Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 9
marikiyarta ce ta saka mata IMTEE, Ama sunnanta na gaskiya shi ne *HALLAH* an ce ta ci sunan mahaifiyar mamanta ne wai......" Murmushi ya saki ya dubi mahaifiyarsa yace" Ke da kanki kin san ai itace ta dace ta zama surukarki............ Duba fa ki gani.....MRS ANAS HALLAH.............mts kama sauran kudin kawai , Allah ne yayi yau za'a cire ni koda bana so" Ya mika musu sauran kudin ya nufi dakinsa sai sake murmushi yake yi da nufin da an jima zai kirayi Fa'iza ta bashi numbarta, kai idan ya samu a yau sai ya je zance inda take, sai dai idan bai samu hakan ba! *JAMA'A NAZOMUKU DAWANI TSARI NASAMUN KUDI TA HANYAR AMFANI DA WAYAN HANNUNKU WANNAN TSARIN SHINE METAFORCE MENENE KASUWANCIN METAFORCE* ???? *Metaforce kasuwancine ingantacce halattacce Wanda yake biya 100 πŸ’― Wanda ake Gudanar dashi da wayar hannu,METAFORCE is also a part of network marketing,is a 100 percent decentralized project da aka daurasa Akan Blockchain technology Wanda babu wani mahalukin daya Isa YAYI editing,hacking ko deleting wani abu acikin sa,Kuma yanada matakai yanada rassa Wanda kowane reshi ka rike a METAFORCE to ka samu GUDUMAR DUKAN TALAUCI*🌎 METAFORCE ANASAMUN KUDI ACIKINSHI SOSAI MATUKAR ZAKAYI ABUNDA AKEBUKATA zaku iyahada miliyoyin kudi aranadaya acikin wannan kasuwanci me albarka in sha Allah Duk wacce tashirya zata iya tuntubanmu akan wannan number 09136899615 Hajja DataπŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’… *KISAN MUMMUƘE* πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’… _PAID BOOK_ *BY* _SAJIDA NIJAR_ *Yan Naija Mutanen mu 1k ne a kan wannan account number 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank* sai a bani shedar biya ta layi na kamar haka +22793811618 *Yan Nijar mutanen mu zaku turo da hoton kati ta airtel ta dala dari , wato 500francs cefa a kan Numbarna kamar haka +22793811618* *Na gode, sai kun zo.....taku ce SAJIDA NIJAR* Bismillah, na zo muku da zance mai daraja.....wallahi Ni ganau ce ba jiyau ba...... Ga tallah *JAMA'A NAZOMUKU DAWANI TSARI NASAMUN KUDI TA HANYAR AMFANI DA WAYAN HANNUNKU WANNAN TSARIN SHINE METAFORCE MENENE KASUWANCIN METAFORCE* ???? *Metaforce kasuwancine ingantacce halattacce Wanda yake biya 100 πŸ’― Wanda ake Gudanar dashi da wayar hannu,METAFORCE is also a part of network marketing,is a 100 percent decentralized project da aka daurasa Akan Blockchain technology Wanda babu wani mahalukin daya Isa YAYI editing,hacking ko deleting wani abu acikin sa,Kuma yanada matakai yanada rassa Wanda kowane reshi ka rike a METAFORCE to ka samu GUDUMAR DUKAN TALAUCI*🌎 METAFORCE ANASAMUN KUDI ACIKINSHI SOSAI MATUKAR ZAKAYI ABUNDA AKEBUKATA zaku iyahada miliyoyin kudi aranadaya acikin wannan kasuwanci me albarka in sha Allah Duk wacce tashirya zata iya tuntubanmu akan wannan number 09136899615 Hajja Data *6* A sanyaye ta ce" Tana da sunnaye har kwaya uku, mahaifiyarta da ta haife ta tana kiranta da NUR, ko tace da ita KHAIRY, ita kuma mamanta, wato marikiyarta ce ta saka mata IMTEE, Ama sunnanta na gaskiya shi ne *HALLAH* an ce ta ci sunan mahaifiyar mamanta ne wai......" Murmushi ya saki ya dubi mahaifiyarsa yace" Ke da kanki kin san ai itace ta dace ta zama surukarki............ Duba fa ki gani.....MRS ANAS HALLAH.............mts kama sauran kudin kawai , Allah ne yayi yau za'a cire ni koda bana so" Ya mika musu sauran kudin ya nufi dakinsa sai sake murmushi yake yi da nufin da an jima zai kirayi Fa'iza ta bashi numbarta, kai idan ya samu a yau sai ya je zance inda take, sai dai idan bai samu hakan ba! Mahaifiyarsa na ji tana gani ya shige, bayan tarin abinda yake ranta shine ta ja masa kashedi cewar kar ta ji kar ta gani, ama Kashhhhh, maganar da ake fada cewar yawanci idan d'a ke rike da ragamar gida, to fa hatta iyayensa biyayya suke yi masa hakan ne, in dai abu take so to fa sai dai ta yi rarashi ta bada hakuri, ba dai tace zata hau ta tsiya tsiya ba, dan kuwa shi din nan shine mai fada a ji, koda an yanke hukunci sai idan ya masa a gidan su! Da ace A'isha bata yi gaggawar cin mata ba, da tabas sai dai ta sameta a gida har ta huta, ama da yake ta yi mugun sauri sai ya zamo ta sameta tana daf da shiga gidan nasu, sai suka shige tare Magana ke cin bakin A'isha, cike da zumudi ta ajiye hijabinta saman dardumar da mamansu ta shinfida zata dama fura ta sha, dan kuwa har yanzu bata dora tukunya ba, hasali ma bata da niyar Ι—orawa sai bayan magariba dan ta yi da su ai su wuni a cen , da daren kuwa makaroni ce zata dafa, , mai ci ya ci, wanda baya ra'ayi ya ajiyewa masu so, sai ga yaran sun dawo bayan ita bata wani tanadar musu komai ba, to ai ta zata sai dare su da gidan nan ne. A'isha da zumudinta ta ce" Innalilahi, Imtee, wallahi kin yi baban kamu, wayo Allahna Shikenan sai tafiya ta kasaita ta kama mu a makarantar islamiyya, wannan yar gidan Elhaji zakarin kuma sai mu ga karyar bude kafada da daga kai dan tana soyayya da yaya ANAS, ita da akace ita tace tana sonsa, ke kuwa shi ya nuna yana son ki, wayo Allahna dadi...... Kiskirim maman yara ta yi tana sauraron su a cikin daka, dan ta san idan ta fito suna iya tsayar da maganar domin wani lokacin munafurcin su ya fi tunanin bawa. Imtee murya cen kasa ta ce" Kai, A'isha yanzu ke har abin nan ya burge ki? Ni kuwa in rasa da wa zan yi soyayya sai da namijin da ya zama abin wawar yan matan anguwar nan?, ki barni in mutu maza su kai ni ba mata ba, ni walahi da ba dan maman nan tasu datijuwa bace da sai na fada mata magana, a kan me zata wani bamu dubu daya? An ce mata dan kudinta muka je ne? Hum!" A'isha tana dubanta ta ce" aya, aya, dan Allah kar ki mayar min da farin cikina ciki, ke kin san matar cushe ce bata daraja ba wace ake bi ba, ba ruwanki da yan matan anguwar nan, ke du inda namiji yake ai yaya Anas ya kai, gaskiya Ni yau farin cikina ban san inda zan iya kai shi ba, duba ki ga yadda yake maki barin kuΙ—i daga farawa da iyawa, saura ki koya masa kin amsa idan shi din mijin ki ne in an daura kuma ya ki baki, dan kuwa yawancin lokuta mu ke janyowa kanmu da iya yin tsiya mu Ι—orawa kanmu fitinar da ta fi karfin mu, kudaden nan fa sun kai dubu talatin kika ki amsa......" Wani irin dokawa da kirjin maman yara ta yi sai da ta ji kamar jiri zai debeta ya buga da kassss Da sauri ta rike garu ta rintse ido tana fitar da numfashi har ta ji zuciyarta ta saku sannan ta yi motsin da ya sa suka gane da mutum a ciki, ai kuwa nan da nan sai suka bar firar, ya zamo ma ita A'isha ta fice dan tara ruwan wanka, ita kuwa Imtee ta shige ciki ta shiga yiwa mamansu Ι“aci irin na sangartar nan wai ita auta. Cijewa sosai mamansu ta yi bata nuna musu komai ba har ta haΙ—a kayan girkinta tace su zauna ta musu su ci, suka zauna din kamar yadda ta saba musu ta gwammace ace aiki zai kasheta da ta sa su dauke koda tsinke, dan kuwa zata yi bakin cikin ace sun taya matar babansu aiki koda da sanu ne bale har a kai su kama mata aiki dan ta huta. Tana jan jiki da girkin nan har sai da suka yi sallar isha'i ta zuba ma kowa ta saka suka dau nasu suka shige dakin su, tana nan zaune ta kasa ta tsare , auntyn yara bata zo ta dauki nata abincin ba, hakan ya sa ta sake shaΖ™ar wani bakin cikin zuciyarta kamar zata fashe dan tunanin ta ya gama bata cewar kudi ne da ita shi yasa bata ringa kai kawo tana dakon a gama abinci ta dauka ba, gayanan har ta yi ta gama bata dauka ba A haka malan ya shigo ya sameta da fitilar kwoi a zaune ta haske mata inda take. Karamar tabamar da suke shinfida masa ne ta shinfida masa sannan ta kawo masa abincinsa Bayan ya saka jalabiyar zama a gida wace ta gama mutuwa murussss ya zo ya zauna a hankali sannan ya bude kwanon abincin yana amsa gaisuwar da take masa sannan ya dan dubeta ya ce" Yau lafiya kuwa ba'a kai mana abincin rana ba Sai kwado Sulaimana ya mana muka ci?" Maman yara ta tabe baki cikin duhu ta gyatsine bakinta sannan ta dube shi ta ce" Na yi girkin kuwa, bai zo ya dauka bane kawai dan ya ja min fushin ka, sulaimana na kara girma kishin mahaifiyarsa na sake kama zuciyarsa da gasken gaske, sai dai Ni Allah na rike ba kowa ba, na tabbata zai min maganin komai....." Ya dakatar yana dubanta dan yana son gaskata zancen ta Gannin hakan ya sa ta sake gyara zama tana sauke ajiyar zuciya ta ce" Ka duba ka gani, ita din da kanta haka na ajiye mata na rana, sai daukewa na yi na bada sadaka, ga kuma na daren nan shima zai kai wani lokacin bata dauka ba, malan idan wani abin dadi kake bata a daka tana ci ya sa bata kula kwanonta ranar girka na sai a sanar min in fasa cire rabonta, in kuwa a tsayin zaman da na yi da ita shekara ashirin da daya har yanzu bata yarda da Ni ba ko kuma tsoro take kar na zuba mata wani mugun abin shima sai a sanar da Ni in sani, tunda kana gani, bata kiran ya'yan nan cin abinci sai ta ga bana nan, ta zuba musu abinci daga ita sai su ta yi ta nuna musu Ni din nan makiyiyarsu ce, ama da ace kiyaya nake yi da su ai da ban rike IMTEE har tsayin lokacin nan a hanuna ba, Ni ce kashinta, Ni ce fitsarinta, yau in Rahama bata gode min ba ai gani nake na wuce ta zage Ni, ta zarge ni ko kuwa ta wulakanta Ni ko?" Har ga Allah sai da gaba daya abincin ya fice masa a rai, haka kuma sai jin zafin auntyn yara ya sarke zuciyarsa Shin yaya zai yi da ransa ne? Da ace yana iya hakura da auntyn yara da ya jima da sawake mata , ta yadda zai samu hutu a zuciyarsa da cikin gidansa, saboda fitinar da kullum ta Allah zata hadasa masa a cikin gidan nan, sai dai kashhhhhhh, a yau idan ya rabu da ita ya tabbata hatta nutsuwa irin ta gangar jiki sai dai ya gani a mafarki ba dai a tare da maman yara ba....., to maman yara fa tsakaninsa da ita yanzu sai dai su yi fira irin wannan, tuni ta sahalema kanta lalurori masu saka shakuwa tsakanin mata da miji, tuni ta ajiye diyoyin dake kanta.....to maman yara ai ta yaranta kawai take, shi kuwa har ga Allah har yanzu da dan saura, dan wani lokacin idan lamarin ya juyo masa tamkar mai shekara arba'in haka yake jin kansa, kuma mai daukan lalurar dai auntyn yara ce, ita kuwa zuciya da kwalafa wa abinda take so yake sakata a shauki Kai, shi bai ga meye auntyn yara ke nema a duniyar nan ta rasa ba Shin tsabar godiyar Allah ce ya sa take so dole sai ta bakantawa masu son ta, take iya jin dadi a ranta? Daga shi har maman yara ai masoyanta ne na karshe a duniyar nan, Ama kuma daga shi har maman yaran bata bari ba da fitintunn yau da kulun..... Rai bace ya daga murya yana kiran auntyn yara Kirjinta na dokawa ta karaso ta duka da nufin gaishe shi ya dakatar da ita ta hanyar daga mata hannu rai bace ya ce" Rike gaisuwar ki isashiya! Kiran da na maki dan in tambayeki ne shin Ni da hanuna na dau kwandala na baki ko kin samu hanyar shigo da kudin da bani da labari a gidan nan?" Auntyn yara ta Dube shi, fuska a raunane sosai, dan wallahi ita yinwar da take ji ma ta isheta, jira take yi idan sun tafi kwonciya ta dau abincinta ta tura hakanan da wanda ya rage , dan ta tabbata idan ta bude kwanon nan abincin kadan ne ba zai isheta ba, shi yasa take jira in ya gama sai ta bi kwanukansa ta hade da wanda aka bata ta ci, dan maman yara bata cika bin ta kan kwanuka ba, sai da safe take wanke su bayan sun gama tsumama din nan A sanyaye ta ce" Kudi kuma? Ni kuwa ina zan samu kudi? Na yi me da su kudin ma to?" Yar yatsarsa ya nuna mata ya ce" Ki kiyayeni, Ni zaki tambaya inda zaki samu? Ki fada da bakinki tsakanin ki da Allah na taba ware ki na kawo maki wani abincin da zai sa ki ki cin na gidan nan?" Zuwa yanzu auntyn yara ta gama gane mai aiki ce ta gama aikinta, dan haka sai ta ari hakuri ta sakawa zuciyarta sosai ta ringa ayana sunnayen Allah a cikin ranta A sanyaye ta ce" Aa ko daya" " To ki fada min dalilin ki na kin cin abincin ki, kina tunanin maman yara zata maki wani abu ne da zai cutar da ke?" Ya sake fada rai bace Auntyn yara ta yi murmushi domin yawancin lokuta idan yana fada, tak da tak abinda aka kuno masa ne yake maimaitawa, dan haka a sanyaye ta ce" A'a fa, azumi nake yi yau, kuma ka ga da na sha ruwa sai kawai zazabi ya rufo min, tun Dazu ai jira nake ta leka ni sai in ce mata ta taimaka ta zubo min abincina a kwano in ci a daka, sai na ji shiru, na tabbata aiki ya mata yawa, maman yara banda lafiya shi yasa baki ganni ba du wunin yau, ki yi hakuri dan Allah " Maman yara ta zuba mata ido da mamakinta, shima malam sai da yayi mamaki , dan a da takan fashe da kuka ne kawai ta nuna an mata kage, Ama yau ta amshi laifinta ashe ma bata da lafiya ne???? A sanyaye ya ce" Allah sarki, sannu auntyn yara, Allah ya baki lafiya, je dakin ki kwonta zan kawo maki abincin, ko kuma ita zata mika maki, zan sa sulaimana ya samo maki magani ki hadiya, Allah ya baki lafiya" Auntyn yara ta amsa sannan ta mike ta yi ciki abinta, Yana juyowa da nufin sanar mata ta mika mata abincin nata sai ya ga mama na wani irin abu irin na idan ranta a mugun bacen nan, tamkar kububuwa ta mike daga zaunen da take ta ce" Ba laifi, sai ka ci gaba da goya mata baya, Ama Ni kam ba zan kai mata wani abinci ba, ka yiwa matarka kashedin tsare min ya'ya tana kitsa musu munafurci, bana so, bana so a daina min , idan kuwa kunne ya ki ji, jiki magayi!" Daga haka ta yi dakinta rai bace, hakan ya sa ya kame haba a ransa ya ayyana ' Ikon Allah, yau maman yara ranta a bace sosai, Allah ya sanyaya, bari Ni in kai mata, du tsanani ai za'a daga mata kafa tunda bata da lafiya, wannan yan ciwo na auntyn yara Allah ya sa mai tafe da zigege ne' Daga haka ya dau samirar abincinsa ya shige dakin auntyn yara , ita kuwa ta kara hasken fitilar kwonta ta bude musu kwanon ta kawo masa ruwa ya wanke hannunsa suka shiga ci tare, bale da ya kula kamar bata son ci sosai din nan sai kawai ya ringa tursasa mata har sai da ta koshi sosai sannan ya kyaleta hakanan yana mamakin auntyn yara ba zata taba girma da yan rigingimu ba irin na tabara, wanda hakan ke sakawa a kulun yake Dada yi mata uzuri du irin laifukan da take yiwa mama wa'inda maman ke fada kullum ta Allah, sai ya tashi da karfi zai salameta ma sai ya ji tausayinta ya kama shi, idan ya salameta ina zata je? Ai ko ya rabu da aurenta baya jin in zai rabu da ciyar da ita da kula da lafiyarta a karkashin innuwar gidan nan, gwara dai a ci gaba da mata fadan da nasihar ta yiwu idan ta kara girma ta daina rashin ji. ( ita shagwaba a gaban miji na sakawa mace har su kai ajiye jikoki a duniya yana yi mata kallon yarinya karama, har ta tsufa a idannuwansa da zuciyarsa yarinya karama zai ringa daukanta, anfanin hakan kuwa shine idan har yana daukan ki a yarinya karama tabas zaman sai ya fi armashi, zai ringa yiwa duk wani abu da zai shiga tsakanin ku uzuri na bacin rai, zai ringa mararin yin fira da ke yana murmushi , zai zamo yana tsokanarki ne idan kuka zauna dan kawai ki masa yar rigimar nan yayi dariya, zai zama alkali tsakanin ki da kowa ne, zai zamo baban malami , baban masoyi a duniyar ki.........😁🀌🏻) Maman yara sai da ta ga sahu ya dauke sosai da sosai sannan ta shige ciki ta tada Imtee ta fito da ita falo suka zauna Kasancewar Imtee bata da nauyin barci ko kadan , nan da nan ta wartsake daga barcin da take yi tana kallon mama hankalinta na neman tashi dan ta tabbata ba lafiya ba Mama na dubanta ta ce"πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’… *KISAN MUMMUƘE* πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’…πŸ’… _PAID BOOK_ *BY* _SAJIDA NIJAR_ *Yan Naija Mutanen mu 1k ne a kan wannan account number 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank* sai a bani shedar biya ta layi na kamar haka +22793811618 *Yan Nijar mutanen mu zaku turo da hoton kati ta airtel ta dala dari , wato 500francs cefa a kan Numbarna kamar haka +22793811618* *Na gode, sai kun zo.....taku ce SAJIDA NIJAR* Na zo muku da alkhairi ......, Zance ne a kan Meta Force, wanda muka ci, muke kan cin ganiyarsa a kwonce a dakin mu ...... Bismillah *JAMA'A NAZOMUKU DAWANI TSARI NASAMUN KUDI TA HANYAR AMFANI DA WAYAN HANNUNKU WANNAN TSARIN SHINE METAFORCE MENENE KASUWANCIN METAFORCE* ???? *Metaforce kasuwancine ingantacce halattacce Wanda yake biya 100 πŸ’― Wanda ake Gudanar dashi da wayar hannu,METAFORCE is also a part of network marketing,is a 100 percent decentralized project da aka daurasa Akan Blockchain technology Wanda babu wani mahalukin daya Isa YAYI editing,hacking ko deleting wani abu acikin sa,Kuma yanada matakai yanada rassa Wanda kowane reshi ka rike a METAFORCE to ka samu GUDUMAR DUKAN TALAUCI*🌎 METAFORCE ANASAMUN KUDI ACIKINSHI SOSAI MATUKAR ZAKAYI ABUNDA AKEBUKATA zaku iyahada miliyoyin kudi aranadaya acikin wannan kasuwanci me albarka in sha Allah Duk wacce tashirya zata iya tuntubanmu akan wannan number 09136899615 Hajja Data *7* Maman yara na dubanta ta ce" Ban ji da kyau ba batun saurayin da kuke yi ke da A'isha" Sai da Imtee ta sake jin ta wartsake sosai , domin yawanci kawayensu sukan nuna idan suka yi saurayi iyayensu na masu fadan a taka a sanu, a kula, a bari a kara girma kafin a fara tunanin yin kule kulen samarin nan, wasun kuwa sukan ce gaba daya an musu fadan da ba zasu kuma yinkurin kula samarin ba sai dai mijin auren su, hakan ya sa ta dan daburce kafin ta shiga kame kame ta ce" Mama, am, dama, ehin, um, dama fa yayantan nan ne , wannan da akace yana aiki a gidan cen na bayan layin nan, shine wai yake wasu abubuwansa, ama Walahi Walahi mama ni babu wani abu da yake iya sakawa in yarda , banma kai soyayyar ba ai!" Gaban Mama ya kara yankewa ya fadi, zuciyarta ta nemi sake cinkushewa da wani baki......, kai, soyayya? Saurayi ne Imtee zata yi A'isha ki sinsinowa bata yi ba? Saurayin ma mai wani mukami ? Yaya za'a yi zuciyarta ta iya daukan wannan lamarin......?, yaya za'a yi tana ji tana gani rahama ta fi ta da wani abin?????? Ta jima da ta yi shiru, tana ta sake sake, lokaci daya ta samu kanta da yin murmushin gefen baki a lokacin da ta ji a ranta kwarai wannan din ma wata hanya ce da zata iya amfani da ita dan ta sa zuciyar rahama ta kumbura, ........tabbas Idan har ta iya takunta wannan hanyar itace ta fi dacewa da itadasa cuzgunawa Rahama bakin cikin da zai sa zuciyarta ta kumbura..... "Mama, dan Allah ki yi hakuri, in sha Allah Ni ko inda yake Bama zan yarda in kala ba, Ni da kaina na san ban kai wajen nan ba mama sai na girma ki?????" IMTEE ta fada a raunane , dan shirun na mama ya yi yawa " In ji uban wa? Innalilahi Imtee me kike fada? Baki kai soyayya ba so kike yi in kwada ki in cinye ko so kike ki tsofe min a gidan nan?, wani munafukin ne ya saka maki wannan shirmen a kwakwaluwa bayan Ζ™atuwar budurwa kike gakinan komai ya bayyana ya gama nuna? To ahir din ki, kar na kuma jin wannan batu, da ace ma wani sakarai marar katabus ne Bama zan yarda ba, dan nan da kika gani ban ga amfanin badi ba rai ba, ba zan taba yarda in bari ku kula banzan namijin da bai ajiye ba bai ba wani ajiya ba irin Sulaimanan gidan nan, asara ce, fitina ce, tashin hankali ne auren talaka, sai ma ka zo zama da shi kunci yayi kunci ga shegiyar gabar tsiya da fuska uwa kunun safe, ba'a saki fuska ba bale a ji dadin zama sai dai a kare da auro wata karshe ma a koro min ke ina ciyar da ke da ya'yansa, ki ji da kyau gobe in sha Allah da Yama zaki koma ki yi alamun kin zo ku gaisa da kawar taki, ki tabatar da kin zauna har ya shigo sanan ki maido batun soyayya, kin ji ni da kyau?" Maman yara ta karashe tana riko hannayen Imtee da ta yi suman zaune jin hudubar mamanta ta sha bamban da ta iyayen kawayensu da suke fadin an fada musu .......... Tausasa murya sosai Maman yara ta yi tana dubanta ta ce" Ai na san cewa kin san du duniya babu mai son ki sama da Ni ko? Kin yarda da Wannan ko?" A hankali Imtee ta gyada kanta tana sauke boyayiyar ajiyar zuciya A tausashe maman yara ta ce" to ki kara yarda, Ni MAMANKI baki da wani sama da ni a duniyar nan, baki da wani wanda ya san ciwon ki sama da Ni, haka kuma shekaruna sun tabbatar maki na fi du wani makusancin ki sanin duniya da abinda ke cikinta ko?" Imtee ta gyada kai zuciyarta na fara amincewa da batun Mama Maman yara ta murza hannayanta kasa kasa sosai ta ce" Maganar ba zaki amshi abin hannunsa ba, kanmu ne zamu cuta, kuma idan Allah yayi shine mijin ki Walahi ba zai baki ba in ya aure ki, kin kuwa san irin burin da na ci a kanki? Burina ki samu mijin da zaki huta, burina ki samo miji mai kudi Imtee....." Ta karyar da muryarta sosai ta ce" Ki duba ki ga a dakin da muke, ki duba ki ga yadda nake wahala idan ina son siya Miki dan kwalli sai na yi ta asusun kwana da kwanaki kafin in damu yadda nake so in siya Miki, ina so in ga kin yi kudi, kin dauke Ni daga Ni sai A'isha mun yi tafiyarmu, mu bar wancen da baya son mu da kuma wace ya zaba fiye da mu su yi ta zama a wanan wahalalan gidan kin ji imteena????" A hankali bayanan ke ratsa zuciyar Imtee, har ta ji a ranta kwarai zata iya komawa

Chapter 5 of 9