Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 11
shi Mujeeb ya rasa me zai ce wa Munceban? Yusuf sarkin magana shine yayi magana ganin duk sun kasa cewa junansu komaikila nauvin juna sukeji, a 84 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria dalilin wannan al'amari na bazata da ya faru akansu yacе, "Amarya Munccba ya hidimar biki, anyi komai Lafiya?" fuskarta cikin lullubi tayi magana da 'yar siririyar muryarta tace, "Alhamdulillah an yi lafiya, kuma kun iso lafiya daga Gombe", yace, "Lafiya lau, ai muna ta zumudin mu zo mu yiwa su Baffa godiyar wannan muhimmin al'amari da suka kulla, sabo da shi angon baya garin an tura su Lagos daga Makaranta, nima naje Bauchi, shi yasa muna dawowa muka taho dan kada ki cinye kajin amarcin ke kadaimu ma aci da mu". Dariya tayi bakinta tamkar a cikin gyalenta tace, "Sannunku da gajiya" ta dan risina gaban Mujecb tace, "Yaya Mujeeb ina yini, bamu gaisa ba?" yace, "Lafiya lau, ya taro?" tace, "Alhamdulillah, ka dawo lafiya", "Lafiya lau nima naje (Excusion) ne jahar Lagos ban san abinda ke faruwa ba sai- da na dawo yau, ina fatan zamu yi wa Iyayenmu biyayya, mu gina so da kauna a tsakaninmu, kuma mu rike amanar juna". Tacе, "Insha Allahu ta 6angarena ba za a sami matsala ba. Allah ya shige mana gaba". Yace, 85 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "Ameen". Yusuf ma ya basu shawarwari na gari ta yadda za su zauna lafiya tunda sun yi wa iyayensu alkawarin yi musu biyayya. Mujecb ya dubeta yaсс, zamu wuce can gida, bamu je ba nan muka la. sauka, akwai wani abu da kike so?" tayi sauria girgiza kai tace, "Babu abindanake so. Allah ya huta gajiya a gaida min Goggo". Ya ciro dubu biyar ya mika mata yace, "Ga wannan sai ki rike idan kina bukatar wani abu, don gobe zamu wuce akwai test da zamu yi jibi a makaranta don kun kusa fara exaın ban sani ba ko zan sami dawowa next weck ana goben idan zam wuce zamu biyo mu yi sallama". Ita ta fara fita ta shige cikin gida, nan ta ci karə da ‘yan tsegumi gidansu ana zaune ana jiran a ga dawowarta. Su ma suka fito suka nufi gidansu Mujeeb da ke Duggc. Goggo na zaune fana jan casbaha, bayan ta kida da sallar isha'i su Mujecbu suka yi aliama suka lhiga suka zauna bisa tabarma suna jiranta ta tagama laziun. Bata dade ba ta shafa addu'ar da tayi sannan ta fuskancc su. Gaba daya suka risina suka gaida Goggo ta amsa tare da cewa, "Saukar yaushe da daddaren nan ba kwa bari sai da safe ku taho?", Yusuf yace, 86 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "Wallahi muma mun so sai gobe mu taho Alhaji ne yace lallai lallai ya taho yau, shinc direba yakawomu har yakoma yanzu mai ai ya dade da isa Gombe", Goggo tacc, "Da zu baka biyo Alhajin ba lafiya", Yusuf take tambaya, yace, "Nima nayi sammakon zuwa Bauchi ne, shi yasa ban samu zuwa ba.An daura aure Lafiya?" Goggo taja tsaki tace, "Sun daura lafiya ni ai fin karfi aka yi mini, da an bi nawa ra'ayin anyi shawara da ni, inda anbi nawa ai da ba ayi wannan hadın ba. Kun biya ta can gidan namu ne?' Yufus yace, "Eh, can muka fara biyawa, su Baifa sun yi mana bayanin komai, Goggo hakuri zaki yi mu fawwalawa Allah al'amarin tunda ya riga ya kulla addu'a zaki bisu da shi, Allah ya basu zama lafiya ya kauda fitina a tsakaninsu, Ai kinyi dace da sirika Goggo yarinyar tana da ladabi gata diyarki kinga ai ba matsala" ta ja tsaki, "In bata da matsala ai uwarta na da shi, tunda ta mallake mini dan uwa, shima haka za su mallake mini shi, kuma wallahi bazaı yardaba sai na nuna musu idan sun iya sammako to ni a tafe nake kwana". Yusuf dai ya ta bata hakuri yana nuna mata sam haka ba zai yiwu ba, ya 87 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Karfafa da ccwa, "Wallahi Goggo wani lokacin ladabi da biyayya idan mace tana yiwa mijinta shine yake sa agą tamkar ta mallake shi, saboda miji zai kyautata mata kwatankwacin irin ladabin da biyayyar da take masa. Wannan diyar taki a yadda nagantą zata yi miki ladabi da bin duk umurninki Goggon kiyi hakuri tunda Allah ya Kulla wannan al’amarin". Shi dai Mujeeb yana zaune tamkar mutum mutumi, ya rasa bakin magana saboda rudan da Goggonsa take neman jefa shi, alhalin ya daukarwa Baffaninsa alkawarin zai yi musu biyayya bisa hukuncin da suka zartas a kansa, sai gashi tana nuna zahirin adawarta ga hukuncin yayyin nata, mai makon itace mai tausarsa ko da zai nuna bijirewa ta karfafa masa gwiwa da ya bi umurnin 'yan uwanta sai gashi itace zata ja masa ragama don ya bijire musu, shi kam tunda abin da suka yi ba sabawa umurnin Allah bane sunnar Annabi suka kula to in sha Allahu ba żai biyewa hudubar mahaifiyarsa ya karya alkawarin biyayyar da ya yi musu ba, sai dai zai san yadda zai yi wajen zamansu gida daya da Goggon, zai fifitata fiye da matarsa, zai dinga binta sauda kafa akan duk wani umurni nata in dai ba zai tauye hafkkin matarsa ba. 88 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Goggo ta watsa masa idanunta cike da tuma tacc, "Kana ji muna magana kayi mana shiru tunda ka rigaka je Yaya Adamu sun shirya maka kalamai masu dadisun kwakkwafcka, to ba zance ka bjire musu ba amma ka sani, wallahi ba zan dauki duk wani abu da bai yi mini ba a zaman aurenku, ka sani ni mahahifiyyarka ce babu wanda zaka so fiye da ni a duniyar nan".Mujeeb yace. "Wallahi ni bani da kamarki a duniyar nan, ke kadai kika rage mini da nake kalla inji sanyi, ta yaya za ayi in fifita wani kina rayc, ai ba zai yiwu ba ki kwantar da hankainki in dai wannan ne matsalarki". Tashi tana cewa "bari in kawo muku abinci". Yusuf tace, "Wallahi a koshe muke Goggo, mun ci abinci a gurin Baffa zamu je mu yi sallar isha'i ne mu kwanta a gajiyc muke sosai". Tace, "Ai dole ku gaji daga dawowarku daga tafiya Alhaji yace sai kun taho da ya barku sai gobe". Suka sallame Goggon suka wuce dakin Mujeeb da ke soron gidan. Suna shiga da yake akwai bayi a dakin Yusuf ya shiga yayi alwala, sannan Mujecb yayi suka yi jam'in sallah. Bayan sun kwanta ne Mujeeb ya kasa hakuri da abinda ke mintsinin zuciarsa yadan muskuta daga kwance yace, 89 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "Yusuf ya kake ganin zanyi da al'amarin Goggo tunda bata son auren nan?" Yusuf yace, "Ni dai shawarata ka rike aurenka hannu bibbiyu kada kayi sawarwarin da yarinyar nan zata subисе maka, con wallahi komai nata yayi daga dabi'u har yanayin ta, ita kuma Goggo tunda na lura bata son aka so wani fiye da ita to sai ka kula kada dadin amarci yasa wata ran ka makale ka manta da fitowa duba lafiyarta". Mujeeb yayi tsaki yace, "Dadina da kaisai ka fara abu na arziki sai ka soma slashanci, ni akwai wani dadin duniya da zai sa in manta da Goggo? In ma akwai shi to bana tetan yayi təsiri a kaina. In sha Allahu zan kiyaye ka san i'a Goggon da aminiyarta suke son hada aurenmu ni da 'yarta, goggon ace in je in nemi yarir ar wai idan nagama karatu na fara aiki sai ayren, a lokacın na nuna mata bana ra'ayin yarinyar, da ta nuna min ranta ya baci sai nace to ta cari idan nagama karatu sai in fara zuwa gurin suwaiban don bana son hada karatu na da komw shine fana samu ta bar maganar a haka, shi yasa abinda su Baffa suka yi ya har zukata tunaa ita ga shirmta 3a kuma sun yi mata bazata, ni garama da haka ta faru don wallahi na tsani yarinyar idanunta waje suke, ita goggon da take ganin gara in aureta da in auri Munceba ba WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria ta son ita aminiyartata itace mai cutarta ba 'yan uwanta ba, duk san da zata yi wa Suwaiban ai na Muneeba shine gaba, Wata Kusanai tafi gaban wata Yusuf yacc, "amma ita ma Munecban naga kamar ba wani sonta kake ba". Yace, "Eh to ba zance maka bana sonta ba, sannan bazan ce maka ina sonta, ni dai na san akwai kauna ta 'yan uwantaka a tsakaninmu amma nan gaba ina fatan kyakkyawar mu'amalar da zamu yi ta sa muso junanmu". Da safe bayan sun yi wanka suka shirya cikin shadda Galila iri daya mai ruwan bulu ta Mujeeb tayi duhu saboda shi fari ne ta Yusuf kuma tayi haske sabida shi baki no amma bakinsa mai sheki da daukar idanu a dalilin hutu da cima mai kyau. Dadduma suka shimfida bisa dakalin kofar gidansu Mujeeb suka zauna suna ta hira da abokan Mujecb dinna nan Dukku a da ilin sun sami labarin yazo gari shine suka zo yi masa Allah ya sanya alkhairin auren da aka daura masa. Kafin su Mujeeb su bar garin sai da aka tattauna aka tsayar da cewa nan da sati biyu za ayi tarewar Munceba kuma anan gidan Inna za a yi katanga a fitar mata da sasanta, za ayi mata 91 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria can gefe sai daki falo babba sai dakuna guda biyu a ciki falo babba sai dakuna guda biyu a ciki wannan gyara su kawai aka yi a fidda su yadda ake so. Da Mujecbun ya zo ya gani abin ya birge shi yadda masu aikin suka tsara komai cikin tsari da birgewa tamkar sabon gini tsari da birgewa tamkar sabon gini haka suka maida gurin, sannan ya yabawa Isah yadda yayi tsayin daka har sai da ya ga komai ya kammala, Bangaren Gogon ma tamkar sabon gida haka ya koma saboda fentin da aka yi wa gidan duka, komai dama yana son gyara sai dai in bai samu ba. Tun ana gobe tarewa Inna Amina ta iso ita da 'ya'yanta, sauran jama'arta sai gobe washe gari za suc iso. Tare suka taho da motar kaya na dakin Munceban da aka siyo su a Gombe. Innar su Munecba ta sayar da daya daga cikin shanunta, shima Babansu Munceban kudin da 'yan uwansa suka hada suka bashi ya hada da na hannunsa duka akaba Inna Aminan shine ta yo kayan daki masu nagarta da kyau kowa ya gani sai yayaba. Ita kuma a nata guddummuwan da WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria kicin da bayi duka a sasanta, diban ruwa a rijiya ne kawai zai fito da ita tsakar gida. Dasu Mujeeb suka koma Gombc Alhaji ya tambaycsu me aka zartas a Dukku game da lokacin tarewa, sai suka gaya masa an tsayar da nan da sati biyu zata zauna a Dukku tare da Goggo". Yace, "me zai hana ka kawota nan Gombe sai in baku gurin zama, naga hakan zai fíi maka sauki" Mujeeb yace, "Furucin Goggo ya nuna min bata son in kai Muneebar ko ina, shi yasa ban nemi izinin in kawo ta nan ba tunda na lura ba zata yardaba, zan barta a can in yaso na dinga zuwa week end nan gaba idan naga yiwuwar tahowa da ita sai in taho da ita”.Alhaji yaba Mujeeb kudi yace ya je Dukku ya sami masu gini a sayi komai na aiki su fidda sasan Muneeban ayi duk yadda ya kamata ita Goggon ayi mata gyare-gyaren idan an gama sai ayi fentin gidan duka don ya tashi bai daya. Isah Kanin Mujeeb din shi Mujcebun a bar komai a hannunsa na kula da aikin tunda shi ba zama zaiyi ba. Kafin satibiyun nan su cika har an kammala tsara gurin yadda ake so an fidda kofa tsakanin tsakar gidan Goggo da sasan Munecban, kana shiga zaka iske dan madaidaicin takar gida ga bayi guda biyu a wanka da ba haya sai kicin a 92 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria can gefe sai daki falo babba sai dakuna guda biyu a ciki falo babba sai dakuna guda biyu а ciki wannan gyara su kawai aka yi a fidda su yadda ake so. Da Mujecbun ya zo ya gani abin ya birge shi yadda masu aikin suka tsara komai cikin tsari da birgewa tamkar sabon gini tsari da birgewa tamkar sabon gini haka suka maida gurin, sannan ya yabawa Isah yadda yayi tsayin daka har sai da ya ga komai ya kammala, Bangaren Gogon ma tamkar sabon gida haka ya koma saboda fentin da aka yi wa gidan duka, komai dama yana son gyara sai dai in bai samu ba. *** Tun ana gobe tarewa Inna Amina ta iso ita da 'ya'yanta, sauran jama'arta sai gobe washe gari za suc iso. Tare suka taho da motar kaya na dakin Munceban da aka siyo su a Gombe. Innar su Muneeba ta sayar da daya daga cikin shanunta, shima Babansu Muneeban kudin da 'yan uwansa suka hada suka bashi ya hada da na hannunsa duka akaba Inna Aminan shine ta yo kayan daki masu nagarta da kyau kowa ya gani sai yayaba. Ita kuma a nata guddummuwan da WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria mijinta sukasaya T.V inci goma sha takwas da DVD da Firiji, da kafet na tsakiyar daki sai dangin kayan kicin na girki irin na zamani. Da aka gyara dakin Goggon sakin baki tayi tana kallon dakin wanda ta san ko 'yar Hajiya Harira da take takama da ita aka auro irin kayan da za a yi mata kenan. Nanfa ta tuma gefe ta ce sam wannan dukiya da aka kashewa Muneeba a daki shanu i Baban Muneeban ne aka sayar don ayiwa Muneeban kayan garari wai duk wannan kinibibir Innarsu ne da na 'yar uwanta Inna Amina. Aifa nan gida ya hautsine da rikici tsakanin Goggo da 'yar uwar Innarsu Munecba da suka zo gyara daki, har sai da Malam Adamu ya zo gidan ya tsawatarwa Goggo Rahin sannan abubuwa suka daidaita yayi mata fada da nasiha sosai akan yarda girmanta da take yi a idon duniya, alhalin ko 'ya'yan cikinta basa son wannen ri halayya ta ta, su kansu ba za su iya abinda takc yi ba. a Dama Mujeeb bai taho ba, yana jin abinda ke laruwa sai yaji ba zai iya zuwa Dukku ranar ba. saboda kuyan 'yan uwan Innarsu Muneeba ba ma ya son su hada idanu da su, shi yasa yayo waya yayi karyar za su yi Test a makaranta ba zai sami zuwa ba sai washe gari. WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Muneeba dai ta cỉ kuka har ta bauku lada sabo da abin da ya faru sannan tana tananin yadda zamansu zai kasance tare da Gog go. tunda bata son auren nan ita kam zata yi mata biyayya İya biyayya, zata bi ta sau da kafa iya iyawarta ta yadda da wuya zata ga baikenta ko da yake wanda ya nuna baya kaunarka ko nonon uwarka ka yanke ka gasa masaba zai ga kayi masa gwaninta ba, gwasaleka zai yi. Su Khausar ne suka dada gyara dakin na Muneeban suka turara su da kalolir turaren wuta, ta yadda ba ma dakin Munneban bagaba daya gidan har sasan Inna yadauki kainshi, kai har kamshin ya fita cikin unguwansu ti Dugge. Inna Amina ta 6alle Jakarta ta fiddo litta fai DON MAʼAURATA tamikawa Munneba tace, "Duk wani fada da iyaye keyi mun yi miki, ga wannan littafin ki zauna a tsanake ki karanta sni, kuma ba wai ki karanta kawai ba a a kiyi anfani da abubuwan da ke cikin littafin don ki gudanar da kyakkyawar mu'amula da mijinki a rayuwar aurenku abinda baki fahimta ga nambar marubuciyar littafin nan ki kirata ki tambayeta zata yi miki bayani sosai don ina kiranta mu yi shawarwari harmun kulla amintaka sosai daita, na aminta da ita a dalilin shawarwarin da take bani, zata zo Gombe a dalili na, nima za ıje Zaria 95 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria kinga zumunci mai karfi ya kullu a dalilin littafi da kuma shawarwarin na gari da take bani, har fa babban su Khairi ya santa suna gaisawa a waya yayi matagodiya shawarwarin da take bani, tunda yana jin dadin sauyc-sauycn da yake gani a rayuwar aurenmu to ina san kiyi koyi da ni kin zauna da ni kinga irin mu'amalar da nake yi mai tsafta da mijina ban da kazanta banda zama ba kwalliya ki kasancc mai iya girki nau'i-nau'l shima ga littafin girke-girken ta da tayi mai suna SIRRIN GIRKE-GIRKE na daya da na biyu ne, ki dinga kwatanta duk girkin da ke ciki inda baki gane ba ki kirata, abin da babu a garin nan ki yi mini waya zan tado Malam Musa ya zo ya kawo miki, sannan ki kula sosai da uwar mijiknki ki kyautata mata, duk abinda kika girka komai Kankantarsa ki diba ki bata, idan tana aiki ki je ki taya ta, ki kyautatawa 'yan uwansa idan sun zo, ki so su ki so 'yan'yansu, kiyi musu alkhairai idan kina da hali. Allah Ya baku zaman lafiya, ya kawo zuri'a mai albarka a tsakaninku". Su Khausar da ke zaune sun yi tsuru suna sauraren nasihar da ake yi wa Munceba Khairi tace, "Mama dama ina ta son inyi miki tambaya akan littafin nan DON MAʼAURATA mu ba zaki siyamana ba?" ta ce, "Guda hudu nama siya nawa daya guda uku kuma naku yanzu na ba 96 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Muneeba nata saboda lokacin in bata yayi ta zama daya daga cikin ma'aurata ku kuma naku yananan na 6oye sai naku lokacin yayi sannan zan baku saboda anyi littafine domin masu aure ko baku ga unan littafin bane DON MAAURATA? To ba domin kowa aka yi shi ba sai domin su, naku na nan zan baku idan lokacin ku yayi". Khairi ta :e, "Mama don A lah kada ki ba wata cikin kawayenki don na sanki da kyauta, mu zo kuma idan namu lokacin yayi ace babu a kasuwa sai an sake bugawa, gara ki boye mana don Allah". Tace, "Babu wandazan ba, inma na bayar na san ba zaku rasa ba tunda zata zo ida bikin naku ya tashi, sai tazo muku da shi ko babu zata nemo ta zo muku da shi balle ma ba zan bayar muku da shi ba tunda na san muhimmancin littafin". Ta kalli Muneeba tace, "Kin cinye kazar da nazo maki dashi ko?" ta gyada kai tace, "Na cinye, sauran kince a hankali zan dinga sha da nono ko madara ko yogot ko?" tace, "Eh, ki adana su inda wani ba zai gani ba, dukkuma abinda baki gane ba ki yo mini waya idan wani abu kike so shima kimin waya kada ki dinga damun mijinki idan kina son abu kin san WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria dai dalibi ne, duk da yana dan taba,kasuwanci, amma ai bai yi karfi ba, kiyi hakuri ku lallaba rayuwaar aurenku wata rana sai labari". Ta dubi 'yan biyunta tace, "To 'yan matana dare yayi a tashi aje a kwanta,kun san gobe da wuri zamu tafi saboda shirin makaranta". Muneeba tayi karaf tace, "Yanwa Mama banji anyi maganar ci gaban karatu na ba". Tace, "Eh, karatu zaki ci gaba insha Alahu duk da bamu yi maganar ba, amma na san mijinki ba zai barki zaune haka ba, in ma naji shinu zan neme shi yazo gida ya same ni sai cuu yi maganar". Suka mike gaba daya zasu tafi Muneeba tayi kwal-kwal da ido zata yi kuka.. tace. "Yanzu Mama ba zaki barsu su kwana ba runda ba yau zai dawo ba?" tace, "Gara da ki fara koyon kwana ke kadai tunda shidin ba mazauni ba ne, kuma in banda abinki ga mutane gidan kina can kuryar gida meye abin tsoro, kiyi aaddu'o'in tunda kina da alwala idanna baki daia akije kiyi ga' ki rufe koina kiyi addu'o'i ki kwanta addu'a ai garkuwa ce", tace, "shike nan Mama na gode zai da safenku". Suka fito ta sake rakosu har suka fita a harabar sasanta taufe kofar ta shiga dakinta ta rufe ko ina WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria sannan ta je tayi shirin bacci tayi addu'o'i sannan ta kwanta. Da safe Munecba tana tashi daga baccin da ta koma bayan tayi sallar subahi, ta bubde sasanta tayi tun bata yi komai ba nasa sasan ba, ta nufi gurin Goggo. A dakinta ta iske ta a zaune da yara masu siyan kamu na yin koko, shine sana'arta suna ta siya, da masu siyan suga. Koda tayi sallama har ta shigo ta zauna goggon bata dubeta ba har sai da ta gama sallamar yaran da ke dakin sannan ne ta dubeta. Munceba ta tashi ta risina a gaban Goggon ta gaisheta, wannan karon ta amsa bayabo ba fallasa, sabanin yadda ta amsa mata sallamar da ta yi. Goggo ta dubeta tace, "Ga yayyinki can cikin daki, ki shiga ku gaisa", (yayyin Mujeebu kenan mata guda biyu da ke aure a nan Dukkun). Ta mike ta shiga cikin Dakin Goggon ta same su suna ta gyaran dakin tace, "Sannunku Adda Fadima, ashe kuna ciki, na sha kun tafi gida ne" Fadima itace babba kuma mai kirki irin mahaifinsu, halayyarsu daya da Mujeeb da autansu Isa, ita kuma mai bi mata Adda Zuwaira, irinta irin Goggo har kamannunta. Fadimata juyo cike da fara'arta tace, "Bamu tafi ba sai anjima, saboda saimun gyrama Goggo gida, kinsan taro akwai lalata 99 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria guri". Ta zauna bisa tabarma ta gaisliesu, ta kamo 'ya'yansu tanamusu wasa. Sannan ta tashi ta soma taya su gyaran dakin har suka gama, suna yi suna hira da Fadima, ita kam Zuwaira sai jefi-jefi take saka musu baki. Suka dawo falon Goggon shima suka gyara shi tastas. Munceba ta fita ta soma sharara tsakar gidan, Fadima ta leko ta ce, "La Muneeba shara kike yi? Don Allah ki barshi yanzu Isah zai shigo zai share, amarya da shara da sassafe ai ba kanta". Ta yi murmushi tace, "Bari kawai zanyi ai ba wata wahala a sharar". Ta ci gaba da sharar har ta gana, ta zo ta same su a dakin Goggon suna hada abin karin kumallo koko ne da kosai. Fadima tace, "Ki je ki kawoguri a zuba miki, naki abin karyawan, kada ince kizo cikinmu kunya ta hanaki sakin jiki ki ci abin kirki". Hakan ya fi mata don ita koko bai dameta ba gara nma kosan tana ci, amma sai bata nuna bata ci ba ta je ta kawo jug da karamin flas din abinci aka zuba mata, ta rike hannun filas din abicin aka zuba mata, ta rike hannun 'ya'yansu guda budiu ta ce su zo su je sasanta. Da yake Inna Amina ta kawo mata manyan gwangwanayen kayan tisai ta tafasa ruwa ta hada ti ta sha da biskit, yaran ta raba musus biskit amma bata ba su tin bạ don kada su 100 1 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria je su ce sun shati Goggo ta fsassara hakan da wata manufa, zata iya cewa an bata abu bata ci ba, sai tayi nata taci.. Ta sake dafa ruwan wanka da yake yaran kanana ne, duk ta yi musu wanka ta aje ta amso kayansu ta sa musu. Matan guda biyu tayi musu kwalliyaa fuska suka dinga murna an sa musu janbaki da abin ido. Itama wankan ta yi ta shirya cikin wata doguwar rigar (bu berry) mai tsukakken hannu kalarta ja, ta nada gyalan rigar a kanta zuwa kafadanta, sai zahirin kyanta ya fito ita kanta da ta duba kanta a madubi tayi mamakin irin kyan da ta yi. Ta kama hannun yaran suka koma sasan Goggo. Ta tambayi Adda Fadima tace, ko akwai wani aiki da za ayi yanzu. Fadima tace "Babu wani aiki da za a yi yanzu ai duk kin gama, wannan uban aiki dakikasha, tunda kika tashi bakihuta ba, idan ma akwai wani aikin zamu yi abinmu kada ki bata kwalliyarki kanina ya dawo ya ganki butu-butu, gara ma ki tashi kije ki shirya masa abin da zaki tarbe shi don yanzu muka yi waya yace yana nan a hanya, ko ya kira ki?" tayi karyar bai kira ta ba,duk da dai ya turo mata text a wayauarta cewar yana hanya wai me ta tanadar masa tana ganin text din, girgiza kai kawai tayi cikin jin nauyin kalmar da ya yi, 101 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria kawai saita bashi amsa, Allah ya kawoka lafiya tace Fadima, "Ni babu abindazan shirya masa, wanda za a yi anan ai ya wadatar ko?" Fadima tace, a "To ki ne 'yan boko ke kikasan abinda za a yin tarbanshi a matsayisa na ango, sai ki fadi abinda za ayi in yaso sai Isah ya je ya siyo kayan yin girkin". Таce, "Adda ni kam da kunyi abinda kuka yi niyya, ko tuwo kuka yi ai zai сỉ”. Adda Fadima ta ce "Tunda kin ambaci tuwu to bari ayi tuwon, amma na shinkafa ba na hado komai sai kiyi mana miyar tunda kina da risho, sai kiyi a sasanki mu kuma anan saimu yi tuwon, bamu takuraki ba ko?" tace, "Haba Adda ko duka kika ce inyi ai bazan takura ba", Adda ta ce :"Ai ni wannan kwalliyarce bana so ta baci kanina bai zo ya gani bashi yasa kika ga ina kaffa-kaffa da duk wani abu da zai 6ata miki kwalliyar". Munecba ta yi murmushi cike da jin kunyar kalaman Adda Fadima, Goggo tacе, "Ke kambaki da girma kannankima ba ki jin nauyin fadin abinda zaki sa su jin kunya, wannan dai sirikarki ce yanzu sai a kama girma", Adda tace, "Goggo inaban yi raha da kanina na basu shawara ta gari ba da wa zanyi, ni kam har yanzu 102 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Muneeba Kanwata ce ba ruwana da wani sarakuta, gara ma ki saki jiki da ni kamar irin da, mu yi hirar mu cikin raha, kin san sanni duk Kannena ina raha da su kuma hakan bai sa wani ya raina niba". ta kare maganar tana kallon Munceba. Adda Fadima ta sa aka nemo mata Isah ta bashi sakon cefanen da zaiyo mata harda nama ta ce ya siyo yau zasu ci girkin amarya. Isah yaje ya sayo komai ya kawo, Adda ta damka a hannun Munecba, ita kuma ta wuce sasanta don yin aikin da aka bata. Cikin irc-iren miyar da Inna Amina ke koya musu a Gombe, irinta ta zauna ta shirya lafiyayyar miyar alayayyahu da gyada, wanda ta nama sannan ta sa kori mai dadin kamshi, kuma ta yi amfani da magi kusan kala goma, duk cikin irin sayayyar kayan girki (spices) da Inna Amina ta taho mata da su ne. ji Nan da nan gidan ya dauki kamshi har sai da Isah ya leko sasan nata yana tsokanarta, "Wai Amaryar Yaya har yanzu miyar nan bata kammalu ba ne, kamshi ya cika gida, yawuce ya fita har. waje ya cika unguwa, kowa miyansa ya tsinke, ni dai nawa har zubowa yayi saboda kosawa yau jama'ar unguwar nan ma sun son an kawo amaryar da ta iya girki, wannan kamshi 163 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan

Chapter 5 of 11