nasan zai cinye na zuba a girkin.
Na rufe, na koma gefe, gabaɗaya ƙamshi ya cika kicin ɗin na tabbatar har gidan gabaɗaya ya karaɗe. Rabon da na ga sinadaran girki masu ƙamshi irin wadanccan sai a shekarun nan bayan ma haihuwar Farha.
Spice ɗin Amreesh spice's Kano duniya ne, domin suna saka armashin girki, suna mayar da ƙamshin gida ya zama na alfarma, haka nan ko baka jin yunwa ƙamshin zaɓaɓɓun spices na sanya ka ci abinci ba tare da ka farga ba.
Tabbas spices ɗin Amreesh ba shi da na biyu a wajena da wajen duk wanda ya taɓa tu'amalli da su. Ku nemi naku kai tsaye ta wannan lambar..09093510131 Tana aika ko ina a ƙasar nan. Ga mutanen jiharmu ta Kano da Katsina kuwa kakarku ta yanke sa'a domin takuce, ku hanzarta tuntubarta.
Dinner bowls ɗin da na san ana zuba masa abinci na dauko na zuba a ciki. Na shirya komai hatta coffee ɗin da yake sha duk dare sai da na shirya, hakan kuma bai hana na saka masa ruwa da lemo masu sanyi ba.
Na kinkima na nufi falon. yana hango ni ya zabura ya miƙe tare da faɗin "standstill! Ta ya ya zaki kinkimo wannan tray haka ba ki san illar da daukar abu mai nauyi yake yi muku ba?".
Ya ƙaraso ya karɓe. Maimakon ya dire a dainin tunda shine kusa da kicin sai kawai ya wuce cikin falon da alamu so yake yana ci muna hira, domin ni dai ban taɓa ganin ya ci abinci ba akan dainin ba, tunda muka zo.
Hakan kuma bai mini daɗi ba domin takura zan yi, so nake kuma na dawo da kallon baya domin an wuce ni da yawa, tunda CD plate ne a lokacin.
Muka zauna ya fara cin abincin cikin nutsuwa. Ya kalli yadda na mayar da hankalina kan kallon. Ya ce "To zo mu ci mana yayar Abida". Na yi murmushi tare da ce wa "Alhamdulillah tuni muka ci abinci bana tare da yunwa".
Ya ce "Jiya Abida ta siyar mini da jaridarta da maƙudan kudaɗe.
Zuciyata ta harba, na tabbatar labarin jaridar ya shafe ni ko da kuwa ba gabaɗaya ba.
*A lame skin & Beauty Zaki samu dukkan nau'in kayan oriflame da dukkan mayukan da suke gyara fata **07036662633*
Ya cigaba da cin abincin ba tare da ya fasa labarin ba.
Ni kuma na cigaba da kallon da ba fahimtar komai nake yi ba, tunda ya zauna. Jira nake ya kammala na kwashe kwanukan na tashi Abida mu yi ɗaki na kalla gobe idan Allah ya kai mu.
Sai da ya kammala ya yi gyatsa tare da hamdala. Ya ce "Sarauniyar shaibah ashe kin iya girki mai ɗanɗano na musamman?"
Bansan ya aka yi ba dariya ta ƙwace mini na ce "Kasan me yasa ka ji daɗinsa?"
Ya girgiza kai da azama ya ce "Faɗa mini sirrin, nasan dai Madam ma ba baya ba wajen shirya girki, amma dai ke da nasan ba shiga kicin kuke yi ba, na yi mamakin yadda kika yi shirya shi cikin nutsuwa, kuma cikin ƙanƙanin lokaci."
Da dariya sosai na ce "Sai dai ka yi hakuri domin ka ci majina haɗi da tasonon Bilki. Hakan ne ya sanya ya maka daɗi da yawa.
Ya maƙe kafada tare da miƙo mini tafin hannunsa na dama ya ce "Fato mini, ki ga idan ban lashe ba, bare wanda ya ɓace a cikin abinci wuta kuma ta ƙone dukkan bacteriya ɗin da zai yi illa."
Na yi ƙasa da kaina domin wani irin kallo yake yi mini da na kasa gasgatawa. Zuciyata ta harba da tsananin gaske domin gaskiyar magana Sahal kawai ke mini irin wannan kallon, domin ko yaya Faruku ban taɓa ganin ya yi hakan ba, duk da na tabbatar yana sona bilhakki, kawai bansan me ya hana shi zama serious ba.
Hakan da ya yi kuma shine yafi domin ba zan taɓa yarda na auri mai mata ba, bare matarsa azababbiya ta ɗauki karan tsana ta ɗora mini haka siddan matsalakan
Kunya ta rufar mini, jikina ya yi sanyi sosai domin har cikin zuciyata kallon ya taɓa ni ƙwarai da gaske.
Ya haifar mini da wasiwasi da sanyin jiki.
[8/24, 12:53 PM] Surayya Dee: *Wannan littafin na kudine pay* *1k via 2384876855*
*Surayya Ibrahim Zenith Bank.*
*A tura shaidar biya ta wadannan lambobin*
# 08032773332#
# 09069067488#
*Littafi na d'aya zai zo kyauta a WhatsAp yayin da na biyu da na uku zai zo a Telegram da arewa ga wadanda suka biya kudin karatu*.
*DINGISHIN KWADO*
*BY*
*SURAYYA DEE*
*MARUBUCIYAR*
*HALIN YAU*
*SABO DA KAZA*
*BAK'AR TA'ADA*.
*9*
*Lame.Ng Skin Beauty and wellness*
*Duk masu son sanin mayukan da azsu dace da skin dinsu to A lame skin Beauty and wellness zaku samu.*
*07036662633*
*Ga mutanen jamhuriyar Niger ku tura 500f ga wannan lambar+227 96451253*
Ya numfasa bayan ya janye hannunsa. Ya ce "Ashe kun sake hadewa da yaron da autar momi ta ce ƙiris ya rage ya shiga sahun zabiya".
Na kasa amsawa domin nasan babu labarin da yafi wannan tashe a cikin jaridar Abida.
Murya babu amo ya ce "Wai har iyayensu sun zo wajen baba babba?".
Na ɗaga masa kai dan ya gane tabbas zancen da ya ji a wajenta gaskiyar lamari ne.
Murya babu amo ya ce "Anya baki yi rushing ba kuwa Maigado?
Kina kallon kan ki a madubi kuwa? Ke fa gaba ɗaya ba'a miki zubin da ƙananun maza zasu same ki ba. Kin fi dacewa da zaratan maza musamman na jami'an tsaro".
Na kiɗeme ainun domin na kasa gane shima son nawa yake yi ne ko kuwa? Ni kuwa me zan yi da shi? Ban so yaya Usman ba a matsayin saurayi, sai shi? A ture ma yaya Faruku bai zama serious da maganarmu ba, amma kaf ya'yan baba babba shi kaɗai zan iya yin haƙuri na karbe shi a matsayin mijin aure ba dan komai ba sai dan tarin alherinsa da sadaukarwarsa, sannan ina jin zuciyata tana bugawa akansa. Ban da shi kuwa ban ga wanda zan iya yiwa alkunya ba a cikinsu, domin na tsani auren zumunci har zuciyata. Bare yaya Asad kwata kwata bai mini a matsayin mijin aure ba. Ya mini baƙi da yawa, ba shi da kyawu irin wanda nake so, sannan ƙarfinsa ya yi mini yawa, a lokacin sai nake ganin kuskure kaɗan zan yi masa ya targaɗa ni. Bare kuma ga matarsa da ta fini ilimi da gogewar rayuwa dan kuwa da kaɗan ya girme mata shekarar da suka yi aure ta kammala digirinta na farko a jami'ar Maiduguri. Yayin da shi kuma a lokacin shekararsa ɗaya da kammalawa.
*Gunis hijab ba na biyunta wajen kawo hijaban da suke da kyau da nagartar.*
*Gunis hijab ado cikin wayewar addini da rayuwa*
*08163761797*
Da suka yi aure ta yi digirinta na biyu a Ɗanfodiyo University Sokoto a lokacin yana aiki a Kebbi. Dan haka ya ajiyeta a Sokoto yake jele tsakanin Kebbi da Sokoto.
Yanzu kuma ƴaƴansu uku tana shirin dire masa na hudu. Waya kai ni cusa kaina a tsakaninsu ta riga da ta fini wayewa da dabara, shi ɗin ma kamar a hannunta yake.
Ganin na kiɗima ainun da furucinsa, watakila kuma ya hango ban taɓa tunanin zai iya ƙulla wata alaƙa ta daban da ni ba, sai ya yi maza ya ce "Wani abokinane matarsa ta rasu watanni uku shine ya ganki ya ce yana son ki, mutumin kirki ne yaransu huɗu suma".
Yana rufe baki na ce "Abokinka fa! Tabdi gaskiya he is too big for me. Ka bashi haƙuri kawai!
Na faɗa bayan na tsuke fuskata ainun .
A tausashe ya ce "Ai na bashi haƙuri tunda na samu labarin kin bada damar da aka je gaisuwa wajen baba babba ai magana ta ƙare".
Jin haka na ɗan saki fuska kaɗan.
Sai kuma ya ce "Amma shi kuma ya ce "Tunda ba ƙudin aure aka kai ba, ba kuma auren aka ɗaura miki ba, zai jarraba sa'arsa domin kin shiga zuciyarsa kin yi kane kane".
Yana rufe baki na ce "Wallahi ka ba shi haƙuri dan kuwa ba zan yarda na saurarere shi ba, tsoho da shi zai ce yana sona?"
Jikinsa ya yi sanyi ya ce "Shi ke nan zan ba shi haƙuri tunda na gane da gaske ba zai ci albarkacina ba. Dama gani na yi mutumin kirki ne, kuma zai yi miki adalci.
Wasa ma nake yi miki matarsa da ranta kawai tana Kano tana karatu ne, shi kuma so yake ya samu wacce zata zauna da shi a Kaduna."
Na ce "Ya bincika a wani wajen ka ga nima ai karatu nake yi a Zaria. Ko kuma ga Abida nan ko zasu shirya".
Da sauri ya ce "Ya ga Abidan amma bai nuna ita ba, dama kuma mai irin yanayinki yake so marar hatsaniya, wacce zata ɗauke kai game da sha'anin yara da matarsa."
Na yi kamar na ce "To ba zai samu ba indai sai ni, amma kwarjininsa ya sanya na kame bakina. Amma raina ya ɓaci akan me ba zai ba shi Abida ba sai ni zai liƙawa sa'ansa mai ya'ya da kuma matar da bata iya sarrafuwa. Domin da ya isa da ita ai da ta bar karatun ta zauna da shi, ko ta yi karatun a Kad poly. Ya miƙe tare da sakin ajiyar zuciya ya ce "Na gode Maigado, na gode da girki, yanzu me kike so na baki dan ki san na yaba da karamcinki?"
Na yi murmushi na ce "I need nothing, amma na roƙeka?"
Da sauri ya ce"Ina jin ki?"
"Ka daina ce mini Maigado. Su Baba kaɗai ke faɗa mini, yanzu tunda ka fara faɗa mini Abida da sauran jama'a sun ɗauka".
Ya murmusa ya ce "Ina takaicin sanar miki kin roƙi abun da bazan iya yi miki ba. Domin ina matuƙa jin dad'i idan na ce miki sarauniyar shaibah ko Maigado. Kinsan kuwa duk Bilki ai mai gadon zinari ce."
Na tsuke fuskata na ce "Ni kam bana so, yanzun nan mutanen gidanmu zasu riƙe su bar Bilkin".
"To ki dinga rubuta sunan duk wanda ya ƙira ki da Maigado idan na zo ki faɗa mini, zan yi miki maganinsa ko waye."
Na ce "Ba zaka daina ba ke nan yaya Asad?"
Kai tsaye ya ce "Ina jin daɗin sunan ne, sannan kuma ban iya yaudara ba, tunda bazan iya dainawa ba".
Ya fita waje ya dauko bandir ɗin 500 a motarsa ya ajiye mini akan cinyata, ya ce ki ajiye idan kin koma gida ki siyi abin da kike so, na gode sosai sarauniyar shaibah"
Ya wuce wajensa ba tare da ya sake ce wa uffan ba.
Na kashe kayan kallon na hau tashin Abida.
Abin mamaki ban wani sha wahalar tashinta ba. Mamakin da na yi ita ɗin mai nauyin barci ce, hakanan mai wahalar tashi ce a barci.
Kwanaki biyu Anty Maryam ta haihu still dai mace.
Hidima sosai maigidan ya yi, cikin farin ciki.
Gaba-daya Aysha babbar ɗiyarsu shekarunta takwas, amma an mata ƙanne hudu, shiyasa a jere suke fikon ƙadan kaɗan ne a tsakaninsu. Khadija a ce ta biyu, sai Saudat ta rasu bayan an haifi Hafsat, sai kuma Hafsat da ita aka yaye akan dole.
Duk inda na yi Hafcy nan take yi, hatta da mamanta ta tafi asibiti haihuwa a wajena ta kwana.
Ba kuma ta yi mini rikici ba duk kuwa da yadda take da maƙon uwa.
Kwana da yini kawai ta yi, aka sallamosu bayan an tantance lafiyarta da ta jinjira. Kusan ni ke hidimar gidan, yaya Munirah tana taya ni da shara ne da moping, amma girki da kula da yaran duk ni nake yi, wani zubin ta kan yi wanke wanke. Abida kuwa kullum a naɗe take wai bata da lafiya, sai dai kuma jinyar bata hanata cin abinci da wanka da kuma nazari a mujalloli da littafai daban daban.
Ganin hakan da masu gidan suka yi ya sanya suka raɗawa ɗiyarsu Bilkisu. Ranar da ya faɗa mana sunan diyar kenan Abida wiwi ta rushe masa da kuka hannuwa a ka, tana ce wa "Yaya Asad haka zaka yi mini, lillahi wa Rusulihi ai kowa yasan ba shiri kake yi da ita ba. Ni ce taka ita kuma ta yaya Faruku sai kuma ka tashi kasa sunanta alhalin ni yafi cancanta ka saka. Wanne iri kunyata ni ka yi haka?"
Da rarrashi ya ce "Kwantar da hankalinki autar momi! Ba matar Usman an ce ta kusa haihuwa ba, to ki ji a ranki matuƙar mace ta haifa to sunanta Maryam-Abida."
Ta sassauta kukan ta ce "Ni dai na fi so kai ka yi mini".
Ya ce "zan yi miki matukar ina raye. Sannan zan saka miki ma a gidan Usman a kusa, sai dai idan ba mace aka haifa ba.
Ta sassauta kukan, duk da so ta yi a canjawa yariyar ta amsa Abida. Yayin da Yaya Munirah ta saki gauron numfashi ta ce "Allah ya bani haƙuri!
Ya yi gajeriyar dariya tare da faɗin "Ke ai yayarsu ce Munee".
A kuɗin da ya bani na ƙirgi dubu ashirin na bashi na ce ya siyo ragon suna, sauran ya yi hidimar sunan Bilkisu. A lokacin ragon dubu goma na bada labari ne.
Ya karba da murmushi ya ce "Lallai kin iya karrama takwara sarauniyar shaibah!
Na sake ɗaukan dubu biyar na kaiwa Anti Maryam na ce idan ta fita ta siyowa little Bily ɗankunnen gold.
Murna da godiyar da ta yi ya sanya na gane ta iya mu'amala da mutane. Na sani tafi ƙarfin abin, sannan na tabbatar ɗan kunnen gold za'a siyo a sanya mata, tunda dukkan ya'yan uku ko wacce zagayayyen ɗan kunnen gold ne a kunneta.
Da matuƙar murna ta ce"Ai kuwa gobe zan fita da kudin nan zan siyo mata Bilki".
Tana mini godiya, nima, ina yi mata godiyar, domin na tabbatar da bata yarda ba, ba zai soma saka ma sunan nawa ba.
Cikin dare Abida ta tashe ni. Ta zuba mini ido ta ce "Bilkisu a ina kika samu kudaden da kike ta wadaƙa da su haka ne?
Nima na zuba mata nawa idanuwan na ce "satowa na yi Abida" Na bata amsa a kufule domin na gaji da abubuwan da take yi mini, tunda aka ce sunana aka sawa jinjira. Bayan haka kuma, na fara ƙosawa da yadda take yawan haiƙe mini tamkar dai itace gaba da ni.
Ta jijjga kai ta ce "Na rantse zaki san kin mini gatse. Ai na riga na gane shima sonki yake yi, duk hirar da kuka yi rannan da daddare idona biyu bakam na yi, duk ɓare ɓaren da kika yi na girki, da yadda ya kaikaice yake faɗin abokinsa na sonki duk na ji, kin sani, nima na sani ba wanda ya aiko shi, kansa yake ƙwanƙwasawa ƙofa. Na rantse gari na wayewa zaku ga tsiya sai na tsarawa matarsa komai na ga yadda za'a yi ta cigaba da yarda da ke, shima kuma na ga ƙarshen juya mini baya. Muna komawa gida kuwa zan siyarwa Baba ƙarami da yaya Faruku wannan labarin domin shine shafin farko kuma mafi tsada a jaridata."
Jikina ya yi sanyi sosai. A raunane na ce "Kada ki yi mini haka Abida! Kin ga haka matar yaya Faruku ta tsane ni, ki taimake ni, mu bar garin nan lafiya, ina kuma roƙon ki kada ki saka baba ƙarami a maganar nan kinsan dai yarda zai yi, alhalin kuma na turawa baba babba wanda nake so."
Ta ja tsaki mai tsananin gaske ta yi kwanciyarta bayan ta juya mini baya. Hakan da ta yi mini tabbacin ne na ba zata sake yin magana ba, domin haka ka'idarta take matuƙar ta kwanta ta juya baya to ta gama.
Kan dole na kwanta nima. Amma na shafe awanni barci bai sure ni ba.
Washegari na dinga yi mata shisshigi da azarbabin ta kula ni, ita kuma tana yauki gami da cin magani tare da muzuran yau ƙwai zai fashe. Idan ta ce zata fasa ƙwai din nan sai na ji cikina ya yamutse.
Kai Abida ta mini iyashege iyaka. Ban da rashin wayona ai da na barta ta fasa ƙwan tunda dai da ɗan uwanta zai tashi, kuma ma ai bata da garantin son nawa yake yi. Amma gabaɗaya ta kiɗima ni. Ta firgita ni, ganin na matsu ta huce ya sanya ta ce sai dai na sayi gatsen da na yi mata.
Jiki na rawa na zaro dubu biyu na ajiye a gabanta. Ta dauka tana juya su.
Tsawon lokaci ina dakon mai zata ce, sai da gama ja mini rai sannan ta ce "saura wata dubun dan ba zai yiwu na sarayar da wannan labarin cin amanar a dubu biyu ba. Ki dinga soyayya da mijinta a cikin gidanta ita kuma ta dauki dukkan yarda ta zuba miki. Komai Bilki, Bilki dai, gara na taimake ta na faɗa mata yadda kuke son nukurkusa ta da baƙin ciki."
Ban ce komai ba, na sake zaro dari biyar biyu na ajiye mata. Ta haɗesu waje guda ta buɗe tsakiyar Mujallarta ta zubasu.
A tsume ta ce "Shike nan ba zan faɗa mata ba. Amma ki tabbatar idan kika janye biyayyar da kike yi mini zan faɗa ne kawai, ki cigaba da kawo mini abincina d'aki."
Dad'i ya ratsa ni na ce "To Abida ƙanwar Bilki na gode!
Daidai lokacin yaya Munirah ta fito daga banɗaki da yake cikin ɗakin.
Ta ja tsaki ta ce "Bilki ki rabu ita da mana sai wahalar da ke take ta yi, komai zata yi, ki barta ta yi ɗin ai dai ba za'a kashe ki ba, sai gana miki azaba take yi ke kuma kina ta bin kanta."
Da azama na ce "a a yaya Munirah ai mun ma saito ta."
Yayin da Abida ta ja tsaki ta ce "To ta zuga ki kwabarki ta yi ruwa.".
Bojuwa herbs*
*Na ce kin taba shan sanyin flusher Dinmu?*
*Ko kinsan takanas ake kawo mini saiwowin da suke dagargaza dukkan sharrin sanyin da yake yiwa mara har ma da jijiya?*
*Ko kinsan sanyi flusher na kan gaba wajen garantin aikinsa a dukkan kayan da nake siyarwa?*
*Muna dafa ciccibin da yake ciki da mace, yake kyautata matuncin mace komin tsufanta*
*Kazalika muna sayar da saiwowin dahuwar idan ke kike so ki dafa da kanki*
*Muna dafa kazar sababi gangariya,mai saukar da niima da kuma hade mace*
*Akwia kuma saiwowin dahuwar idan zaki dafa da kanki*.
*Bridal package*
*Maijego package*
*Uwargida maijego*
*Bazawara package*
*Man ayun Chad da Marwa Wanda Babu algus, zumar silki kola*
*Hakkkn daka emergency na mussaman*
*Tightening set*
*Kudai ku tuntube ni dan samun naku kayan cikin aminci da rahusa, bana siyar da abin da bashi da inganci*
*A Dade ana yi sai gaskiya*
*08032773332 what'sapp only*
✍️
[8/24, 12:53 PM] Surayya Dee: *Wannan littafin na kudine pay* *1k via 2384876855*
*Surayya Ibrahim Zenith Bank.*
*A tura shaidar biya ta wadannan lambobin*
# 08032773332#
# 09069067488#
*Littafi na d'aya zai zo kyauta a WhatsAp yayin da na biyu da na uku zai zo a Telegram da arewa ga wadanda suka biya kudin karatu*.
*DINGISHIN KWADO*
*BY*
*SURAYYA DEE*
*MARUBUCIYAR*
*HALIN YAU*
*SABO DA KAZA*
*BAK'AR TA'ADA*
10
*Umm Aslan&Asalah Egyptian Items*
*Egyptian abayas*
*Egyptian nighties*.
*Bags and jewelries*
*Dukkansu a sassuakan farashi da ya dara na saura, don kuwa a can take zaune tana turosu Kano kaitsaye, daga nan sai a turawa kowa inda yake a fadin tarayyar Nigeria*
*Tuntubeta a wadannan lambobin dan ganin kayayyakinta na alfarma*.
# +201121544627
# +2349162662750
Ni dai na kame bakina dan nasan tana iya cewa ta fasa siyar mini da rikicin.
Dan haka kaffa kaffa na dinga yi da ita har muka fara shirin barin garin.
Ranar da zamu tafi Hafcy kuka har da bubburwar zata bini.
Su Khadijah ma duk sun yi lamo domin mun saba da su matuƙa gaya, direbansa ne ya tukomu a motarsa. Muka dawo gida lafiya dauke da tsaraba da kayayyaki masu yawa.
Murnar da iyayenmu suka yi da hidimar da yaya Asad ya yi damu ba kaɗan ba ce. Kwanaki biyu Baba Babba a cikin murna da kuzari yake yi. Motsi kaɗan zai ce "In sha Allah ko bama raye Abubakar zai jagoranci kula da dukkan alhalinmu . Barin idan Abida na rattaɓa masa irin kuttu da ta shaƙa a gidansa a dalilin fifita ni da yake a kansa. Sai ya sassauta murya ya ce "Hakan na sake alamtar da ni halin girma ne da shi, sannan zai cigaba da zama babba a tsakaninku muddin rai, ai itace ƙanwarsa ta tashin ƙiyama, kema yi maza ki ƙwace Sulaiman".
Ta kyaɓe baki haɗi da buɗe ƙofofin hancinta ta ce"Hmm Baba ke nan! Akwai something behind his caring to her! Definetly akwai wani abu a mind ɗinsa abun ya yi yawa. Bayan haka ni Yaya Sulaiman ina ruwana da shi bare yanzu da baya k'asar."
Jikina ya ɗauki tsuma tare da hirji.
Domin na tabbatar baba babba zai so ace wani cikin ƴaƴansa ya auri wata a cikinmu dan sake cure zuri'a ta zama dunkullaliya.
Sai dai ni kam ba qdai a kaina ba. Shiyasa na toshe dukkan ƙofar da za'a mini auren zumunci.
Tunda har yaya Faruku bai furta so ko wani yin motsi mai ƙarfi akan akan soyayyata da shi ba, ai kuwa sai dai a yi a bar ni, babu wanda zan so, in ba shi ba a cikinsu.
A kai a kai Sahal yake zuwa zance. Duk ranar da zai zo bana cikin sukuni, girki kwalliya duk na musamman ne. Abida kuwa bata sake cewa komai akan lamarinsa ba. Da gaske ta runtse idanuwanta daga lamarinmu. Sai dai akai akai take yi mini habaicin na ƙi ƴan-uwana ko karar zumunci ban iya ba.
Ranar da ƴan kirkin suke kusa ta leƙa su gaisa, ranar da take a botsare ko tunkararta bana yi. Yaya Munirah dai duk sadda ya zo sai ta je sun zanta akan shirye shiryensu na tafiya call to bar a jihar Kano.
Wata ranar juma'a da yamma muna tare da Sahal na ci kwalliya ta burge wa. Sai jifan juna muke yi da wani irin murmushi da yake fitowa daga ƙasan zuciya. Ina samun nutsuwar zuciya idan ina tare da shi. Ina jin farin ciki mai daɗin gaske. Domin tunda ga ƙasa zuciyar nake jin farin ciki da zumudi.
Muna haka yaya Faruku ya shigo harabar gidan.
Kai tsaye ya iso inda muke ya mikawa Sahal hannu suka gaisa. Cikin barkwanci ya ce "Dama na matsu na ganka na ga mai ka taka ne daga zuwanka ka rushe gwamnatina a wajen Bilkisu tashi guda?".
Kunya ta kama shi ya ce "Yayanmu ba rushe ka na yi ba, girma ka ci ka matsa mini kaɗan".
Yaya Faruku ya faɗaɗa murmushinsa ya ce " Tunda kasan ba ƙarfina kafi ba shike nan, na zama surukinka, ka riƙe mini ita amana domin ita ɗin mai haƙuri ce kuma mai nutsuwa ce."
Cikin kunya Sahal ya ce "Da ikon Allah zan rike ta da kyautatawa".
Daga haka ya kalle ni, Ni kuma cikin nauyi na ce "Yaya Faruku barka da yini."
Ya amsa yana faɗin ai na ɗauka kin zama kurma". Ya wuce cikin gida.
Ya numfasa ya ce "Yaya Faruku mutumin kirki ne Bilkisu".
Na ce "Sosai fa"
Muka cigaba da hira cikin shauki domin ban ƙi mu tabbata muna hira cikin wannan yanayin mai dadi da walwala ba.
A wannan dogon hutun mun sake shaƙuwa domin tsallaken kwana ɗaya kacal yake yi. Wani zubin ma kullum ne sai ya zo ko tsoron titi ba ya yi.
Ranar wata Laraba da ba na mantawa da yammaci lis muna hirarmu a inda muka saba zama wato harabar gate dinmu daga gefe, domin mu a gidanmu ba'a yarda da hirar falo. Sai dai a filin Allah ƙarkashin bishiyoyi da furannai.
Ba zato yaya Asad ya bayyana shi kaɗai babu ƴan rakiya daga dukkan alamu a jirgi ya iso Kaduna. Sai kuma ya iso Funtua tunda haka yake yi matukar zai zo ganin gida.
Ya hango ni, ya dunfaromu cikin saurinsa domin shi mutum ne mai hanzari ga shi ƙarfaffa na gaske. Zuciyata ta buga, bansan me ya sanya nake matuƙar nutsuwa idan na ganshi ba, hakanan a duk sadda idanuwana suka hango shi ko da ban ji kalaman bakinsa ba sai zuciyata ta harba da tsananin gaske. Na kan rasa wannan kasafi sai dai na fi tunanin tsoronsa da ya gina a zuciyata tun ina mitsitsiyata. Duk da a yanzu kirki yake yi