bai taba tunanin kwatanta kara aure ba duk da mai hali ne ba talaka ba, sannan ita ce ke jan ragamar gidan, komai zai yi sai da izininta ya ke yi ta raba shi da 'yan uwansa kaf bai zuwa gidansu, haka suka yi rayuwarsu har Allah ya amshi ransa.. ya'ya dama kuma ta raba su da dangin ubansu da ya rasu sai ta zamo ita cc uwarsu itace uwansu, ko da neman aurensu aka zo sai ta wakilta wani kawunta da yake mai son abin duniya ne ta dan yi masa hidima to shi yake shigewa gaba gurin auren 'ya'yanta kunga ko ta 175 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria nan manema auren za su gane ba su zo gidan mutunci ba tunda babu dangin uba a neman auren. Mujeeb ya jawota jikinsa ya rungume yana kara lallashinta, a kan wannan al'amari da ya same su tare da tabatar mata In Shaa Allahu ba zai wofintar da ita ba, ba zai ci amanarta ba, ta kwantar da hankalinta. Ta dube shi idanunta sun yi ja saboda kuka tace, "Don Allah ina son ka yi min wata alfarma", yace "Fadi ina jin ki in dai zan iya to In Shaa Allah duk zan yi miki'. Ta ce "Na amince ka kara aure amma don Allah ba da Suwaiba ba ka canza wata, don ina tsoron al'amuran Suwaiba da Hajiyarta, sannan kai kanka shaida ne a kan irin alakar da Suwaiba ta ke yi da ni idan ta zo gidan mu, ji take tamkar ta sheka ni don na aureka, bata kaunar gani na tare da kai sam, to ka ga ina ga muna kishi kuma ai bani ba zai yi mini kyau ba". Yace, "ba zai yuwu ba in fasa Muneeba tunda na riga na anince wa Goggo, idan na ce na fasa ke za su cc kin hanani tunda sunce sai abinda kika ce na ke yi, abinda na ke so da ke shine ki yi hakuri ki kwantar da hankalinki,. varinvar nan ko ta zo gidan nan ba za ta WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria kamo matsayinki ba, balle har ta ce za ta zarta ki, kuma bata isa ta zo ta raina ki ba ko ta tayar miki da hankali, wallahi ba zan lamunta ba zan nuna mata kurenta, saboda haka ki kwatar da hankalinki ni da ke nan gani nan bari kuma mutu ka raba takalmin kaza”. Da zai tafi ta roke shi cewa tana so za ta je gidan Inna Amina ya dan tsaya yana dubanta cike da nazari sannan yace "Za ki kai karata ne gurin Inna Aminan? Ki yi hakuri kada ki sa 'yan uwanki su dinga jin haushi na, ke ma kin san bin umurnin Goggo na yi ba don in 6ata miki rai ba, in banda Goggo babu wanda zai sa ni in yi abinda ban yi niyya ba". Tace, "Ni ba karar ka zan kai ba kawai abinda dama zai kaini, maganar maganin nan ne, ai na gaya maka mai maganin nan ne yace dole sai nazo ya yi mini tambayoyi kafin ya bani magani, ba zai yiwu ya bada magani da ka ba". Yace " OK na tuna to amma na san ai sai kin gaya mata wannan maganar, sai dai na san Mama ba zata baki gurguwar shawara ba, za ta tayi ni lallashinki tare da baki shawarwari na gari, kuma dama ina so in gaya miki ina son za muje Umara kafin bikin saboda ki ga likita, wai abokina ya gaya mini wani asibiti a Jidda zan kaiki a duba ki, da ban yi niyyar gaya miki ba na bari ne sai 177 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria na gama shirin komai sannan in gaya miki". Тасс, "Amma kana ganin Goggo ba zata ce a bata yardaba, gani na yi ita ya kamata ka fara biyawa aikin Hajji kafin ni in je". Yace, "To ai ba aikin Hajji ba ne ganin likita za mu je tunda dole har dani za a duba din ba a san wa ke da matsaar ba, kinga a nan duk sun ce lafiyarmu kalau a can kuma ba mu san me za su ce ba". Tace, "Sheke nan Allah ya kaimu, ya sa a dace". Yace "Amin". Ya kamamla shirinsa tsaf ta rakashi har jikin motarsa ya shiga ya tafi, sannan ta dawo gida ta soma gyaran gidan kamar yadda ta saba kafin jume ya zo ya yi nasa ayyukan gidan, kamar su shara wankin kayan shi da yin guga sai kuma aike idan suna da shi. Ta isa gidan Inna Amina ta iske ta yi bakuwa, hakan ne ya sa suka shige dakin su Khairi suna ta hirarrakinsu duk ta kosa bakuwar Inna Amina ta tafi don su kebe da ita ta gaya mata abinda ke faruwa, abin yana ta tsinkunkuninta har sai da ta gayawa su Khausar, salati suka dauka suka dire mai karfin gaske wanda har ya jawo hankalin Inna Amina da ta dawo rakiyar bakuwar ta, ta shiga dakin nasu a 178 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria hanzarce tana tambayarsu "Lafiya? Mutuwa aka yi kuke salati mai karfi haka?" Khairi tacc, "Ai mama da jin sakon mutuwa da irin wannan mummunan labarin da Munceba ta bamu duk daya ne a kunnen wanda aka gayawa in dai ya shafe shi". Ta сe "kai wai me ya faru ne? ku fito direct ku gaya min bana son shirmenku Khausar tayi karaf ta ce, "Hum Mama wai kinji Mujeeb aure zai yi nan da wata biyu". Ita kanta Inna Amina zancen ya soki zuciyarta, amma don kada ta nuna ta dada ingiza su ta kuma karyawa da Muneeba zuciya sai ta yi jarumta ta ce, "To meye don zai yi aure a kanki matar zata zauna, ta so nan mu je daki ki kyale wadannan sakarkarun, in baki dau abin da zafi ba damuwar da za su nuna sai ta sa ki zafafawa kanki, taso mu je”. Muneeba ta mike idanunta cike da kwalla Inna Amina ta ruko hannunta ta rungumota tana share mata hawayen da hannunta har suka isa dakinta. Ta zaunar da ita a gefen gado itama ta zauna sannan ta ce, "gaya mini me ke faruwa da gaske auren zai yi ta gyada kai sannan ta labartawa Inna Amina yadda maganar auren ia ke da adadin lokacin da ya rage. Inna Amine. WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria tace, "Yanzu wannan yarinyar 'yar wajen Haj. Hariran zai aure" tace, "Itace zai aura kin san tun tuni Gggo ke son hada auren yaron ya nuna baya so, ko lokacin bikinmu ai rigimar da ka yi ta yi da ita kenan sai dai ya auri Suwaiba, to yanzu sun samo kanshi shine ya amince, ni na san zama na ya zo karshe a gidan Mijceb, saboda halayyar Haj. Harira kowa ya sani bata son kishiya, kin ga ba zata so a'ce 'yarta na da kishiya ba, ko yanzu da ya yarda zai auretan akwai abinda suka yi masa har ya amince, Adda Fadima ta yi mini waya dazu haka tace, amma tayi ta bani hakuri, ta ce ita sam bata goyon bayan wannan aure don dai babu yadda zata yi ne da ta hana shi, tunda abin hadin Goggo ne sai dai mu yi ta addu'a duk sharrin da zata shigo da shi gidan ya kare a kanta":. Inna Amina ta ce "ni ma shawarar da zan baki kenan ki yi hakuri ki kwantar da hankalinki ki sa Allah a zuciyarki kuma ki kudirta cewa zaki zauna da ita tsakani da Allah babu cutarwa, sai ki ga Allah ya dube ki ya yi miki kariya idan ita ta zo gidan da mugun kudiri, kuma kada ki sa maganar rashin haihuwar ki a ranki ki yi ta damuwa, Allah ya na sane da ke bai manta da ke ba, In Shaa Allah zai dubeki ya azurtaki da haihuvar 'ya'ya masu albarka, in ma bai bakin WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria ba kiyi godiya a gareshi da ya baki rai da lafiya, ki na cikin rufin asirinki wani shi kuma Allah ya bashi ‘yan'yan amma ba da lafiya, wani babu wadatar abinda zai ciyar da su, babu muhalli ba ba ba tayi masa yawa, sai arzikin 'ya'ya amma ba arzikin kwandala, to kowa da irin na sa arzikin sai ki yi ta yi masa tasbihi, da tahmidi da taklili, ki yi ta gode masa, kada ki yi kukan rashin haihuwa ki yi wa Allah batulci don ya baki rai da lafiya da arziki dai dai gwargwado. Bari in kira aminiya Rahman Zaria ta sake baki wasu shawarwarin a waya tunda ni ma mamanki tana bani shawarwari ina amfana da su sosai". Muneeba tace, "mama wace ce Rahma Zaria?" tace, "Au har kin manta Rahmatu Hassan Zaria da na baki littafinta DON MAʼAURATA da SIRRIN GIRKE-GIRKE 1&2 ko kin watsar da littafan ne? tace, "Lah! Mama na tuna ta wallahi na karanta littafan su ne ma abokan huldata ko da yaushe, na karu da littafan sosai don na koyi girki kala-kala a ciki wanda da ban iya ba, sannan ta fannin kula da miji na koyi abubuwa da yawa, gaskiya ta yi mana taimako mu ma'aurata Allah ya biya ta da gidan aljanna. Don Allah Mama kirata na san za ta bani shawarwari masu alfanu". Mama ta yi dailing numbarta bugu daya biyu zuwa uku saita dauka suka yi wa juna 181 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria sallama sannan gaisuwa ta biyo baya

Chapter 9 of 11