yar fira a hankali, yana amsata a nutse har suka karaso filin jirgin
Da kula yana dubanta ya ce" Gine ginen kamfanin tatar mai ya yi nisa tuni....., na makarantun reshen nawa na nan ma, haka kuma sauran kamfani irin su harkar shopping da sauran su..........., ki shirya zama da mijinki a kusa ok.....?"
Murmushi ta yi ta ce" Na fi kowa murnar haka, Allah ya kawo min kai lafiya...."
Daga haka ta fita daga motar, ta nufi sama, yana kallonta sai da ta shige wajen da kawai zata karasa ne a yi mata duk procédure din da zai bata damar zuwa wajen da zata zauna daga jirgi ya zo sai shigewa , wanda aka tabbatar masa nan da minti ashirin zai sauka, nan da minti goma zasu rufe enregistrement (registration), sai tafiya Nijar.
Motarsa ya ja ya nufi gidansa dan sai ya huta sosai zuwa yamma sai ya je gidan su Abdul bassit, domin yana son ganawa da mahaifin su, wato sir .
MAZNA kuwa bata tsaya bata lokaci ba ta wuce sama ta zauna lokaci daya ta shiga kiran yan uwanta, kowane ta bashi aikin da zai mata, sannan ta kashe wayar ta ringa maimaitawa zuciyarta cewa komai zai je mata yadda take so, zata je ta samu abinda take so a kan kari, kuma zata magance damuwarta......,
Ana daf da fara kira wanda ke kula da harkar tafiye-tafiyen su ya zo mata da komai bayan ya gama yiwa kayanta registration ya bata
Cike da jin haushin sa ta amsa ta mike tana saka bakin glasss din ta ta nufi filin da jirgi yake da jakarta ta hannu karama mai dauke da yan abubuwan bukatar ta, kwarai yana bata haushi wannan Aliyun domin mutun ne na gaskiya wanda babu wata hanya da zaka iya bi ka sa ya ki bin umarnin uban gidansa, kuma in dai a nan ne ta ciri tikiti to tabas sai an bashi allrt, shi yasa ta so daga ta tashi ta yi shatar mota a kai ta RIYAD wato baban birnin Saudi Arabia ta je aéroport din cen direct ta samu jirgi a filin jirgin sarki Khaled (RUH), sai gashi sun bata mata komai........
(Wannan kenan....)💅💅💅💅💅💅💅💅💅💅
*KISAN MUMMUƘE*
💅💅💅💅💅💅💅💅💅💅
_PAID BOOK_
*BY*
_SAJIDA NIJAR_
*Yan Naija Mutanen mu 1k ne a kan wannan account number 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank* sai a bani shedar biya ta layi na kamar haka +22793811618
*Yan Nijar mutanen mu zaku turo da hoton kati ta airtel ta dala dari , wato 500francs cefa a kan Numbarna kamar haka +22793811618*
*Na gode, sai kun zo.....taku ce SAJIDA NIJAR*
Tallah tallah tallah
*JAMA'A NAZOMUKU DAWANI TSARI NASAMUN KUDI TA HANYAR AMFANI DA WAYAN HANNUNKU
WANNAN TSARIN SHINE METAFORCE
MENENE KASUWANCIN METAFORCE* ????
*Metaforce kasuwancine ingantacce halattacce Wanda yake biya 100 💯 Wanda ake Gudanar dashi da wayar hannu,METAFORCE is also a part of network marketing,is a 100 percent decentralized project da aka daurasa Akan Blockchain technology Wanda babu wani mahalukin daya Isa YAYI editing,hacking ko deleting wani abu acikin sa,Kuma yanada matakai yanada rassa Wanda kowane reshi ka rike a METAFORCE to ka samu GUDUMAR DUKAN TALAUCI*🌎
METAFORCE ANASAMUN KUDI ACIKINSHI SOSAI MATUKAR ZAKAYI ABUNDA AKEBUKATA
zaku iyahada miliyoyin kudi aranadaya acikin wannan kasuwanci me albarka in sha Allah
Duk wacce tashirya zata iya tuntubanmu akan wannan number
09136899615
Hajja Data
*10*
Nijar
Yau kam kamar da wasa Imtee ta shirya dan tafiya makaranta ba tare da kowa ya takurata ba
Sosai auntyn yara ta ji farin cikin ganin wannan lamari har ma ta budi baki tana dubanta ta ce" NUR, Allah ya tsare, ya sa ku dawo lafiya"
A'isha ce kawai ta iya amsawa, ita kuwa murmushi kawai ta yi zuciyarta na daukan wani salon harbawa daban , sai dai bata iya budar bakinta ba dan tana gudun ta bada amsa maman yara ta yi fushi domin tana tsaye tana jira su fice, hasali ma da ta shirya dan tafiyar tasu sai da maman yaran ta mata tsaye kan abinda zata saka, ta sa ta saka abayarta ta sallah harda takalmin Sallah sannan ta ringa tuna mata ta fa je gidan kawar tata, kasa kasa ta yaɗa ba wanda zai ji
A nutse suka fice suka dauki hanya suka karasa makarantar
Sosai suka sha mamakin ganin wani fitinanan ginin da aka dauko na makarantar ya zamo an mayar da yan makarantar gaba dayan su cen bangaren da malamai ke zama a da, an sayi manyan filaye an hade an tada manya manyan gini a kwanakin nan da suka yi basu zo makarantar ba, wanda ko su da ba architect ba sun gane cewar ginin nan ba na wasan yara bane ake rantsawa...........
Ajin su suka shige, malamar hadisi ta shiga da lokaci ya yi ta shiga amsar harda, ya zamo du Wanda bai bada harda ba sai ya sha bulala, ciki kuwa harda Imtee domin bata iya ba, hakan ya sa Malama ta daki hannayanta sosai ta bata punichment a kan lalle lalle ta fita ta zagaya baya wajen shukoki ta dauki hadisin nan ta zo ta bada Tata hardar, saboda sabuwar tafiyar da za'a yi ta makarantar ya sa an dakatar da malamai da yawa, ana cen ana yi musu gwaje gwajen da zai sa a ware wa'inda suke da ilimin a sake saka su aji su din ma dan a kara musu stratégie na koyarwa ta yadda zasu zama basa shafuwa a wannan fanin, domin kamar yadda makarantar Saudiya take ne ake so a yi, ta yadda in dai ka shiga tun daga kan Kur'ani har larabcin kansa zaka iya ka goge a dan kankanin lokaci da izinin Allah
Litafin kansa bata da shi bale har a kai ga maganar ta iya karanta shi, ta amshi na kawarta wato Fa'iza ta fice ranta a mugun bace, idannuwanta kuwa sun gama kumbura da abin kukan da ta ci ta nufi baya cike da tunanin ai kuwa sai dai ta wuni a bayan nan dan ita ba iya karantawa ta yi bama bale har ta bada hardar Gashi dan bakin hali irin na Malama du Wanda bai kawo hardar ba kawai wani wajen take tura shi ya dauka bata bari sun hadu da wanda ya iya bama bale wani ya koya mata.
Kujeru ke ajiye jifa jifa irin masu dadin zaman nan a katon gardin din
Tunda ta karaso mutun daya jal ta samu, mace , wace sam bata gane ko wacece ba, domin tana sanye da nikaf din ta ne harda su Safa da katon hijab baki sidik kuma tana amsa waya, duda ba'a jin amon muryarta ama irin yadda ta saka hannu wajen kunne ke nunin waya take yi
Waje Imtee ta nema ta zauna, ta shiga bude littafin nan tana bi da kallo
Ga dai harufan nan, ga rubutun nan , ga komai ama ta kasa hade na Hausan ta karanta ma bale a kai ga larabcin, to a ina ta tsaya ta wani iya karatun Hausan da ake musu a makaranta? Da ace da dan turancin ne ma da tabbas ta maida hankali ta ɗan gane wasu abubuwan......
Ta rasa yaya zata yi, ga hawaye lokaci zuwa lokaci yakan dan sauko mata kadan sai ta share ta ci gaba da kallo ba tare da ta san matar nan ta gama wayar ba ita take kallo tun dazu
A hankali ta mike ta karaso inda Imtee ke zaune, a tausashe ta yi mata Salama sannan ta tsaya tana jira ta bata dama ta zauna
Imtee ta dago tana amsa Salamar hadi da zuba mata ido, dan gaba daya ita ba wani yarda ta cika yi da masu saka abubuwan nan ba, a cikinsu babu wanda babu harda aljannu.
Murmushi Anna ta yi a hankali ta ce" Ki bani dama in zauna mana y'ata???"
Kwarai ko daga muryarta zaka gane kamar ba yarinya bace, sai kuma da ta ambaci Y'arta sai ta gane cewar lalle ba yarinya bace a bayan nikaf din nan, dan haka sai ta mike tana fadin" Yi hakuri, Bismillah zauna"
Sannan ta juya da nufin tafiya
Anna ta ɗan sake gyara tsayuwarta ta ce" To ai tare nake so mu zauna din, kuma sai ki tafi?"
Imtee ta juyo da dan yannayin son sanin dalili, sai dai bata yi tambayar hakan ba, hasali ma sai ta nunawa Anna litafin ta ce" Zuwa zan yi in nemi wani ya koya min, saboda Malama tace idan ban kawo harda ba dukana zata yi, Ni kuma ban son Duka......"
Ta karashe idannuwanta na yin raurau
Anna ta zuba mata ido, a nutse ta ce" To ke ba zaki dauka da kanki ba? Kuma me yasa baki dauka a gida ba?, sannan ya aka yi kin san kina tsoron duka ama kike kin daukan karatun ki a gida? Ko na boko kika fi dauka ne y'ata? Zo zauna ....." Ta karashe tana nuna mata daf da ita a nutse, hakan ya sa ta bi hannun Anna da kallo sai kuma ta zo din ta zauna ta ajiye litafin a saman cinyarta ta sauke ajiyar zuciya
A raunane ta ce" ban iya tada baƙi ba, bani da komai da ya shafi hanyar tada baƙi, ban san komai ba ban iya ba"
Da mamaki Anna ta ce" Baki iya ba?, yaushe aka saka ki makaranta?"
Imtee ta dubi Anna , a hankali ta ce" Tun muna yara muke tafiya, ama ni ba kulun nake zuwa ba sai na ga dama, dan mama tace islamiyyar ma ai ba dole bace, ban yi boko Bama bale wata islamiyya....., auntyn yara ce idan ta ji abinda ya hana ni tafiya bata kyale ni, babanmu kuwa shi ya ciro mu daga wancen islamiyar ta gangare ya dawo da mu nan....."
Kan Anna ya so daurewa....., Mama? Mahaifiya? To me ya samu uwar yarinyar nan marar dadi haka?, menene dalilin da zai sa uwa ta ki d'anta na cikinta zuwa neman ilimin da zai zamo garkuwa a gare shi duniya da kiyama?????, sai dai ganin cewa yau suka hadu da yarinyar sai bata kureta ta tambayoyi ba,
A nutse ta ce" To abinda za'a yi, ki bude hadisin naki, in koya maki yanzu ki shanye, ama sai kin min alkawarin wani abu idan har kin yarda......"
Imtee da ta ji zuciyarta ta yi sanyi jin za'a koya mata, ba zata sha wani dukan ba da farin ciki ta dubi Anna ta ce" In sha Allah, Ama menene?"
Anna ta yi murmushi, dan ƙarara take ganin wayon yar budurwar, kawai dai akoy wani abu dake faruwa da ita ne wanda a hankali zata san ko menene, idan bata da wayo ai kai tsaye zata amince da alkawarin da bata dan ko menene ba, domin alamu sun nuna a matse take so take yi ta koyi hadisin nan
A tausashe Anna ta ce" Alkawarin daya ne jal, zaki dage ba ji ba gani wajen ganin kin iya tada baƙi, shi ne shinfida a matakin koyon ilimi, ya zamo kin iya karantawa da kanki, sai kuma ki koma baya a karatun da kuke, dan na tabbata hadisin nan baki iya na bayansa ba, ko kin iya???"
Imtee ta zuba mata ido, to ba hadisi ba, ai ko surar da suka yi harda wancen satin ita ta manta wasu abubuwan a ciki, domin ba tilawa take yi ba, bakinta ta yi kokari ta rike inda in an zo zata karanta dan kar a dake ta, daga nan an wuce wajen, dan ko a makarantar aka fara tilawa lungu take samu ta ja hijabinta har kusan idonta ta nemo barci,dan gani take yi ai wani nacin zance ne, abu idan aka yi daya ya wadatar ba sai an ba sha'a wahala ba
A hankali ta ce" Bani da litafin komai , bani da wanda zai koya min wanan, a ajin mu an yi nisa sosai ai Mama"
Anna ta yi murmushi tana sake riƙe litafin hadisin ta ce" Baki san cewa a makarantar nan ko wani aji kake idan kana da abinda ya shige maka duhu kana da damar zuwa ka fada, kuma za'a kula da kai har sai ka samu haske a lamarin? Ko kin san cewa a sababin dokokin da aka zuba bama za'a amshi dalibin da bai iya tada baƙi ba?, idan kuwa iyayensa suka nace a dauke shi sai sun saka hannu cewar aikin ba na makaranta kadai bane a dan kankanin lokaci ya iya tada baƙi ta yadda karatun ba zai bashi wahala ba?, yaya ake yi kuna iya shanye abcd kamar ruwa ba wahala aman alif ba'un ta'un ya zamo rikicin kwakwaluwar ku bayan duniya din nan hanya ce da muka shigo zamu wuce mu je inda zamu yada zango, wanda a hanyar nan tamu ne zamu yi guzurin abinda muka ga ya fi yi mana ta yadda zamu samu wajen zama a inda zamu tarda matsayin sakamako wato wuta ko gidan aljana?"
Imtee kawai ido ta zubawa matar ta kasa motsi, har sai da Anna ta ce" Hey....., kina fahimtar abinda nake fada kuwa? , shekarun ki nawa??"
Bakin Imtee na dan rawa ta ce" Sha....sha.....sha tara"
Anna ta lumshe idannuwanta, a hankali ta ce" To shikenan, its ok, kar ki saka tsoro a ran ki, in sha Allah kafin a zo tantance yan aji zamu yi kokari Ni da ke ya zamo kin karanta du inda za'a bude maki kin ji?"
Da dan tsoro Imtee ta ce" Tantancewa? Muma dake cikin makarantar a cikin hatsari muke mama? Ana iya korar mu?"
Anna ta fuskance ta, a tausashe ta ce" Kun fi kowa zamowa cikin hatsari, bale idan har baku mayar da hankali ba, akoy jarabawa da za'a ringa yi du wata uku uku, wace idan aka fuskanci kawai kai baka son karatun ne za'a salame ka, har sai iyayenka sun zo da kai ka fada da bakinka cewa zaka gyara, da wannan za'a baka dama , idan ka gyara sai a ci gaba , in baka gyara ba sai a salameka gaba daya, mai makarantar ya fada ne ba zai dauki du wani lako lako ba, du Wanda ya kawo d'ansa ya tabbatar da ya kawo shi a koya masa kuma zai dage ya koya.....ke Bakya sha'awar son ganin ki gobe a musabaka? Ko Bakya sha'awar ace gobe ga ki nan a Saudiya kin ciyo mana baban rabo....? Yaya sunnan ki ma????"
Imtee ta ɗan bude bakinta a hankali ta ce" Im....immmteee"
"No na kirki nake son ji" Anna ta fada a tausashe
Imtee ta ce" HALLAH ne"
Anna ta yi murmushi ta ce" Masha Allah, kin san tarihin mai sunnanki kuwa?"
Imtee ta girgiza kai
Anna ta ce" mu yi karatun idan muka gama sai mu je in baki dukan abin bukata na karatun, sai kuma mu ɗora lokacin da zan ringa koya maki kulun a nan, ya zamo idan aka tashe ku ne, ko kafin a shiga aji ne, ko dai-dai lokacin da ake baku na hutu da cin abinci... Kin amince?.."
A hankali Imtee ta gyada kanta sannan ta gyara zamanta ta nunawa Anna wajen, Anna ta shiga koya mata a hankali , a nutse, hade da fasara da komai, wanda minti ashirin tuni har ta shanye ras ya kuma zauna a kanta , a lokacin ne Anna ta mike ta fara yin gaba a nutse, Imtee na biye da ita cike da mamakin wai wacece matar nan? Suka nufi baban office din makarantar tana kula du inda suka zo ma'aikata sai su miko gaisuwar girmamawa har suka je kofar office din ta ga ta saka yar yatsarta wajen empreinte ya bude ta shige kafin ta juyo dan ganin idan imteen tan shigo, nan ta ga ta tsaya tana kallon ta ta kasa shiga din
Nikaf din fuskarta ta dage, yayi dai-dai da bugawar zuciyar Imtee sakamakon kyakkyawa, ni'imtaciya, sananiyar fuskar da ta bayyana a gabanta mai cike da kamala wace tsoron tashin hankali ya kamata a lokacin da ta gane dama fuskar nan fa ta taɓa gani sau daya jal a lokacin da aka musu wata gabatarwa ta baban screen din computer matar na murmushi kamar a fuskarta aka zano shi, sai hannun namiji a gefen kafadarta rike da nata hannun wanda ta ɗan daga ta sama sama haka ta rike, Ama nasa ya cika nata sosai alamu na namiji ne kuma namijin ma ba karami ba, sai muryarsa da ya yi larabci wanda suka jima suna kus kus din ai Balaraben Saudiya ne, meye meye dai sanadiyar basu da amsa suka zubar da zancen suka dangana.....
A hankali ta ɗan daga kafarta da nufin yin baya
Ku gane, ire Iren maganganun dake tashi a kan dangin baiwar Allahn nan ba kadan bane, kai hatta uwar dukiyar da ake hange daga waje ba'a riga aka shiga cikin gidanta ba cewa ake yi wai harda yankan kai suke yi......to ita ta ina, ta yaya zata yarda ta shiga office din nan daga ita sai ita ta wule kanta????
Kara daga kafa daya ta yi ta yi baya jikinta na rawa.....
A taudashe Anna ta furta" HALLAH, Bismillah????"
Imtee ta girgiza kai a hankali, kafin ta juya da sauri ta yi gaba harda dan gudu gudun ta.
Anna ta bi ta da kallo kafin ta yi murmushi ta rufe office din ta karasa ta yi bayi dan dauro alwallah domin lokacin sallahr azahar na kusa, ita kuwa dama takan yi alwallah ne ta yi jiran SALLAH wani lokacin har awa biyu saura ko fiye da haka.....
Imtee kuwa du ba a cikin hayacinta ba ta fice a makarantar da dan sauri domin lokacin sauka ya yi bai fi minti ashirin ya rage a sauko su ba, hakan ya sa mai tsaron dan matsawa saboda get dama tunda aka fara aikin nan a bude yake sosai ana kai kawo da harkar kayan gine gine
Cikin sanda ta fito a hankali ta dauki hanya tana tafe tana dan waige waige dan gudun kar ta hade da masu kula da su a cikin makarantar .................
Daf da ita yayi parking din motarsa, tunda ta fito ya saki murmushi domin ya fi minti talatin a kofar nan yana jiran tsamani dan a jiya da dare da ya matsawa Fa'iza kan lalle lalle sai ta raka shi gidan su ko ta bashi numbarta , fa'izan tace yayi hakuri yau ya zo su hadu idan ta bada damar ya je gidan su sai ya je, bata da waya an hanata rike waya a gidan su kwata kwata........
Tsorata ta yi sosai da farko, sai da ya zuge madubin motar ne ta ga ko waye sannan ta sauke wata boyayiyar ajiyar zuciya lokaci daya tana furta" Da kai ne.....?"
Da alamun tambaya ya ce" to wa kike jira da?, waye ya biyo ki kika Tsorata haka?"
Tana dan haki ta girgiza kai hadi da fadin" Ba komai "
Murmushi ya yi ya ce" Zagayo ko shigo mana in kai ki gidan , yau ke daya ce???"
Motar ta bi da kallo, a cenn kasan zuciyarta take jin kamar ba dai-dai bane haka kawai ta fada motarsa , domin bata ga wata shakuwa ko dalili mai karfin da zai matse musu waje har haka ba, sai dai hudubar maman yara ta gama rike mata zuciya a lokacin da ta tuno bayanan ta, da irin yadda ta nuna mata tashin hankalin da take ciki na rayuwa wanda ta tabbatar mata idan ba ita ba waye zai fitar da ita daga kangin talaucin nan ne? Sai kawai ta sake duban fuskarsa a hankali ta ce" Motar taka kake so in shiga????"
Kai ya langwabar, a matukar raunane ya ce" eh, idan har kin yarda da Ni, ki yarda cewar son ki nake yi, ba zan iya cutar da ke ba, ki shigo Mu je dan burina in adana ki , in hana ranar nan dukar min wannan fatar taki mai tsananin haske da shiga zuciya........"
Tunda Imtee take bata taɓa soyayya ba, bale har ace wai irin kalaman nan ba zasu shige zuciyarta ba
Kwarai suka shige zuciyarta da gudun gaske har ta ji numfashinta na karbar kalaman da kyau da kyau
A hankali ta zagaya ta saka hannu ta bude ta shiga motar hadi da rufewa sannan ta rintse ido tana sauke ajiyar zuciya
Wani farin ciki ya ringa ji a zuciyarsa da tunanin ashe ba zata masa taurin kai ba......? Ta yiwu itama ta gama kamuwa da kaunar tasa.............
Da kula ya ce" Shashekar me kike yi haka ? Me ya koro ki?"
Gaba daya ta manta cewar a gidan matar da take gudu yake aiki, sai kawai ta gyara zama irin hankalinta tashen nan ta shiga koro masa bayanan yadda suka yi da Anna, gaba daya ta karashe da fadin" Ban san ita bace, da ba zan taba yarda mu yi doguwar fira haka ba, ta yiwu ta mana min Numbar yan yankan kai a jikina ta yadda da sun gani zasu gane Ni? Dan Allah duba ka gani? Cewa ake yi dukiyar mutanen nan harda tsafi a cikinta!"
Ido ya fara zarowa jin kalaman ta, kafin ya ce" Kina nufin Anna ce ta yi maki magana da doguwar fira haka har ma tace ki shigo office din ta kika gudo?"
Imtee ta zuba masa ido ta kasa amsa shi, saboda a bayane yake yannayin maganarsa wata iri ce, ita gaba daya ma bata san wace Anna ba, sai kuma tunawa da ta yi cewar shi fa ma'aikaci ne a gidan mutanen nan sai ta ji jikinta ya yi sanyi
A hankali ya ce" Waye yace maki jita jita kowace ake kamawa?????, Dube Ni, fuskance ni ki ji, shin zaki iya yarda da maganata kuwa? Look at me NUR "
Duban nasa ta yi ido cikin ido, domin ya kama sunan da du idan aka fada sai ta tsayar da abinda take yi ko menene
A tausashe sosai ya ce" Waye yace maki mutanen nan yan yankan kai ne?, kin kuwa san su wanene su?, Shikenan ba za'a iya tara dukiya ba sai an yi mata fasara? Allah ne fa, yana iya malakawa bawa abinda ya fi wannan, ai an yi a zamanin su karuna ko?, haba NUR yannayinki kin yi kama da mai hankali, bai dace jita jita ta ringa shiga kwakwalwar ki ba, Fisabililahi a firar da kike nufin kin yi da Anna a shekarun da na dauka ina aiki gidan su ban taba yin doguwar fira irin haka fa ita ba....., tabbas irin yadda kika kama zuciyata farat daya dama na san ke din nan y'ar baiwa ce........., Ama in tambayeki a kaf firar da kika yi da ita har kuka gama kin ga alamun cutarwa a tare da ita? Kin ji a jikinki zata iya cutar da ke?"
Imtee ta sada kanta, wani gefe na zuciyarta na ce mata yaya za'a yi ya kasa kare iyayen gidansa to? Wani sashi na zuciyarta kuwa na tuno mata irin nutsuwar da ta shiga na dan lokacin da ta yi fira da matar nan, a lokacin da ta fara koya mata karatu kuwa sai ta ji kamar da yaran Hausa kadai take yi mata bayani irin yadda ta bata lokaci, ta bi ta a hankali, ta yi mata koyarwa mafi sauƙin da kanta zai iya dauka......., a gaskiya idan tace ta ji kanta a hatsari a katon gardin din nan daga ita sai matar nan ta yi karya, dan haka a sanyaye ta girgiza kanta
Murmushi ya yi ya ce" To kin ga, sauka zaki yi ki koma ki amso littatafan sannan ki bata hakuri, matar nan idan har ta yarda da mutum in sha Allah ba zata cutar da shi ba, a lokacin da na je gidan su neman aiki zuwana ya fi a irga, ban taba samun dama ba sai ranar da Allah ya sa ta dawo daga anguwa , ita ta sa aka saurareni , tana jin bukatana ta tambayeni karatun da na yi, Ni na sanar mata bakina secondry, aiki nake nema da zan taimaki iyayena, shine tace na iya mota? Na nuna ban taba jan mota ba, nan ta ce in hada takarduna in kai baban makarantar koyar da mota idan na je in ce SIR IMAD ya