Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
10 / 11
tare da tambayar iyali sannan Mama tace "Don Allah sahiba wata 'yar matsala ke gare mu 'yata da na ce miki tana da matsalar rashin haihuwa din nan, to ita cc kuma mijin zai yi wa kishiya yanzu shine na ke son gata ki bata shawarwari na gari yadda za ta yi juriya da hakuri sannan da shawarar yadda za ta zauna da ita kishiyar tata, amma ina fatan kina da lokaci yanzu". Ta yi murmushi tace, "Haba, haba aiko bani da lokaci, zan baki aron lokaci na in dai ba ibada na ke yi ba ko hidimar maigida, sune kawai ba zan iya bada lokacinsu ba, sannan wani lokacin kuma zaki ga ina islamiyyane shi kuma malamin mu ka'idarsa idan yana darasi bama daga waya wani lokacin kuma ina makarantar nasara su kuma lecturers din basa yarda mutum ya daga waya ko dai ka kashe ko ka saka ta a silent, to ni na kan barta a silent saboda idan malami ya fita inga wadanda suka kira ni, don in bi bayan kiran muhimmai cikin masu kiran, to shine fa wasu idan sun kira ba a dauka ba suke jin haushi maimakon su yi mana uzuri a a sai su ce an yi musu wulakanci na kin daga waya, dole sai mun yi hakuri da juna, ku masoyanmu ne, mu ma masoyanku ne, kinga 182 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria ai ba a fushi da masoyi sai dai hakuri da juna, yanzu ina diyar tamu bata wayar mu yi magana". Mama ta mikawa Miniba wayar tayi sallama sannan tace, "Antinmu ina yini?" ta ce, "Lafiya lau uwargida don har na nada miki sarautar uwargida sarautar mata don wannan matsayin na ki mai muhimmanci nc, ki rike shi sosai kada ki yarda ya kufce miki in dai kin rike shi tsakaninki da Allah to ba ita abokiyar zamanki ba har shi mijin sai sun dinga baki wani muhimmin matsayi na darajaki da za su dinga yi yin shawara da ke sannan kc ce zaki zamo ja gaban gudanar da komai na gidanku sai sunyi shawara da ke sannan abu na farko da nake son in baki shawara a kansa kada ki yarda kina cewa kishiya! kishiya! Fadin sunan nan kishiya shine farkon abin da yake haddasawa mace tsananin kishi a ranta idan ta ambaci kishiya! "A a ki ce abokiyar zama zai fi sa zuciyarki a natsuwa, sannan ki sani shi kishi ana yin sa ne FI HUSNIL ASHIIRA, ana yin shi ne na kyautatawa, ba na hauka ba da jahilci da rashin wayewa saboda ba za a taba raba mace da kishi ba tunda shi haliita ne a zuciya, kin ga ba mai raba mutum da shi, to amma ana yinsa ne ba yadda zuciyar ki ta raya miki ba, ai ia mace ma idan bata kishin mijinta ba ta cika mace ba, WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria matukar irin kishin da shari'a ta yarda da shi nc, ba ne shirme da wuce gona da iri ba. Kishi ya kasu kashi biyu mai kyau da mara kyau. Mai kyau shine ki bi duk hanyoyin da shari'a ta amince miki don ganin kin sami zaman lafiya da mijinki, da ita abokiyar zaman ta ki idan ta zo, ki kasance mai kula da lamuran da suka shafi mijinki, ki yi tattalin sa da yin tsafta, iya magana iya girki da jin maganar miji, ya masa biyayya da umarni ko hanin da miji zai yi miki, girmama shi da kaucewa duk wani abu da zai Gata masa rai, kuma ki kaunaci duk abinda ya ke kauna har da ita abokiyar zaman na ki, ki so 'ya'yan da za ta haifa tsakaninki da Allah sai ki ga ke ma Allah ya tausaya miki ya baki naki, kuma ki so iyayensa da yi musu biyayya ki kyautata masu da dukkan 'yan uwansa ko da suna munana muki babu ruwanki ke dai kike kyauata musu, wata rana sai labari, sannan ko shi mijin ne ya munana miki to ki biyo bayan munanawan da kyautatawa, saboda ki saukc nayir hakkinsa da ke kanki, babu ruwanki da cewa zan munana masa tunda nima ba ya kyautata min, idan ki ka yi haka ba za ki samu mafita ba a gurin Allah ranar gobe kiyama, shi kuma kishi mara kyau da mata ke yi idan za a yi musu abokiyar zama ko idan an yi musu shine WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria kuma wada sam! shari'a bata yarda da shi ba; shine zuwa wurin boka ko malaman tsubbu 'yan duba don a mallake miji, ta hanyar yin tsafi da yin shirka ga Allah, ta irin wadannan hanyoyin ne sukc korar kishiya ko su haukatar da ita su malllake mijin shike nan gida ya zama na su, idan kuma aka taki rashin sa a sai kaikayi ya koma kan mashekiya. Wasu mata saboda bakin kishi za ki ga sun rame sun kekashe saboda ba sa cin abinci duk a dalilin kishi, wata macen kuma idan miji ba a dakinta yake ba, yana dakin 'yar uwan zamanta to sai ta ta kasa bacci saboda tsabar kishi, ko ta kirkiri rashin lafiya na karya ta hana su bacci don dai ta dagula musu nishadinsu na wannan daren. Wata kuma idan mijin na gida zata yi ta nuna halin kirki ga kishiyar, amma da zarar mijin ya fita zata yi ta kuntatwa abokiyar zaman, ta yi ta bala'I da tijara, wannan duk rashin hankali ne da damsil basira tare da son zuciya na su matan da suke daukar abokiyar zama a matsayin abokiyar gaba, shi yasa ba a son ace kishiya gara ace abokiyar zama, sannan ki sani Allah ne ya ba maza damar su kara aure, duk kuwa abin da Allah ya halasta bai kamata bawa ya bijire ya ki yarda da hakan ba, kada ki zamo cikin masu bijirewa abin da Allah ya halasta, kada abokiyar 185 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria zama ta zama abar gabanki abar jin tsoron zuwanta, da fargaba, ki sa a ranki za ta zo ne da nufin alkhairi sai ki ga zuciyarki ta yi wasai baki da damuwa. Idan ta zo da alkhairin shike nan da ma zaton alkhairi ki ka yi mata sai ku zauna lafiya hankalinku da na mijinku a kwance in kuwa ta shigo da nufin sharri ne to kada ki biye mata ke ki nuna mata ba ki san sharriba alkhairi ki ka sani kuma shi za ki yi mata. Ina son ki sani kuskure ne ga mace ta nuna bata son abokiyar zama, ke dai idan za a yi miki an san ba dadi, amma ki yi ta addu'a ne akan Allah yasa gari za a kawo mai akhairi, sannan ki sani mazon Allah (SAW) ya auri mata fiye da daya kuma sun yi zaman kishi mai tsafta a tsakaninsu, rashin tawakkali da rashin tauhidi da raunin imani ga mace tace bata son abokiyar zama domin kina yin fito na fito ne da ikon Allah, wannan babban kuskure ne, abin da ya kamata ki yi shine ki ba mijinki hadin kai, kada ki bari faraka ta shiga tsakaninku balle idan ta zo ta ga kofa kada ki nuna damuwa ko 6acin rai ko ki ce lallai sai kin hanashi, idan kika nuna kina taya shi farin ciki da nuna yardarki sai ki ga ya kara kyautata miki da kara rikeki cikin so da amana har ya kasance ke zai dinga neman shawarwarin abinda zai gudanar na harkar bikin. 186 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Ya kasance ke zai dinga nema shawarwarin abin da zai gudanar na harkar biki. Ya kamata ki nemi tarihin nana A'isha uwar muminai matar manzon Allah (SAW), don ki yi koyi da ita wajen kishi, saboda ta yi kishi ne mai ma'ana da kuma tsafta, wanda ya sa ta yi fice wajen 'yan uwanta iyayen muninai. Ki kasance mai juriya, da tsananin hakuri da yi wa miji kissa amma ba ta mugunta ba, akwai kissa ta iya magana kawai ta wajen yin girki, akwai ta yin tafiya akwai ta kyautatawa miji, wato idan 'yar uwan zamanki ta yi abu ta kyautatawa miji to ki yi burin ranar girkinki ke ma ki kyautata masa fiye da nata, sannan akwai kissar kwanciya wannan ba sai na yi miki bayani ba, kin karanta a littafina DON MA'AURATA, duk na yi bayanin irin wannan ne a littafin ba don rashin kunya ba ko fitsari na yi a dalilin la'akari da yanayin mazajen yanzu 'yan bana bakwai ne idan baki iya kisser kwanciya ba to za ki sha mamaki, mai krki ne zai iya gaya miki baki ya ba ki koya kı ya, ko ya koya miki, wani uwa ba zai gay 2 mici ba sai dai ya rangado miki amarya wayayyiya ita idan ta zo ta gano matsalarku ta yi ta mil i habaici, shi ya sa na yi filla filla a littafin. Ki kasance da kanun kai a gidan aurenki ba ballagaza ba ke ce can gidan makota kece can, ana shiga gidan makoci amma WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zarnia sai larura ta auku, ba kawai don ki je hira ba, ke kin bar na ki gidan mijin kina can kina gulma, irin su ne ake turkesu can a makotan gurin yawon gulma, to ki tsare mutuncinki da na aurenki banda shashanci, kuma ki yi ta adu'ar Allah ya zaunar da ku lafiya ke da mijinki da ita abokiyar zaman taki, da sauran jama'a makotanki. Sannan idan kina da zafin kishi to ki dinga addu'a ki na rokon Allah akan ya rage miki shi ko ya raba ki da shi. Kuma ya kamata ki san wani misali kamar idan mutum na da sutura masu kyau da tsada, da zarar ya dinka sabuwa ko da bata kai tsadar nasa na baya ba, zai yi ta doki da zumundi hankalinsa ya karkata zuwa ga sabuwar rigar nan na dan wani lokaci sai ya sa ta hankalinsa zai kwanta zai bar wadancan rigunan, kafin' daga baya ya koma ga tsofaffin nasa ya dinga canzawa da sabuwar tunda ita ma ta shiga sahunsu, to hakika haka namiji yake idan ya kara aure, zai yi zumudin amaryar nan tamkar sabuwar riga sai ya saka ta hankalinsa zai kwanta, don haka ne ma aka umurci ya zauna a dakin amaryar na iya kwanakin da musulunci ya tsara idan budurwa ce kwana bakwai idan bazawara ce kwana uku. A wannan lokacir. sai kin kai zuciyarki nesa kin yi hakuri karla ki WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria kuskura ki nuna damuwarki akan wasu al'amura da zaki gani suna faruwa a lokacin ba ga mijinki ba ga ita amaryar ba, kuma idan kin yi hakuri wannan zumudin na wani fan lokaci nc, zai dawo gareki za ki ga ma har ki fita in dai ba ta bashi kulawa irin yadda kika saba bashi ba, sai hakurinki ya yi miki rana. Kuma kada ki yarda da zugar kawaye ko wasu cikin 'yan uwa, domin kila kin yi hakuri kin nuna rashin damuwa, sai ki ga wasu kawaye ne za su saki cikin damuwa, har su sa ki ki aikata abinda bai dace ba, kuma da can baki yi ba sai da suka zuga ki, saboda haka sai ki kiyaye ki gane cewa duk wanda zai zuga ki ba masoyinki bane, wannan zai lallashe ki ya baki shawarwari na gari shi ne masoyinki, duk wanda ba zaki amfana da shawararsa ba to ki yi watsi da duk abinda zai gaya miki, Allah (SWT) ya ce, HAIRUNNASI MAN ANFA"AN NAS, mafi alkhairin mutanc shine wanda mutanen suka amfana da shi kuma ki kiyaye kada zuciya ta kaiki ga aikata abinda ranki ke so, in dai ba alkhairi ba ne abin to kada ki aikata domin Annabi (SAW) yace, MAN FA"ALA ΜΑ SHA"A YALKAMAASA wanda ya aikata abinda ya ga dama to zai ga ba daidai ba. 189 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Rayuwan nan fa ba ta da tabbas gabadayan ta ma tana KURBIN NIHAYA ne ta zo Karshe to me zai sa ba za mu gyara rayuwarmu ba da al'amuranmu don lahirar mu tayi kyau? A karshe ina kara baki shawarar ki yi hakuri! Ki yi hakuri! Ki yi Hakuri! Domin shinc babban jarinki a nan duniya da kuma lahira, Allah ya baku zaman lafiya, dukkanku ya azurtaku da 'ya'ya masu albarka, da fatan za ki yi amfani da shawarwari na?" Tacc, "Anti na gode! Na gode Allah ya saka miki da mafificin alkhairi duniya da lahira bisa ga irin shawarwarin da kike ba mu a littafinki da kuma idan an kira ki a waya ga maman". Mama Amina ta mashi wayar ta cс, ""Sahiba gaskiya mun gode da wadannan shawarwari don mi ma na karu sosai tunda an sa wayar a hands free ne, In Shaa Allah za ta yi amfani da shawarwarinki, kuma zata cigaba da kiranki don neman wasu shawarwarin akan abinda ya shige mata duhu da fatan ba zaki gaji da ita ba". Tacc, "Sam! Babu maganar gajiya kofa ta a bude take ga kowa ba ma ita ba. Allah dai ya yi mana jagora a al'amuranmu amin". Suka yi sallama da juna kowa ya ajiyc wayarsa. Mama Amina ta sauke ganinta ga Munceba tace, "To, kin dai ji shawarwarin da 190 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria nasihohi ba ma sai na kara miki da komai ba, sai ki yi aiki da-su". Munceba tace, "Ai ni Mama yanzu hankalina ya kwanta, In Shaa Allahu zan yi aiki da shawarwarinta ba zan bari wani abu ya bullo ta wajena ba". Ranar yini Mama ta yi tana kara ba Muneeba shawarwari. Da Mujeeb ya zo daukanta ma Mama ta hadasu ta yi musu nasihohi kuma ta nuna taiji dadi da bai bijirewa Umurnin mahaifiyarsa ba, don idan ya bijire Munceba abin zai shafa, gara da ya yarda tunda ya dauko Muneeba a hanya ya lura şam ba ta cikin damuwa, walwalartà ta dawo tamkar yadda ya santa, ba kamar da safcba lokacin da ya gaya mata batun aurensa. Tun a ranar da suka koma gida, ya nemi shawarwarta, suka soma tsara yadda sha'anin bikin zai kasance, sannan ita ya dorawa ragamar komai na bikin, hatta sayan kayan akwati ita zata yi, kuma set biyu yoee, za ta saya nata da na amarya, da ta tambaye 'shi dàlili sai yace ai ita ma bai yi mata akwati ba lokacin bikinsu, wanda aka yi mata ba shiya yi ba, yanzu ko dole ne yayi mata tink li va hore mosa abin y kayan daa don la Sad ne da sH ma ya canza mata, amma duk da haka yace zai bata kudi isassu ta sa yi abinda take so. 191 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria *** *** *** Tun bikin yana saura sati faya Goggo ta iso garin Gombe, ta sauka a dakin da aka gina dominta wanda ya kunshi komai na jin dadin rayuwa, har da kayan kallo da AC da gadonta na alfarma da kujeru, dakin ya ji tayals ko ina. Falo ne babba sai dakin bacci guda daya. Da ta zo ta ga akwatunan da Mujecbun ya yi wa Muneeba, fada ta dinga yi, da ya ke na amaryar can Dukku aka kai gurinta sai 'yan uwa suka hadu suka kai a cewarta duk surutun da Muneeban ke da su, sai yayi matą wasu akwatuna don gata da barnatar da kudi sai ya nuna mata to ai lokacin bikinta bai yi mata ba, shi yasa ya hada ya yi musu tare, tace sam wannan ba wai dole ba ne, tunda Alh. Sani ya yi mata ai a iokacin ta yi ta fadanta yana bata hakuri don ma bata san Munceban ba ce da kanta ta hada akwatunan da sai ta kusa tsine masa albarka don cewa za ta yi an dada shanyc shi an mallake shi, abin da Munceban ta guda kenan don bata so ya nunawa Goggo kayan ba a dalilin abin da zai iya biyo baya ba zai yi musu kyau ba dukansu. Munceba ta yi tamkar ba ita ba ce ake yi wa kishiya ba, komai da ita ake yi, to me zai tasbi hankalinta tunda mijinta bai ragea da WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria komai ba, ita ma shi ya sa ta sha alwashin ba marada kunya, Goggo kuma ba haka ranta ya so ba, duk yadda ta so ta tinzira Muneeban don ta yi fushi ko ta nuna an yi mata ba daidai ba ta canzawa mijnta a dalilin irin abubuwan da Goggon ke ambatawa ce wa Mujeeb din ya yi wa Suwaiba na karya don Munceba ta tinzira sai take yin sakuratin bangaro da duk wani sha ci fadin da kalaman tinzirawa da Goggon ke yi, kullum sai dai ta ganta suna raha da dariya ita da mijinta, kuma suna gudanar da harkokin bikin a tare, don wani lokaci abubuwan da Goggon ke yi na damunta kishi kuma yana tinkaho, amma sai ta dake ta yi saurin shigewa daki ta dauko alkur'ani ta karanta sai ta ji natsuwa ta zo wa zuciyarta. Ana saura kwana biyu kikin Adda Fadima ta iso a dalilin Munecban ta matsa mata da waya tana son ta zo da wuri kuma ranar ne bayan isowar Adda Fadiman, masu motar kayan amarya da masu yin gyaran daki mata 'yan uwan Hajiya Harira suka iso. An yi girki wadatacce domin zuwan nasu, ga abin sha na katan katan haka aka yi ta kai musu, duk yadda Goggo ta so aga gazawar Muneeba ace ta yi ba dai dai ba, abin ya faskara, don wani abin haushi ma da ta ji kunnenta na 193 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria jiye mata shi ne yabon Munecban da suke yi tunda har dakin Suwaiban ta biyo su ta gaişhe su cikin girmamawa, sannan ga tarba abinci da abin sha masu dadi da ka yi musu, su kam ba su ga aibun ta ba, idan Suwaiba ta so za su zauna lafiya haka suka yi ta fada. An gama gyaran dfakin Şuwaiba har sun koma Dukku. Daki kan ya yi kyau sai dai bai zarce na Munecba a komai ba illa ma na Muneeban da ya fi yin tsari irin na 'yan boko. Ranar bikin gida ya cika makil da jama'ar Dukku da nan a Gombe yawanci jama'ar Inna Amina ne, sai kawayenta Munecban na jami'a da ta hadu da su gurin karatun da ta fara, ita kam ba za ka ce ita kake yi wa kishiya ba saboda kazar-kazar da walawalar da ta ke yi, sai ka rantse itace amaryar don ko amaryar ba zata kaita yin kyau ba. a Shi kanshi angon kasa tafiya gurin daura auren ya yi, suna dakinsa yana yabawa irin kyan da ta yi ta ce, "yanzu ni har na isa in kamo kyan kwalliyaur ka kaifa ango nc? ya kara matseta jikin shi yace, "Wallahi duk cikar taron bikin nan idan aka tara matan nan za ki zamo tamkar Zarah ne cikin taurari sannan ....". Mujecbu! Mujecbu! Mujccbu! Wai wanc irin shirmc ne wannan a kule a daki kabar mutane a waje su na 194 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria jiranka". Kwaratsin Goggo ne wannan lokacin da ta zo kofar falon Mujecb din tana kwarara masa kira. Ya yi saurın sakin Muneba, ya gyara. hularsa da malun-malun dinsa ta asalin shaddar gezna mai tsada fara sol da ita, ya sumbaci labban Muneeban yace, "Shike nan mun tafi, take care". Bata iya ce masa komai ba illa hannu da ta daga ta yi masa bye-bye. Ba ta fito dakin nasa ba sai da ta tabbatar Goggon ta dade da tafiya, sannan ta fitó. A dakintá kawayen ta na jami'a suna ta mamakin wannan hali na sirikarta, a cewarsu meye nata na bin danta daki don ya na tare da matarsa, to me take son ta gani in ba kwakwafba. Taro ya watse lafiya, an kawo amarya washe gari an dada gyara mata daki sánnan kowa ya watse, sai Goggo ta řage da tace ba zata tafi ba sai ta watstsake gajiyar biki. Misalin tara na darc Mujceb ya yi sallama ya shigo dakin Muneeba ya isketa a zaune gaban madubi tana shafa mai shirin kwanciya take yi, ya zo ya sumbaci gadon bayanta sannan ya dan rage tsawo ya risina ya buba hannuwansa bisa cinyoyinta yace, "Ke shirin bacci ma ki ke yi ba zai yi cigiyar ina mijinki ya ke ba tara na darc". Ta saukc ajiyar zuciya tace,"Ya za a yi i WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria nemeka, na sani ko ka dawo ka na can dakin Kanwata". Ya ce, "Haba Muneeba idan na yi haka ai ban yi adalei ba, a ce in zo ban neme ki ba in wuce wani guri, ai ke rabin jiki na ce komai zan yi sai da ke, yanzu ma taso ki rakani gurinta". Ta yi murmushi tace, "haba Yayana kada mu yi haka da kai, ba sai na raka ka ba, don ba na son yin katsalandan a rayuwar wani, ka yi hakuri ka tafi kai kadai za ta fi son ganinka ka je gurinta kai kadai, ba tare da 'yar rakiya ba". Ya tubure sai sun je tare ko ya fasa zuwa ya wuce dakinsa, da kyar ta lallashe shi zai je shi kadai amma sai ta rakashi bakin dakin Suwaibar in yaso sai ta dawo Ledojin da ya shigo da shi, ya cire mata nata da na Goggo sannan ya dauki ra su ta raka shi har kofar falon Suwaiba, sai da ta ga ya shiga sannan ta jawo, karaf ta hangi Goggo na leken wucewarsu ta labulen windon Dakinta, alhalin gurin Goggon ya fara shiga ya yi mata sai da safe ta, rufe kofar sannan ya shiga gurin Muneeban shine don fitina ta tsaya tana leken ta ga shigarsa da fitarsa. Muneeba bacci ta yi sosai a wannan dare wanda aka sarin mata da aka yi wa kishiya a irin wannan daren ba sa bacci sabanin ita da ta yi 196 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria baccinta har da makara don bata tashi ba sai shida saura na safe sannan ta yi Sallah ta je ta gaida Goggo ta dawo ta shiga kiein don hada abin karyawa. Har ta yi ta gama da misalin tara na safe ango da amarya ba su tashi ba balle su bude kofar falonsu, wannan abu ya saka Munecba cikin kokwanto ita ba abin ta je ta tambaya ba ko lafiya har yanzu ba ta ji duriyaursu ba, tuda ita dai ta saba mijina idan ya tashi tun asuba ya je masallaci ya dawo to baya komawa bacci tarce suke shiga kicin su yi komai, sai gashi yau daya har an fara sauya masa rayuwa. Allah sarki Munceba ai wasa farin girki kenan a al'amuran Suwaiba diyar Haj. Harira, sauran al'amura ma na can gaba na ban mamaki. Ku biyo Rahman zaria a littafi na biyu tare suke fito da na dayan 08068895555, 08028434948. 197 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria FILIN RAHA LABARIN MAGIDANTA GUDA UKU Wasu magidanta ne guda uku suke zaune a bakin dakin haihuwa, kowa ya kawo matarsa, can sai norse ta fito ta ce, "waye ya ke aiki a (Two Towers)?" dayan cikinsu ya ce "Ni ne". tace ina taya ka murna matarka ta haifi 'yan biyu" ya yi godiya ga Allah yana murna, can ta dawo tace ina mai aiki a (3crowns) ya ce "Ga ni" ta ce matarka ta haifi 'yan Uku. Ta na shiga dakin haihuwan sai fayan wanda matarsa ta rage bata haihu baa ka ji ya saka kuka, duk suka dubeshi a tsorace suka ce, "Lafiya malam? Ya ce, "wallahi ni a kamfanin 7up nake aiki na san zata cc an haifar mini 'yan bakwai! AISHA IBRAHIM LABARIN ‘YAN BAUTAR KASA Wani dan bautar kasa ne yana cikin rashin kudi, Sai aka biya masu kudin alawas dinsu naira dubu talatin da biyar. Yana dawowa gida sai ya yi wanka ya je ya dauki budurwar sa suka tafi super market zai yi mata siyayya. Ta zabi mayuka da kayan kwalliya, ashe ma su tsadane, da aka zo 198 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria gurin kashiya ta yi total din kudi sai suka kama dubu talatin da hudu da dari uku (N34,300:00). aka gaya masa ido fa ya raina fata, hakanan ya dauko kudin ya bada. Sai aka ce sunan wa za a sa a rasit din sai yace wa kashiyar ki sa MARIGAYI. LABARIN WASU MASALLATA Wasu masallatane an yi Sahun Sallah da su a Masallaci, liman ya zo ana shirin tada ikama, sai suka ji wani daga harabar Masallacin ya na waya yana cewa, "Eh na aje jakar tana nan a gaban liman daga gefe, Eh, yanzu kuwa. Liman yana kai idonsa gefe sai kuwa ya ga jaka, ai kafa main a ci ban baki ba, ka fin ka ce kwabo da liman da mamu sun arta waje da gudu, ana ta gwabza gudun ceton rai. Sai a waje mutumin ke muşu bayanin ashe kudin zakkane wani ya aiko da su ya aje a in aka idar da Sallah ake so ayiwaliman bayani. 199 * * * * LITTAFAN MARUBUCIYAR SANIN HALI 1,2,3 HUJJATA 1,2,3 MENE AIBUNA? ALKAWARIN DA CIWO 1,2 NA YI BIYAYYA 1,2 WA YA CUCE NI? 1,2 BAYAN WUYA 1,2 SAIHAМ 1,2 MU YI HATTARA 1,2 AUREN MANUFA 1,2 Ana iya samun wa yannan littafai, a SIRRIN GIRKE-GIRKE 1,2 MIJIN ARO 1,2 ILLAR KUSANCI 1,2, DON MAʼAURATA WATA KUSAN 1,2 MUHAMMAD SANI BOOKSHOP CHARANCI ROAD KASUWAR BARO 080332684404,07089897389 AL-MUSTAFA BOOKSHOP BAKIN RIMI GIDAN JUMA S/GARI ZARIA 08026570893, 08130616029 Z RABI'U WUSE BOOKSHOP Wuse market zone I Abuja. 08030777669, 08091331166 AL-AMIN BOOKSHОР No Aq 1 Anguwar rimi market Kaduna 08023607345 SPU NAFPU BOOKSHOP Behind Kofar Doka Central Motor Park, Zaria 08028341964, AL-AMIN BOOKSHОР Layl Na Hudu Bayan Masallacin Abacha A.A. Rimi Market, Kano ABUBAKAR ABUBAKAR BOOKSHOP Inside Club 69 Garejin Hayi-Hayl Sheik Abubakar Gumi Central Market Kaduna 07066706030,08029646961 Designed Printed by: ZAZZAU VENTURES General Printing & Publishing 08028401199, 08035336868 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi

Chapter 10 of 11