Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 11
da sunan karatu ba. Allah bar shi sai ta cigaba da karatunta a dakinta." Ta ce "To shike nan ba zan sake ba, ta kallo ni ta ce "Sorry Bilki solar soyayya". Yaya Salaha ta ce "Allah ya shirye ki kawai Abida." Ta matso kusa da gadon da nake kwance ta ce "Yi hak'uri kin ji Bilkisu. Tashi ki yi alwallah an fara kiran sallah. Sai kuma kunya ta rufe ni haka siddan. Na kasa koda motsi, yayin da ta juya ta tafi a dalilin ringin din da wayarta ke yi daga falo. Abida ta saki gauron numfashi ta ce "Bilhillazi shiyasa jinimu bai jitu ba, yanzu yadda kike sokokuwar nan ashe abin da yake zuciyarki azim ne, ke ce da kuka akan wanda yau d'aya tak kika d'ora idonki a kansa?" A sanyaye na ce "Kin ga Abida bana shiga shirginki irin haka, kin fitinane gaskiya, ina ce kin yaga takardar kin jefar? Na ro'ke ki, ki shafa mini lafiya pls and pls". Bata kula ni ba, ta dauko littafin HAMIDA na Maryam Kabir Mashi ta hau dubawa sai kuma ta kallo ni ta ce "Sai na ga kamar S.S Mashi ya rubuta ko?" Ban kulata ba na mike na shige bayi domin na sani idan ba wuri na bata ba, tana iya sake sa ni sabon kuka. Ilai kuwa da na fito daga bayi ta bini da ido ta ce "Da kika share ni kanki kika yiwa asara. Niyya na yi a turo mini lambar Anty Maryam Mashi tunda marubuciya ce na sayi shafi d'aya a cikin littafinta na gaba da zai fito kasuwa a yi miki cikiyar S.S Mashi. Nasan da wuri za'a samo shi tunda garinsu d'aya. Watak'ila ma wata cikin danginsu ta ga cikiyar tunda mata mun raja'a a karatun littafi". Na ja dogon tsaki na tada salla na kyale ta. Ita kuwa ta fashe da dariya mai hade da ihu ainun tare da ce wa ",Oh ashe sola macijin sari ka nok'e ce, ana miki kallon salaha nutsatssiya ashe abin da yake ranki kabiran ne. Bilhillazi gwara ni sau milyan da nake fito da zahirina a fili. Haba ai kina cutata Wallahi. Ana ta miki kallon hankali, ni kuma ana mini kallon buzu buzu saboda kawai ban iya nunkufurci irin na ki ba. Komai na ki kunbiya kunbiya, ni ban da gayunki da tsananin son turarenki ban ga me kike yi mai kyau ba ". Har na idar da sallah bata daina zungure zunguren magana ba, har da fad'in tafi kowa shan wahalar rayuwa a gidanmu tunda ni da muka taso tare zuciyata mai fad'i ce, ana mini kallon tausayin ta matsa mini ashe ingiza mai kantu nake yi mata a wajen jama'a, na barta tana ta bankaura tare da harigido, yau Allah ya bayyana mata gaskiyar lamari. Tsananin tisa ni a gaba da Abida ta yi akan maganar S.S. Mashi ya sanya na ware na daina tunaninsa akan dole. Har zuciyarta kuma na fahimci bai yi mata ba da gaske. Bamu koma Funtua ba sai ana saura kwanaki biyar hutunmu ya k'are. Muna sauka a mota da Baba babba muka fara yin tozali. Sanye yake cikin farar jallabiya fara kal haka hular kansa ma fara ce irin ta larabawa. Idonsa sanye da farin gilashi. A tsaye yake cak, duk da ya tsufa amma yana nan da k'arfinsa garau dan kuwa da mai ra'ayin aure ne sai ya auro yarinya k'ankanuwa tunda da kudinsa. Ban ankara ba na ga Abida ta fetsa ta isa gare shi. Shi kuwa ya mik'a mata dukkan hannunwasa yana fad'in lale da Abida k'anwar Bilkisu." Ta kame baki ta ce "Ai Baba na zo maka da sabuwar jarida mai dad'i nawa zaka siye ta?" Ya murmusa ya ce "Na siye ta da d'awisu" Daidai lokacin na kariso na tsugunna ina gaishe shi, ya miko mini hannunsa guda na rik'e nima. "Cikin kanzagi ta ce "To Bilki dai ta yi kasuwa ta samo wani irin mutum da kiris ya rage ya shiga sahun zabiya ta makance a kansa, gara tun wuri ka sani babu ajandar karatu a wajen ta." Tana rufe baki ta falfala a guje ta yi cikin gida. Yayin da na yi k'asa da kaina ina jin kunya da nauyi suna mini kawanya. Ya sassauta murya ya ce "Mai gadon zinare da gaske kanwar ki take yi ko kuwa shegantakarta ce?" Murya babu amo na ce "Yaya Salaha ce ta aike mu gidan inlaws dinta, sai suka tare mu a k'ofar gidan, d'aya ya ce ni, d'ayan kuma ya ce ita." Ya murmusa ya ce "Ashe har da ita ma ta yi kasuwar?" Na sake sunkuyar da kaina kasa ban amsa ba. Ya ce "To sai kuka yi ya ya?" A hankali na ce "Ita ta ce ba zasu shirya ba domin karatu zata yi mai yawa. Ni dai ban yi magana ba, amma ya ce na ba shi lambar wayata, na ce ba ni da waya, shine ya rubuta mini tasa." Ya numfasa ya ce"idan kin nutsu ki kawo mini lambar ". Murya babu amo na ce "Abida ta yaga tun a ranar". Da azama ya ce "Saboda me?" "Ta ce siffar munafiki ne da shi, sannan tunda fari ne bai yi ba". Dariya ta sosia ta kama Baba ya ce "Allah ka shirya Abida." Ya ce "Ki yi hak'uri, idan daga Allah ne zai kawo dalilin da zai sake had'aku. Sannan duk wanda ya nuna yana sonku lallai lallai ku turo shi gidanku ya nemi izinin magana da ku. Tashi ki shiga, ki fad'a mata kuma bata ci kyautar d'awisu ba". Na yi murmushi na ce "To ni kuma da na fad'i gaskiyar magana fa Baba?" Ya ce "Kin ci kyautar talo talo sai ki soya ki tafi da abinki makaranta." Da murna na ke yin godiya. Sannan na isa cikin gidan. Bangarensu Abida na fara isa, abin farinciki na tarar da Yaya Munira ta zo hutun mid semester. Da gudu na rungume ta ina jin farinciki har cikin zuciyata. Na sake ta muka zauna muna gaisawa sosai. Abida ta fito daga bayi tana fad'in Yaya Munira na siyarwa Baba jaridata ta yau, amma me za ki ba ni na fesa miki?" Cikin sace iska Yaya Munira ta ce "Rik'e abar ki dan kuwa ba ni da abin bayarwa." Domin al'adar Abida matukar ta baka labari sai ka biyata, shiyasa tafi kowa y'an canji ko abin dad'i. Yayyenmu maza Abida guntsi fesa suke ce mata, kuma ko a kwalarta, haka nan idan ta fad'a maka abin da baka sani ba, baka biya ba, to ta ringa yi maka bak'in naci ke nan, ko ta dauke wani abu naka mai muhimmanci, shiyasa Yaya Munira bata yarda ta sayi jaridarta, dan kuwa k'arshe sai dai Momi ta biya ko Baba ya biyata da kaza ko tattabaru. Shiyasa ita kad'ai ce mai dakin kiwo a gidanmu. Daga can bayan gidajenmu aka yi mata dakunan kiwon tattabaru da na dabbobi. Wato Abida kes ce babba. Kowa kuma ya sani ta shiga ran Baba babba ainun, duk da yana iyakacin k'ok'arinsa wajen dannewa baya ware ta ya fifita ta. Amma matukar ta murde akan ta siyarwa wane ko wance jarida ba'a biyata ba, to fa dole Baba ya bata auren tattabaru, ko kuma ta tubure sai tunkiya shiyasa ta had'a nata garken. Ban da haka ko labarin littafi bata yinsa a banza siya ake yi. Ta kan ce ba zai yiwu ta zauna ta bata lokaci ta yi karatu ba, sannan ace ta bada labari a bagas ba. Ba ta yi arahar hakan ba kuma zata zama haka ba. ✍️ [8/24, 12:52 PM] Surayya Dee: *DINGISHIN KWADO* *BY* *SURAYYA DEE* *MARUBUCIYAR* *HALIN YAU* *SABO DA KAZA* *BAK'AR TA'ADA* 5 *Umm Aslan&Asalah Egyptian Items* *Egyptian abayas* *Egyptian nighties*. *Bags and jewelries* *Dukkansu a sassuakan farashi da ya dara na saura, don kuwa a can take zaune tana turosu Kano kaitsaye, daga nan sai a turawa kowa inda yake a fadin tarayyar Nigeria* *Tuntubeta a wadannan lambobin dan ganin kayayyakinta na alfarma*. # +201121544627 # +2349162662750 Yini guda muna ta namu kasafin a dakinmu, sai da muka sallaaci la'asar sannan muka dunguma sashenmu suka gaida Mami muka cigaba da yin shiriritarmu. Sai da magariba suka tafi. Yaya Munira tana ta jaddada mini na taho mu kwana tare sai gobe mu zo nan mu kwana. Bayan sun tafi Mami ta zuba mini ido cikin takaici ta ce "Sokokuwar banza sai yanzu kika ga damar zuwa mini? Tun azahar kuka dawo amma kika kasa zuwa sai dazun nan! Munira tun safe ta zo gidan bata zo ta gaishe ni ba. Abida kam ai ko motar bata gama tsayawa ba ta yi wajen uwarta, amma ke da yake baki bani muhimmanci a duniyar ki ba, ai kin bisu kin tayasu adana uwarsu. Ke kam kin yi asarar hali gabadaya, sunan Saratu kika fi dacewa ki amsa ba mai gadon zinare ba." A tausashe na furta "Ki yi hak'uri Mami". Tsaki kawai ta yi, ta shige dakinta. A wannan ranar a sashenmu na kwana domin fargaba nake yi na ce zan tafi wajensu Yaya Munira. Da daddare Yaya Sulaiman da su Ansar hadi da autarmu duk muna falo tare da Mami sai fad'a mana rikicin da take yi da yan'uwanta, tare da ankarar da mu y'an uwanta sun wareta ne dan mijinta ya zarta nasu. Sannan dangin Babanmu kuwa suna fifita Momi a kanta dan suna ganin Baba babba ne don 1. Alhalin arzikin tare da mijinta ne. Ni dai ban tofa ba, ina safare ina jin babu dad'i, domin kaf dinmu bamu son yan'uwanta a dalilin yawan laifinsu da take furzarwa a gabanmu babu sassauci. Sannan dangin Babanmu ma a hagunce muke kallonsu muna ganin sun fi son Momi da y'aya'nta. Ansar da yafi kowa bin ra'ayinta ya ce "Rabu da y'an kusun uwa Mami! Shiyasa gabad'aya bana musu gaisuwar arziki daga dangin na ki har na su Baban, gabad'ayansu na washe su, me zan yi da wanda zai musgunawa uwata?" Ta muskuta tana jin dad'in yadda yake taya ta son komai tamkar dai mace. Ta numfasa ta ce "Da wayonka ka taso ka ga yadda nake tiritiri da y'an uwana menene bana d'ora maka ka kai musu, duk zanin da na cire idan zan bayar su zan bawa amma tsabar hassada basa yarda su fad'i alherina, komai zan basu a raine ne, kowacce ta zuba mini ido, ina auren mai wadata alhalin asirin ciki sai hanji. Komai d'an-uwa ya yi babakere a kai, me za'a yi da kasafin gidan nan ne?" Suka had'a baki wajen fad'in "Ai Baba k'arami ne ya sarayar da y'ancinsa gabad'aya fa ya koma tamkar yaron Baba babba ne ba wai d'anuwa ba. Kuma abin kaicon dukiyar tasu ce gabad'aya, watak'ila ma ta Baba k'aramin ta fi rinjaye, ya kasa tsayawa waje d'aya, yau na Katsina gobe na Funtua. Idan ya zo garin ma idan kana son ka samu hankalinsa ainun sai dai ka bishi Ladi farms yana can yana k'arar da lokacinsa cikin dabbobi". Na saki gauron numfashi tare da kame bakina duk kuwa ina da kalamai fal a zuciyata. Nan da nan Mami ta hauro ta dinga surfa mini sababi tana furzar da kalamai masu ciwo. "Shashar banza mai za'a yi da zuciya irin ta ki. Munafukar wofi, to duk iyashege irin na ki, ni ce dai kanki ya dawa, domin ni din da ba kya so, ni ce na kawo ki duniyar." Murya babu amo na ce "Ta ya ya zan k'i ne Mami? Na roke ki yi hak'uri." Gabadaya suka yi mini ca suna kaico da ni, a lokacin kuma na fara fahimtar dukkan y'anuwana suna matukar jin zafina a dalilin nafi shaƙuwa da yaran Baba Babba a kansu, duk da basu tab'a tunkarata kai tsaye ba. Amma maganganun da suke amayarwa tare da yi mini kaico ya sanya na fahimci dukkansu masu wahalallen ra'ayine, basa raina abin yin sarhutu. Hatta su Ansar da suke kannena sai da suka saka baki wajen caccakata. Babban abin da yake ba ni mamaki idan an had'u basa nuna adawarsu da iyalin Baba babba, hatta Mami idan suna tare da momi da yaranta sai ka rantse babu komai a ranta na gilli saboda tsananin yadda ta iya hadiye komai. Idan na zauna ni kad'ai ina nazartar yadda al'amarin yake gudana sai kaina ya yi mini nauyi ainun. Tare da hasashen ko Momi da yaranta ma suna adawa da yadda Baba babba yake wahala da mu babu banbanci da iyalinsa? Wannan tunanin na matukar caja mini kai, domin ni a lokacin ban yi zaton za'a iya mua'amala da fuska biyu ba. Kullum kwanan duniya wannan tunanin na dabiar ahalina ya haifar mini wani irin tunani dangane da mutane, a hakan na samo sha'awar son nakaltar halayyar danadam. Sai dai ban samu damar hakan ba, a dalilin zuciyata a sake take. Sai nake yiwa mutane hukunci da yadda nake. Bana zargi, bana munanan zato. Da naga tunanin halayyar momi da yan'uwana zai gigita ni, sai kawai na daina matsawa kaina, bana tunawa sai idan ina gabanta, sa'a d'aya ma bata nunawa a waje ,sai imu imu. Sai dai kuma hakan ya janyo kulli da yawa a zukantanmu. Misali mafi yawa muna yiwa kowa kallon munafukanmu ne. Ma'ana a bazance muke kallon danginsu Baba, tare da zargin sunfi son su Abida. Haka dangin mami. Tsakanina da Allah ni bana wannan akidar haka ma Yaya Sulaiman yana da sassauci, to amma Shi wani irin mutum ne da Magana ma bai cika yi ba matukar bata shafe shi ba, dan haka Duk abubuwma da Mami take fada ko take yi, a dunkule zai ce "Yi hakuri, Ki cire komai a ranki,, Allah ya Baki Ni, ba abin da ba Zan yi miki ba na jin dadi". Ga shi a wajenta ba ni da kwarjini ko kad'an. Haka nan yan'uwana basa yarda su yi maganar sirri matukar ina wajen, sun riga sun yi amanna nafi son Momi akan Mami na kuma fi kaunarsu Yaya Munira akansu, wanda ba haka ba ne duk yadda nake son y'aya'n Baba babba dai bai kai y'aya'n da mahaifiyata ta haifa ba, hakanan ba zai yiwu na so uwar wasu sama da tawa uwar ko hauka take yi kuwa. Haka dai na lallaba kwanakin hutunmu suka k'are. Ranar da zamu koma makaranta an kammala shiri tsab har mun shiga mota mun zauna, sharrin karfe juyin duniya mota ta tashi amma ta ki. A lokacin motocin gidan hudu ne, ta Baba babba d'aya, ta Baba k'arami d'aya sai guda biyu ta amfanin gida. D'aya ta amfanin gidan ta yi faci, wacce kuma aka shirya a kaimu a ciki ta k'i tashi.nBaba babba da yake tsaye ya ce "Sai a nemo bakanike dan kuwa ta'azziya zan je Maska." Abida ta ce "Gaskiya Baba motarka ce baka son bamu, tunda motar nan ta iso kake kaffa kaffa da ita. A lokacin mota kirar 190 ta hamshakan Alhazai ce. Ya ce "Da ace yayanku na gari da sai na bashi motata ya kaiku domin na gamsu da tukinsa. Amma babu yadda za'a yi Faruku ya ja mini mota". Yaya Faruku ya bata fuska ya ce "Baba kana bada ni a gaban Abida, domin Bilkisu a nutse take." *MalaysianFabrics* *Materials masu aji, masu class, na manasana sirrin gayu irinsu jacquard, luxe, viscose, dobby, embroidered jacquard da dai sauransu.* *Materials masu quality masu dadin sakawa a jiki basu da zafi ba suda nauyi.* *7020695644.* Abida ta yi caraf ta ce "Yaya Faruku na rantse maka nafi Bilki hankali, green snake ce ita. Da kasan abin da ke zuciyarta da ka fasa yin amaryar da ita." Na galla mata harara na ce "Yo ni ma tuni na fasa yin da shi, tunda ya riga da ya yi aure har ya haihu ai ya zama cus". Baba ya yi dariya ya ce "Ai kuwa dai Mai gado tunda bai jira ki ba, ba zai same ki ba". Cikin barkwanci Yaya Faruku ya kalle ni ya ce "Kada ki bari su ruguza ginina a zuciyarki? Ba kin ce ko matana uku ke ce ta hudu ba?" A zabure na ce "Da ne Wallahi! Ai garama Yaya Usman da kai, tunda dawowa kawai na yi na ga ka yi aurenka! Ko a fuska baka tab'a nuna kana da wata budurwar ba". Baba babba ya fashe da dariyar da bai cika yinta ba. Abida kuwa har wani juyi take yi, tana fad'in "Yau an ji kanku da Yaya Faruku" Domin mutumina ne na gaske. A zahiri kuma yake nunawa yafi sona akan Abida. Kafin ya bata abu d'aya ya bani sau biyar. Idan kuwa tare ya siyo mana sai na zaba sannan zai bata wanda na bari, ko kuma ni ya tambayi ra'ayina kafin ya siyo abu, ita kuwa baya tambayarta. Hakan da yake yi yana dadawa Baba babba da Momi zuciya. Tunda haka siddan Yaya Asad ya tisa ni a gaba ina k'arama a dalilin ba ni da gashi. Ina kuma shan majina sannan shiru shiruna ya yi masa yawa. Matukar yana falon momi bana iya ko da wucewa ne. An yi anyi ya daina mini muzurai da razana ni, amma fir ya ki, shiyasa na taso da matsanancin tsoronsa. Bama shiri ko kadan Kamar dai yadda Yaya Sulaiman ya tisa Abida a gaba Duk da Shi ba cin zalinta yake yi ba, kushe ya yake tare da gwasaleta. Sadda muke firamare shine yake kaimu makaranta a mota idan ya zo hutu daga makarantar horar da y'an sanda ta Wudil. Matukar Baba babba ya ga na bace masa a gidan to Yaya Asad na gari. Wata rana na shiga wajensu, banbsan dodon ya zo ba, sai ganinsa na yi gurfane gaban Baban yana sanye da kakin yansanda wanda a lokacin bai fi wata da fara aikin ba. Ina ganinsa na juya zan zura a guje. Yaya Faruku ya yi maza ya ruko ni ya ce "Ke ba abin da zai yi miki." Yayin da shi kuma ya galla mini harara tare da ce wa "Nutsu ki zauna ko na d'ora miki duniya a kanki ". Ai kuwa jikina ya hau tsuma domin kakinsa yasa na sake tsorata da shi, hakanan ni da Abida muna matukar tsoron ya d'ora mana duniya. Wani abu ne da shi mulmulalle mai tsananin nauyi da yake dagawa na motsa jiki, idan ya so mana mugunta sai ya ce sai mun yi kama kama mun matsar da shi gefe wanda bama iyawa ko motsa shi, a haka zamu yi ta yi har sai mun gaji sannan zai ce mu bari. Baba ya kalle shi ya ce "Ba dan ka yi mata tsufa ba da na baka aurenta na ga yadda zaka yi, ka takura sarauniyar shaiba da yawa Asad." Yaya Faruku ya yi fit ya ce "Haba Baba a gabana zaka bawa tsoho auren amaryata, ai Bilkisu tawa ce". Yaya Asad ya ce "ina da shekaru ashirin da bakwai kana da ashirin da biyar menene banbancin namu da zaka jingina mini tsufa? Ni mai zan yi da wannan y'ar tastitsiyar yarinyar da har yau da ta ke cika shekaru goma bata bar cin tasono ba". Sanin da na yi ya hana ni cin tasono ya sanya ina rawar murya na ce "Wallahi ban ci ba, ko rannan da Abida ta ga nasa hannuna a hanci na kai baki ba tasono ba ne, amma ta ce sai ta fad'a maka ". Gabadaya suka saka dariya ban da ni da nake ta zufar fargaba. Domin wahalar gaske yake ba ni wajen cewa sai na d'ora duniya a kaina. Baba babba ya ce "Ke rabu da shi kin ji. Daga shi har Faruku duk sun yi miki tsufa". Da sauri na ce "A a Baba Yaya Faruku ne" Suka sake yin dariya, yayin da Yaya Faruku ya yi ihun murna tamkar ba a gaban Baba yake ba. Da alfahari ya ce "ai tuni mun saito ta da Bilki komin tsufana ita ce amaryata". Na numfasa daga hakaito kuruciyata da ban yi nufin budewa gabad'aya ba, na kalli yadda Abida take murnar gwale Yaya Faruku da na yi, tunda har yau da muka zama y'anmata yafi jana a jikinsa fiye da ita, ko gidansa muka je yafi haba haba da ni, lamarin da yasa matarsa ta washe ni ainun tun ban fahimci inda ta dosa ba har na gane, shiyasa da na yi wayo sai na daina zuwa, domin muddin muka je hutu to fa ba shi ba zama lafiya a gidansa har sai mun bar gidan. A garin Funtua yake zaune, shine kuma yake kula da shige da ficen kudi na Ladi farms, tunda Yaya Asad ya yi nisa yana Kebbi shekaru biyu kenan ya bar Asaba. A lokacin kuma yaransa biyu duk mata. Yayin da Yaya Faruku yake da yaro namiji. Na tausashe murya na ce "Har gobe ni ce amaryar Yaya Faruku" Da yake shi mai haba haba ne yafi dukkan mazan gidanmu wayayyen kai, domin idan ya shiga cikin mata sai ka rantse shima mace ne, idan biki ake yi a gidanmu kuwa cikin su Yaya Salaha yake shiga a yi rawa da shi yana musu liki, gabadaya rayuwar Yaya Faruku abin sha'awa ce, baya da damuwa, ba shi da tsanani ga shi dan gaye na sosai kuma fari irin wanda nake so. Amma Yaya Asad ga bak'i, ga shi mummuna, duk da dai Abida ta ce nice nake ganin muninsa tunda na rufe zuciyata a kansa, ni kuwa bana yarda da maganarta duk da ban tab'a tsayawa na masa kallo sau biyu ba, amma nasan dogo ne mai murdadden jiki tunda ma'abocin motsa jiki ne ainun tun tasowarsa. Tabbas sifarsa ta dace da jami'in tsaro. Ya yi tafi ya ce "Ni nasan duk yadda ake kushe ni nasan sarauniyar shaiba tawace". Baba ya sake murmusawa, yayin da Abida ta yi gum alamun bata da tace wa. Tamkar jifa sai gani muka yi mai gadi na bude tangamemen get din gidan. Moto kirar pegoeat ta shigo, sai kuma wata irin ta y'ansanda mai dauke da logon y'ansandan k'asa reshen jihar Kebbi. Motocin na tsayawa wani ya yi saurin fitowa ya bude k'ofar Yaya Asad ya fito da alamu shine jagorar tafiyar gabad'aya. Yana fitowa suka fito da azama. Shi kuwa ya durfafi Baba babba kai tsaye. Yana zuwa gabansa ya cire hular kansa ya kame tare da sarawa Baban wanda hakan shine kololuwar gaisuwar girma a gidan jami'an tsaro. Haka tawagar y'an sanda har su takwas suka yi layi suka yi Baba kwatankwacin yadda ogansu ya yi. Shaukin gaisuwar ta debi ni, karon farko na ji sha'awa aikin damara ta shige ni. Domin an yi ittikafin babu inda ake girmama wanda ya wuce ka mukami irin a aikin d'amara. Abida sarkin kankanba ta yi maza ta matsa jikin baba tana ce wa "Baba pls na shiga rigar nima a mini wannan gaisuwar dan girman Allah." Baba ya bibbigi bayanta tare da ce wa "Ho Abida! Su kuwa da suka koma gefe sai suka sake matsowa suka jeru, suka cire hulunan suka yi mata tata gaisuwar tamkar ita ce momi. Dad'i ya kamata ta dinga dariya tana fad'in thank you so much ". Yaya Faruku ya matso gabana ya yi mini yadda ya ga sun yi, ya ce "Bilkina duk da ni farar hulane karbi tawa gaisuwar." Na yi murmushi tare da ce wa "Na karba da godiya Yaya Faruku". Ba zato kawai Yaya Asad ya yi mini yadda ya yiwa Baba babba. Kaina ya fasu na kasa boye kaduwar da na shiga a dalilin yadda ya girmama ni. Ba tare da bata lokaci ba yaransa ma suka ƙame mini. Karon farko da Yaya Asad ya kambaba ni. Murya ba amo na ce "Na gode sosai Yaya! Takaici ya shake Abida. Ta ce "Bilhillazi Bilki kin shiga uku, ni dai kam bansan me yasa aka had'amu sa'anni ba, haka kawai sai gana mini azaba kike yi. Ni sai da na roka aka k'ame mini, amma ke baki roka ba, har shugaban bataliyar ma ya rusuna miki, ga Yaya Faruku farar hula, haba haba gaskiya kina k'warata! Gabadaya wajen aka dauki dariya domin kowa yasan zata mayar da gaisuwar da aka mata wani abin alfahari ne. Sai gashi nima an mini fiye da tata. Daidai lokacin Yaya Sulaiman ya shigo harabar gidan a lokacin kuma yana ta shirin tafiya k'asar Germany dan yin karatun likitanci. Duk da basa shiri ko kadan ya ce "Abida yau d'aya bari na miki alherin da kike ta fadin ba ni da shi". Ta galla masa harara tare da ce wa "Ba an mana iyaka ni da kai ba? Na rantse sai na fadawa Baba k'arami". Ya k'ame mata tare da sara mata ya ce A yafi Malam Sule Abidan Baba". Ta wani dauke

Chapter 4 of 11