Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 9
za'a iya bi a ga gazawarta a aikace a kansa, domin mace ce mai boye da iya kisa na tashin hankali wanda hakan ya sa sai wanda ta yiwa zai iya gane wacece ita......Ama lokaci zai bayyana mana abinda ke duhu a tare da ita koda akoy shi.......... Hannunsa ya mika ya dauko tawul din da ya gani a rufe saman abin kanshi a nutse ya ware shi ya nada a kugunsa sannan ya karaso ya tsaya kofar bayin yana jira har sai da ta gama dukan abinda zata yi ta yi wanka ta dauro tawul bayan ta saka abinda zai tare mata jinin dake zuba a jikinta sannan ta nufo waje tsaf cikin shirin abinda zata bashi amsa da shi idan har ya yi mata tambayar abinda yake faruwa Tana buɗe bayin idannuwanta suka fada cikin nasa, lokaci daya gabanta ya buga har sai da ta so komawa , domin wani tsoro ya kamata lokaci daya, sai dai tuna cewar idan fa ta kuskura ta aikata lamari irin na ta ji tsoro tabas zata jazawa kanta baban tashin hankalin da kanta ba zai iya dauka ba. Kallonta yake yi yana karantar ta. A nutse ya saka hannunsa ya dauke ta cimak ya nufi wajen doguwar kujerar abin turaruka dake jere ya ture su sannan ya ajiyeta a sama ya dan ja baya ya sake zuba mata ido sannan ya nufi bayi da hannunsa yana mata alamun minti biyu , wato yana zuwa Tunda ya shige bayin sai ta ringa maimaita abinda zata fada masa a cikin zuciyarta tana sake sanarwa kanta abinda take da bukata a yanzu shine jajircewa, idan har ta yarda, in ta yarda ta nuna tsoro ta mutu ta lalace, tabas sai ta saka kanta a halin kaka naka yi da bawan Allahn nan....... Ya dauki lokacin da yana fitowa yayi dai-dai da lokacin Sallah, sai kawai ya sake tsayawa ya dubeta sosai ya ga a zaunen take bata murkususu bata komai, hakan na nufin yana iya zuwa ya gabatar da sallah ya dawo cikin nutsuwa, sai ya mata Salama ya fice daga dakin da dan hanzari Da sauri ta sauko daga saman kujerar nan ta karasa da sauri ta dauki wayarta lokaci daya ta nufi wajen kofar ta rufe da ky sannan ta dawo ta shiga dana Numbar likitan da ya yi mata aiki a Turkiyya A kira na biyu ya daga, saboda a zaman da ta yi a wajensa sai da ta mugun shiga jikinsa har suka yi sabo na mamaki "Mrs IMAD...." Ya fada a tausashe A hankali MAZNA ta furta" Docter na shiga uku....., docter jini da ciwon ciki , jini docter" Likitan ya dafe gaban goshinsa ya ce" Ina fata ba sex kika yi hvng da wuri ba, bayan na fada maki a kala sai kin kai wata shida baki yi sex ba, zuwa lokacin kin samu lafiya sosai komai ya zauna yadda ake buƙata?" Shashekar kuka ta kama yi yannayinta na nunin tashin hankalin da take ciki ta ce" na so hakan docter, na so hakan, OGA ne ya nemi in sauka a jidda kwana uku da suka wuce , yace in zo ya gani in koma, shi yasa dole na taho, kuma kuma.......ban san haka jini zai iya zuwar min ba......" "Mrs IMAD, aiki uku fa na miki a lokaci guda wanda da ba dan kin saka na ji a raina eh zaki iya kula da lafiyar ki ba, da sai kin yi wata uku a wajena....., MAZNA an Miki abdominoplasty or tummy tuck fatar jikin ki ta cikin ki da kitsen dake cikin cikin ki ne muka kwashe muka rage girman tumbin ki muka maida shi madaidaici ta yadda idan kika koma cin abinci cikin ki ba zai taba zama kato ba, an maki buttock lipofilling wace ke sakawa a kara maki girman duwawu ta hanyar daga su, a daidaita su a saka musu kitse, sai ta mama wato Breast lift wace muka daga mamanki muka rage bajewar da suka yi muka saka musu implan madaidaita suka tsaya...., kin kuwa san girman hatsarin aikin nan? Kin kuwa san ba dan in maki surutu bane nace dole ki yi hakuri da mijin ki har sai kin warke? Why kika yarda kika bashi kanki da wuri haka ko wata biyu ba'a yi ba? Kin kuwa san abinda hakan ke iya haifar wa.....??????" Hankalin MAZNA ya idasa tashi, sai kawai ta fashe da kuka tana fadin yaya zata yi?????? Docter ya ce" Ki saurara, ko me kike yi ki dauko jirgi ki dawo gobe in duba ki, duka aikin da na yi zan duba sannan sai an sake wata jinyar daga farko, zan fada maki ba ke ba namiji sai kin warke, zan sake fada maki ki kula, dan hakan na iya taba ranki....., a cikin magungunan ki akoy baki shi zaki sha har ki zo nan, zai tsaida zubar jinin ya kuma hana ciwon cikin dan ciwon cikin murdawar zubar jin ne kin fahimta??????" MAZNA jikinta na rawa ta mike tana duba maganin, ta dauka ta hadiya hadi da fadin zata yi kiransa kar ya kirayeta . Daga haka ta ajiye komai cikin saurin tsiya ta shiga saka tufafi , ta fesa turare , tana cikin daure gashin kanta ya dan buga kofar, saboda sai da ya yi sallar isha'i sannan ya nufo dakin A nutse ya shigo bayan ta bude masa tana bashi hanya Karasawa yayi ciki ya fan riinga kai kawo kadan kafin ya juyo ya sake zuba mata ido A tausashe sosai ya ce" Me yasa yannayin ki ya yi kama da idan baki da gaskiya? Me yake faruwa ne?......" Da sauri ta girgiza kanta tana jure murdawar cikin, a harhade ta ce" A'a, ba rashin gaskiya bane, banda lafiya ne" A hankali ya zuba mata ido, sannan ya karaso ya kama hannunta suka karasa saman lalausar kujera mai girman gaske suka zauna, yana rike da hannun nata a tausashe ya ce" Me yake faruwa?, " "Fama na yi ta yi da ciwon ciki, to kwana biyun nan na damu sauki sosai fa, ban san me ya dawo da shi yanzu ba" ta fada tana dubansa da kyau da son ya yarda da bayanin ta "Subahanalah, ciwon ciki.....????????, kin ga likita? Me ya ce????" Ya fada a nutse yana sake zuba mata ido A tausashen itama ta ce" Eh na ga likita, yanzu haka da maganina ina sha na ji sauki kana gani da sauki, sai dai périod dina ya zo min a ba zata......" Idannuwansa ya lumshe kadan, sai kuma ya bude ya zuba mata su, a hankali ya ce" Dama ba sai 05 kike périod ba?" Gabanta ya sake faduwa, ta dan daburce kafin ta sauke wata irin ajiyar zuciya a boye, ta yi mugun kalar tausayi a birkice ta ce" Ka san tunda aka samu matsala wajen haihuwar yaran nan menstru dina ya rikice, ban kuma samunsa dai-dai ba, ai ka ga likitan da nake gani dan maganar haihuwar ta yi bayanin wasan da yake min yanzu ya sa ba'a samu wani cikin ba....." A hankali ya dan murza hannunta, cen ciki ya ce" MAZNA, tsaikon samun cikin ki daga Allah ne, kin taba haihuwar ai Allah ya amshi abinsa......ki ci gaba da addu'a tunda lafiyar ki kalau in sha Allah zaki samu......, NOW Tell me about your shape... your stomach, everything.......MAZNA.........." Ya dan dakata yana dan lumshe idannuwansa kafin ya riko hannunta da kyau ya matsota ta yadda zasu fuskanci juna da kyau sannan fuskar da ta fi sakata faduwar gaba ta bayyana a tare da shi, lokaci daya jikinta ya dauki rawa hadi da tashin hankali, a lokacin da dukan yannayin serius ya bayyana a tare da shi da kuma yanayin da wahala ya sassauta mata ya ce"........💅💅💅💅💅💅💅💅💅💅 *KISAN MUMMUƘE* 💅💅💅💅💅💅💅💅💅💅 _PAID BOOK_ *BY* _SAJIDA NIJAR_ *Yan Naija Mutanen mu 1k ne a kan wannan account number 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank* sai a bani shedar biya ta layi na kamar haka +22793811618 *Yan Nijar mutanen mu zaku turo da hoton kati ta airtel ta dala dari , wato 500francs cefa a kan Numbarna kamar haka +22793811618* *Na gode, sai kun zo.....taku ce SAJIDA NIJAR* Bismillah , ki gwada kafin ki gane abinda muke nufi *JAMA'A NAZOMUKU DAWANI TSARI NASAMUN KUDI TA HANYAR AMFANI DA WAYAN HANNUNKU WANNAN TSARIN SHINE METAFORCE MENENE KASUWANCIN METAFORCE* ???? *Metaforce kasuwancine ingantacce halattacce Wanda yake biya 100 💯 Wanda ake Gudanar dashi da wayar hannu,METAFORCE is also a part of network marketing,is a 100 percent decentralized project da aka daurasa Akan Blockchain technology Wanda babu wani mahalukin daya Isa YAYI editing,hacking ko deleting wani abu acikin sa,Kuma yanada matakai yanada rassa Wanda kowane reshi ka rike a METAFORCE to ka samu GUDUMAR DUKAN TALAUCI*🌎 METAFORCE ANASAMUN KUDI ACIKINSHI SOSAI MATUKAR ZAKAYI ABUNDA AKEBUKATA zaku iyahada miliyoyin kudi aranadaya acikin wannan kasuwanci me albarka in sha Allah Duk wacce tashirya zata iya tuntubanmu akan wannan number 09136899615 Hajja Data *9* A kausashe da yannayin serius ya janye rigar dake jikinta kasa kadan, a hankali ya sauke dubansa a kan mamanta irin yadda aka mikar da su, suka rage fadin nan da bajewa a jiki ya kai dubansa kan cikinta har zuwa kasa..........mmm A tausashe ya ce" Ya rab......., na san kina da ilimi, kina da ilimin da zai sa koda wani ya sa ki aikata abinda nake tunanin kin aikata zaki ce masa a'a ko dan lafiyar kanki da kanki, kuma na san kin san haramun ne aikatawa jiki duk wani abin da zai iya zamowa ila har ya taba lafiya, .....abinda zai cenza halitta gaba daya ma ba kyau....., nd kin sani.......idan dan kwaliya ki burge wasu a waje kika yi ....ina nufin gasa irin ta kawaye ke matar aure ce, wace na killace abina ta ni kadai..... MAZNA idan kuwa dan ni kika yi kin sani In kika taba halittar ki ta hanyar da bata dace ba ba zaki taba birgeni ba............" Ya saurara yana kallon yadda fuskarta ke kara daukan ja A hankali ya ce" Ki fada min gaskiya, cewar baki yi abinda nake iya jin kin fice min a raina ba, ki fada min cewa baki je kin yi surgery ba MAZNA....." Du irin yadda ta shiryawa tambayoyinsa bayan dogon lokacin da ta dauka tana bita tun kafin ta dauko jirgin zuwa nan sai da ta ji kamar zata kifa a zaune a gabansa......... Wato da ace ya zama lauya tabas da karya kake ya saka ka a gaba baka tonawa kanka asiri ba Ilimin karantar bawa Allah ya bashi abinsa, kuma ya lakanci makaman saka bawa fadin abinda bai yi niya ba..... Ya ilahi...... Da kyar ta iya hadiye yawun bakinta, ta fara Hanna kanta fashewa da kuka dan ta sani tana fashewa da kuka ko wata kururuwa zai dago cewar du abinda ta fada karya ne, dan haka ta mugun kama kanta a raunane sosai ta ce" Surgry.....? Subahanalah..... Surgry......? Akul Abinda na san ba kyau? Abinda na san cewa ba taba birgeka zai yi ba?, yaya zan iya zuwa innyi Surgry bayan adinina bai bani wannan damar ba......?????" Sai kuma ta mike ta janye rigarta duka ta mike a gabansa a tsaye tana nuna masa ta ce" Ka san me da me na yi dan jikina ya koma irin yadda yake da cen cen kafin mama ta rasu dépression ya da in yi ta cin abinci ta du yadda ya zo min har in kwashi kibar nan da na samu na rage a yanzu? Akul jikina na ina budurwa ne wannan, Ka san irin yakin da na yi dan in gyara jikina in birge ka?.....Yes in birge ka, kai nake son birgewa ya sa na dage da sleeming, ina yin exercise mai girman gaske, ina shan magungunan narkar da kitse na Hausa da basu da ila, ina daura gaine a duk inda yake da bukatar daidaituwa........, na jajirce sosai dan ganin jikina ya zama ɗan carasssss har in samu ya koma min irin na lokacin da mama na raye......Ama sai ka yi tunanin Surgry zan iya yi Ni?????? Haba Akul , kai da kanka??????" Idannuwansa ya dauke daga jikinta yana sauke ajiyar zuciya.......ya Salam........a yanzu kirjinta ne kawai bai zo dai-dai Yadda yake so ba, saboda yana matukar son masu dan girma haka ba miri miri haka ba........Ama dama ana iya rage kirji ya koma haka naturly? Ikon Allah dama tana iya gyara jikinta har haka??????! A hankali, cike da tsoron kar ya ce zai sake yin wani abu ta ja rigar ta saka har sama ta haye ta riko hannayensa ta ɗora kanta a kafadarsa murya a raunane sosai ta ce" Gayanan du shirin da na yi dan mu hade a yau yana neman lalacewa........, ban bjrgekan ba, ban samu tsadadan lokacin da nake ta missing ba saboda zuwan périod ya Allah......" ta karashe tana jan shashekar kukan da ya sa ya dan shafa bayan ta.........., A hankali ya furta" ai zan zo karshen watan nan in sha Allah......, idan na zo........zan rama dukan kishirwar da na dauka Bakya nan.....nd zai zamo alll time bcz zan jima a Nijar" Fuskarta ta dago, kirjinta na dan bugawa da tunanin yaya maganar warkewarta Kenan....? Haka kuma jin zai jima ya kara neman daga mata hankali. ..... A tausashe ta ce" Kenan zaka jima sosai da sosai???? Ama aiyukanka na nan fa?, makarantar nan fa???????, me zaka yi mai yawa a Nijar, yaya zaka iya jure zafin Niamey?????" Murmushi ya yi ya mike ya cire tufafin jikinsa ya saka dogon wando na shan iska sannan ya karasa ya budewa masu kawo abinci ya amsa daga nan ya rufe kofar ya ajiye mata dan shi bai cika cin abinci da dare ba sai madara kawai yake sha ya kwonta, A hankali ya karasa saman lalausan gadon ya kwanta yana lumshe idannuwansa cen kasa ya furta" Daga yau, bana so ki kuma sauka a hotel din nan, idan kika juya gida zan sa a dakatar da du wani abonnement namu na hotel......idan kin shigo ki sauka gidan da aka gama ginawa......" Karasawa ta yi ta zauna daf da kafafuwansa a hankali ta shiga dan matsa masa kafafuwansa a sanyaye ta ce" In sha Allah,......" Ta ɗan saurara kafin ta ce" Baka ce komai ba , yaya zaka iya jure zafin Niamey????" A hankali ya bude idannuwansa ya juyo da kyau inda take ya ce" Niamey kasata ce, idan lokacin zafi ya yi a garin nan ya fi na Niamey karfi......, cikin gyara takardun da ya shafi dukiyata ne nake yi, daga yanzu idan na shigo Saudiya sai dai dan in yi ibada in gana da yan uwa......" Daga haka ya mayar da idannuwansa ya lumshe alamun barci yake ji Tashin hankali ta ji yana neman dauke hankalinta, sai dai ta yi iya yinta ta dane har sai da barci ya dauke shi sannan ta mike a hankali ta karasa saman kujerar nan ta zauna a hankali ta janyo abin turawar mai dauke da abincin nan ta bude ta ɗan fara saukewa sannan ta shiga tabawa kamar ci take yi, lokaci daya zuciyarta ta tsunduma a baban tunanin abinda yake jiranta Kwarai abinda yake jiranta take nufi....... Ita Bama matsalar mahaifiyarsa ba, domin Anna irin iyayen nan ne wa'inda ba ruwansu da lamarin matan ƴaƴansu, ko me zasu yi ba zasu taba zame musu matsala ba a zamansu sai dai su musu nasiha ko fatan shiriya bale irin yadda ta zamo mai uzuri da hakuri da kawar da kai a lamarin ta ba na wasan yaro bane, ko dan takan ce ita a ya'ya ta dauke su ita da kannenta ne?, saboda du idan yayi tafiya umarninsa daya ne su koma gidan kusa da anna su zauna saboda akoy bangare nasa daban a gidan, sai dai cikin ikon Allah ba wannan a cikin tsarin ta, domin akoy lokacin da ta roki annar tana so ta koma gidanta na plateau Ama kar ta fadawa shi IMAD din, annar bata tambayeta dalili ba, sai fatan alkhairi da ta yi mata kawai ta zuba mata ido....., ta san cewa anna ba zata zamo matsala a lamarin ta ba kamar wannan yar banzar mai aikin nata da take daukan kanta tamkar Y'ar gidan har take ba kanta damar yin katsalandan a abubuwan da suka shafi IMAD, Kwarai ta tsani baiwar Allahn nan, bata son abinda ya hadata da ita, domin gani take yi ta samu damar da bai dace ace talaka marar galihu irinta ta samu ba, wato irin yadda ta shaku da IMAD hankalinta ba zai dauka ba! Sanadiyar ta ne IMAD ya fara tunanin mayar da su anguwar nan, saboda a lokacin da ta samu wani ciki nakuda ta kama ta, mijinta wanda shi ne mai malamin baban su IMAD ya dauke ta ya kai ta wata yar karamar asibiti a nan anguwar wace itace asibitin anguwar ta haihu, a ranar aka nemi babyn aka rasa, sama ko kasa, sun ce mace ce, wannan dalili ya sa du idan ta fita sai ta nufi asibitin har abin ya so taba mata kwakwaluwa sai kawai shi IMAD din ya shiga lamarin tun bai gama karatunsa ba ya sa aka fara siyan asibitin da komai da komai har ya dawo kasar ana ta kokarin mayar da anguwar yadda zai iya bincikensa son ransa, har aka kwashi shekaru goma ya yanke shawarar attitude din kanwarsa da kuma wannan dalili zai sa ya mayar da kowa anguwar, farkon dalilin fara siyan filin nan da fara ginin, haka kuma daidai auren su ne....., ya zamo har yanzu ba'a ga yarinyar nata ba, dalilinta an dawo da su anguwar nan an zubar......... Sai ta biyu kanwarsa, wato FARHANA A da sunna mugun shiri da Farhana, bayan an aureta ma kafin su kaura anguwar nan ta talakawa sosai suke shiri da Farhana dan bata cika zama Bama ita bale har a samu sabawa da ita, sai dai daga bakin lokacin da ya yi ginin nan ya mayar da kowa cen ita ta ringa nan nan tana kaucewa zama idan baya gari , ita din ma Farhana din ba so take a san nan take rayuwa ba, ama tsabar raini da shiga abinda ba'a sakata ba sai Farhana ta fara tsanarta har ma suka fara fito na fito da ita, domin abu ƙalilan take jira ta yi mata karan tsaye a lamuranta ko na kannanta, wa'inda kannenta namijin ke son farhanar ama kiri kiri tace masa ai ba zai taba yiwuwa su hada shirgi daya ba dan kyar ta san kyar ne, domin shima mutun ne marar jin magana sosai, kuma hanya ta san hanya ne. Sai tsananin tsoro da tunanin yaya mijinta zai rayu a gari irin na Niamey, garin da yan mata ke kwatar miji ido da ido......, a garin Niamey kina ji kina gani idan gabdi ta rike mijin ki sai dai ki hakura, ko ku rabu, ko kuwa ki jira idan ta gama cinye duk wani abu da ya tara sai ta Bara maki katon kawai....... Kwarai mijinta yana da kamewa, yana da aji, bata tunanin ajiye wata yar balaja'u da zata janye shi da gaggawa.....sai dai tana tsananin tsoron MACE, domin a garin nan ta gama baza karya da kuri ta yadda da yawa na jiran damar da zasu hadu da mijinta dan su dandana ko su ga abinda ya da take wannan dan banzan rawar kan! Abu na gaba shi ne batun aikin nan da ta je aka yi mata, ta shiga cikin wannan lamari ne dan ta san idan ya jima a Nijar a shekara yayi wata uku ko hudu, yawanci yakan zo ne ya yi sati Daya ya juya saboda komai nasa a Saudiya ne , ta san cewa watanni shidan da likita yace ta ringa komawa ana yi mata binciken lafiya zata ringa yi hankali lwonce ba tare da hankalin kowa ya kai kanta ba, saboda ko anna tana iya shafe wata biyu bata leka inda take ba, dan bata wani yarda ta sabawa anna zuwa gidanta ba bale har a mayar da abin dole! Innalilahi, nan da karshen watan da har ya kai tara? , nan da karshen watan nan zai zo Nijar da nufin yin watanni tara ko fiye da haka har sai ya yi niya ya zo hadj ko umara ko kuwa ya zo su gana da abokansa.....? Wace irin rayuwa ce zasu yi a yanzu kenan? Yaya zata yi yana kusa da ita ta iya gudunsa har na wata shida??????..... Tabas dole zata je Turkiyya a gobe gobe dan ta gana da likitanta, zata fada masa ne babu wata dama da zata iya hana ta saduwa da mijinta nan da sati uku, idan da wani abu da zai iya yi a kai tabbas ya zama wajibi ya yi ko menene, dan ba zata taba bari ya sake yin dogon lokaci bai samu abinda yake kira gishirin zaman aure ba.......... ( Wannan kenan) Da asubahi bayan ya dawo daga Masallaci ya zauna saman cafet, sai ta zo ta zauna a jikinsa ya zamo ya wara kafafuwansa tana tsakiya a zaune, bayanta a kirjinsa a lafe A hankali ya shafa cikin ta yayi dan murmushi yana Ayana abubuwa da yawa a ransa, ciki kuwa harda bincike a kan maganar da ta fada, dan shi ba jahili bane a jiya ya saurareta ne yana mamakinta......kwarai zai waiwayeta a lokacin da bata shirya ba..... Ba wai bai yarda da matarsa ba, ko daya.......ya yarda da ita sosai da sosai Sai dai akoy abinda idan aka fada hankali bai cika gaggawar dauka ba................hmmmm "Anna ta jima tana hakurin nisa na da ita....., na yi mamakin da na ce maki zan dawo daf da ke........., irin kusancin da du dare kina saman kirjina....irin wanda du safiya zan tsotsi leben ki in ji yaya kika tashi........Ama sai kika kasa mikewa kina dira dan murnar haka........., girl........ar u stilll lv ur hsband ????" Da sauri ta zarro ido ta juyo tana kallon sa......., to ita in bata so mijinta ba ta yi me a duniyar nan?, kai......... Da magana mai fitar da iska irin ta tarin mamakin kalamansa ta riko hannunsa tana duban fuskarsa ta ce" What? Anya akoy aikin da na fi jin dadin yi irin na soyayyar mijina kuwa......?????" "You're lying....." ya fada cen kasan makoshi....... A dan birkice ta rike hannayensa duka biyu ta ce" believe me, ina son ka fiye da rai na......., kawai banda lafiya ne jiya, Ama yanzu cikin ya fasa ciwo gaba daya......." Jikinsa a mace , muryarsa cen ciki din nan ya ce" the blding stopped too?....." MAZNA ta lumshe idannuwanta a hankali ta girgiza kai, cen cikin kunnansa ta furta" Ina iya aiki da ......da............" "No............" Ya katse ta a hankali ya mayar da ita irin kwoncin da ta yi da farko a jikinsa, cen kasa ya ce" Ban san yaya wasu mazan ke samun nutsuwa da haka ba....., Ni kam a'a, its ok." Ajiyar zuciya ta sauke bata ce komai ba Sun jima a haka kafin ta ce" Yaushe zan koma?" Bai bude idannuwansa ba ya ce" Yau , akoy jirgin sha daya shi zaki bi zuwa Nijar......" Ba yadda ta iya haka ta gyada kanta, ta kwonta a jikin nasa kawai a ranta tana tunanin tun kafin ta shiga jirgi zata sanarwa kaninta ya je aéroport ya cirar mata tikitin tafiya Turkiya , tana sauka a nijar ta wuce Turkiya idan da halin haka, ko nawa za'a cire shi maza ya je ya cira.........., haka kuma ta yiwa kannanta msg cewar su hada du wani abin bukatarsu dake gidan su na plateau su kai gidan anna kafin ta dawo sai su koma gaba dayansu cen dan idan ya sauka ya same su a cen din......... Karfe goma na safe sun gama shiryawa, suka fito , nan ya samu direba da kuma daya daga cikin masu masa aiki duka shiga daukan kayansu sunna kaiwa motar dake kasa Kasancewar da mota biyu suka zo manya lafiyayu sai kawai ya amshi ky din guda a mutunce ya sanar musu su gama da Salamar hotel din sai su kai kayansa dake nan gidan sa. Daga haka ya ja motar ya nufi aéroport da su a nutse cikin kwarewa Sunna tafe tana yi masa

Chapter 7 of 9