Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 11
take yi irin tafarfasa, tamkar na ciro ta na wanke komai ko na huta da tsananin da nake ciki. Da k'yar na dinga ambato ya Hayyu ya Kayyum bi rahamatika astagisu. Na jima kafin na fara samun sassauci. A raina na fahimci manufar shari'a da ta yi togaciyar tsananta bincike kan abin da ake boye maka ko wanda baka san da shi ba. A da zato nake yi wanda ban gasgata ba. A yanzu kuwa na bankadowa kaina damuwa da kunci. Domin zan rayu ne cikin zullimi da zargi. Na saki gauron numfashi. A fili na furta k'arin aure ba laifi ba ne a wajen namiji mai ra'ayin k'arawa. Sannan Ubangiji da bibbiyu ya ce su fara domin yasan ya haliccesu da son mataye da yawa. Ba kuma zan bijire wa ayar Ubangiji ba ne ta hanyar kin amince wa da k'arin aurensa ba. Zan bijire ne don na tserar da shi tashi da shanyayyen bangare daya ranar alkiyama. Domin yadda na shaida Annabi manzon Allah ne haka na shaida k'arin aure bana maza irinsa ba ne. Ba zai iya adalci ba tabbas. Har aka k'ira assalatu ban iya tsinana komai ba, sai kuka da sake saken zuciya. Har ya fito ina zaune ko yunkurin tashi ban yi ba. Ya k'araso kusa da ni murya babu amo ya ce "Ashe kina nan?" Bai jira amsawata ba ya fara tafiya yana fad'in sai na dawo. Na bi bayansa da kallo ba tare da na iya fad'in uffan ba. Da k'yar na tokara na tashi, na dauro alwallah. Ba k'aramin jarumta na yi ba, kafin na samu hankalina ya daidaita na yi sallar cikin nutsuwa ba. Gabadaya fuskata ta aune, na yi fiyau da ni. A yadda nake jina ko ina da darasin da zan bayar da safe ba zan iya halatar makaranta ba. Sai kuma ya kasance sai karfe 4-6 nake da darasi. Dan haka ina layi na nufi dakina na kwanta, sabon kuka ya k'wace mini tamkar dai ba kwana na yi ina yi ba. Da k'yar na yi k'ok'ari hadiye kukan saboda sanin da na yi a ko wanne lokaci yarana na iya shigowa idan basu ganni a kicin ina hidima kamar yadda na saba ba. Na ja duvet na lullebe jikina. Ilai kuwa sai ga Amrah ta shigo. Da kulawa sosai ta ce *Mahmah* ba kya jin dad'i ne yau?" Murya ta babu amo na ce "Kwana na yi da ciwon kai da zazzabi. Na sha magani yanzu shine na kwanta ko zan samu na rintsa." "Ayyah sorry Mahmah! Allah ya baki lafiya". A hankali na ce "Ameen. Ki je kicin ki tayasu ku shirya komai, ki kula da Farha". "To Mahmah". Ta amsa a nutse ta fice ba tare da ta ja k'ofar ba. Ko minti daya ba'a yi ba, suka dawo dukkansu har Faruk. Suka gaishe ni sannan suka mini sannu. *Kun tuna Umm Nihla mai yadinkan Yan gayu da Yabin Bulkacuwa ta yi ta kece raini da su?* *Tana nan tana kawo muku su zuka zuka, na alfarma, amintattu, akan farashi mai rahusa* *Malaysianfabricsng* 07020695644. Amrah ta kadasu suka fice bayan ta rufe k'ofar dakin. Na sani ta kawo sune dan kada barci ya sure ni su tashe ni. Bai shigo ba sai bakwai da mintina daidai lokacin da muke fara karyawa. Da kulawa ya ce "A kwance kike, ba ki da lafiya ne?" Na kasa amsawa domin ji na yi gabad'aya haushinsa ya turnike ni har wuya. Ya zauna a bakin gadon. Ya tab'a jikina ya ji da zafi, ya ce "Zazzabi ne a jikin ki, amma kin kwanta. Ki tashi ki shirya na ajiye ki a asibiti idan kin kammala sai ki dawo gida ki kwanta." Na girgiza kai na ce na sha magani yanzu, barci zan yi, nasan zai sauka in sha Allah ". Ya mik'e ya ce "Allah ya kara lafiya sai na dawo " Ya saka kai ya fita, ya karya sannan ya fita da yara gabad'ayansu. Hawaye ya sake silalo mini, ba dan komai ba sai na takaicin yadda na dauki dukkan so da yarda na damkawa Baban Amrah. A haukana na dauka a yanzu ne zan ci moriyar hak'uri da sadaukarwa da na yi. Ashe wanccan tunanin nawa ne ni kad'ai. Domin a yanzu ko bai bude baki ya ce mini ba na burge shi, na yi masa tsufa ba, ayyukansa da yadda yake mu'amalantata ya fahimtar da ni. Na goge hawaye na kalli fanka yadda take wulwulawa da k'arfi. Na saki ajiyar zuciya. Ina sake gane haka alamuran duniyar nan suke jujjuyawa tamkar fitar kibau a jikin mashi. Na rufe ido ina tariyo abubuwan da suka yi ta faruwa a tsakaninmu da ya kamata na fahimci al'amarin da yake ransa, amma saboda na riga na bashi total submission sai nake dada nausawa tare da zama bagidajiya a kansa. Dirin wayata ya ankarar da ni, ana kirana, domin na saka ta a vibration ne. A kasalance na dauka ganin sunan aminiyata kuma y'ar uwata ya sanya na dauka babu b'ata lokaci. Karon farko da na dauki wayarta ba tare da na yi tsaki ba. A sanyaye na ce "Maman Abdul ya family?" Ta amsa da ce wa "A kwance kike ne?" A hankali na ce "Eh bana jin dad'i ne fever da ciwon kai suka taso ni a gaba." Ta bude murya ta ce "Kuma sun taso ki a gaba, sai kika nade a gado, kika kasa gane kamata ya yi ace kina gaban likita, dan a duba ki a d'ora ki kan magani?" Na saki ajiyar zuciya na ce "Maman Abdul na sha magani idan bai sauka ba zuwa anjima zan je na ga Dr din". Ta ja tsaki ta ce "Nan da mintina kad'an zan zo na raka ki, tunda shi ya fice ya barki a kwance." Na kasa bata amsa domin ba k'aramin aikinta ba ne ta hau zagina tunda tana cikin jerin mutane masu hangulalliyar zuciya. Kazalika bata sassauci akan lamarina da Baban Amrah. Ilai kuwa sai ji na yi ta yi tsaki ta katse wayar. Na ajiye wayar na yunkura na zauna da k'yar a dalilin yadda nake jin rashin k'arfin jikina na tsananta. A hankali na muskuta na sauka na doshi bayi. Na sakarwa kaina shower. Domin na tabbatar sanyin ruwan zai rage mini dumin da jikina ya had'a. Na kammala saka undies na zura doguwar rigar batik ta Malaysian Fabrics. Babu nauyi haka dinkin ma plane ne. Na daura dankwalin. Na feshe rigar da tauraren kaya tunda na fesa na jiki kafin na saka kayan. Na shafawa lebena wet lips. Na fito da mayafin da ya dace da atamfar. Hakanan takalmi da jakar kalar mayafin ne. Na makala barima wacce a cikin jakar na dauko. Na dauki wayata na fita falo. Na tarar ko ina a gyare. Na leka kicin na tarar da su biyun suna fere doya. Daga k'ofar baya. Suka hau gaishe ni da yi mini sannu da jiki. Na amsa musu da ce wa na ji sauki. Na kalli Alawiyya na ce "Ki je ki gyara dakin". Na dubi Alti wacce ta fita a haife na ce "asibiti zan je. Ki kula da gidan, kada kuma ku je ko ina". Da ladabi ta ce "Mahmah a dawo lafiya, Allah ya kara sauki". Na amsa da "ameen na gode " Har na fara tafiya ta biyo ni ta ce "Mahmah ki dan sha kunu mana. Na dama ya yi kyau." Na murmusa mata na ce "To zubo mini Alti". Da murna da rawar jiki ta tafi dauko mug din da nake sha da shi. Ta dauraye sannan ta goge da wankakken kicin towel. Ta ciko shi taf. Ta tsugunna ta ba ni, na karba na ce "Na gode sosai Alti". Ina kurban kunun Maman Abdul ta shigo, sanye cikin gown din wani fitinannen material da ya yi matuk'ar yi mata kyau ainun wacce order ce da ba'a samu a koina sai a *Malaysianfabricsng* 07020695644. Bata zauna ba ta ce "Ta so Malama". Na kalle ta na ce "Rigimaatu zauna ki sha kunun gyada". "Na karya already idan mun dawo zan sha." "To ba ni mintina biyar na kammala Sha". Bata ce komai ba, ta zauna tabbacin zata jira ni din. A hanzarce na shanye. Na ajiye cup din na mike muka tafi. Su Alawiyya suka biyomu suna mana fatan dawowa lafiya. Muka gaisa da Baba mai gadi a mutunce muka bude k'ofar k'aramin get muka fita tunda bata shigo da motar ciki ba. Muna tafe tana tukin ta cikin nutsuwa, ni kuma na yi zurfi a tunanin halin da nake ciki. Ina son na fad'a mata abin da na ga ni a wayar mijina. Ina jin tsoron tention din da zata kara mini. Na riga da na sani ko yanzu aurena ya mutu murna zata yi watak'ila ta had'a da k'warya k'waryar walima. Ba kuma zata yi hakan dan murnar aurena ya mutu na rasa wata daukakar duniya ba. Zata yi ne domin tana ganin zan samu y'ancin zuciyata. da kuma farinciki. Har muka isa bamu yi maganar da zarta uku ba. Ba b'ata lokaci muka ga Dr ta rubuta mini magunguna ta kuma gargade ni na k'aranta damuwa domin jinina ya hau sai dai ba sosai ba. Ni kuwa nasan rashin barcin da ban yi ba, da kuma tsananin da na kwana a ciki ya isa ya sababa mini komai. A hanyar komawarmu ta sassauta fishinta ta ce "Ba zan gaji da fad'a miki ce wa aure is not all about do or die ba ne. Allah da kansa ya yi maganar idan kun fahimci kun kai lokacin da ba kwa burge juna, ko ba kwa son juna ya fad'i yadda al'amarin zai tafi cikin ihisani da kyautatawa. Amma gabad'aya hausawa bama amafanin da wannan nafsin! Sai mu yi ta zama irin wanda babu lada a cikinsa sai zunubi ma. To zunubi mana tunda duk zuciya babu dad'i an koma ana zaman y'aya', ba zaman Allah da Annabi ba. Duk abin da za'a yi ba dan Allah ba, ba zai yi albarka ba. Y'aya' nawa ne uwayensu suka fad'i suka mutu a wannan duniyar? Sun mutu ne ko sun kasa rayuwa? Bare kuma da ranki da lafiyarki. A lokacin da mijin da ya k'arar miki da kuruciyarki ya gundura da ke, a lokacin kuma Ubangiji zai turo miki wanda shi kuma a hakan yake son ki, yake kaunarki. Bilkisu kin yi hakuri, kin biyayya, kin yi sadaukarwa, kin yi adalci, kin yi komai. Amma fad'a mini what do you have in return?" Na fara kuka sosai. Ta gangara gefe ta ce "Bude baki ki mini magana Bilki. Kin sani bazan yad'a sirrinki ba, na damu da ke tamkar ko ma fiye da kaina. Kalle ni, ni ce ta ki BBM ". Hawaye na zuba murya na rawa na kalle ta na ce "Baban Amrah ne, soyayya yake yi da k'ananun yan mata wadanda basu bawa Amra shekaru biyu ba! Kuka mai nauyin gaske ya kece mini. Amma ita bata ka'du ba. Sai ma ce wa ta yi "soyayyar da yake yi da y'an mata ya kamata ki saka a ranki, ko kuwa kamata ya yi ki gane irin kuskuren da kika rayu a kai, ki yi d'amarar gyarawa? Bilki ba fa zan rufe ki ba, domin ni da ke bamu hadu dan munafunci ba. Dan haka bazan yaudare ki ba, tamkar yadda bazan yaudari kaina ba. A halin yanzu mijinki zai bukaci yarinya k'arama. Domin shi a yanzu yake kan ganiyarsa. Kinsan kuma na tab'a fad'a miki da jimawa har muka samu sabani akan hakan. Ni yanzu ba soyayyar da yake ba ne cikas ba. Yadda kike ragaita a hannunsa ne tashin hankalina. Bilki kina da zafafa soyayya. Anya kina yawan tuna hadisin Annabi da ya ce mu takaita soyayya da k'iyayya domin komai na iya juyawa. Ma'ana masoyi kan rikide ya koma makiyi. Haka nan makiyi kan rikide ya koma masoyi. Menene something precious a tare da Baban Amrah da kika zama haka ne?" Na kalle ta ina son na fahimce ta da kyau. So take na kashe aurena ko kuwa? Duk abin da nake yi ina da damar da zan yi ne. Allah ya yassare mini. Na yi k'asa da kaina domin na hakkake ba ingiza mai kantu zata yi mini akan halin da nake ciki ba. Tun fil-azal take adawa da yadda nake gudanar da rayuwar aurena. Ta rayu tana kaicon yadda komai ya cukurkude mini. Na nisa na ce "Ba yadda kike zato ba ne. Kin ringa kin sani ban dauki abin duniya da muhimmanci ba. Dan haka duk abin da nake yi a gidana ban tab'a jin kaicon yinsa ba. Na fi son soyayya fiye da kudi. Na fi son a ririta ni, fiye da a ajiye mini komai babu kulawa. Na fi bukatar kulawar miji sama da na tara abubuwan kyalekyale." Ta numfasa ta ce "Yanzu fad'a mini kin samu yadda kike so din ne? Kusan asara biyu kika yi Bilki. Ke baki yi tattali kin mori karatunki da aikinki da kike yi babu hutu ba. Sannan kuma baki samu yadda kike so a wajen mijin da kika d'ora dukkan fatanki a kansa ba. Tun farko na fad'a miki kada ki bada k'ofar da zaku yi joint pocket. Amma kika k'i." Cikin kuka na ce "Yanzu "Maman Abdul ina da kudi sai na bar mijina yana ragaita? Ina da hali sai na bari mu zauna da yunwa! Ina da dama sai na bari mu zauna a gidan haya, ko kuwa na zuba ido a dinga ganin y'aya'na kamar almajirai saboda rashin sutura da kyakkwar makaranta?" Idonta ya ciko da k'walla. Ta yi dabarar daukesu ta ce "Ba ina nufin haka ba. So nake ki gane ba kowa ne yasan alheri ba. Yanzu fad'a mini da kika yi hakan kin samu abin da kike so? Har yau baki samu ba. Ni da na bar mijina da hidimar gidansa na fiki samun kulawa, na fiki nutsuwa, na kuma fiki gamsuwa da kokarin miji. Ban tab'a yarda na yi abin da nasan ba hakkina ba ne. Na yarda zan yiwa kaina irin suturar da ta dace da ni ko da shi ba zai mini ba. Zan siyawa y'aya'na suturar da nake son ganinsu a ciki, mussaman idan zan je taro da su. Haka nan idan ta tura ta kai bango zan shiga cikin tallafin karatunsu domin idan na ginasu kaina na yiwa sabida na yi amanna y'aya' mallaki uwa ne. Ko ina nake a duniya zasu nemi ne ba kuma zasu canja ni da wata ba. Sai kuwa magani idan ba ni da lafiya ko su. Sai kuma na tabbatar miji ba shi da sukunin yin wannan hidimar. Idan kika cire wadannan ba abin da zan yarda na daukewa miji, komin kashin abin da yake da shi sai ya kawo ya bamu tunda shari'a ma bata dauke masa ba." Ta nisa ta cigaba da ce wa "Mafi yawa fa mazan yau da zarar suka ga kana tausaya musu kana sana'a kana hidima a gidan wai maimakon su karfafa ka, su yaba maka, sai su dinga sakar maka ragamar rik'e gidan a hankali. Kafin a ankara sai su bar maka kaso takwas na rik'e gidan gabadaya. Ranar da baka yi ba kuwa sai ya zama ka yi zunubin da zasu juya maka baya ko ma su sallame ka. Kuma akan idonka zasu yi aure su dinga yiwa d'ayar matar hidima da dukkan iyawarsu. Da zaka yi magana sai a taru ace kishi kake yi, da ai baka yi k'orafin ya barka da wahala ba sai yanzu. Shi kuwa gogan ko d'ar ba zai ji ba zai ce "Ai ita yarinya ce, yaro kuwa bai san babu ba, ke ma lokacin da kike kamarta ai ba abin da bai miki ba. Dole ki hak'ura idan kina son zama da shi, rikicewarki kuwa na iya sawa ya sallama ki ya cigaba da zama da matarsa ba tare da tunanin kun tara yara ba." Na kalle ta na ce "Na gane na kuma san gaskiya kike fad'a mini wacce babu son kai a cikinta." Ta ruk'o hannuna ta ce "Ki fara nazarin yadda za ki gyara kuskurenki. A yanzu yana da halin da zai rik'e gidansa Bilkisu. Dan haka ki zame ki bar shi ya dauki nauyin da Allah da kansa ya wajaba masa. Idan ba shi da hanyar samun kudi ta yaya zai fara tunanin k'arin aure, ko kuwa itama ke zai aurowa ki cigaba da rik'e masa ita?" Na kalle ta a matukar kidime na ce "Sai ka ce na zama sauna Basma?" Da rauni ta ce "Ai kuwa shasha ma ya mayar da ke ba sauna ba Maman Amrah! Muka yi shiru a dalilin na kasa magana, gabadaya kaina ya kulle. Ina ta tunanin fad'i tashin da na dinga yi a baya amma gabadaya ban ga ribar hakan ba. Na fesar da ajiyar zuciya na ce "Zan gyara abin da zan iya gyarawa Basma. Amma ba duka ba. Domin kinsan idan ina son abu to ina sonsa ne da dukkan zuciyata. Ba abin da zan mallaka da zan yi masa iyaka da shi. Allahu yana kallona yana kuma kallon zuciyata. Idan abin da nake yi saboda shi ne to da sannu zai kawo mini mafita, na yi imani zan ga alheri ko da kuwa ba nan duniya ba ne. Abu d'aya na kudire idan har ya yi aure a wannan halin da muke ciki to tabbas shine tikatin sakina. Domin hakan da zan yi shine cikakkiyar soyayya tunda zan tsallakar da shi fad'awa halaka ne. Baban Amrah ba zai iya ba, na yi imani ba zai iya ba. Zan yi kokarin na danne komai domin ina son shi, ina son na rayu da shi, ina tausayinsa da y'aya'nsa. Amma idan har ya zabi wata saboda ni, to zan kauce na bashi waje domin ba zan hana shi abin da Allah ya ba shi dama ba. Da ace shi din jarumi ne, na tabbatar zai iya rik'e mata biyu cikin mutunci da adalci, da zan danne komai na jagoranci k'arin aurensa na bashi dukkan gudunmawar da ta dace tunda ga kan kudi har zuwa samar masa da kwanciyar hankali. Son da nake masa ba zai ba ni kuzarin da zan hana shi morewa rayuwarsa ba. To akasin da aka samu shi ba jarumin ba ne ta ko wacce fuska. Ni kuma bazan yarda na yi hakurin da babu lada sai cutarwa a cikinsa gabad'aya ba." Wata irin salama da annuri ya sauka a dukkan jiki da fuskar Basma. Ta ce "Na ji dad'i Bilkisu! Na gode miki, na kuma fahimce ki a yau k'warai da gaske. Zan fara yi miki addu'ar Allah ya mayar da shi irin yadda muke son ganinsa, daga yau na daina fatan ki bar shi, zan kuma tsaya miki har ki tsallake dukkan kalubalen da kike fuskanta a rayuwarki". Hawaye ya tsinke mini da rawar murya na ce "Na ji dad'i da kika fahimci sonsa kaddara ta ne ba wai ni ce na makale akan dole ba. Babu abu mai azabtarwa irin so. Mussaman son da ake yinsa babu dalili. Domin idan duniya zata hadu ana son fahimtar da kai had'arin da kake ciki ba zaka gane ba. Illah sake nausawa jeji tare da k'ullatar mutane da kuma ƙalubalantarsu. *Umm Aslan&Asalah Egyptian Items* *Egyptian abayas* *Egyptian nighties*. *Bags and jewelries* *Dukkansu a sassuakan farashi da ya dara na saura, don kuwa a can take zaune tana turosu Kano kaitsaye, daga nan sai a turawa kowa inda yake a fadin tarayyar Nigeria* *Tuntube ta a wadannan lambobin dan ganin kayayyakinta na alfarma*. # +201121544627 #+2349162662750. Surayya Halin yau ✍️ [8/24, 12:52 PM] Surayya Dee: Follow this link to view our catalog on WhatsApp: https://wa.me/c/2347020695644 3 *MalaysianFabrics* *Materials masu aji, masu class, na manasana sirrin gayu irinsu jacquard, luxe, viscose, dobby, embroidered jacquard da dai sauransu.* *Materials masu quality masu dadin sakawa a jiki basu da zafi ba suda nauyi.* *7020695644.* A hankali ta yiwa motar ki ta hau titin da zai kaimu gidana da yake cikin Shagari lowcost. Zuciyata ta buga ganin motarsa a harabar gidan tabbacin ya dawo. Bamu tarar da shi a falo ba. Muka zauna Alawiyya ta kawo mata kunun. Ta sha, sannan ta mike tana gyara mayafin ta. Ta dauki jakarta ta kalle ni ina shirin tashi dan yi mata rakiya. Ta ce "Wallahi na yafe miki. Zauna ki huta, tunda kin sha magani ki kwanta ki yi barci idan kika tashi In sha Allah you will be better" Na ce "Zan kokarta." Ta tafi tana fad'in"Sai mun yi waya, ki sha magani, ki kuma kwanta ki huta sosai. Fiye da shudewar sa'a ina zaune a falon ni kad'ai. Gyangyadi ya fara cafka ta. Na tabbatar a cikin magungunan akwai wanda zai saka ni barci. Baya ga hakan ma na ci bashin barci jiya. Da k'yar na yunkura na yi dakina, ina yaki da sashen zuciyata da take son na je na gano halin da yake ciki. Amma na daure na kwanta. Na fara barci na ji muryarsa tamkar a mafarki. Na bude idona da suka canja launi saboda barci da kuma rashin isasshiyar lafiya. Fuskarsa babu fara'a ya ce "Tunda Basma ta zo ai yau kuma sai abin da na ga ni a gidan nan. " Murya babu amo na ce "Babu kyau zato fa". A hanzarce ya ce "menene zato a cikin maganata? Na ce zan kai ki asibiti kin k'i, saboda kin raina k'ok'arina! Amma da yake tana da tasiri ta shigo har gidana ta dauke ki, ta kai ki asibiti ta dawo da ke bayan ta gama yi miki hudubobin da na yi amanna na hure kunne ne. Kinsan ina gidan, amma ki kasa zuwa ki ga halin da nake ciki, ko ki tambayi ba'asin dawowar da na yi, sai kika yi kwanciyar ki saboda kin riga kin fara gina katangar karfe a tsakaninmu! Ya fad'a cikin bacin rai da ya bayyana a fuskarsa da gangar jikinsa gabad'aya. Na zuba masa ido, na kasa ce wa komai. Domin ya riga da ya bari na fara fahimtar ainihin kalarsa. Ba abin da yake buguna irin idan na tuna yadda ya kaikace yake fad'awa yarinya k'ankanuwa maganata. Wai ni ba yarinya ba ce bare ya lallaba ni. Sa'a d'aya da na yi dai duk tsufana ya kere mini. Na murmusa kad'an na dauke idanuwana akan kyakkwar fuskarsa da ta fara bak'ancewa a idanuwana. Na kuma yi amanna kishin da yake yagalgala ni ya janyo na ga bakinsa. Na kuma gamsu ba za'a dauki lokaci mai yawa ba zuciyata zata yafe masa, ta cigaba da ganin farinsa. Ganin na yi shiru kuma ina kallonsa sai ya fahimci akwai al'amarin da yake zuciyata mai nauyi. Ya matso ya zauna murya babu sukuni ya ce "Maman Amrah wannan kallon na ki, ina buk'atar fashin baki" Na dauke idanuwana, na lumshe su ba tare da na ce kanzil ba. Ya numfasa ya ce "Fad'a mini matsalar ki, ban gamsu da kallon da kike bina da shi. Haka nan ban gamsu da yadda kike mu'amalanta ta ba." Na sake yin shiru. Don bansan abin da zance masa ba. Domin duk yadda na tunzura bazan iya bude baki na yi masa gatsali ba. To na ce masa me ma? Tunda ni na binciko kuttu da kaina. Da na cigaba da dauke idanuwana daga kan wayarsa da ban ga abin da ya gigita ni ba. Ya yi k'wafa ya ce "Basma ba zata ga alheri ba in sha Allah." Har cikin zuciyata na ji rashin dad'in kalamansa. A sanyaye na ce "Basma na cikin jerin masoyana, tana cikin wadanda suka damu da damuwa ta. Ban zaci zaka iya mata mugun fata haka ba." Ya mik'e a kausashe ya ce "Yadda kika gamsu masoyiyar ki ce haka na tabbatar makiyata ce. Kuma ni Wallahi ko yanzu kasuwa ta tashi d'an koli ya ci riba." Ya fice cikin sauri tare da bugo k'ofar da k'arfi tabbacin ya yi fishi sosai. Na sauke nannauyen numfashi. Na furta "Subhanallah! A bayyane. Zuciyata ta sake nauyi wato ko mun rabu ba shi da kaico. Na fara gasgata da gaske yanzu babu soyayyata a tare da shi tunda har ya yi irin wannan furucin tare da rantsuwa. Ina kwance lamo ba abin da nake yi sai tunanin rayuwarmu. Tunanin k'alubalen da na ratsa. Hawaye ya silalo mini a dalilin mahaifina da ya fad'o mini. Badakalar da ke faruwa a cikin zumuncin zamani na matukar tsorata ni. Na sha jin labaran damalmalewar zumunci daban daban amma ban tab'a cin karo da irin na gidanmu ba Ban tab'a ganin rashin kunya da mutunci irin wanda na ga ni a zuriarmu ba. Idan na tuna abin da ahalinmu suka yi sai na ji kunya da tashin hankali na rufe ni irin mai saukar da zazzabi da kasala. Hakan na cikin dalilin da ya sanya bana kaunar aurena ya samu tasgado domin bana fatan na

Chapter 2 of 11