Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 11
musu don kada ina nan ina yada manufata ban sani ba kawai in ji ance anba wani kato a can Dukku, da anyi yaki na kin karawa don bazan yardaba, don 'yan gidansu irin auren da ake musu kenan a hade-hade". ita dai Muneeba barinsu ta yi a falen ta je duba girkin da ta dora. Tana kammalawa ta sl irya masa a babban tire ta dora ruwa da juice dak da ta san akwai ruwan da juice a dakinsa hak an bai hana ta hada 44 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria da su. Tana fitowa falo ta aje tana jiran wani cikin yara ya shigo ta bashi ya kai masa. Khausar tadubeta tace, "Amma ba ke zaki kai masa ba?" tace, "Haba dai tunda Mama tace yanzu mun fara girma mu daina shiga dakunan Yayyinmu maza ai na dauki maganarta". Khausar ta ce, "Ranar baki ji surutan da Yaya Sadiq ya dinga yi ba, wai an hana mu zuwa gyara masa daki ko kai masa wani abu me ake nufi da haka, ba a yarda da tarbiyyar da aka yi masaba ne ko mene, shine Mama tace ai duk gidan anan babu yaron da ta yarda da nagartar tarbiyyyar zuciyarsa irin sa, sai dai bata isa ta hana sharrin shaidan yayi tasiri a zuciyarsa ba, saboda alkawarin da shaidan yayi na yin galaba gurin cusawa 'yan adam duk irin abubuwan da yake so don su sabawa Allah”. Munecba ta ce, "Allah dai ya tsare zuciyar mu daga afkawa sharrin shaidan, amma mutane nawa ne nagartattu masu riko da adddini irin Yaya Sadiq, la'ananne shaidan yake yin nasarar gurfata musu zuciya har su afka cikin tarkonsa, shi yasa idan Allah yayi hani da abu to ko kusa da shi kada ka kai kanka, ka nisanci abin sai Allah ya kiyayeka, sannan yin addu'a babban abu ne Allah dai ya 45 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria tsare dukkae musulmi, ya bamu ikon bin dokokinsa Sai da hutunsu Muneeba ya saura sati daya aunan ta je Dukku, tayi sati daya sannan suka koia makaranta suka kama karatu gadangadan babu kama hannun yaro a dalilin zasu sa ajuuku na karamar sakandare. *** vunecba don Allah ki ware kafa kiyi tafiya vonnan irin lakai-lakai tafiyarmu sama ta ki sa ri", Murja ke wa Muneeban korafi, unguwan zasu je kusancewar duk hutu in dai Munecba na gari o tare zaka gansu. Munceban ta harari Murja tacе, "Wallahi baki isa ki sani tafiya ina sassarfa ba ina haki ki barni inyi tafiyata yadda na iya ke ma saan na dole kike saboda Yaya Mustaha yace yaua jiranki, ni kam tunda ba mai jirana sai a kyaleni in yi lakai-lakai dina". Murja taja tsaki tace, Ai gashı nan kin ja maza sai kallonmu suke yi”. "To ke yanzu ina ruwanki da kallon da suke mana, sun dade basu kallemu ba". Dai dai kofar gidan Hakimi suke hangi dandanzon amari a zaune ana ta hira, ai ba bu WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria arziki Munecba ta ware kafa ta soma sauri saboda ji da tayi wani cikin samain nen yace, "Kai!Kai! yau ga mutuniyarka a gari ashc ta dawo, walalhi wannan karon kada ka yarda ta sille maka baka gabatarda kanka garcta ba idan kuma ka tsaya kallon ruwa to kwado zai yi maka kafa wallahi". Wadannan kalmanne suka sa Muneeba karawa kafarta kaimi tana ji Murja na tsokanarta "Kinji ko Muneeba da ke suke gasu nan ma sun biyo mu". Ashe kuwa da gaske sun biyo su, sai takun sawunsu ta ji a bayansu suna magana. "Salamu Alaikum, don Ailah Muneeba ki tsaya ba wani abu ba ne izini zaku bamu sai mu iskoki gida". Takaici ya cika cikin Muneeba na yadda aka yi har sunanta ya zauna radam a bakin wannar saurayin, lallai yayi bincikene akanta har ya san sunanta. Ta juyo a fusace rantaa басе tace, "Don Allah Malam ka yi hakuri ba ma hira da samari ko gidan kuka biyomu balle akan hanya". Tana gama fadin haka ta kara sauri. Ganin Murja zata fita sauki shi yasa suka maida akalar maiyarsu ga Murjan yace, "Ranki ya dade ki rokar mana ita ta dan sauraremu, wallahi aboki na gashi nan Badaru dan wajen Hakimi shine ke tsananin sonta 47 WATA KUSAN 1 Ranmatu Hassan Zaria wancan karon da ya ganta kafin yaje gida aka се ta koma makarantar kwana haka na lallashcshi da kyar ya hakura, shine yau kwatsam muka ganta kinga ai ba zamu yi saken da zatą sake subuce masaba, kinga itaba zama take a garin ba, shimaba nan yake zama ba, gara tunda yau Allah yasa ya ganta ta dan saurareshi". Murja tace, "Eh to żata saurareshi amma ba a titi ba hakan ba tarbiyyarmu bace dukanku tunda kunsan gida kuna iya zauwa anjima, ni na ari bakinta na ci mata albasa”. Sai a lokacin Badarun da kansa yayi magana, ""Shike nan mun gode zamu zo gidan anjima, sai ki gaya mata, kuma don Allah a isar mini da sakon gaisuwa kafin inzo”. Da gudu-gudu Murja ta kamo Muneeba, saboda tafiyarta tayi ta barta. Suna haduwa tace, “Amma dai kin zubar da ajinki, meye na wani tsayawa kina sauraron maza a titi kinsan kuma an hanamu, zan gayawa Yaya Mujaheed zaki yi masa bayani wallahi ba ruwa na”. ta riko hannun ta ta na cewa, "Haba kawalli kada mu yi haka da ke, nima bada son raina na tsaya ba, jin sun cе don Allah shi yasa na sauraresu sannan ga uban kwarjini da shi Badarun ke da shi, kema da kin tsaya kwarjinin zaiyi miki harki saurare shi". Tace, 48 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "Ni bai isa ya yaudareni da kwarjininsa ba dama haka na ji labarinsa yaudara 'yan mata gare shi ko can inda yake aiki ance mata yake tarawa a gidan sa". Murja tace, "Kai Muneeba zato dai zunubi ne, sannan ba kyau kayi mummunan zato ga dan uwanka musulmi kuma nace idan ba zaka fadi alkhairi ba to kayi shiru, ke kuwa duk inakika samu wadannan labarin?"tace, "Ai kuma na daina magana akansa kada in hanaki sonshi, babu ruwana idan kina sonshi kada kiji haushi na akan ina aibunta miki masoyi". Tace, "Kina dai aibunta masoyinki, ni 'yar aike се zuwa gareki, yace yana nan zuwa gida anjima sai ki san yadda zaki yi da shi idan ya zo, ni babu ruwana". Muneeba tace, "Za kuwa kiga na turo miki shi tunda ke kikajajibo shi". Da ire-iren hirarrakin har suka canza hanya don kuwa Muneeba ta ce ba zata bi hanyar ba, gara su bi hanya mai nisa, sannu ai bata hana zuwa inda za aje sai dai a dade ba a jeba. Da daddare bayan sallar isha kawai sai ga dan aike yayi sallama a tsakar gidansu Muneeba, abinka ga lokaci na zafi duk jama'ar gidan suna 49 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria tsakar gida wasu akwanece bisa tabarma wasu a zazzaune ana hira. Yaron yace, "Anee ana kiran Munceba a kofargida". Matan gidan sukanuna masa kofar dakinsu Munceba inda take zaune kan tabarma da fitilla a gabanta tanakarat Yaron ya sake maimaita mata aiken da aka yo nasa tace, "Kaje kace tayi bacci".Yaron ya juya ya tafi. Matan gidan sai aka soma 'yan tsegungumi su a tunaninsu bataji yo hirarasu, "Af ai daman a san za a rina, yarinya na tinkahon da ilimin boko ne zata saurari samarin garin nan, ai wuce nan miji sa a garin Gombe ko Bauchi ko Yola". Abokiyar hirar ta ce, "Su ma samarin basu da zuciya ne, yarinyar nan duk zuwa sai sun aiko don kiranta bata taba fiita gurin kowa ba amma basa dandara gobe ma zaki jı kirar wani, wahala bata ishe suba tunda tta natsu" Sai ga yaron ya sake dawowa wann karon da Katuwar leda a hannunsa fara sol riai tambarin shagunan kas ashen ketare, kai tsayə inda aka nuna masa dazu ya zuce bayań saliama da yayi. ya aje kayan a gaban Muneeba yace, "Wa gashi iden ta tahi baccin a bata akwai takarla a ciki wai ta karanta". Munecha ta ja tsaki tace, "dauka ka mayar masa ka ce wai ya 50 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zara rike abinsa ta gode". Matan gidan kwa duk sun zuba idanu suna son ganin ko M.uneeba za ta amshi kayan alhalin ta ki fito sai suka ji taсс amayar, har yaron ya dauki ledar sai mariya ta yi karaf ta ce, "Idan baki so mu ki bamu, wa ke maida alheri in ba shaidan ba, in banda abinki wannan da gani ko wanene dan boko ne irinki kuma yana da maiko ko da ganin wannan ledar kasan ta fito ne daga gidan mala'u. kai ajc ka tafi ka ce angode" Yaro ya aje ka ledar a gaban Muneeba ya wuce ya tafi abinsa. Innarsu Munecba tana daga daki tana jin wainar da ake toyawa. Larai ta gaza hakuri ganin Munneeba tayi biris da kayan bata ko kallesu ba balle ta taba. tace, "Muneeba ki duba abin da ke ciki mana idan akwai na lasawa a bamu namu rabon dama muna zaune baki yayi tsami kwadayi ya addabemu, mun rasa abin lasawa sai ga tsuntsu daga sama gasasshe kinga ai ba maki ci ba". Abin yaba Muneeba takaici da dariya, a zuciyarta tana ta addu'ar Allah yasa babu abin ci a ledar ta ga ta karyar kwadayi. Ranta baisoba ta taba ledar tunda ita bata yiniyar ta6aledar tunda itaba tayi niyyar taba komai nasa ba don ba sonsa take yi ba, idan ya dawo maida masa kayansa zata yi. Ta duba 51 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria kayan shafa ne sai wasu biskita da chakulet masu tsada su ta diba ta kai musu suna amsa suka soma kasafi, nan da nan kika ji santi na tashi. Ita dai Muneeba ta wuce daki da ledar, ta zayyana wa Innarsu wanda ya aiko mata da su kuma ta bayyana mata ita fa bata sonsa sai Innan tace to aje kayan har babansu ya shigo sai suyi masa bayani Sai da safe sannan Innarsu ta yi wa Babansu bayanin komai. Shima tunda yaji bayanin Muneeba da dalilinta sai shima ya goya mata baya don ba zai matsa mata don ta so Badaru ba duk da irin dukiyar da suke da ita, kuma yace tun kafin maganar ta girmama zai yi nasa bincinken akan Badarun. Kwana biyu tsakani Badarun bai sake zuwa ba tunda aka yi haka, sai ga dan aike daga gidan hakimi wai yana neman Mahaifin Muneeba. Sakon na isa gareshi yasan neman ba akan komai bane sai akan maganar Badaru da Muneeba, shi kuma tunda yarinya tace ba ta so to ba zai yi mata dole ba, kuma ko zaiyi mata auren son ransa ko ta so hakika zai duba miji na gari ne ya bata shi ba irin Badaru ba wanda ya rayu a turai yana karatu idanunsa a bude suke, sannan yayi tsananin bincike ya gano a can Kadunan ma da yake aiki banda neman mata har 52 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria ruwan barasa an tabbatar masa yana slaa, shi yasa ya sha alwashin dukiya da girmar, hakimi da yake gani ba zai rude shi ya kai diyarsa inda zaman aure ba zai yi mata dadi ba, in da za a wulakanta rayuwarta, dama dein uwansa ne Adnan kowa yanayabon halay'ensa zahiri da badini, toko da shine zai iya tirsasa Muneeba ta amince da auransa tunda ya sami shaida ta gari kuma mutum na gari shi ake ba aure. Baiyi kasa a gwiwa ba ya isa gidan Hakimi, aka yi masa iso gurin hakimi suka keбс su biyu a babban falonsa na shakatawa inda yake saukar muhimman bakinsa. Bayan gaishe-gaishe da tambaye-tambaye akan hidimar iyali da aikin gona sai hakimi ya aika kiran Malam Auwalu. "Daman na kiraka ne akan wani muhimmin al'amari da ya taso dangane da 'ya'yanmu, shì dana ne yaga diyarka yace yana so kuma so bana wasaba aurenta zaiyi, nayi murna kwarai da ya nemi aure a gidan dadttako gidan mutunci da ya gayamini shine nace to ya dakata bana son rawar jiki ya bari in nemi iyayenta inji in basu yi mata mijiba, don kada ayi nema cikin nema". Ganin girma ta martaba hakimi da jama'a keyi yasa Mal. Auwalu sai da ya yi dan jinkiri yana nazarin irin kyawawan kalaman da zai WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria gayawa hakimi ba tare da ya ji zafin ya nemawar dansa aure ba a bashiba. Ya gyara zamansa yace, "Gaskiya naji dadi da har babban mutúm da ake ganin Kimarsa mai nagarta irinka zainemi hada zuri'a da mu, wannan abin farin ciki ne, sai dai wani hanzari ba gudu ba 'yan uwana suu riga sun shaida mini sun fidda mata miji, ża ayi bikin sauran 'yan uwanta to har da nata za a hada amma Allah ya sani zan so mu kulla zumuncin auratayya a tsakanin 'ya'yanmú, sai dai hakan ba zai yiwu ba a dalilin alkawarin da 'yan uwana suka yina aurar da ita, ni kuma binsu nake sau da kafa, amma zan turo Malam Adamu ya zo yayi maka karin bayani tun da komai su kė zartarswa magana tana hannunsu". Hakimi yace, "To shike nan ka turo mini shi, zamu tattauna, babu matsala da ma abinda nake gudu kenan kada yaie y. nemeta alhalin anyi mata miji kaga an aka shari'ar Allah anyi ba dai-dai ba, shi yasa za a nemi aure ya kamata a fara sanar da iyzyen yarinya ga den jin ko anyi mata mji, idan ba a yi mataba saisu ba da izinin a ci gaba da nema,haka ake so". Sun karasa tattaunawa sannan suka sallami juna Mal. Auwalu ya koma gida yana komawayasami 'yan uwansa guda biyua shaida musu halin da ake ciki, sannan ya 54 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria gaya musu abinda ya riga ya gayawa hakimi. Malam Adamu yace, Kayi dai dai abin da ka fada nima idan naje haka zan gaya masa, don ba zamu dauki 'yarmu mu ba dansa ba tunda mun san halayensa sarai jama'ar gari má saisu zage mu ace kwadayi ne yasa muka ba yaron aure alhali kowa ya san halinsa, idan aka yi auren kuma wani abu ya faru da ita ayi ta yo mana Allah ya kara, tomaganin kada a yi ma kada a fara. Bari ma inje gidan hakimin".Ya shura takalmansa ya fice daga zaurcn. Maganar dai gudadayace hakimi yaji anyiwa yarinya miji kuma dan uwanta ne, jin haka yasa hakimi ya cc babu komai zaiyiwa dansa bayani tunda anyi wa yarinya miji sai yayi hakuri ya nemi wata. Sun sakc zama 'yan uwan guda uku malamAuwalu, Malam Audu da Malam Adamu suna sake tatatunawa Malam Adam yace, "To yanzu an gama da maganar dan wajen hakimi saboda haka aurensu Lawisa da za ayi to za a hada da nata ayi". Mal. Auwalu yacc, "Har da nata?" to karatunta fa? Da wa za a hada ta?" duk suka zuba masa ido sabɔda jin wadannan tambayoyi da ya jero musu guda uku, WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zeria wadanda yanzu kuwa zai ji amsar su. Malam Adamu yасe, "Kwarai da nata za a hada, karatu kuma tunda kana so itama tana so to zata ci gaba, shi yasa mа wanda zamu hada ta da shi dan boko ne irinta kuma dan uwanta ne dan wajen Goggonta Kanwarmu Rahin wato Mujcebu, hadın ya yi maka ko kana da ja?" ya girgiza kai yaçç, anlsil "Wallahi ni bani da ja a duk hukunci da zaku yanke a kan iyalaina Allah ya sanya albarka yasa ayi da mu". Suka amsa da Ameen Malam Audu yacc. SSIHLCD "Abin da yasamuka zaba mata Mujcebu sabida mun ga dacewar hadin nasu ne, tunda tayi ilimin boko ba zamu tauyc ta mu bata mijin da baiyi boko ba sannan kowa ya sani Mujccbu ya ro ne na kwarai mai kyakkywan dabi'u ga natsuwa uwa uba yana riko da addininsa sosai ga girmama nagaba da shi, ita kanta Munceban mun tabbata ba zata ki wannan hafin ba kumainsha Allahu aurensu zai zamo mai albarka". Mal. Adamu yaсс, "Yanuzu ma abari in tashi yaro yaje ya kira mana Rahin din, don mu shaida mata shima Mujccb zanje Gombe da kaina gobe in sanar masa ya fara ji daga bakina, a matsayi nana wan mahaifiyarsa uwa daya uba daya kuma kani da 56 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria muke 'ya'ya maza da ubansa kuma nine jagoran wannan aure haka duk zan karanta masa don ya Kara sanin muhimmancinmu a rayuwarsa Dunsu sun bada goyon baya fari bias dari. Malam Auwalu yana shiga gida ya kira Mahaifiyar Muneeba can uwan daki don kada suyi magana ajisu a tsakar gida tunda bai san a yadda zaa dauki al'amarinba, ya bayyana mata yadda sukayi da 'yan uwansa har da auren Munceban da za a hada da na 'yan uwanta da za ayi nan da kwana biyar masu zuwa. Inna ta jinjina kai cike da alhani ta ce "Amma kana ganin Yaya Rahin ba zata kawo matsalaa maganar auren nan ba, ka dai san niba dasawa muke ba, haka Munceba kullum cikin kyararta take yi wai ta dauko halin miskilanci irin nawa niban san me na tsarewa Yaya Rahin ba ko da yake ta ce na mallake mata dan uwa, ni kam banga mallakar da nayi maka ba tunda kai ke sani kai ke hana ni kuma in yi yadda kace, amma matar da ta mallake miji ai itace ke sa shi ya yi kuma dole sannan ta hana shi kumaya hanu dole, ni na san matsala ta a gurinta ba a jin fadanmu ni da kai bana yamadidi da kai in ce ka yi min kaza kayi min kaza, bata taba jin rigima ta kunnu a tsakanina da kai bashi yasa za a ce na mallake ka”. Ya yi ajiyar zuciiya yace, WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "Ki yi hakuri kuma ki kwantar da hankalinki, ki natsar wa da Munecba hankali kada ta sa damuwa ko da lana da wanda take so, tayi hakuri in sha Allah aurenta da Mujeebu ina hango alkhairi, Mujecbu halinsa mai kyau ne, kuma ya banbanta da sauran yara halinsa kyakkyawa ne abin son ko wace yarinya, ga tsafta gailimi duka guda biyu to meye matsalar aurensa?"tace, "Ni ban ce maka Mujeebu na da matsala, ni dama Yaya Rahin kawai nake ji, amma ba komai zamu mikawa Allah al'amarinmu ya kawo mana mafita mai kyau, kuma yasa hakan da ka kulla ya zaio alkhairi". Da yamma sai ga Goggo Rahin ta zo kiran da Yayanta Mal. Adamu yayi mata suka kebe su hudu a turakar Mal. Adamu, bayan gaishe-gaishe ne ya koro mata jawabi tun daga nemanwa Badaru aurenta da hakimi yayi da inats lar da yasa suka ki bada goyon bayan suba Kadurun aure itama tace sam ba zai yiwu a ba Badaru aure baya tafi da ita yayi ta wulakanta rayuwaita, gara da suka yi hikimar hana shi: Daga Karshe suka zayyane mata hukuncin da suka yanke wanda kuma babu mai tada wannan hadi da suka yina hada auren Mujeeb da Munecoa, ai kuwa Rahin ta tuma tayi tsallen WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria albarka tace sama bata san wannan hadi ba ta yarda da shi ba. Wallahi Yaya ban amince ba, kuma ba ku yi min adalci ba, ai kafin ku zartar da hukunci sai a nemi shawarata, bazan yardaba uwarta ta mallake mini dan uwa gashi nan bashi da katabus sai abin da ta gindaya masa sannan ace Munceba mai hali iri na uwarta ta auri Mujecbu shike nan burin ta a kansa ya tarwatse shima mallake shi za ayi". Malam Adamu ransa ya 6aci yace, "Kinga Rahin ba neman yardarki muke yi ba, mun kira ki ne kawai don mu sanar da ke kuma mu fita hakkin ki kada ki ji daura aure kice anyi miki ba daidai ba, kuma maganar mallaka da kike yi, mu dai ke muke jin kina kuzuzuzta an mallake Auwalu ke da ba kya zaune tare da shi, amma mu da muke zaune da shi ai mun san irin ladabi da biyayyar da matarsa keyi masa, matan rufin asiri ai itace mata, to ita ma 'yarmu haka muke fatan tazamo a gidan mijinta, ko kinaso ko bakya so nan da kwana biyar za ayi bikinsu". Таce, "Gaskiya ba zai yiwu ba, kun dai san yaron nan karatu yake yi, da wane zaiji da kujiba kujiban karatu ko da nauyin iyali da za a dora masa. Ni burina sai yagama karatu ya sami aiki sannan zai 59 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria yi aure kuma ni da 'yar aminiyata Hajiya Harirа zan hadasu tun tuni muka yi magana da ita yarinya an gaya mata ita ma karatu take yi shima an gaya masa to na mene ne za a gwada mini fin Karti a rusa mini nawa tsarin da nayi". Mal. Audu ya harzuka yace, "Isa da mallaka kyauta da dan kishiya, shi yasa muka yi miki haka, saboda mun isa da ke a matsayin yayyinki uwa daya nba daya, shi kuma da naki ne ke kika haifi abinki amma baki isa muna raye kiyi iko da shi ba mu ne dai kuma 'yan uwan ubansa 'ya'ya maza muke sai ki gaya mana wanda ya isa yayi mana iko da dan dan uwanmu. Aurc ne mun kulla babu mai tada shi, 'ya'yanmu muna shaidar dabi'unsu duka su biyun babu wanda zaiyi mana musu ko tawaye kuma da kike maganar zaku hada auren su shi da 'yar aminiyarki Hajiya Harira ai Wata Kusan, tafi wata duk amintarki da ta bata yi ya dan uwanki da kika sha nono dan uwa ba, kuma duk tsiyarki da amintar da kukewa juna idan aka tsaga jikinki ba aza ga jinin Harira ba, haka nan idan aka tsaga jikinta ba za ga jininki ba, kc kuwa da dan uwan ki da 'y'yanku jininku iri daya ne kinga kuwa ruwa bii isa yace ya kai kaurin jini ba balle yayi takara da shi su yi gogayya. Jinin dan uwanki Auwalu wato 60 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Muneeba ta fi diyar aminiyarki Harira ko kinki ko kinso shasha wadda ba ta san dadin zumunci basai son ranta". Nan da nan Rahin taballe da kuka ta shiga hayagaga bufan kan karya abinda ya janyo hankalin duk jama'ar gidan suka yi cirki-cirko a tsakar gida suna jin abin da take fada. Larai ta dubi Mariya tace, "Kinji wata sabuwa kuma auren Munceba da Mujceb 'yar boko da dan boko, sannan nan da kwana biyar za a hada da aurensu Lawisa ba shiri ba sanarwa". Mariya ta cc, "Sai a kaita da biro da littafai da ba tsiyar da uwar ta tanada ai kinga yau sai boko yayi musu rana". Asabe ta tsoma musu baki duk da ba ta shiga shirgin gulmace-gulmacensu ta ce, "Ai kuma kun san 'yan uwanta masu zuciyar yi ne kun san tuwon dan dangi baya ruwa wannan ya miko gari wannan ya miko sai ku gaya tuka kákkauran tuwo". Larai ta ce, "Sai ki fito fili ki gaya manaba mu da dangi tunda ita tana da dangi da yawa har a birni, 'yan birnin marowata maga uwar da za su tsinana matahar a sammiki ke 'yar kanzagi". Mariya ma ta mashe ta fara jero nata zafafan kalaman ganin ida ta ci gaba da tanka musu za su hautsine ga gidan dama a hautsine yake sai ta kyale su ta 61 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria wuoe dasinta ta barsu suka ci gaba da raddi akan maganar da ta aje musu. Iaka aka rabu baram-baram dutse a hananun riga tsakanin Rahin da 'yan uwanta. Muneeba ma tana daki tana aikin kuka a dalilin a da ta yi Gagonta tace, sam bata yarda da aurenba seine itama take kuka akan bata so nama gara a hakura da wannan hadi, amma da farko da aka gaya mata tare da nasihar da Innarta tay mata ya natsar da mata da zuciya ta yi na'am da hadir iyayen nata amma yanzu jin kalaman Guggo yasa ta ji sam bata son hadin auren nasu. Babanta ya shigo shima ya dasa nasa lallashin ya totsirayeta da bata tabbacin idan an sami matsala aa Guggonta to tabbaci hakika ba za asami matsala da Mujeebu ba din ba ya iya mušu da suba, ba zai taba kyamatár hadin auren suba Washe gari saura kwana hudu daura auren, Mal. Adamu ya shirya ya tafi Gombe gidan da Mecb ke zama daga nan yake tafiya makaran, guan aninir mahaifinsa ne, da suka taso ture a yara a Duk harkar kasuwanci ta dawo da shi Gombe har yayı gidan kansa yake zaunc da iyaiansa. A bakin Alh. Sani (maigidan) ya sami labarin Mujecbu sun tafi (excusion can jahar Lagos da oyo yau kyannansu daya da tafiya za 52 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria su yi kwana biyar. da Mal. Adamu yayi tunani sai ya ga sai ranar daura auren zai dawo. Ya bayyanawa Alh. Sani abinda ke faruwa ya Kara da cewa, "Shine na zo in sanar masa da kaina inyi masa bayaniyadda zaiyi kyakkyawar fahimta ga faruwar al'amarin sabanin yadda idan ya je yiwa al'amarin bahaguwar fahimta muddin uwarsa ta fara shaida masa al'amarin tundata nuna rashin amincewarta ita tafi son ya auri bare 'yar aminiyarta, ni ban taba gani inda ka so na waje fiye da dan uwanka ba duk kuwa irin amintar da kake da mutum ai Wata Kusan tafi wata ko yaya ne balle kusan jini ai ba wasa ba ne". Alh. Sani yace, "Ai su mata al'amarinsu yana da bar. mamaki suna da zumunta ta ziyarar dan uwa, am ma rikon amanar zumunta har cikin cuci ai sai namiji, in banda abin Rahin ai jini ya daranma ruwa nesa ba kusa ba, ni ma nan ai na so hada shi da diyata ban gaya wa kowa ba a zuciyata kawai nake wannan sake-saken saboda kyawawan halayen Mujcebun, yaro ne na gari mai addini gashi da neman na kansa, yanzu haka duk da karatu yake yi amma bai hana shi neman kudi ba, sana'a yake yi a garin nan ni na kara masa karfin gwiwa don ya tallafi kansa da mahaifinyarsa da kannensa tunda shine na miji babba. Allah ya 63 WATA KUSAN 1 Rehmatu Hassan Zaria sanya alheri zanyi Kokarin inzo in halarei faura auren shi kuma da ya dawo zan turo shi nima anan zan fara yi masa bayani. Alh. Sani ya tashi ya shiga can eikin dakinsaba jimawakadan ya fito da kudi a hannunsa ya mikawa Mal. Adamu sannan yаce, "Gawannan na biya wa dana sadaki duk da ban san me kuka yanke ba, naira dubu talatin ne". malamAdamu ya shiga zuba godiya yace, "Mun gode Alhaji Allah ya saka da alkhairi ya Kara budi. sadaki dama mu ne zamu ba da, kuma idan aka daura aure ba a lokacin za a tare ba tunda abin ya zo a kurarren, lokaci, zamu gyara masa nan cikin gidan da mahaifinyarsa takc, mu fidda masa sasansa a cikin gidan su fara zama tudan shi ba zama yake ba nan gaba sai ayi tunanin abin yi". Alh. Sani yace, "Wannan duk babu matsala, Allah dai ya dawo da shi lafiya". Yacc "Amcen amen. Mustapha yana zuwa ya sami labarin abinda ke faruwa, ya yimurna

Chapter 3 of 11