Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 11
suke cushe da jin haushin Munceba da 'yan kanninta guda biyu da su ma duk an sa su a makarantar bokon. Har suna aka sa musu a gidan wai 'yan fi'ili 'yan bokoko a wuta, tun suna kulawa har sun daina kulawa sun maida hankali ga karatunsu. Ita ma Innarsu ta daina doramusu talla Muspha ya hana sai dai Innartana 'yan kulle-kulle a zo a siya a gida, shi kuma yana yin duk sana'ar da ta zo masa yana taimakawa iyayensa don dai kada kannensa su yi talla. 23 WATA KL SAN 1 *** Rahmatu Hassan Zaria *** *** Jarabawar su Munceba ta fito, Allah cikin ikonsa Muneeba ta sabu ci gaba da karatu a Makarantar 'yan mata ta garin Gombe. Nan ma anyi tirkatirka da iyayensu Muneeba maza kafin su yarda suka barta ta wuce aji daya na karamar sakandirc, su a cewarsu lalacewar ta yi yawa da har sai ta da Murja duk sun sami gurbin karatu zata dauki diyayrta mace ka kaita wani gari makarantar kwana alhalin ga makaranta anan ta sakandare a gainsu na Dukku me zai sa har sai ta tafi cikin garin Gombe. Mustapha ya hana kansa sakat saboda saye-sayen da za ayi wa Muneeba na tafiya, haka nan ma Babansu shimaba shi zaune ba shi tsaye don ganin komai ya kammala tunda a 'yan uwansa ba mai taimaka masa da kwandala a cewarsu shi yasa kansa. Mutum daya tasan zai iya taimaka musu a halin karatunta a 'yan uwa da yana da rai Baba Aminu wato mahaifin Mujeeb saboda shima yana bada goyon bayan karatun 'ya'ya mata haka Muiceb da ace yagama karatu ya fara aiki tabbas zai taimaka tunda a cewarsa yana alfahari da kanwarsa ke karatun boko. 24 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Ranarda za su tafi saiga Murja ta zo da safe ta iske Munecba na ta shirya kavan tafiyarta, ta aje wata katuwar leda a gaban Mane ban tace, "Gashi nan inji Abbanmu ki Kara ba yawa. Munccba ta jawo ledar tana dubawa tacc, "Kai, kai ina Inna ta zo ta ga abin arziki". Sai ga Innar ta shigo rikeda buta daga bayi ta fito tace, "Me ye zan gani ake kira na?" tace, "Kayan provision ne inji Hedimasta wai in Kara Inna dubi masu yawa". Inna ta kai dubanta ga murja ta ce, "A'a Murja ce sannu da zuwa har tafiyar ta tashi ne?" ta risina ta gaida Innar sannan ta ce, "A'a ba yanzu zamu tafi ba, sai anyi sallar azahar zamu biyo ta nan mu dauketa a motar Abba, Yaya Mujahced ne zai kaimu naji yace ma har da Yaya Mustapha za su kaimu". Inna ta zauna ta soma duba tulin kayan masarufin tana zuba godiya da sa albarka. Da Murja zata tafi ta bata tukwici wanda da kyar ta ansa tace ta yiwa Abbansu godioya sannan ta ce itama tananan zuwa da daddare yi masa godiya na dawainiyar da yake yi, ban da wahalar nemo adimishon ga kuma sayayya Allah ya bi ya shi. Muneeba ta raka Murja, ta dawo taji gungun matan gidan suna ya da magana WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "Wannan dawainiya hala kamu yake wa dansa, don naga shi ma dan kullum yana gidan nan sai ya shige har kuryar faki wai abokin Mustaha". Larai tace, "Uhm ba dai girin girin ba ta yi mai, Allah yasa kada ta badawa iyayenta kasa a ido sun dage 'yarsu sai ta yi boko ta je ta dauko musu abin kunya tunda gani suke yi 'ya'yanmu da suke talla sune lalatattu alhalin lalacewa an ce tana makarantar kwana", ita dai Munceba ba ta tsaya ci gaba da sauraronsuba ta wuce dakinsu ranta a Gace da Innarsu ta tambaycta dalilin Gacin ranta shine ta gaya mata, Innan tacс, "Kina son ki bata ranki a banza ne, in da sabo ya ci ace kin riga kin saba da halin da muke ciki a cikin gidan nan sara da sassaka kin taba ganin ya hana gamji tifo? Ko kin isa ki hana su su fadi abin da ransu ke so nc? to ki maida hankali ga abinda ke gaban ki, ki bar wandaba ya gabanki, wuce ki karasa shirinki, da izinin Allah zaku yi karatunki, lafiya ku gama lafiya kuma bamu ba waninmu ma sai ya amfana da iliminku in Allah ya yarda". Munceba ta turo baki gabaki ta cc, "Hum uh, ni Allah a matan gidan nan babu wadda zan ba kwandalata idan nayi ilimi na soma aiki ina samun kudi, har gara Inna Asabc 26 WATA KUSÁN 1 Rahmatu Hassan.Zaria ban taba jin ta aibunta niba a dalilin bokon nan'. Inna ta yi murmushi ta ce, "Yarinta manya ai a gidan an babu wanda zaki ki yiwa alheri ko ba ta dalilin boko baai duk wanda ya zalunce ka ko da da harshe ne to kada ka rama, kai ka biyo bayan zaluncin nasa da alkhairai sai ka gaya ji kunya hakan zai sa yayi na dama ko nan gababa zai zalunci wani ba, balla kai, balle ma dukansu iyayenki ne kada ki tsani kowa cikinsu ki kyautata musu tamkar yadda zaki kyautata mana". Bayan sallar azahar misalin karfe biyu da rabi motar Hedimasta fijo 504 tayi fakih a kofar gidansu Munceba, anan suka iske Mustapha yana tsaye da alamu isuwarsu yake jira Mujahced ya fito daga motar yaba Mustapha hannu suka gaisa yace, "Hala har kun gaji ruwan kale da gajiya, ni ai ku nake ji kada ku zo wannan ‘yar shirritar batagama shiri ba kasan mata tun suna kanana haka suke da nawa". Mujaheed yace, "Allah yasa dai baka rudamini itaba da fadanka don an san halinka, kuma ka san nima zan iya ramawa". Yace, "Ayi hakuri tuba nake na sanka mugu ne kai fadanka har ma da duka kake hadawa don mugunta".Suka kyalkyale da dariya.Gaba dayansu har da Mujaheed da Murja 27 WATA KUSAN 1 Fahmatu Hassan Zaria suka shiga cikin gidan har dakin Inna suka gaisheta, sannan suka fito da kayan Muneeba suka sa a mota, Inna ta dube ta tace, "Ki shiga kiyi wa mutan gidan nan sallama, kowa ki bita dakinta". Haka nan tayi faki daki tana musu sallama duk suka firfito yaransu da manya suna "Allah ya kiyaye ya bada sa'ar karatu", 'yan kananan yaran kuwa har jikin mota suka raka Munceba. Inna sai dada nasiha takeyi musu a bakin motar, Don Allah Murja kukula da kanku kuyi abinda ya kaiku banda wasa banda sakarci, duk wanda kuka ga baya maida hankali gurin karatu, kada ku rabe shi mutumin kirki da shi akc abota ba shashasha ba, ku dage ku ba marada kunya, Allah Ya yi muku albarka, Allah Ya kiyaye hanya, kada ku manta ku biyata gidan ku". Duk suka shige motar Inna tana saye har motar ta tashi. 'yan kananan yaran gidan sai ihu suke zasu bi Muneeba har da masu birgima sai daukansu aka yi aka shiga da su cikin gida don kada suce zasu bi sawun motar. Matan gidan sai hayaniya suke basu masan Inna ta shigo ba ita dai ta tsinkayi suna fadin, "Wannann karfin hali har ina da zan dauki da na in kai wani gari yin karıtu, shi karatun ma bana Allah ba, na neman duniya". 28 4 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "Yo ai abin. kama gasa ake da 'ya'yan Hedimasta, su ai ubansu dan boko ne babu aibu idan 'ya'yansa sun yi boko, kuma shi yana da albashin da zai dauki nauyin karatun 'ya'yansa. Su fa? Sai dai kame-kame da neman taimakon 'yan uwa". Wannan karon ai ba a nemai 'yan uwa ba bakigashi Hedimastan ba ne yayi mata hidimar makarantar nifa ina ganin alkawarin ba dansa aurenta suka yi shi yasa yake mata hidima ba gajiyawa". "Lałlai kam zamu ga inda tusa zata hura wuta, aure ai basu ke da ikon yiwa wani alkawarin ba 'yarsu su akwai manya dole sai abinda suka ce. Ni Allah ma yasa ta gama gwalangwason yin bokon su Malam su hada ta aure da wanda baiyi bokon ba sai in ga ta karyar tsiya".. ita kam Inna tana jinsu ta yi shigewar ta daki ta kama gyaran dakinta bayan ta kunna 'yar rediyonta tana sauraron wa'azin da ake yi a rediyo, ya fiye mata jin jirwayen da ake mata. A kofar gidan Goggo Rahim Mujahced yayi fakin din motar yace ta shiga ta fito Mustapha ma yace ba zai shiga ba don kada su dade. Mujceb ta fara gani a tsakar gida yana dauraye kayan Innar yana shanyawa. Ya amsa sallamar da tayi yacс, WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "A'a Muneeba sai Ina haka da Uniform?" Tacс, "Kar dai kaee ka manta na gaya maka yau zamu tafi makatrantar kwana a Gombe?" yace "Oh wallahi shaf na manta, wa zai kaiki? Kinga da nagama shiri da mun wace tare nima yau zan koma". Taсe, "Su Yaya Mustapha ne da Yaya Mujahced, sauri muke yi shi yasa basu shigo ba". Mujeeb ya bi bayanta suka shiga daki gurin Guggo. Ta dubi Muneeban a yatsinc ta ce, "Ke kuma ina zuwa haka da kayan makaranta *yan dingıl-dingil?" ta duka gaban Innan ta fara gaishe ta sannan tace", Na zo inyi miki sallama ne yau z2n wuce makarantar kwana a Gombe?" Gogga Rani ta iafa hannuwa ta ce, "Au shine zaki tafi makarantar kwana ban taба sani ba sai yau da zaki tafi, tunda ni talaka сe bani da abin da zan baki amma na san ai kinje gidan Guggonki Hinde tunda ita kunfi dasawa da ita", (Guggo Hinde kanwa ce itama gurin Guggo Rahin amma ha!i ya banbanta). Munceba tace, "Wallahi banje gidan ta ba gidanki kawai nazo". Muie b ransa baya son irin wadannan kananan maganganu na mahfiyarsa da irin halin da takc nunawa mahaifiyarsu Moeban da 'ya'yanta, Mustapha ne kawai suke dasawa, yayi saurin cewa, WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "Ayi hakuriGoggonmu, ke Munccba tashi ku tafi suna jiranki a waje". Ta mikcGoggon ta ce, "Ke da wa zaku tafí makarantar?" Mujccb yayi saurin taran numfashin Muneeba yace, "Ita da yarinyar wajen Hedimasta ne za kaisu", tacс, a "Oh! Hedimasta wato har yanzu bai gama dawainiya da ke ba, hala dai so yake aba dansa ke?" ita dai Muneeba shiru tayi, Guggo ko habar zaninta ta kwanto kudi, ta ciro gudar dari biyu ta mikawa Munceba tana cewa, "Gashi sai ki rike ba yawa kya sayi wani abu”.. Muneeba ta sa hannu biyu ta amsa don ta san idan tace gogonta barshi nan ma wani kalubalen za ta yi mata suka yi sallama, Mujecb ne ya rako ta har jikin mota, suka gaisa da su Mustapha sannan ya sallame su ya koma cikin gida. Daga nan suka yada zango a kofar gidan Goggo Hinde. Gaba dayansu suka shiga saboda sanin halin kirki irin nata, gata da barkwanci, idan tana wasa da su Munecba tamkar kakarsu ba kanwar ubansu ba, shi yasa har su Mujahced da Murja duk sun saba da ita. Suna shiga ta tarbesu da fara'a tana cewa, "Lale marhaban da 'ya'yana. Idan dai an ga Zahra lalai aga wata, mu kam zamu gidan hedimasta oyo mana musanye, a bamu muma mu 31 WATA KUSAN 1 Rhmatu Hassan Zaria ba da wallahi hadin nan yayi ko ya kuka ce 'ya'ya nan?" dukkansu suka yi dariya don sun gano me Goggon tasu kenufi. Mustapha yace, "Kai Goggonmu ke dai akwai ganewa wallahi", tace, "Ai nituni na gane ku sannan gashi kun dace, Allah ya tabbatar mana da alheri". Babu wanda ya iya cewa amen cikinsu a fili, amma a zuciyarsu duk sun amsa da amen. Bayan sun gaishcta ne Mustapha ke gaya mata yaune tafiyar Munceba da Murja makaranta shinc suka zo mata sallama, tace, "Yo tafiyar har ta zo ashe? To Allah ta bada sa'ar abinda za a je nema, ku dage kuyi karatu sosai banda wasa, tunda dai Allah ya taimakeku kun sami damar da ba ko wace diya bace iyayenta ke barinta ta yi nesa da su don zuwa karatun boko, gara mu su Murja mahaifinki danboko ne, ke kuwu Muneeba iyayenki a ruwansu da bokon diya mace, sai ku dage ku ba mara da kunya. Allah yayi muku albarka".Suka amsa da "Ameen".Dukansu. Nan da nan ta tashi ta dinga bankada kwanuka, ana dauko musu abin tsarabarmakaranta irinsu garin kwaki, dakakken kuli da yaji har da mai, daddawa na din tuwo, da ragowar dambun nama da tayi da sallah duk ta juye musu, tana cewa, 32 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "Ni wallahi ban dauka yau ne tafiyar ba, da nayi muku tanadi sosai, da har kilishi zansa ayi muku, amma ba komai idan za ajc y muku ziyara zan taho muku da shi, suka mike don tafiya suna ta yiwa guggo Hindu godiya, ha da naira dari biyar ta kara musu tace su sayi wani abu, cikin jimami da kewar juna suka yi sallama da ita Mujahced ya ja motar suka dau hanyar Gombe. Su Mujaheed sai da suka tsaya aka yi ivasu Muneeba komai da komai aka basu aji, kuma ya kasance ajinsu daya dakkinsu ma daya sannan suka yi sallama da su suka baro makaratar ta G.G.S.S.S Doma. Amma fa sun lallashe su sannan suka hakura da kukan sai da suka daukar musu alkawaarin idan za a zo ziyara (visiting) za su zo dukansu sannan suka barsu suka tafi. 2 WATA KUSAN 1 *** *** Rahmatu Hassan Zaria Hutun farko da su Munecba suka dawo, sai abin ya zama abin zunde a gidansu, a cewarsu wai ta yi kiba tayi kyau tamkar ba karatu taje ba. Hakan da taji ne yasa tasha alwashin idan an basu hutu nagaba ba zata zo Dukku ba, a Gombe zata tsaya gidan Inna Amina (Yayar Innarsu ne) ta yi hutunta a can, ba zata zo ba balle a dinga zundenta ana yayata tsegumminta. Ko Innarsu ta ga canji sosai a gurin Munceba, ta zama fes-fes da ita, ta kara kyau kuma tunda ta dawo ta daina barin dakin Innar su da kazanta, hatta gidansu da ke da girma haka take yin sam nako ta share shi fes-fes sai daisu sake fatawa ua gangan tunda suba za su share ba kuma ba za su sa 'ya'yansu su share ba, idan ma za s. share sai dai kowa ya kewaye harabar dakinsa ya share itama da ta dauki jimirin sharewa kullum sunce zatayi ta gaji ta daina don ta shekara sharewa bata isa ta hana su 6atawa ba, ke `ya'yansu su Gata, don woni lokacin tana gamawa za su tsiri shan rake su da 'ya'yansu gidan ya sake yin kaca-kaca sai dai idan sun gama ta sake sharewa, ba ya damunta. Haka nan bayin gidan guda biyu ne, na wanka da na ba haya, kullum sau biyu take wakewa, sabo da ta karanta illolin da kazantar 34 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria 9 bayi take haifarwa, shi yasa ko ta wanke idan zata yi wanka take sake wankewa. Nan ma sun dinga tsegumi kenan wai ta je makarata ta dawo da sabon salo da kafidiri, nan gaba idan karatun yayi nisa basu san ya zata dauke suba, tunda yanzu kowa kazami ne a gidan su ne kawai masu tsafta su 'yan boko. Su Muneeba sun shiga aji buyu a lokacin ne Mustapha da Mujahced suka sami gurbin karatu a jami'ar Gombe (Gombe state university. a lokacin shi kuma Mujecb ya shiga shekara ta biyu a (Feersl University Kashere) wadannan samari sun shiga jami'a da kafar dama saboda sun mida hankali sosai babu wasa. Mustapha kam dole ya maida hankali gurin karatun domin a hidimar karatunsa sai da babansu ya saida sanuwarsa guda daya sannan aka yi masa rigista da biyan kudin daki da sauran hidimu, duk dahedimasta ma ya yi musu hidima, shima wannan karon Malam Auwalu ya taka muhimmiyar rawa gani domin ya hana hedimasta takurawa kansayace komai sai ya yi musu tare da Mujaheed, shima da ya sai da shanuwar sai ya hidimta ma Mujaheed duk da ran hedimasta bai so aka sai da shanuwar ba. Tun hutun farko da Munecba ta zo akayi ta mata habaici a gidansu sai ya kasance idan 35 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria anyi hutu ta daina zuwa Dukku sai tana tsayawa a Gombe gidan Innarta har sau hutu yakusa Karewa sai ta zo ta kwana biyu a Dukku sannan a maida su makaranta. An ma ba ta sake zani ba saa aka ce ilimin da ta samu yasa ta guji asalinta ta guji iyayenta, tafi son zama gidan Inna Amina don mijinta mai kudi ne gidansu gidan jin dadi shi yasa take zama a gidan (kunji fa ita da gidan 'yar uwarta uwa daya uba daya, zumunci ya zama kwadayi. Su Mustapha a Gombe ba karatu kadai suke yi ba har da 'yan sana'o'i su kan taбa domin su ragewa iyayensu nauyin hidindimun da suke yi musu, duk da daishi Muajheed ya san bai yi sana'ar komai ba mahaifinsa zai iya daukar nauyin karatunsa, amma hakan da yayi shima mahaifın nasa zaiji dadi ya san cewa ya haifi dan da zai iya tallafa ma kansa, shi kumasai ya ji da sauran kanin Mujaheed din. Wannan hutun ma ana yi da Mujahced yazo daukarsu a mota ya dubi Munceba yace, "To 'yar gidan Inna Amina, Dukkun zamu wuce ko gidan Innar?" ta yi murm ushi tace, "Kaima ka sani cikin gari zan fara zuwa na zo Dukku daga baya".Ya dan rage murya cikin marairata yana dubata yace, 36 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zara "Ayi min alfarma wannan karon mu wuce Dukku muna bukatarki a can, ko kinfi son inyi ta kewarki?" ta sa hannu ta rufe fuska saboda kunyar kalamansa tana dan murmushi bata iya се masa uffan ba. ya juya bayan motar inda Mustapha da Murja suke yana duban Murja yace, "Kanwata please ki rokar min kawarki mu wuce Dukku", Mustapha yayi karaf yace, "Kai ka damu sai ta zauna a Dukku tunda tafi son zaman Gombe basai mu kaita ba", tawaigo a marairaice tace "Haba Yaya Mustapha kafifa kowa sanin matsalar zama na a Dukku, nima in ba dole bana fi son zama gani ga Inna da Baba", ya ja tsaki "Shirmen banza har sau nawa zan baki shawarar ki fita harkar al'amuran cikin gidanmu kuyi abin da ke gabanki". Tace, "Shike nana mu wuce Dukkun, amma gani nayi ku ma idan kun kaimu Gomben zaku dawo makaranta". Yace, "Eh, zamu dawo Gombe yau dinnan amma zamu sami hutu zuwa next week". Tace, "Shike nan mu wuce kawai”. Muneeba na shiga gida da jakar kayanta yaran gidan suka yo kanta da ihun murnar ganinta, ko ba komai yaran gidan na kaunarta 37 WAT A KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria suna kaunar kasancewa da ita ko don koya musu karatu da takeyi idan tana gari. Matan gidan duka suna zaune a inuwa bishiyar mangwaron da ke tsakar gidan suka yo mata caa da idanu suna cewa, "A'ah 'yan makaranta yau kuma an tuno da mutan Dukku ne, aimun dauka boko ya sa kin manta da asalinki". Batayi niyyar ce musu komai ba, sai wata zuciyar ta zugata cewa wani abu tace, "Haba dai ai dan halas baya maya asalinsa, can ma tasu sau na taho ba goben nan za ku gansu sun biyo ni". Ta wuce dakinsu ta barsu suna cі gaba da hirarsu. Da gudu ta fada cinyar Innarsu da ke zaune ta fada cinyar Innarsu da ke zaune, Innan ta tureta tana cewa, "Ni matsa kada ki karya min cinyoyi, ke sam ba kya girma da aikin shirme, ko su Maimuna (kanwarta ba za su dinga fado min a cinya ii haka ba". Ta jingina kanata a kafar Inna ta "Haba na wata hodu aban ganki ba dole inyi murna a tunda ke keziyara idan za a zo baky. bivo su, haba Inna kamar ba kya sona, Murja fa duk zuwa Mamansu sai ta zo". Inna ta ce; "Ita kika ce ni daban ita daban, kuma ai jama'a na zuwa miki, ko zuwan da Yaya 38 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Amina daiyalantakeyibakigodebane?" ta yisaurincewa, "Wallahina gode ni dai ina so ko su daya i zo kinji Innanmu?" tacc, "Zanzo wataran insha Allahu". Ta raba da jikin Innan ta rusuna ta gaisheta, sannan take tabayar Babansu tace, "Yanzu ya fita, ba a kofar gida da kun hadu". Mustapha yayi sallama ya shigo rike da hannun Kanensa Maimuna a autansu Baffa ya risina gaban Innarsu yagaisheta tace, a "Ku ma kun sani hutun kirismetin ne? yace, "Sai sati mai zuwa zamu samu, Malam ne yayi waya yace idan anyi musu hutu yau mu dauko su motar haya shine wani aboin mu ya bamu aron motarsa yace mu yi amfani da ita damu yi wahalar shiga motar haya, shine nake gaya miki muna dan taba kasuwanci da shi, amma shi iyayensa masu hali ne". Inna tace, "To Allah ya taimaka sai ku yi taka tsantsan da duniyar mutane, ku ci halas din da kuka samu kun nisanci haramun sai ku ga nemanku yayi albarka", yace, "Insha Allahu muna wannan kokarin", tace, "To Allah ya taimaka ya rufa mana asiri duniya da lahira", yace, "Ameen". Ya dubi Munecba ya dubi Innarsu yace, "Baki tambayi ya aka yi 'yar gidan Inna 39 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Amina ta fara zuwa muku hutu ba wannan karon?" tace, "Na san ai ba zai wuce ku kuka sa ta ba. tunda na san ta fi son yin hutunta a Gombe, can ga 'yan mata sa'o'inta 'yan biyu Khausar da Khairi, kuma ka san in basa a ba gobe zaka ga aiken Yaya Amina tun da ita ma ta fi son Muneeban ta je matahutu". Ilai kuwa washe gari misalin karfe goma na safe sai ga direba da su Khausar sun zo tafiya da Muneeba. Suna shigwa suka ganta a tsakar gidatana wanke-wanke. Khairi ta soma balla mata harara tana murmushi, sannan suka gaida matan gidan da ke ta aikace-aikacensu, suna isa gurin Muneeba Khair ta duma mata dundu tace, "Ai kin kyauta muna ta murnar dawowar ki jiya kawia sai muka ji shiru sai Yaya Mustapha ne ya bigo da yama yake gayawa Mama wai sun wuro dake gida, da ta ce a barki k fara yin hutun a anan in yaso sai ki karashe a Gombe mu muka ce bamu yardaba yau zamu zo nu dauko ki". Khairi tace, "Bari mu gaida Inna muzo mu taya ki aikin ko kya gama da wuri mu wuce". Suna gaida Inna suka aje gyaluluwansu duk da gayun da suka yona wani matiriyal ja mai kwalliyar goldin, sun yi kyau sosai, amma haka suka fita suka tayata wankc-wanke suna 40 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria gamawa, suka taya ta ta share tsakar gidan tas sannan suka shige ſakin Inna don ta hado kayanta, Inna ta ha fo musu dangin tsarabar yara su goruba, magarya, kurna da aduwa cike da babbar leda ta basu tace su kaiwa kannansu, Khairi taсс, "Inna muma fa muna sha za dai mu sammusu, Muma fa yaran ne Inna". Tace, "Shike nan tunda kun maida kanku yara, da-za a yi wata maganar kuma kuyi tsalle kuce ku ba yara ba ne tunda kun shiga ajin sakandire". Suka yi dariya. Ta sake miko musu wata ledar tace, "Ga wannan na 'ya'ya ne kuka ce da kubewa da daddawa". Khairi tayi saurin. mikawaKhausar ledar tace, "Allah ke zaki rike wannan daddawar, ni na rike tsarabar yara". Ita ma Khausar tacс "Ai baki isaba ni da ke waye babba?" Inna tace "Ka ga min yara da tsiya daddawar ba za ku rike ba, ina ce a but zeku saka, gayun banza da na wofi da zaayi miya 'da daddawar dukanku ci zaku yi ku arta na gayawa Yaya Aminan kwahadu da ita". Munceba ta sa hannu ta dau ledar ta сс, "Barni da su zamu je gaban maman za su yi mata bayani".Suka yi sallama da Innan suka fito suka yi sallama da mutanen gidan sannan suka tafi. 41 WTA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria Yaran gidan Inna Amina suna ganin anzo da Munceba suka cika falon gidan da ihu da tsallen marna. Inna Aamina da ke dakin baccinta ta fito doa ganin me ake yiwa murna sai tagansu Kankame da Muneeba suna murna tace, "liaba ko da naji wannan irin ihun murna, KiriKiri dai mun kwace musu 'ya ba dama taje gida sai ar. bi sawunta, to da malam yace shima yana son ganirta a kusa da shi ya zakuyi?" ta dubi su Khairi tana maganar, Khausar tace, "Ai mun san va zai hana mu tahowa da ita ba, da ya hara ma zamu ceke kika turo mu, ko yanzu ba mu iske shi a gida ba, amma Inna tace ba komai mu taho zata gaya masa idan ya dawo. Babban dan Inna Amina ya shigo Khairi da Khausar suka hada baki wajen gaisheshi "Ina kwana Yaya Sadiq?" yace, "Lafiya wai har kun dawo daga Dukkan? Ina Munceban?" "Gata nan a bayanka tana boycwa" ya juyo yan Harararta cikin sigar wasa yace, "Kc ko! Ke ko! Zan damke ki. Mun sakankance nan zaki fara zuwa shine kika gudu jiya na ci burin da kinzo zaki yi mini irin dambun nah sai haka na kwana da yunwa" ta marairaice murya tacc "Ayya Yayana kayi hakuri, yanzu sai in yi maka". Khairi tayi karaf tace, idan kin gama 42 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zara masa muma fan waken nan kin tuna? Inna Amina da ke gefe tana jinsu ace, "O.K wato kunje kun dauko tanesaboda kudinga damunta da yin girke-girke, ku ba za ku koya ba sai ku dameta, to ba zata yi banutu ta zo yi kada ki sake'in ganki a kicin duk wanda ya matsu da cinabinda ransa ke so to ya shiga kicin da kansa ko ku sa Laminde ta yi maku". Sadiq yace, "Mama kiyi hakuri ni nata nake so irin na Innarsu ne na mutan Dukku na Fulani, na Laminde kuwa bairin nasu ba ne shi yasa", Inna Amina taсс, "Allah dai yasa ka sam mata da ta ya girkegirken gargajiya, gaka dan boko amma bakacin cimar 'yan boko", yace, "Ai Mama a kauye zanje in auro mata wanda ta kware wajen iya dambu da tuwo, da bira bisko, ba ruwa na da cimar da bazata cika mini ciki ba, ni ban yarda da wannan gayun ba". Inna Amina tayi dariya ta wuce ta barsu: Ko hutawa bai bari Munceba ta yi baya jata kicin ta fara hada masa dambun. Su biyu a kicin yana taya ta aikin suna hira har ta kammala ta dora a wuta sannan suka dawo falo. Khausar da Khairi suka dube su suka yi dariya amma suna 6oye dariyar Sadiq yace, 43 WATA KUSAN 1 Rahmatu Hassan Zaria "Ku kuma wa kukewa dariva kamar taба66u?" Khairi ta gimtse dariyarta tace, "Khausar ce fa da ta dubeku waitace kamår mata da miji, yace. "Au kama ce ma aimun wace kama, gara tun yanzu ku aje girmanta da kuka yi matar yayanku ee. ku farace mata Yaya ko anti". Suka yi dariya har da tafawa. Khairi tace, "Bari inje in yadawaMma wannan farin labarin, dama Mama bata sani ba". Munecba ta yi farat tacе, "Don Allah Khairi kadaki je, in kuma kika je yau dinnan zan koma Dukku". Khausar tace, "Kin gani zaki ja mana ta gudu, ina ruwanki aka ce miki Maman bata gano su bane?" kallonsu kawai takcyi, Sadiq yace, "Yauwa ai na fi son Maman ta sani saboda ta je Dukku ta sanar

Chapter 2 of 11