Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 11
in ma ya kama yayi wa Munceban fada ne a gabanta yana yi in ya so idan suka shiga daki sai ya lallashi matarsa tunda ya san yawanci ita akc kwara, idan abin ya ci tura sai ya dangana da kiran Adda Fadima a waya don ta zo ta taya shi lallashi. Yauma haka ta kasance bayan sunci abinci sun gama, yacc, "Tashi ki shirya mu je anguwa". Ya yi shirin fitar ta su ne don yasa mai walwala. Tace, "Iana kuma zamu da daren naan, baka bari sai gobe ido na ganin ido mujc “, yace "ke dai shirya yanzu nake sin muje". Ta tashi ta shiga dakin baccinsu ta sako jibi bisa atamfar dake daure a jikinta ta fito tace, "na. shirya muje". Suka fito suka rufe sasansu suka shiga WATA KUSAN nde Rahmatu Hassan Zaria suka yi wa Goggo sallama cewa za su anguwa ta dube sutace, "Da đareni na ku kuwa ina zaku je?" nyace,bg lneg n eua! AT"Za mu je can gidansu Baffane za ta yi musu sallama gobe/idaizanowucc za mu tafi tare" Goggo tace/"Au zaka tafi da ita gobe shine baka gaya min ba sairyanzu da na tambayi inda za ku jeplallaiMujeebu dabi'unka sun canza". Yaсe, i "Kiyi hakuri Goggi da bań shirya tafiya da ita ba Hajiya ce ta damu ba su ganta ba kwana biyu tunda zanzo taceinzo misu da ita, ni na ma imanta shine dazu talyi mini waya take tuna mini, kin galai babu abinda za ta ce tana so in kasa yi mata, ko ke za ki ce ban kyauta ba", tace "Ai fa ga ka dariya kare kanka, wannan hujjar ta shiga, shike nan sai kun dawo" ima ed Gidansu ya fara kaita dama ya dade bata jo ba tana ta yi masa nacin za ta je don tana kewarkistInnarta da Kannenta amma ya dinga share zancen sa yau da ya yi niyya don kansa; bata san døn ta samu walwala ya yi mata haka ba danoya san zatassamu müddin ta ga innarsu da 'yaniuwantan da baban ta da take mararin son ganinsa.ni ndansg 8 Yana biye a bayanta suka yi salama suka shiga gidansua tskar gida suka iske matan gidan tawbinsu ta gaishe isuuran ta bar Mujeeb suna WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria gaisawa ta wuce dakinsu. A gado ta ga Innan a kwance sallama kawai ta yi ta isa kanta tana taımbayar "Lafiya Innarmu na ganki a gado? Ba dai har zaki yi bacci bane haka da wuri". Та yunkura ta tashi zaunc tana cewa, "lafiya ta kalau gajiya ce kawai nayi, yau na yi ayyuka da yawa. Daga ina kike da daren nan?" tacc, "daga gida muke ni da Yaya Mujeeb ne, gaya nan shigowa", tana cikin gida Innan ne suka ji sallamarsa daga falo suka fito, ya risina ya gaida Innan ta amasa cike da sakin suka ta cc, "ashe baka koma ba?" Yace, "Eh, ban koma ba sai gobe, tare da Munceba ma zamu tafi shi yasa nace a bari mu zo tayi muku sallama". Tace, "Goggon taku ta yarda ka je da ita nc?, yace "E, ta yarda, ni ma can su Hajiya suka damu in zo musu da ita, wai ta kwana biyi bata je ba sati na sama tarc zamu dawo". Tace, "To Allah ya kiyayc hanya don Allah a gaishe mana da su idan an je". Yace, "Za su ji Insha Allar Sun dan yi hira sanan yace Mustafa ya koma ne?" Inan tace, "Shima paji yace gobe zai koma yanzun nan ya fita, ina jin yana dakinsa". Mujeeb ya mike yacc "Bari in ganshi in bai fice ba". Yana fita hira ta 6arke tsakanin uwa da 'yarta, cikin hirara ne Munceba cike da damuwa 146 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria take labartawa Innarsu irin gorin rashin haihuwa da Goggo ke yi mata da abinda ya faru yau da aka zo áka ce mata wata da aka yi aurenta а bayan na su ta haihu. Inna ta girgiza kai tace, "Shin sau nawa zan gaya miki ki daina damuwa da surutan batanci irin na Goggonku, kuma sai nawa nake miki nasiha kan ccwa ki dauki hakuri da kaddara da ta sauka a kanki ta rashin haihuwa? "Shi fa duk abinda kika ga mutum ya samu a duniyar nan arzikin kudi ko arzikin 'ya'ya to Allah ne ya nufa zai samu, idan kuma bai nufe ka da samu ba to duk duniya nan babu wanda ya isa ya baka", sannan idan Allah ya baka to babu mai hanaka wannan abin da ya baka ki sa wa zuciyarki hakuri da dangana ki yi ta addu'a idan rashin samun haihuwarki shinc alheri a garcki to Allah ya baki ikon cin jarabawar da Allah ya yi miki. "Idan kuma kina da rabon za ki haihun to Allah ya baki masu albarka" In banda abin mutane shin yaushe ma aka yi daren balle gari ya wayc? Kuma haihuwar nan ai ba ke za ki ba kanki ba, in da ke za ki ba kanki ai da tuni kin ba kanki ko don gorin da Goggonki ke miki ki cire damuwa a ranki, ki ci gaba da walwallarki in ba haka ba ki je ki jawa kanki ciwon damuwa babu gaira babu dalili, inda sabo WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria ma ai ya kamata a ce kin saba da ire-iren wadanan halayyar na Goggon, meye jiya ta yi bare yau, ni mayye ba ta mini ba da na yi biris da halinta me ya tsunkuni namana? "To ki ci gaba da hakuri da zama da ita wata rana zai zamo labarai". "Haka innarsu ta yi ta mata nasihohi da misalai na mata masu hakuri da kuma irin ribar da suka samu a dalilin hakurinsu, har Mujecь suka shiga tare da Mustapha daga gidan har gidan Adda, Fadima suka je daga nan ta rokeshi da ya kaita gidan kakarsu wato mahaifiyarsu Innarta da suka ki Daddi wadda ke can a ruga, ya dube ta yace, "Dadaren nan za ki samu shiga daji, so kike tsofaffiin samarinki na rugar su tare ni su kwakkwabde ni ko dan haushi na suke ji na aurc musu buduwa". Ta yi murmushi taсс, "waya cc maka ina da samari a rugar nana? Ni an gaya maka ma ina kula samari nc?" Yana 'yar dariya yace, "A dai bar kaza cikin gashinta", ya karkata mashin dinsa zuwa rugarsu Diddi (mashin din abokinsa nc). A zaunc bisa katifa ta iskcta ta na mutstsika man zafi a kafafuwanta. Munccba ta zube wa 'yar tsohuwar a kafafu ta rungume ta, ta soma tureta tana ccwa "Ni dagani kada ki karya min kafa ki bar ‘ya'yana da daukan kasha don WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria dai su ne zasu yi jinya ta ke kina can gidanaki da mijinki". Duk suka yi dariya Muneeba tace,"Allah iyayena ba zasu yi jinyar kasha aba sai dai 'yar warki ta zo tayi jinyaki". Mujeeb ya zuana daidai kafafun Diddi ya amsi mana ya lakuta sanana ya dubi Muneeba yace, "Ke daga min kafar amarya idan kika karyata kin kwari kanki don nana zan dawo in tare inyi jinyarta sai dai ki biyoni manana mu zauna". Ta tashhi tana dariya tace, "Bari in tashi kada na tun bn karyata bata langwabe tace ta karye tudn ataji yau itace amarya". Bayan gashe-gaishe ne Diddi take musu fadan me yasa suka zo da daren nana ko rsoro bas a ji, suyi su zo su tafi gashi goma ana dare ta kusa. Sun gaya mata dalilin ziwansu. Ta tashi ta dinga bubbude kwanuka da korai ta hado kaya rankatakad a babbar leda ta mikawa Muneba tace, "Gashi nan kyayi wa su Hajiyar tsaraba, ba kya je hannu salin alin ba, mai sonka ai ya gama maka komai. Innarku ta baki wani abu ki kai masu ko?" ta ce "Eh itama ta bada su kuka daddawa da kubewa da sauran tarkace a kai musu ga su can a bayan mashin". Diddi ta ce, "to gasu mana sai ki hada musu a gaishe su da 149 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria kyau a gaida Alhajin". Suka ce "Duk za su ji da yardan Allah". Mujceb da zasu fafi ya laluba aljihunsa ya ciro kudl ya mikawa Diddi yace, "Ga wannan ki yi cefane kafin in dawo, ai zasu isheki, ko da yake ba kya girgki". Ta amsa tayi godiya 'yar tsohuwar nana da yake garau take jin kanta har kofar gida ta rako su ta ga tafiyarsu sannan ta koma cikin gida. Diddi kenan 'ya'yanta su Inna da Inna Amina da sauransu haka suka taso suka ji kannenta na kiranta diddi suma su sake kiranta da hakan, suma nasu 'ya'yan wato jikokinta su Muneeba suke kiranta da hakan, kusan kowa ma Diddi ya ke gaya mata. Tsohuwace lafiyayya ko da yake 'ya'yanta sun tsayu a kanta suna ginata da kayan dadI, cima sai wadda ake so suke bata haka ma sirikanta matan 'ya'yanta sa ji da ita, a dalilin ita ma ta rikesu tamkar itace ta haifesu. 150 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Shckaru uku da watanni kenan da auren su Munceba, cikin wadannan shckarun abubuwa da dama sun faru na farin ciki da na bakin ciki, na farin ciki da na bakin ciki, na farin cikin da ya same su shine kammaluwar karatunsu dukansu, ita ta gama kartunta na sakandire kuma har sakamako ya fito ta samu mafi kyawun sakamako har ta zana jarabawar (JAMB) shima ta sami point din da ake so yanzu shirye-shirye tafiya jami'ar Gombe take yi inda mijinta ya yi Federal University Kashere shi kuma nasa abin farincikin ya kammala bautar kasa shi da Yusuf wani aminin Alhaji ya sami masu aiki a mabanbantan gurare kowa cikinsu ya fara aikinsa, sannan ga katafaren shago na hadaka shi da Yusuf da suka bude na sayar da zannuwar atamfofi da leshina da shadda a babar kasuwar Gombe, a wannan lokacin duk sun mallaki motocin shi Mujeebu har ya kammala kerarren gidan sa na nan Gombe a Unguwar Buhari estate yanzu haka ma yana shir-shiryen dawo da Muneeba ne tunda zata fara karatunta a Gomben don ma Goggon tana ta ja musu tsaiko ne da tuni sun tare. Abin bakin ciki kuma da ke damunsu tuna ci mus tuwo a kwarya kuma ba ya wuce WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria irin gori da bita kulli da gwarza ba da Goggo ta saka Muneeba a gaba dasu na rashin haihuwa, babu abinda ya fi tada wa Munecba hankali irin farin cikin da take yi na gorin rashin haihuwar wai lallai-lallai sai Mujeebu ya kara aure tunda yana da arzikin da zai iya aje mata hudu ma ba biyu ba, shi ya sa ta dage dole sai ya auri Suwaiba 'yar aminiyarta Haj. Harira don yanzu ma ya kamata ayi aurensu a cewar Haj. Hariran tunda yana da abin hannunsa, take gayawa diyarta anya kuwa ko anyi auren ba wata tsiya zata tsinta ba tunda karatu yake yi, ita ma karatu ta ke yi, yanzu kuwa ta gama shi ma ya gama nasa har ya sami aiki, sannan ga taura biyu da ya hada a baki yana tsotso, aikin gwabnati da kasuwancu shi yasa farat daya arzikinsa ya bunkasa, ko motar da yake hawa idan ka kalla kasan ruwan arziki ya sauka a gidansa. Wani zuwa da Mujecb ya yi ya sami Goggon yana tuntubarta game da komawarsu Gombe ya kara da cewa, "Kinga Goggo ko auren zanyi ai ba nana zan aje matar ba dole Gombe zan kaita tunda can nake aiki shi yasa nake son mu fara komawa in yaso maganar aure sai ta biyo baya, in ba haka ba jama'ar gari ai sai su zage ni ace na yi gida ban saka matata 'yar uwataba sai da zan yi aurc sannan zan ce ta 152 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria koma". Goggo ta tabe baki tace, "Zagi? Jama'a sun dade ba su zage ka ba, kaine kake shayin zagin jama'a nan da ka ganni da zagi yana tsiri da yanzu ya firfito mini, amma da yake bana shayin uban kowa me ka ga ya same ni, kawai dai zan barka ka tare dama ai ni ina bakin cikin ace wannan katafaren gida mace daya jallin jal ce zata,zauna a cikinsa ba abokiyar zama ba yara 'yan bari bari ai kaga arziki baiyi ba, amma yanzu tunda ka amince zaka kara auren to ni ka amince zaka kara auren to ni ka gama min komai ka faranta mini rai yanzu zan yi waya in shaidawa Haj. Harira ta soma shiri bikin 'yar lelenta ya zo". Ya yi saurin tarar numfashin Goggo yace, "A'a kada fa kice mata tayi shiri yanzu don abin ba na gaggawa ba ne, mu bi komai a sannu gaggawa aikin shaidan ne tunda nace zanyi ai zanyi ne", shi kam ya fadI zai yi auren ne don Goggo ta sakar musu mara su yi fitsari, su tare a gidansu in yaso daga baya ya san zilliya-zilliyar da ya yi ya zille wa auren. Yana shiga dakinsu ya suri Munccba yana juyi kyalkyatar dariya. Ta kankame shi tana cewa, "Yayana wai me ya sa ka murna ne haka, har ka yamutsa min 'yan hanji, sauke ni jiri nake ji". Ya direta kasa ya zauna sannan ya janyita ta zauna a jikinsa yace, 153 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "Goggo ta amince duk sanda muka gama shiri mu koma gidanmu na Gombe". Tsallen murna ta Kara yi sannan ta rungume shi tana tsallen murna tana tambayarsa, "Yaushe tace zamu koma?" yacc, "Sai lokacin komawa tana gurinmu shine nake son mu yi shawarar lokacin da ya dace, ni dai kinsan na gama sa kayan falo na da bedroom dina kece ya rage baki amso kayan gadonki da kujeru ba". Ta ce "ai na gaya maka akwai balance din da zan basu sai in amshi daman a barine sai an sa ranar tarewar sai muje in anso". Yace, "nawa ne balance din na fa manta?" tace, "Dubu dari biyu ne ya rage", ya се, "OK gobe sai mu je Gombe mu kai musu cikon mu amso, duk dai wani shirye-shirye ki yi shi cikin satin nan sati na sama sai mu tare ranar asabar Karshen wata kenan", tace, "Allah ya kaimu lokacin, na gode da kulawarka a gare ni, da irin dawainiyar da kake da ni, Allah yay budi ya tsaremin kai". Ya janyota jikinsa ya rungume yace, "Nima ina godiya da dawainiyar da ki ke da ni da kulawar da ki ke bani, Allah ya barni cikin da kaunar juna ya bamu abinda muke nema duniya da lahira". 154 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Fadin kalmarsa ta karshe ne yasa ta fara hawayc, ya kai hannunsa ya lakuci hawaycn yace, "To meye abin kuka kuma?", tayi ajiyar zuciya tace, "a kullum ina rokon Allah da ya bani haihuwa, don duk abinda zan yi maka ka yi farin ciki ba zai kai farin cikin in Haifa maka 'ya'ya ba, domin su ne sanyin idaniya a garemu, sannan in huta da gorin da ake mini na rashin haihuwa, in fita daga kangin da nake shiga idan na ji an furta dole sai ka kara aure tunda ni har yau ban haihu ba tsawon shekaru hudu da aurenmu", ta ci gaba da sharen hawaye da ke ambaliya a kuncinta. Mujeeb ya kara matseta a jikinsa yace, "Sau nawa zan gaya miki ki cire damuwar rashin haihuwa a ranki, kin taba jin na yi miki gorin baki haihu ba?" ta girgiza kai ya ci gaba "ko a taba canza miki wani yanayin mu'amalarmu ne, nan ma girgiza kai tayi, yace, to ki kwantar da hankalinki tunda mu jejje asibiti sun dubaki sun dubani sun tabbatar mana dukkanmu lafiya kalau muke loakci ne kawia bai yi ba da zamu haihu, idan lokaci ya yi zaamu ganki dauke da ciki, kai wallani ko cewa suka yi daga gare ki matsalar take ba za ki haihuba zan zauna da ke har karshen rayuwarmu balle sunce mahaifark: afiyarta kalau, to me zai damcki, duk 155 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria wanda zai yi miki gorin baki haihu ba ki kyale shi, tunda ba shi zai bakiba Allah ne zai baki shi za ki kaiwa kukanki, kuma In Shaa Allahu za ki Haifa min 'ya'ya masu albarka" Haka ya ci gaba da lallashinta har sai da ya ga ta sami natsuwa, sunci gaba da shiryeshiryen suna komawa sabon gidansu a Gombe. Washe gari suka tafi Gombe gidan Mamam Amina suka sauka. Sai 'yan biyu ne gida Sadiq ma yana gidan duk suna main falo har da Mama Amina. Shigowar Muneeba falon 'yan biyu suka hau ihun murna suka rungumeta, jin tare da mijnta take ne yasa Sadiq ya silale daga falon. A gidan Muneeba da Mujeeb suka yi Sallar azahar, suka ci abinci sannan 'yan biyu ne suka yi musu rakiya gurin dauko furnitures din, wai za su taya ta zabar mai kyau. Mama tace, "Zaki je dai ku canza mata ra'ayi, wanda muka mana zamani ne mai kyau, idan kuka za6o wanda ya wuce kudin wanda ta zaba kwa cika kudin, shi ya sa na yi murna ranar da za mu je da ba kwa nan, tunda ba ku ba ku san zafin kudi ba ganinsu kawai ku ke yi". Suka ce "Mama gara muje mu ga wanda kuka zaba, in dai irin naki ne an daina yayinsa yanzu, ya zama eld modern akwai sabbin ya yi new modern masu iyau sai 156 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria mu tayi ta zaba ta canza, ga yaya Mujeeb nan shi zai yi cikon". Mama tace,, "Ba ku isa ku sashi abinda ya yi niyya ba, ku da za ku je ku zabo mai tsadan ku za ku cika". Mujeeb na musu dariya yace, "ba komai Mama gara a dauki na zamani, ko nawa ne zan cika ba matsaka". Mama tace, "Ka kyale yaran nan iya yinsu ya yi yawa, idan kuka je za ka ga gadon mai kyau ne sosai, gadon dubu dari hudu ne za a ce baida kyau, kila a miliyan suke son a siya". Suka cc, "Yauwa Mama ashe kin gane". Mama ta dubi Mujcebu tace, "Ka ji ko yaran nan ba su da hankali kila dai sun dauka hako kudin ake yi a rijiya kada ka biye tasu idan kun je ko zaka canza ka zabi wanda ya yi maka kuma daidai Karfinka kada ka takura kanka don ka yi bajinta ka ji ko?" Ya gyada kai yace, "ba komai mama zan yi iyakar iyawa ta". Sun isa gurin gadon su kansu 'yan biyu sun yaba sosai da gadon sa su Maman suka dauka tun farko, shi ma Mujceb ya yaba shi ya sa ba a ćanza ba, kujeru ma an nuna musu sun zabi masu asalin kyau, da yake akwai shagon kayan wuta sai yace su shiga su duba, yace ta za6i abinda take so, sun taya ta zabi TV na 157 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria bango plasma, sai Home tiyat duk na kamfanin LG da su Fridge da deep frizer da gas cooker da sauran tarkacen kayan girkin kicin, dama sun shiga banki ya ciro kudl masu yawa da yake ganin zasu ishe su siyayya. Daga nan kai tsaye suka wuce sabon gidan dake unguwan Buhari Estate motar da ta dauko masu kaya ta kamfanin funitures din tana biye da su har gidan. Yanayin tsarin gidan Mujeeb ya yi kyau sosai, falonsa ne a gaban gidan mai dauke da dakin bacci bubba da bayi da wani karamin daki shima na baccin ne, ta nan zaka iya shiga cikin gidan mai dauke da filat guda biyu iri dayah aka dauke da haka Goggo tace ayi na Munceba da na matar da zai kara nan gaba. Muneeba ta razana da wannan tsari amma sia Mujecb ya kwantar mata da ahanka cewaar yin goinin ba shine aurensa ba, ya dai zamar masu dole ne ya yi yadda Goggon tace don ya aranta mata rai a zauna lafiya, amma shi ba maganar kara aure a tsarinsa yanzu, a wancan lokacin da zai fara ginin kenan, sai gashi yanzu Goggon ta sami galaba a kansa har ya amsa mata cewa zai kara aure, shi a ganinsa zai iya shshantar da maganar, bai sani baa she Goggon ta dau maganar da muhimmanci har ta labartawa aminiyarta sun ma fara shirya yadda bikin 'ya'yan nasu zai kasance, 158 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria ba tare da Mujeeb din ya sani ba har da shirinsu na boye wanda sai nan gaba za su fallasa Sannan ga fakin Goggo a gidan, babban daki ne guda daya, sai bayi a ciki, ita tace dole a fidda mata dakinta daban duk lokacin da ta zo Gombe a nan zata sauka ba a dakin bakin da akа yi ba tunda ita ba bakuwa bace, idan tag a dama ma nan zata dawo da zama gabakidaya ma ta gani inda mai koranta ita da gidan danta da ta sha wahalar daukan cikinsa ta Haifa ta raini abinda tayi fadi tashi don ganin rayuwarsa ta inganta, ya yi ilimi har ya samu aikin yi sannan ace wani ya more shi ba ita ba wannan ma karya ne a cewarta ita dai Muneeba dan Goggo na wadannan surutan shiru take yi don ta san da ita da iyayenta takc yi saboda hidimta musu da ya ke yi, in banda abun Goggo kaninta fa ya ke wa baffan shi kuma sirikinsa, ita kuma Inna ko ba sarakuta ai matar baffansa ce idan ya kyautatawa baffansa ai zai yi mata itama in har da matar sanin ya kamata to balle yana auren 'yarta ai ta gama masa komai. Shi Mujeeb har ba ya son ya nuna mata wani abin arziki ya ce zai kai gidansu Munceba yanzu zata hau korafi ko kuma tace sai ya sayo kwatankwacin abin an kai gidan Hajiya Harira ai itama sirikarsa ce kuma aminiyar uwarsa dole 159 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria yayi mata, idan yana son tabo Goggon sai yace "In banda abinki Goggo Wata kusan ai tafi gaban wata, Muneeba' fa jininmu daya babanta sirrikina ne kuma Baffa na, Innarta sirikata ce kuma Innata ita fa suwaiban uwarta ce fa aminiyarki shi ke nan alakarmu". Habawa ina wuta Goggo ta sakashi anna żata hau kansa da sababi, "In kana da mutunci aminiyata ta kowace irice zata zamo uwa gareka, balle tana shirin wanke diyarta ta baka ai kuwa ta wuce wargi a gurinka". ta Gagarumar walima aka shirya komawar su sabon gida wadda za a gudanr a can gidan na Gombe illahirin 'yan uwa da abokan arziki duk sun sami harta a bangaren Goggo har da aminiyarta Hajiya Harira taje Gombe nan ta kwana ma tare da Goggo, idan ta dada ba idonta abinci, ta kuma jinjina kokarin Mujeeb saboda wannan kerarran gida da ya gida mata na dada tabbatarwa da cewa lallai ba kananan kudi ba ne Mujeeb din ya yi da har ya iya "kera wannan tsalelen gida. Ganin irin kayan alatun da ya zuba a dakinsa da na Munceba ne yasa Hajiya.Harira ta sha alwashin ko ana ha maza ha mata kota halin yaya sai Suwaibanta ta shigo gidan nan ita ma ta shiga cikin daula a dama da ita, balle idan ta 160 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria shigo da kafar dama ta sami zazzaga 'ya'ya kinga shikenan mai gida ya zama nata, su fantama yadda suke so. Komawarsu dukku da kwana biyu ne Hаj. Harira ta zo gidan Goggo Rahin akan wani sirri da suka kulla tun a can Gombe, tana rigan gero a tsakar gida tace, "Au bai shirya ba ke da nace da na zo za mu tafi da wuri sabida kada mu tadda layin mütane". Tace, "Shiga ciki gani nan geron nan kawai zan wanke a kai mini nika, na yi gudun kada in yafi ban bayar ba mu dade a can, kin san yanzu gidan ni kadaice bani da ma ani, ya daduke abarsa da tana nan wannan duk aikinya ne". Hajiya Harira ta ja tsaki tace "Tini na dauka kin daina yin kamun tinda yace ki daina, bata a ju daua tunda 'yar botin taki ta sami 'yancin kanta, kuma Mujeebu ai ya tsaya miki komai yana miki me kike nema a duniya kin sami da mai ladabi da yi miki biyayya, komai waja-waja in ni ce ke ai ko nawa zanyi in zauna ina cin arzikin haihuwa tuda ta yi miki rana". Tace, "Lallai kam haihuwa mai dadi shi yasa nake tausayinsa, yadda yake bauta mini shi a ce bashi da mai yi masa ai dole in tashi tsaye in ga ya yi aure ko da zan kauce hanya ne in ya so na tuba daga baya amma in da zan yarda da dan da na kallafa rai a kansa ace bashi da 'ya'ya, 161 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria sannan mace ta kanainaye mini shi bashi da wani katabus, ba ya son a fadl aibinta, ai in dai asiri ne mu zuba ni da uwarta shege ka fasa za su ha irin nawa da ya fi nasu wallahi sai ta gudu a gidan ta bar ladarta". Haj. Harira tace. "yi ki taso mu tafi ai da zafi zafi ake bugun karfe, kuma da sanyin safiya ake kama fara, idan takamarsu sammako to mu a tafe muke kwana za mu kara sai a ga wanda zai sha kaye". Sun iso tashar Dukku suka shiga motar kaltungo a can wani dan kauye dake kaltungon ne za su je gurin wani boka ita Haj. Hariran ce ta sanshi shine ta ce su je don ya yi musu aiki a shawo kan Mujeeb ai ance da auren Suwaiban da wurwuri ya daina jan ransu. Sun sauka a kaltungo suka nemi mashin da zai kaisu can kauyen kuma cikin daji boka tsidugu ya ce sunan bokan kenan. Da kyar aka samu masu mashin zasu kaisu a dari biyar-biyar sabida sunce hanyar babu kyau. Da yake sanyin safiyane ba su iske jama'a sosai ba shi ya sa ba su dade ba aka ce su shigo. Hajiya Harira ita tayi wa boka tsidugu bayanin komai da abin da suke so ayi musu, boka ya kece da dariyar mugunita yace, "Ai kinku mai sauki ne, tunda hada aure ne mu kan raba aure cikin 'yan dakikai balle hadawa, in dai mutun zai bi 162 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria umurninmu ba miskila to zai ga aiki babu tangarda", ya daga wani koko sama ya yi sirkulle daga saman dakin sai ga wasu kwalalan turare daga saman dakin sun fado cikin kokon guda biyu rakwacam! Har Goggon su ka firgita ya yi dariyarsa da ya saba ya ce, “Kada ku tsorata taimako ne daga aljani tsinkau uban tsidudu yace a baku bukatarku ta riga ta biya an yi aure an gama har ma yace ayi muku bishara da samun haihuwa a wannan aure abinda zai biyo baya kuma sai a hankali za ku ji".ya mikawa Haj. Harira kwalaben guda biyu yace, "Dauki farar ki bata bakar". Ta rike farar kwalbar ta ba Goggo bakar kwalbar ta sannan ya soma kora musu bayani kamar haka. "Ranar da kika tabbatar danki

Chapter 8 of 11