Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 11
ko bako tayi bazata sami sukuni ba sai ta gama ayyukan da suka zamo wajibi a kanta, idan a haka ba to idan bakin nata suka tafi zaía zo ta iske aikinta na nan yadda ta barshi bata samun sukunin hutawa sai sun gama girkin dare, idan tayi wanka shike nan ta gama na ranar sai kuma ba gobe, yaune don yayi shigowar dare ne tabbas da ya zo ya isketa kaca-kaca cikin aiki. Mujecbu yayi iya kokarinsa don Munceba ta gaya masa abinda yasa tayi rama amma tace masa ita babu komai, kuma ba ciwo tayi ba, sai zuciyarsa ta fara zargin to ko dai Goggo ta fara gallaza mata ne tunda ta rigata fada bata son aurensu? Ai kuwa a irin ladabi da biyyar da Muneban ke masa ya kama ta watsar da rashin son auren nasu ta rungumi Munceban hannu bibbiyu a so ta tunda tana kyautata mata, amma zai cigaba da bincike a hankali har sai ya gano meke faruwa ne a gidan dangane da zamansu. Baisake tsinkawa da al'amarin Muneba baya tabbatar lallai wani abu ya faru da bayanan sai da suka zo kwanciya, sun riga sun san tare suke kwanciya cikin bargo daya, amma yau ko WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria gado daya taki yarda su hada balle bargo daya har da ratsuwarta na ccwa ba zata kwana tare da shi ba, za ta kwana a falo a doguwar kujcra ko, ta kwana a kasa yayi zuru yana kallonta lokacin tana kokarin shimfida bargo a kasa, abin duk ya daure masa kai, tabbas wani ya zuga masa matarsa tunda bahaka suka rabu ba, don ko daren ranar da zai tafi ta sallama masa kanta, shine dai ya kyaleta saboda tausayinta da yake ji, kamar zai kwareta yake gani shiko wasannin da suke yi, suna rage masa karfin sha'awarsa yana wadata da hakan, to yau ta guje shi wannan matsalarma dole ya binciketa tunda ba zai iya jurar hakan ba. Haka suka kwana kowa ransa babu dadi, yana gado abinsa, ita kumatana kasa nade cikin bargo. Washe gari ma hakance ta kasance, don ko da rana tayi mirsisi ta hana ya rabi jikinta, abin ya dame shi kuma ya daure masa kai sosai har ya soma bincikarta dalilinta na gudunsa da take yi yace, "Wai ni Munecba ko wata cuta aka ce miki ina da ita yasa kike gudu baki son ko jikinki in goga kada in shafa miki cuta?" tace, "ni daiban ce haka ba, waya isa yace kana da cuta gaka nan lafiyayyanka da kai", yace, "To meye dalilinki na irin abinda kike mini tun jiya da na zo?" ta soma nuku-nuku sannan da kyar ta iya cewa, 125 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "Ni fa ba gudunka nake yi ba, ni dai tsoro nake kada in samu ciki, idan na koma maaranta a kore ni, kasan basa yarda da mace mai ciki amakarantar kwana ko mace na da miji". Ya yi murmushin ban mamaki yace, "Nima ina son ki karasa karatunki, ai bazan yarda ki samu ciki yanzu ba, ai babu abin da zanyi miki, da ya wuce wasannin da kika ga ina yi miki, ki kwantar da hankalinki bazan yi miki abinda zaki sami ciki ba, nayi miki alkawari". Ta soma 'yar shagwaba "To ai shima wasan da kake mini ance in dai mace ta yarda namiji na wasa da ita yana tattabata zata iya ganin ta da ciki, shi yasa nake tsoro". Dariya Mujecb yayi sosai sannan yace, "Haba Muneeba kada ki bani kunya, yanzu duk karatun islamiyya da na bokon da kikayi da zanki cikin wayyayyun mutane a Gombe baki san cewa sai ta hanyar yin jima'i tsakanin mace da na miji sannan macen ke samun cikiba, duk wani wasan da za a yi da mace ba zata taba daukan ciki ba har sai jima'i ya gifta tsakaninsu. In kuma har yanzu baki fahmci hakan ba, zan kira Malam Ayuba na nan baya ya zo yayi miki bayani dalla-dalla kila zaki fi ganewa. Tace, "Ni kam bance ka kira mini Malam Ayuba ba, ka barni zan a hankali, idan lokacin da zan gane 126 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria gane yayi".yace, "Gaskiya gara in kira shi tunda kin nuna ke kifin rijiya ce bai san komaiba to gara a fayyace miki abinda kika siga duhu akansa, tundani ko nayi miki bayani ba ganewa zaki yi ba", tace, "Don Allah kayi hakuri karda ka kira mini kowa in kuma ba so kake ka tonawa auren mu asiri ba". Ganin ta nuna ta bata son ya gaya wa kowa, abin da ke faruwa tsakannin su, shi yasa ya kyaleta, amma in har ta cigaba da gudunsa to yasan dole ne aji, don da ransa da afiyarsa ba zai yiwu hakan ta kasance a kansa ba kuma ba zai iya jurewa ba. Kwana biyun da yayi, yayi su ne cikin damuwa da rashin gane kan Muneeban a dalilin barinsa da take yi a daki tayi tafiyarta can sasan Goggo, wanda da ba hakatake masa ba, idan yana gida tota kan kasance ne tare da shi, amma yanzu muraran take gudunsa, kuma iya bincikensa da yayi, ya kasa gano ko wane ne ya cusa mata hudubar guduns. Da safe ranar kwannansa na uku, shi yana daki yana nazari ita kuma tana kicin tana gyara kayan wanke-wanke da ta wanke saita ji sallama, tana dago idanunta ta ga Goggosu Hinde, ta saki kwannanon hannunta da gudu ta fita tana WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Oyoyo Goggonmu, Oyoyo", ta rugume Goggon tana murna. Itama Goggo Hinden cike da murna tace, "Sannu 'yar gidan Goggo aiki ake yi ne?" tace, "kicin nake gyarawa, shigo faki Goggo Yaya Mujeeb ma yana ciki". Yana jin zuwan Giggin yay hamdala, dama yasan da zuwanta shi yaje har gida yayi mata bayanin abinda ke faruwa tsakaninsa da matarsa tace ya taho gata nan zuwa zata binciki Muneeban idan ta zo sai ta ji musabbabin daga inda matsalar ta kunno kai. Ya mike tsaye yana yiwa Goggon sannu da zuwa. Bayan sun gaisheta ne ta ke dubansu tace, "Ni ban gane ba ne, na zo inga 'yata tayi cikar daki tayi kyau, sai naga duk kinyi dan wuya, shi ma dan nawa naga a rame, kamar ba amarya da ango ba, me ke faruwa ne, ko har yanzu ba kuyi amanna da hadin auren da aka yi muku bane?" Muneeba ce tayi karaf tace, "Lafiyarmu lau Goggo, babu wata matsala". Mujeebu yace, "Gata nan Goggo Allah tunda na dawo na rasa gane kanta ni ban sani ba ko nayi mata wani abune, tunda satin da ya wuce da zan koma lafiya lau muka rabu", yanayin yadoa, Mujeeb yayi maganartamkar yanzu ne ya fara sanar da WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Goggo Hinde matsalarsu, alhalin ta riga ta san komai. Goggo ta dubi Munceba da ke ta zabgawa Mujccbu harara a fakaice tace, "Gaya min me dan nawa yayi miki? Idan na fada ne in yi masa fada inja kunnensa in ma laifin ya kama naduka ne sai in bugeshi gaya min". Muneeba tanoke tace, "Ni fa Gogga babu abinda yayi mini", tace, "a'aMunecba kinyi masa laifi mana tunda yace ya kasa gane kanki alhalin lafiya ya koma Gombe ya barki ba wata matsala a tsakaninku, kada fa ki bada wata kafar da idan baya nan wani zaizo ya zuga ki, ya hargitsa muku zamanlafiyar da kuka gina, ko waye ki natsu ki lura da shi zaki ga ba mai kaunar aurenku ba ne, ba mai son ci gaban rayuwar aurenku bane, ki yi karatun ta natsu kada ki sake a sake yi miki wata huduba ta banza akan mijinki tunda sai bango ya tsage ne kadangare yake samun gurin shiga". Kalaman Goggo Hinde sun sa jikinta yin sanyi lakwas, har ta gano lallai hudubar da Goggansu Mujcebu tayi mataba abin dauka bace, kasancewar tun fil azal bata kaunar aurensu, kenan kota yaya zata iya bin duk wata hanyar da zata bi don ganin rashin zaman lafiya ya wanzu a tsakaninsu, kai dole ne ma tayi watsida hudubar Goggon ta 129 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria rungumu bukatun mijinta don suna lafiya duk abinda Allah ya nufa zai faru idan ma ta sami ciki sun koreta a makaranta sai yayi mata tiransifa ta koma wata makarantar ta jeka ka dawo. Wai tunanin me kike yi ne?kinga ki natsu kiyi aiki da iliminki ki ba aurenki Muhimmanci ki bauta masa da dukkan iawarki babu ruwanki da 'yan boni naiya, 'yan hana ruwa gudu, su 6ata goma biyar bata gyaru ba naga bakinki da alamun magana, ki gaya min meke faruwa ne?" Muneeba ta soma 'yan noke-nnoke tana son gayama Goggo Hinde hudubar da sirikarta tayi mata, amma tana alhinin fada a gaban Mujeeb, sai Goggo Hinde ta dubi Mujeeb tace, "Tashi ka tafi hidimar gabanka zanyi mata fada da nasihohizata gyara in sha Allahu zamaku daidaita, kuma bana son ka gayawa kowa sirinku ne kaida matarka, ka ji ko?" ya gyada kai tare da mikewa yace, "Shikenan Goggo mun gode, ki gaida gida, kila kuma in dawo in sameki, ki tsaya ki ci girkin diyarki wallahi ta iya girki, kamar kun nin mutum zai tsinke saboda dadi". Dukansu ukun suka kyalkyale da dariya Goggo tace,"haka ake so mai gida ya dinga yabon girkin uwargidansa, kinga kinci jarabawar 130 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria girki saura gurin kula da miji ma ki cinye". Mujeeb ya fice ya bar Goggo da Munecba. A irin hikima ta su ta manya ta lallashi Muneeba cikin hikima da dabara Muneebanta zayyana mata duk yadda Goggo ta gargadeta akan kada ta saki jiki da mijinta ta yadda idan ta kuskure ta sami ciki to karatunta zai zama asha ruwan tsuntsaye, idan kuma ta bi ta son miji taki yin karatun to labudda nan gaba zai auro wadda tayi karatu, ita kuma zata zamo koma baya, wannan kalma ta koma baya da Goggo tace zata zama idan Mujeebu ya auro 'yar boko ita tafi zamowa mafi tasiri da sosa mata zuciya matuka gaya, har hakan yayi babban tasiri a zuciyarta na abin da ta yi wa mijinta da da mara idanu, kawai gara ta hakura ta watsar da hudubar Goggo ta rungumi mijinta hannu bibbiyu. Goggo Hinde ta hau tafa hannu da sallalalimi tace, "yanzu Gogon kuce da irin wannan hudubar da bata dace ba? To ai wannan abinda tayi Mujeebun da take tsananin kauna shi abin zaifi shafa ita kanta ba zata gane kansa ba indai tace irin wannan hudubar zata ci gaba da yi miki ta ki bijircwa mijinki, ke kuma tamkar wata shashasha, kin manta cewa bata son aurenku, duk hanyar da zata bi don ganin baku zauna lafiya ba zata bi, saboda haka ki natsu ki dinga 131 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria daukar huduba ta gari ga duk wandaya baki, wadda kika ga ba ta gari bace to kiyi maza ki watsar da ita, bana son in sake jin wani abu mara dadi ya shiga tsakaninki da mijinki, kada ki zamo mace mai fallasa ssirrin mijinta, ki yi masa ladabi iyakar iyawaki. Allah yayi muku albarka ya baku dawwamamman zaman lafiya amen. Haka Goggo Hinde ki tayi ta ba Muneeba shawarwari da nasihohi da hikimomi da dabaru na zama da miji, kafin ta tafi. Da zata tafi Muneeba ta kawo sabulaimasu Kamshi ta zuba a leda ta kawo mata, da kyar ta amsa suka fito zuwa sasan Goggo. A tunanin Goggo Rahim 'yar uwarta ziyarar zumunci ta kawo mata bata san gyaran auren 'ya'yanta da take son gurguntawa ta zo gyarawa ba, kuma tana fatan ta gyara 6arakar da Goggo Rahin din ta yi a zamantakewar 'ya'yan nata da yarinyar Allah. A kofar gida Goggo Hinde ta sami Mujeeb yana dakon fitowar ta don yaji yadda suka yi da matar sa. Ta gaya masa komai amma ta gargadeshi da kada ya nunawa Goggon ya san meke faruwa ya bi al'amarin a hankali kuma ya ci gaba da yiwa mahaifiyar sa biyaya, tunda bata son auren su dole sai ya bi ta a hankali. 132 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Tunda ya shigo gida bayan rabuwarsu da Goggo Hinde ya iske canji sosai a tare da Muneeba ta dawo da zamansu irin na satinsu na farko, tamkar ba itace ke gudunsa ba. Wannan sauyin ne yasa a daren ranar da hikima irin tasu ta maza wayayyau ‘yan boko ya sami kan matarsa ta sallama masa ragamar kanta. Kwana yayi yana lallashi da tarairayarta; kasancewar ya san Muneeban karamar yarinya cc, 'yar shekara sha biyar, yanzu ne ta farad rayuwa irin ta ma'aurata kuka dai ya sha shi babu adadi da kyar ya samu ya lallasheta tayi bacci, amma taki yarda ya saketa taba jikinta saboda ta riga ta tsorata da al'amarinsa, shi yasa ta koma can Karshen gado ta dunkunkune, da yaga haka sai ya ja bargo yalulluba mata har sai da yaji tana sauke numfashi da ajiyar zuciya a hankali alamun AL ta yi bacci, sannan shima ya kwanta. La.. Co Tun kafin tatashi da asuba shi ya rigata tashi, ya dafa ruwan wanka a risho ya debe a bokiti ya sirka da zafi sosai sannan yaje ya tasheta yalallabata sukaje bayi da taga shi yake son yayi mata wankan sai tace ya kyaleta zata yi da kanta yace, "Zaki iya kuwa, naga har yanzu bacci bai sake ki ba, ga jinki ba kwari? Ki bari inyi miki sai in gasa miki jikinki", ta make 133 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria katada tace, "ni dai ka tafi zanyi da kaina", ya juya zai fita yana janyo mata kofar tare da yi mata bayanin yadda zata yi wankan, da abubuwan da ya aje mata don amfanin kanta. Kwana yayi yana lallashi da tarairayarta, kasancewar yasan Muneeba karamar yarinya cс 'yar shekara sha biyar, yanzu ne ta fara rayuwa irin ta ma'aurata. Da ta fito ta wuce shi ta shige dakin baccinsu ta shafa mai ta saka wata doguwar riga, ta hau dadduma ta soma sallar raka'atanil fajri, kafin ta fara sallah a masallaci. Da Mujeeb ya leko yaga tana sallah shima sai ya fice zuwa masallaci. a Lokacin da ya dawo a gado ya ganta kwance ta dukunkunne cikin bargo ya zauna a kusa da fuskarta yace, "har kin sake kwanciya ne?" ta dan bude ido tace, "bacci nake ji, kuma na ji zazzabi yana son kama ni”. Ya ce, "To ki tashi ki sha magani sannan ki kwanta", tace, "Ai ni bana shan magani idan anyi bacci ma insha Allahu zan tashi garau". Ya ce, "Shike nan to gyara kwanciyarki, ki daina takura anki haka, dubi yadda kika takure kamar alkaki, in don nine ki saki jikinki kiyi bacinki bazan sake matsa miki ba". Ta gyara kwanciyar ya rufa mata 134 65 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria zuwa ma mutum bagatatan daga Allah. Mujahced ya nuna tauhidi don baiyi jayya da Kaddarar ubangij ba a cewarsa dama Muneeba ba matarsa bace kurna wani ai baya auren matar da ba tasa ba. Iyalan gidan Inna Amacena a can Gombc kuwa basu da labarin meke faruwa a Dukku, sannan Muneeba ta zayyanawa Innarta alakar soyayya da suka kulla ita da dan uwanta Sadiq dan Inna Amina, a cewar Muneeban tunda auren zumunci ake so ayi mata ida da an daura da Sadiq tunda shirna ai dan uwan gida ne, kuma shi take so, shima yana sonta sabanin Mujeeb da ba ta da tabbacin ko zaiyi amanna da wannan hadin iyayen, shi ma ta san a can Gombe ba zai rasa wacce yake so ba, Innan ta ce, "Ni dai ina dada jaddada miki kiyi hakuri ki bi umurnin iyayenki insha Allah zaki ga alkhairin ya biyo bayan aurenku, shi ma Mujcebu na tabbata kuma ina da yakinin akansa ba zai nuna bijirewa ko da zai dawo ya tarar da irin bijirewan da Guggoonku tayi, ba zai goya mata bayaba. Maganar Sadiq kuma ni baki taba gaya mini ba Yaya Amina ma ba mu taba zancen da itaba, koita ma bata sani ba nc?" Munecba ta ce "Tа sani don ta taba kirana muka yi maganaganun akan hakan". Inna tace, "Kin gani ta yi nauyin WATA KUSAN 1 6b Rahmatu Hassan Zaria baki, kuma ni duk zuwan da Sdiq keyi gidan nan ban taba lura da wani abu a tsakaninku baai da tuni na sanar da Babanki, kinga da 'yan uwansa suka kira shi da ya gabatar da maganar Sadiq din, yanzu kuwa lokaci ya kure tunda har sadaki gasu can uban dakinsa a Gombe ya bada, bakin alkami ya riga ya bushe, sai dai mu biku da addu'a Allah.ya sanya albarka a auren ya baku zaman lafiya ya kauda fitintinu a tsakani. Barin in tasht in vi shiri kinsan na gaya miki Gombe zanje don in sanar da Yaya Amina, akwai wasu 'yan maganganu da zamu tattauna wadandaba zai yiwu a wayaba gara in je can". Inna a can Gombe sun kebe da 'yar uwarta Amina ta kwance mata zare da abawa ana abinda ke taíe da ita, da maganar daura auren Минес за nan da kwana uku. Inna Amina ta jinjina kai cike da al'ajabi da alhini tace, "Iko sai Allah wannan al'amari da ban al'ajabi yake wan ran yana nan yana nasa lissafin na idan ya kanımala kara'u iama a lokacin zata gama saisu yi aurensu tunda sun daidaita kansu suna son juna, ashe ba rabonsa bacc. Haka Allah ya Kaddara Allah yasa alarkı yaba su zama lafiya, Mujech ai yaro ne na kwarai". Inna tace, "Wallahi ban san da muhimmiyar magana haka tsakanin tà da da na ba, kuma duk zuwan da WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria kwana? ta risina gaban Goggon tana gaisheta, ta cc "Ba sai na zauna ba, dama nazo duba jikinki ne, ya ciwon cikin ya lafa ko?" tacc, "Eh, yayi sauki Alhamdukillahi", tace, "In dai bailafa ba sai ku tafi asibiiti ko in tura Isah ya amso mata na gargajiya don ya fi na asibiti". Mujeeb yace, "Akwai maganin asibiti na bata tasha". Ta ce, "To shike nan Allalh ya sawake" ta juya ta koma sasanta, Mujceb yace,"Ga ruwa can nasa miki sai ki kara yin wanka sannan ga abin break fast can, idan kika ci sai ki sha maganni duk da kince bakya sha dole ki sha in dai kina son jikinki yayi miki dadi". tacc, "Wai du ina bacci kayi ayyukan gidan nan? Lallai yau ka sha aiki sannu da kokari", yana murmushi yace, "Ba dole inyi ba, tunda na tabo lafiyar wanda zata yi, nima aikinyi kokari da hidima ta koba haka ba”, kunya ta kamata tayi saurin fitowa ba tare da tace masa komaiba tanufi kicin, ya iske har ta debo ruwa a bokiti tana sirkawa, yace, "Au ba baki hutun aiki bayau? Ki tafi bayi zan kawo miki ruwan". Dole ta tafi shi ya kawo mata ruwan, wankan ma dolente ya tayata shiri ma shi ya taya ta sannan suka zauna gurin karyawa. A baki ya dinga bata abinci yana tarairayarta tamkar 'yar jaririya, ita kam kallonsa take cike da mamakin 137 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria irin kulawar da yake wadda ta nininka ta da ko da yake ta san Kila hakan baya rasa nasaba da hadin kan da ya sami daga gurinta, tunda tsakannin daren jiya zuwa yau ba zata iya kirga godiya da sa albarkar da ya dinga yi mataba, shi yasa itama ta sha alwashin zata watsar da komai ta rungumi mijinta ba zata sake daukar duk wata huduba mara kyau daga kowa ba balle har hakan ya kawo musu wani nakasu a aurensu. Ranar dai Mujeeb bai fita ko inaba yana gida tarairayar Munceba, ita ma sai ta biye masa ko sasanan Goggo ta kasa barinsa ta fita tunda dama Goggo yau a matsayin maralafiya Muneeban take a gurinta, shi yasa itama ta ba kanta hutun ayyukan da take wuni tana yi a gidan. Mujceb har tsokananta ya dinyi wai yau kadai da ta kwanta taba kanta hutun ayyukan da take yi har ta yi kiba, sannan yau ne ta fara amarci na sosai da duk amarcin karya take yi", tayi masa murmushi tace, "kibar ai bani kadai nayi ba, kaima kayi har haske ka kara yi". Yace, "Ba dole in yi kiba ba angwancin gaske wasa ne, saima nan gaba kila sai an canza mana kofar gida da kofar daki don ni da ke duk kadan zasu yi mana wajen shigowa? Tayi ta masa dariyar kalamansa. 138 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Wannan karon Mujeeb bai koma Gombe makaranta da wuri ba ana can ana ta karatu, shi kuma yana nan yana angwancinshi har sai da Yusuf ya kira shi a waya yana masa tsiya a wayar yana cewa, "Wai kai wanc irin sakaci ne wannan ka bar karatu ka je ka makalewa yarinyar mutanc, idan ba zaka dawo bane ka gaya mini na gaji da karyar da nake sharawa Alhaji cewa bakajin dadin yace yayi ta kiran wayarka baya samu". Mujecb yayi dariya yacс, "kai yaro karabu dani aurefa ba karya bane, gara ma idan za ka yi ka zo ka yi shi tun yanzu da kuruciyarka, ka aje tsarin da mukayi da na cewa sai mun gama masters lokacin ka tsufa wallahi, sai dai ka sami tsohuwa irinka, wallahi baka ga yadda na zama ba na yi kiba na yi fari ba za ka san aure rahama ke gareshi ba sai ka ganni, hankalina kwance kamar ma kada in dawo makarantar ashe yarihyar nan na sona haka boyewa tayi sai yanzu take ta fito min da 6oyayyar soyayya iri-iri". Yusuf ya ja tsaki yana dariya yace, ID "Amma fa kaji kunya, yarinyar da ka ke cewa Karama, kana wani babbasar da ita, harka sauko da ajin ka kasaka yarda ta iya soyayya? Lallai ta ci garinka dayaki ina yimata jinjina tunda har a dalilin soyayyarta zaka iya aje karatun da ke da 039 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria muhimmaci a gareka. Yanzu dai yaushe ka shirya dawowa, ko ingayawa Alhaji ba zaka iya dawowa yanzu ba soyayya ta rike ka?" yace, "Idan ka isa mara kunyar gaskc kana iya gaya masa, kai zaka kwana ciki don Alhaji ba zai yarda zan iya fadın magana makamanciyar wannan ba, ya riga ya gasgata walicci na, gara ma kayi wa bakinka linzami". Yusuf yake ce da dariya har sautinta ya doki kunnen Mujeebu, Mujcebu yacс, "Ni don Allah kada ka kashe min dodon kunne in kasa jin irin kalaman soyayyar da ake gaya min". Yusuf yace, "Ai dariya ka bani saboda ni na san kai ba waliyyi ba nc sai yau, Alhaji kam yayi rashin sa'ar wanda zai gasgata waliccinsa, gara ma tun wuri ya kwance nadin da ya daura maka na walicci, ko da yake babu ruwa na asirinka ai zai tonu waliyyin Alhaji ni dai yaushe zaka dawo?" yace, "Idan ta sasauta min gobe zanyo sammako don in sami test din da zamu yina goman safc", Yusuf kashe wayar kawai yayi don yasan Mujecb tsokanarsa kawai yake yi, don su yi ta kwafsawa. Washe gaari da zai tafi kuka sosai Muneeba ta dinga yi, har sai da ya ji tamkar ya 140 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria fasa tafiya, sai daikomawarsa makaranta ya zama dole, shiyasa yalallasheta da cewar zaiyi kokari ba sai Kashen mako ba zai dinga zuwa duk bayan kwana biyu. Tunda ya tafi sai Muneebata hakura ta saki jikinta ta ci gaba da harkokinta, amma idan ta zo kwanciya kewar mijinta na damunta da salon soyayyar sa da yake nuna mata wadda tamkar soyayya yake karanta a jami'ar. Goggo ta sa idanu sosai akan Munceba, so take ta gano ko ciki kega Muneeba a dalilin ciwon da aka ce tayi sannan gashi ta yi 'yar kiba ta murje ta yi haske fatarta sai sheki baa san bata da komai ba, tsabar kwanciyar hankali ne suka samu da fahimtar juna a rayuwar auurensu. 141 WATA KUSAN 1 *** *** Rahmatu Hassan Zaria Rayuwa ta ci gaba da garawa, Mujeeb yayi cukucuku anyiwa Munecba tiransifar karatunta ta dawo makarantar jeka ka dawo ta 'yan mata anan garin Dukku ta ci gaba da karatunta har tayi zana (JSCE) ta shiga aji daya na babbar sakandare, shi kuma a nasa fannin karatun yana shckarar Karshe. A wannan lokacin shekarar aurensu daya da watanni. Tun goggo na zuba idanu ta ga ciki ya bubllo a jikin Munceba, har ta saduda sai kuma abin ya koma tana gayawa Munccban kakkausar magana akan bata haihu ba don akwai lokacin da ka zo ana fadin haihuwar wata sai Goggon ta kada baki tace, "Oh, kinga duk sa'o'in auren su Muneeba duk sun haihu har ma wadanda aka yi bikinsu a bayan nasu, itakam har yanzu shiru, ko da yake ai 'yar boko ce kwayoyi zata sha bata son haihuwa sai ta gama karatu, ko ka fada mijnta ba yarda zaiyi ba zakiji yace Allah nc bai kawo ba, alhalin ana cutarsa a 6oyc ne bai sani ba saidai Allah ya saka masa kokarinsa ya tashi a banza a sanyc shi an rufe masa baki”. Munceba na gefe tana tankaden garin tuwo, ita kuma Goggon na kicin tana iza wuta suke hira da bakuwarta da ta zo take bata labarin haihhuwar 142 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria da aka yi, shine Goggo ta ke kwararo wannan zance da bai da cc ba. Munceba bata san lokacin da hawayc ya balle mata ba saboda bakin cikin duk lokacin da Goggo ta tashi zancen rashin haihhuwar ta, sai ta danganta hakan da cewa Muneeban ne bata son haihuwa take shankwayoyi alhalin bahaka ba ne, ki yayya ce kawai take sa ta fadin wadanan kalamai, ita da za a riketa da bindiga wallahi bata sanma yamaganin tsarin iyalin yake ba, bata san inda ake yi ba, amma ta lakaya mata har Mujeebu Goggo ta gayawa, shi dai kullun cikin laltashin matarsa yake yi don yasan ba laifinta bane rashin haihuwarsu Allah ne bai basu ba, kuma suna nan suna kai masakukansu insha Allahu zai dube su ya basu tunda ba wai ya manta da su bane ya hana su yana sanc da su lokaci ne kawai baiyi bana yaba su haihuwar. Goggo daga kicin ta hangi hawaycn fuskar Muneeba sai ta. ta6e baki tare da sakin uban tsaki tace, "au kuka kike yi don an fadi gaskiya? Lallai kuwa kuka bai kare miki ba don ba zan daina fadin gaskiya ba sai ranar da naga jika na a hannuna in kuma ba haka ba, wallahi kara aure zaiyi. Ya auro wanda zata haihu tunda ke bakya son haihuwar. Ita dai Munecba ba ta ce uffan ba ta ci gaba da sharan hawayenta ita WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Goggo ta ci gaba da surutanta da ke bakanta zuciyar Munceba, kuma su ke rage mata girmanta da take gani Da daddare da Mujeebu ya shigo tunda yana gari sai ya kasa gane kan Muneeban ya ganta sukuku babu walwala ya yi ya yi ta gaya masa me ke damunta ta ki gaya masa dama idan ya ga haka, to ya san Goggoce ta yi mata wani abin sai taki gaya masa in ba Goggon bace ta gaya masa ya zo ya tambaye ta sam ita bata gaya masa kuma idan Goggon ta tashi gaya masa son ranta take fada, da yake ya san halin mahaifiyarsa sai ya bita yadda take so

Chapter 7 of 11