cikin guda daga cikin kyawawan material din Malaysia, mai kalar siminti da yarfin kwanduwar kwai.
*Contact umm Nihla for all your *Malaysian fabrics.
*Malaysian Batik and more*
*All are unique and classy*
*Available wholesale and retail*
.......
Ya ce "Billy kin kara kyau sosai
Na murmusa cikin kunya na ce "Na gode ".
Ya wuce bayi yana ce wa "bari nima na yi wanka kada tazarar da kika yi mini a kyau ya sake tsananta."
Na murmusa ba tare da na ce kanzil ba.
Bai wani jima ba,¹0 pop-up ya fito daure da tawul na yi maza na dauke kaina. Bai ce komai ba ya fice zuwa daya dakin da yake a matsayin nasa.
Na hanzarta canja zanin gadon da duk ya baci da jinin budurci na canja wani. Na shiga bandaki na kama duk inda ya baci na wanke, na yarfe sannan na ninke na baza shi akan kyauren bandakin.
Ya shigo sanye cikin yadi mai taushi shudi kalar sararin Subhana(sky blue).
Sosai ya yi kyau zuciyata ta doka da tsananin gaske, take raunin da soyayyarsa ta yi a dalilin Yaya Faruk ya kau, mai kyaune irin wanda nake so duk da dai siriri ne irin sosai din nan, na tabbatar sirintarsa tana karawa tsayinsa kaimi. Sabuwar soyayyarsa ta sake yun mmkuro mini tana sake bin dukkan sassan jikina tana mamaya da k'arfin gaske.
Idona ya kada kwallar shauki ta cikasu taf.
Da hanzari ya iso inda nake. Ya ce "sannu da aikin lada Bily. Allah ya yi miki albarka! Mu je mu karya yunwa nake ji sosai."
Gabadayanmu kamshi muke yi. A plate daya ya zuba mana abincin. Ya turo mini kofin shayi gabana tare da ce wa "zuba sugar da su madara yadda zasu yi miki".
Ban ce komai ba, domin kaina a kasa yake, kunya da bakunta ke dawainiya da ni gabadaya.
Cikin nutsuwa da walwala muka karya duk da ni kunya ta yi mini dabaibayi.
Bai fita ba sai da aka yi sallar azahar. Ya yi tafi masallaci ya ce zai shige gida ya gaidasu Baba.
Na idar da tawa sallar. Na dauko wayata da take kashe tun daren jiya.
Na kunna, na jinkirta ta daidiata.
Mami na fara kira, ta amsa da walwalar da take alamta mini ta yi kewata sosai.
Har na ji dadin yadda ta mu'amalance ni. Ta dinga fadin nasan kina da hakuri da shanye damuwa, ki yi kokarin ninka hakurinki Bilki, hakurin nan dai shine aure, shine ma rayuwa gabadaya. Murya babu amo na ce "To Mami na gode Allah ya kara miki lafiya da hakuri. Ta amsa da fadin "ameen, amma ai ni bana hakurin da zan cutu, a sha'anin aure ne kawai nake dukkan hakuri domin zawarci bashi da dadi Bilkisu!
Ko a gaban uwarka da ubanka zaka yi shi kuwa bare ni marainiya ce, tun ba'a aurar da ni ba na rasa uwarta, mahaifina kuwa ban yi haihuwar fari ba na rasa shi. Ga shi ni din an jarrabe da wata irin nannauyar jarabawa.mai matukar nauyi. Y'anuwana suna cikin magautana."
Na nisa na ce "Mami sunnar rayuwace ai, ba ke kadai bace kike da k'alubale da y'anuwanki ba, mutane da yawa ne, kawai ke dan kina yawan furzarwar ne, ba kya iya barin al'amarinsu a ranki ko dan a samu saukin gaba da b'acin rai. Manyan bayin Allah sun fuskanci kiyayya a wajen danginsu, haka Annabawan Allah. Idan kuma Allah ya rufa maka asiri Mami ba wani mahalukin da zai tona maka. Sai dai ya tonawa kansa.
Na numfasa na ce "Allah ya jiqan magabatanki, Allah ya saukaka miki dukkan kasafinki Mami ".
Ta amsa da"ameen ameen a sanyaye."
Karon farko da na yi mata jirwayen hakuri akan shaaninta da danginta bai zame mini sanadin bacin rai ba.
Na kashe wayar na kira su baba daya bayan daya.
Su kam dukkansu albarka da addua suke yi mini. Suna sake jaddada mini basa jin dar a kaina ba zan kunyatasu ba.
Abida na kira daga karshe, muka sha hira, tana ta tsokana tana cewa "Na ajiye mata kazar amarci a fridge tunda satin sama zata dawo makaranta.
Cikin nutsuwa da tattali muke rayuwarmu. Babu damuwar komai, sai dai ni duk yadda Ake fadin ango na gajiyar da amarya ta hanyar kusantarta a kai kai da sunan doki ban ga hakan ba.
Don kuwa ina amarya ma ba wani sosai ba, sai mu debi kwanaki bai yi ba, illah iyaka idan zamu kwanta zai rungume ni mu yi barcinmu. Hakanan da rana yana dan rungamata da sumba idan zai fita ko idan ya dawo shima ba wai dole ba.
Tuni muka koma makaranta.
Abida ga dawo tana hostel, duk yadda na so ta dawo mu zauna a gidana ki ta yi tare da gabatar mini da hujjar ba zata taba munafuntar iyayenmu ba . Don kuwa ba zasu yadda ta dawo ta tare mini a gida ba. Dan haka ba zata yi kuma a boye ba.
Ko weekend Ina son ta dinga yi mini amma yar ra'ayin rukau din bata gamsu ba. Asalima sau biyu tak ta zo mini gidan.
Duk da na shafe watanni da auren.
Zuwa lokacin kuma na riga na gane Sahal na cikin jerin maza da basu damu da harkar auratayya sosai ba.
Sai dai kuma yana kokarin ya ga ya gamsar da ni idan har an hadun.
Watanni biyar da aure ya samu aiki da Nigerian airways na lokacin. Sun dauke shi cikin jerin lauyoyin da zasu yiwa kanfanin aiki.
Dan haka ya wadata ni da komai na more rayuwa tun daga kan abinci har tufafi duk da yana ganin na lefe da yawa ban waiwaiyesu ba.
Duk satin duniya zai bar Kano ya taho Zaria.
Ranar jumaa da yamma zai zo sai ya yi sammako ya tafi litinin da asuba.
Duk wannan jelen da yake yi, sau daya tak zai neme ni, ma'ana idan ya zo jumaar nan aka hadu to fa sai wata jumaar. A kasan raina ina son ace had'uwar tafi hakan yawa ko da sau biyu ne sai dai kunya da nauyi sun hana ni magantuwa ko nuna wata alamar ina bukatarsa sama da yadda yake.
Mamakin da nake yi, idan har yana gida to kuwaa kusa da ni daf yake zama koma nace a jikin juna, haka idan ina kicin ina aiki to yana gefe yana taya ni tare kuma da kai hannunsa duk inda yake son tabawa baya damuwa ko ya zama sanadin da zai ja ni dakin, yayin da ni kuma nake tsintar kaina na jike jagab.
Sadda muka kammala aji biyu zamu shiga na uku muka koma Kano da zama, baban Zaria ya yi cukun cukun da na koma jamiar Bayero na shiga aji ukun na cigaba da karatuna a can.
Na yi kewar Abida sosai. Duk ba wani zuwa gidana take yi ba. Amma kullum sai na yi mana girki na tafi mana da shi makaranta.
Ban wani sha wahala a B.U.K ba saboda Basma Maska anan take, k'awancenmu ya sake zama sabo mai cike da aminci da nutsuwa.
A lokacin kuma ina a dauke da ciki na watanni biyar.
Ban nemi komai na rasa ba, komai daidai gwargwadon iyawarsa yana yi mini. Haka na yi goyon ciki, cikin kulawa da tarairaiya don kuwa duk abin da nuna sha'awarsa ya dinga siyowa har sai ya gundure ni.
Cikin marka markan ruwa irin na watan Augusta na haifo kyakkyawar yarinya mai kama da Babanta sak. Murna kamar me domin ina son abu maikyau a rayuwata.
Daga shi har danginsa sun nuna mana gata da kulawa domin kaya har rasa inda zan ajiye su na yi.
Haka nawa dangin suka dinga zarya tsakanin Funtua zuwa Kano.
An kawo mini yayar Mami da suke 'yay'an mata zar wacce jininsu ya jitu. Zata zauna da ni idan an yi suna sai mu koma Funtua tare tunda na yi sa'a cikin hutu haihuwar ta zo.
Ya dade da fada mini idan mace na haifa to sunan maman Zaria(Hajiya Rabi) zai saka domin kuwa ta yi masa alakairai daban daban da ba kowacce mace zata yiwa d'an k'anin mijinta haka ba.
Dan haka tuni an yiwa yarinya huduba da Rabi'a
Na lank'aya mata Amrah wanda Abida ce ta zabo inkiyar.
Ranar da ta zo ganin baby ta kula da yadda nake yawan kallon jinjirar ga shi ko ya ya ta yi kuka zan mika hannu na karbe ta.
Tana ganin inna ta shiga bayi ta ce "Wato Maigado kina da zurfafa soyayya. Soyayyar Babanta ce ta shafe ta kike kasa kawaici, ko kuwa kina cikin iyaye masu tsananta soyayyar 'ya'yansu ta yadda basa iya boyewa a gaban kowa?"
Na yi k'asa da kaina domin kuwa na sani Abida ta na fahimtata tamkar yadda ta fahimci kanta.
Ta numfasa ta ce "ki sassauta, ki danne, na sani dole ki so ta, amma dinga yin kawaici a gaban manya, sannan fa ki sani wannan ba taki ba ce tawa ce, domin dai ni ce zan haifo miki ta ki"
Na murmusa na ce "Abida to yaushe za ki mayar da ni uwa tunda har yanzu k'in ki kula kowa bare ki yi aure na saka ran zaki haifo mini tawa".
Ta murmusa ta ce "lokaci ne ai Bilkisu! Idan Allah ya kawo lokacin sai ki ga an yi ko da ban so ba".
Na tabe baki tabbacin ban gamsu ba. Dan dai ban isa yin musu da ta mai yawa bane yanzun nan zata murde mini.
Tunda na yi aure bata yarda ta kwana a gidana ba sai sanadin haihuwar. Daga Zaria ta taho kai tsaye har aka yi suna tana nan. Bayan suna da kwanaki uku ya kaimu Funtua da kansa tare da uban kayayyakinmu.
[8/24, 12:53 PM] Surayya Dee: https://chat.whatsapp.com/KK6YX9u8tej7fpnQUEtvGS?mode=ac_t
*Wannan littafin na kudine pay* *1k via 2384876855*
*Surayya Ibrahim Zenith Bank.*
*A tura shaidar biya ta wadannan lambobin*
# 08032773332#
# 09069067488#
*Littafi na d'aya zai zo kyauta a WhatsAp yayin da na biyu da na uku zai zo a Telegram da arewa ga wadanda suka biya kudin karatu*.
*DINGISHIN KWADO*
*BY*
*SURAYYA DEE*
*MARUBUCIYAR*
*HALIN YAU*
*SABO DA KAZA*
*BAK'AR TA'ADA*
14
Duk yadda Abida bata son yara, haka duk yadda bata bada fuskar da iyayen yara zasu hada ta da hidimarsu bare ta yi musu raino. Amma ta zage da dukkan k'arfinta tana rainon Amrah. Bata son goyo a rayuwarta. Amma kullum Amrah a bayanta take yini bata ko gajiya, kowa tu'ajjibi yake yi, ita kuwa fadi take yi, tunda ita aka haifawa dole ta yi rainonta dan ta ji kanta idan ta tsufa, ko kuma ta yi mata addu'a idan mutuwa ta sure ta.
Ranar da ta fada hakan jikin kowa ya yi sanyi, aka dinga fadin haba autar momi ai ba zaki mutu ba, sai kin haifawa Bilkisu tata diyar da kika bata tun shekarun baya.
Ta murmusa ba ta ce komai ba.
Na yi matukar jin dadin zaman jego a gidanmu domin bana aikin komai tsananin na yi wanka na bawa baby nono sai ko barci. Komai yi mini Ake yi tun daga kan iyayenmu har kan yayyen da kaina. Amrah ta sha gata sosai.
Yaya Faruk kullum ya shigo sai ya saka Abida ta kunto masa ita ba zai bata ba, sai zai tafi ,kaya sosai ya kawo mana ni da ita. Matarsa da k'arfin guiwarta ta zo ganinmu har da turmin zanin goyo.
Haka iyalin Yaya Asad duk da basu zo ba amma kayan azriki mai yawa ya iso mana daga garesu.
An hakura an bar komai kamar yadda kaddara ta zabawa kowa rayuwarsa.
Zarya ta sami Sahal domin duk sati sai ya zo ganinmu.
Yaya Hamida babban galon din sanyi ta yi mini order tare da sauran kayan gyara na maijego ko ma na ce maijego package din gabadaya ta yi mini daga Bojuwa Herbals(08032773332) Kazar sababi ce sai na koma Kano zasu aiko mini. Ni da kaina nasan na hade na matse tamkar ban haihu ba.
Satinmu hudu muka tattara muka koma Kano, saboda hutun makaranta ya kare, ba dan haka ba sai na yi watanni biyu, tunda shi uban gayyar ba mai tsananine sosai ba.
A gugguje nake hakaito muku rayuwarmu ta baya iya wanda zan tuna da wanda yake da mahimmaci shi kawaii zan hakaito dan ku fahimci halin da na shiga ku yi mini alkalanci na gaskiya, dan haka ba zan hakaito wuraren da Basu da muhimmanci ko darasi ba.
Ranar da muka koma ya tisa ni da rawar jiki, ya dinga bare bare har sai da muka kebe sannan na samu saukin bibiyar da yake yi mini. Na zuba masa ido yana gefe yana barcin da ya zame masa ka'ida, matukar ya samu nutsuwa da ni to kuwa idan ya fara barci sai asuba sannan zai tashi ya yi wanka ya tafi masallaci.
Nazarinsa nake yi, na gamsu dari bisa dari baya mu'amala da matan banza. Domin shi gabadaya harkar bata zame masa irin do or die din nan ba. Yana iya sati ko sama da hakan bai yi ba, sai dai idan ya so kuma ba zai taba samun sukuni ba idan ba yi din ya yi ba.
Tsura masa idon da na yi kawai tunani nake yi, yadda bai taba hakaito cewar nima zan iya bukatarsa a wasu lokutan da shi na shi da bukatar. A wanccan lokacin da nake cikin shekarun kuruciya ba zan taba iya kada billena na nemi shi ko nuna masa ina da bukata ba, mussaman bisa al'ada an tafiyar da mu mijine yake da hakki akan wannan al'amarin. Kullum karatun da ake yi mana bita shine duk sadda miji ya bukace ki, to ki bar komai ki amshe shi if not ki fada cikin Allah da ma'aiki sannan ki kwana cikin tsinuwar mala'iku.
A fili na ce "To wai ita mace laifine idan ta bukaci mijinta ko kuma shi miji ba shi da wani laifi idan har sai yana da bukata za'a hadu, ko da ita mace tana da bukata?
Idona ya ciko da kwalla domin a kasar Hausa ba karamin abin kunya ba ne ka fito da maganar da shafi wannan lamarin bare har ka yi korafi.
Yanzun nan za'a yi maka mummunan zaton ka saba ma'amala da wasu mazan ne shiyasa ka raina kokarin mijinka daga yin aure shekara daya tak.
Na tuna sadda nake da watanni biyar da aure da na yiwa yaya Hamida korafi akan shaanin ban fahimce shi ba, ba karamin kunyata na yi ba.
A hakan na ba haka siddan na yi mata korafi ba. Maganin sanyi da na mata take ta aiko mini, na gamsu da kyaun kayan Bojuwa Herbals tunda tabbas daga Chad suke kawo wasu saiwowin. Mussaman na sanyi da na dahuwar kazar sababi. Akai Akai Yaya hamida take yin order duk sadda zata siya Kuma tare take siya mana, sai a kawo mini gidana ni sai na tura mata nata Kaduna tunda a can take aure.
A duk sadda na ci kazar sababi din nan yini nake yi cikin wani hali, idan kuma shi bashi da bukata sai dai na gama tsiyayata ni kadai.
Sa'a daya ma sanyi flusher da yake da tasiri nan da nan mai ciki bata sha.
08032773332 order ur sanyi flusher and kazar sababi now.
Dana gaji ranar da ta ce za'a kawo mini na ce mata "Yaya Hamida ni kam Kar a kawo mini, domin gaskiya ni ban wani gane kan abin ba, sannan ba kullum ne ake yi ba."
Salati ta dinga yi tana fadin "Bilkisu ashe baki da hakuri? Har yaushe aka yi auren da za'a ji wannan maganar a bakinki?
To gyara ba dan mijinki ya gamsu zaki yi ba? Duk macen da zai taba nan gaba sai ya gane ke ta dabance. Ni din nan sai da na yi haihuwa uku sannan na gane kan lamarin ban kuma fasa gyara kaina ba.!
Na yi sakato ina sauraren yadda take kunfar baki.
Kunya ta kama ni. Haka na ajiye wayar ban iya cewa komai ba. Hakan da ta yi mini ya sake sakawa na kame bakina ban sake bude maganar ba.
Kan dole na tashi na yo wanka, na gyarawa Amrah kwanciya sannan na kwanta don nasan ba zata farka ba sai asuba.
Tare da shi muke rainonta, Indai yana gida yana bata lokaci wajen rike mini ita. Haka nan siye siye kayan ci da na wasa tun ba'a zo lokacin bukatarsu ba ya yara mata su masu yawa. Haka nima suturar da yake yi mini tamkar an yi masa gorin yana yi mini kwangensu, komai fa ban nema na rasa ba. Shi dai inda mace tafi bukatane hankalinsa baya kai ainun. Don kuwa tunda na haihu sai ya zama dalilin da rungume ni da yake yi idan zamu yi barci ya daina. A bisa hujjar ba za'a bar yarinya a gefe ita kadai ba.
Yarinyar ta shiga ransa ainun ga shi tana girma kammaninsa na sake bayyana a tare da ita. Bayan haka kullum cikin tsabta yake ganinta da kwalliya, ko da fara tumbidi bana gajiya da gyarata don gudun kada a ji karnin nono tare da ita.
Sosai muke zaune lafiya bani da matsalar danginsa ko rashin wani abu. Idan ya kaini makaranta ko idan ya samu sararin dauko ni da yawa mata kallon so da birgewa suke binsa da shi.
Domin kwarai da gaske mai kyau ne, duk da siririne sosai.
A hakan har Amrah ta shekara tana kuma tafiya.
Bani da kawa sai Basma kusan a Kano ma bansan kowa ba sai ita. Shiyasa muka kulle muke aminci tamkar jinine ya hadamu.
Mun kammala karatunmu na fara bautar kasa a cikin Kano bayan an yi cuku cuku an maido ni domin da jihar Bayelsa aka tura ni.
Amma ban je can ba a dalilin an mini marriage certificate. Da taimakon baban Zaria aka bar ni a Kano.
Basma ce aka tura ta jihar jigawa. Satinmu biyu da fitowa daga camp aka bikinta, sosai muka yi hidima ni da Abida, min halarci bikin har Katsina inda aka kaita muka je kai Amarya.
Lafiya lau muke rayuwa har zuwa lokacin da muka shafe shekarun biyu har da watanni ba zance ga babbar matsala a aurena ba.
Na farko Sahal ba shi da takura, ma'ana baya mini kullen nan, shi dai kafin na fita ma sanar masa, ko daga makaranta ne na so wucewa wani wuri ba shi da matsala da hakan matukar zan kira shi na Sanar masa. Haka nan akai akai zai kwashemu mu je restaurant mu yi dinner mu dan zaga malls ya mana siyayya.
Bana rasa kudi a hannuna don baya mini shamaki da kudinsa.
Kawai inda matsalar take sha'awarsa akan mace ne ta yi mini kadan. Dan muna nisa abin na sake yawa, a farkon zamanmu baya wuce sati bai nemi ni ba, amma a yanzu sai mu kwashe kwanaki goma har a d'ora.
Idan aka dauke wannan matsalar bansan matsala a aurena ba. Wasu dararen haka zan yi ta hawaye marar sauti, har barci ya sure ni. Ba Wanda nake son na tattauna wannan matsalar sai Abida aman babu dama dan kuwa ta rufe dukkan amincin da zai sa na kai mata korafin aurena.
A lokacin kuma tuni Yaya Munira ta yi aure amma ba'a kasar take ba, tana Paris, tana ta zurfafa iliminta na lauyanci.
Yayin da Abida na daf da kammala karatun likitanci.
Har kuma lokacin bata bada kofar da zata yi saurayi bare a yi mata maganar aure.
Kwanci tashi asarar mai rai Amrah ta yi watanni goma sha bakwai a lokacin kuma mamanta Abida ta zo daga Zaria ta dauketa suka tafi Funtua zata yayata. Tun watanni biyu na so yayeta domin komai ci take yi sannan kuma ta jima tana yawo ma'ana ta jima da yin kafafuwa, ga ta doguwa tamkar Babanta.
Abida ce ta ki amincewa bisa hujjar Indai itace uwarta, itace zata yaye ta to sai ta samu dogon hutu. Sosai Amrah ta saba da ita. Dan haka bata yi mata kuka ko rikicin yaye ba.
Sannu a hankali rayuwa take tafiya. Ban jima da gama makaranta ba na fara sana'ar kayan fulawa(snacks) tare da abincin yara. Kamar na fada muku na karanci nutrition and dietetics. Muna yawan zuwa kauyuka da asibitoci muna wayarwa jama'a hankali akan abin da ya kamata su dinga bawa yaransu da su kansu saboda lalurar tamowa tana yawaita a kan yaran karkara.
Bincike kuma ya nuna na rashin isesshen ().
Dan haka sai nake yawan rubuce rubuce cikin harshen Hausa da na Ingilishi a kasar sadarwa ya Facebook a lokacin ita kadaice kafar sadarwa da zaka dinga yada manufofinka.
Dan haka na tara mabiya sosai, cikin hikima sai nake tallata hajata na bakery da nake yi. Cikin kankani lokaci na samu karbuwa domin a Kano kusan duk manyan bukukuwan da za'a yi ni nake aikin kayan snack da drinks da za'a sha a bukukuwan.
Sosai Ubangiji ya sanya mini albarka. A hakan Kuma Sahal bai taba kin yi mini hidima dan yana ganin ina samun kudi ba.
A shekarar da Abida ta kammala karatunta ta zama likita ta fito a matsayin physician.
Na haifi namiji. Domin walimar da su baba suka shirya mata na je da tsohon ciki, na dawo Kano da kwanaki uku na haifo yaro lafiyayye fari tas. Sai dai wannan kama yake yi da ahalina, ma'ana dangina ya kwaso.
Cikin kyautatawa Baban Amrah ya bani dama na zabi sunan da za'a sakawa yaro. Kaitsaye na ce masa "Yaya Faruk nake so na yiwa takwara".
Ba ja in ja, take ya yiwa yaro huduba da sunan Umar Faruk. Tare da fatan ya samu albarkar da yake cikin sunan, ya kuma gaji kirki da fara faran din mai sunan nasa.
Na fahimci har zuciyar Sahal na ganin k'imar Yaya Faruk yayin da ko ambaton Yaya Asad ba ya son a yi a gabansa balle a je ga jallin yin hirarsa.
Cikin nutsuwa nake jegon yaya Faruk domin har mun lankaya masa inkiyar, amma da Yaya Faruk ya zo ganinsa ya bada umarnin a kira shi da Faruk dinsa indai shi aka yiwa mai suna to a kira shi da sunansa kamar yadda shari'a tafi so.
Shike nan ake ce masa Faruk yayin da ni sai na hada da Yaya Faruk ko ma na ce yayana kawai.
Wannan karon umma da zo mini zaman jego sati uku kawai ta yi mini ta tafi nisa hujjar mijinta ba ya jin dadi, abokiyar zamanta. Dan haka saddiqa autar Mami da a lokacin tana aji hudu na sakandire sai aka turo mini ita tunda basu jima da yin hutu ba. Amrah kuwa dama tana Funtua wajen Mamanta duk da Abidan Mami ta barwa ita domin tana yin Housemanship a generall hospital Katsina.
Ban jima da yin arbain ba aka yi auren Anisa kanwata da take bin Ansar.
Hatta baba babba bai so aka yi auren Anisa ita kadai ba, ya so ne a hadasu da Abida amma ta kafe akan ita bata sami miji ba. Dan dan haka ayi auren Anisa tunda ita ta samu miji.
Akan dole aka yi bikin Anisa Wanda a lokacin tana shekarar karshe a nursing school ta Kaduna.
An rasa gane inda Abida ta saka gaba akan aure. Gabadaya ta ki daukarsa da muhimmanci, ta ki bawa kowa fuskar da zai tunkare ta. Wani malaminsu a nan jamiar Ahamadu Bello ba irin nacin da bai yi mata ba. Sadda zata zo Kano da na haifi Yaya, zata kwana daya, sai ta dauki Amrah su wuce Funtua, yana jin ta zo Kano ya biyo ta daga Zarian, falonmu aka sauke shi.
Aka kai masa samosa da meat pie tare da lemo da ruwa.
Bai wani jima ba ya tafi. Na kuma tabbatar sallamarsa ta yi, ta hanyar gabatar masa da tana da uzzirin da zata yi a lokacin.
Cikin kwantar da murya na ce "Autar momi wannan kam ya yi ba shi da kyau sosai, sannan cikakken jikine da shi, ga shi d'an boko ne irinki."
Fuska ba walwala ta ce ",Ko kusa da yi bai yi ba, Bilkisu. Kinsan har yanzu bai tunkare ni kaitsaye ba sai dai hannunka mai sanda tare da gifts din da bazasu rude ni ba. Mafi muni ma rainon yaransu zan yi masa. Matarsa ce ta rasu 7months ago. Ta bar masa yara biyu duk maza. Shine yake neman wacce zai aura ya mai mata lalurar yaransa idan kuma ka ce ba zaka yi ba society ma ba zai maka adalci ba, idan kuma ka karba yaran kana musu hidima su yi ta azabtar da kai, kuma ubansu ma ba yaba maka zai yi ba.!
Ta muskuta ta ce "Kin ga na yi kama da wacce za'a aura dan ta yi rainon yara? Ko kin ga na matsu da yin auren ne bare har a yi