Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 9
ama basu fito ba. Har ta cire rai da fitowar tasu ta hangi sawayensu, A'isha na jan hannun imtee da karfi kamar wace za'a kai bakin wuta tana dan tirjewa har suka karaso wajen tabarmar A'isha ta fara zaunawa kafin ta ja hannun imtee da karfi ta zaunar da ita sunna dan yake Murmushi auntyn yara ta yi ta zuba musu abincin sannan ta Dube su bayan ta fara saka hannu a hankali ta furta " Bismillah, ku taba mu ji girkin na yau, Allah ya sa ban yi faduwar murhu ba" Ta fadi haka da dan barkwonci ne, tana hankalce da irin yadda imtee ke kallon A'isha da ta dauki abincin ta kai bakinta a nutse tana taunawa............ Har ga Allah yanayin kallon da imtee ke yiwa A'isha na jira ta gani ne idan abincin ba zai yi mata ila ba, domin bayan ta cin sai da ta dan taba gefen cikinta tana kallonta ta ga ta ci gaba da ci kafin a hankali ta saka hannunta ta dan diba ta kai nata bakin itama duk a tsorace dan a bayane yake a tsorace take......... Ajiyar zuciya ta sauke a karo na biyu kafin ta ci gaba da ci ba tare da ta ankara cewar ci gaba ne ta yi da ci din ba ka'in da na'in dan dandanon girkin da dadinsa har sai da Salamar mahaifinsu da yayansu suka shiga kunnayensu suka dago a tare sunna amsawa, wanda ya dan ja yana kalonsu da mamaki, sai kuma wata annashuwa ta mamaye fuskarsa wace auntyn yara ta jima bata ga irinta ba lokaci daya ya nufo su yana amsa gaishe shin da suke yi a tare kafin ya dan dakata daf da su, shi kuma Sulaiman na hararansu daga nesa, Aban yara ya ce" Ikon Allah, yau me aka samu da dadi haka har inuwa daya ta hada ki da ya'yan naki?" A dole ta ɗan tsare fuskarsa da ido kafin ta yi murmushi ta sada kai tana duban hannayen Imtee ta ga ta yanke akaifun, wani sanyi ya kara shiga zuciyarta har ta kara yarda cewa kwarai zuwa yanzu lokaci yayi da ya dace ace ta fara koyon zama irin na hakuri da dabara bayan sake nin'ninka addu'a dan ganin ta ci ribar zama da mutumen nan da kuma ƴaƴanta na cikinta dan ta gama yarda cewar abinda zai rabata da gidansa mutuwa ce , sai ko mummunar kadara, ya riga ya zama wajibin rayuwarta! A hankali ta ce" Abincin ku na dakina, bari in dauko" Aban yara yayi yar dariya ya ce" A'a yi zamanki, Ni ai in dai irin zaman nan zaki ringa yi da ya'yan Mama farin ciki fal raina, ina maman yaran take ne ? Na san yau itama hankalinta a kwance farin ciki fal ranta, Ka ga babban gida dauko abincin mu je mu barsu su ci gaba da zantawa tsakanin uwa da ƴaƴanta " Baki Sulaiman ya tabe ya nufi ciki ya dauko farantin dake dauke da abincin nasu ya fito ya yi waje, haka shima Aban yara ya bi bayansa suka nufi kantinsa dan su ci tare da abokin aban yaran wanda ya kawo masa ziyara yau Mikewa auntyn yara ta yi a tausashe ta ce" Idan kun gama, ku kirawoni in tatare wajen kun ji? Bari in barku ku gama....." Haka kawai A'isha ta ga kamar bai dace ace sai sun kirayeta ta tatare ba, cike da jin nauyin magana da ita saboda irin yadda aka nuna musu ko waje kar su matse mata tana iya hautsina musu dukan wani farin cikinsu, aishar ta ce" A'a AUNTY, zamu tatare" Aunty yara ta saki murmushi a hankali ta ce" Allah ya muku albarka, Allah ya tsare ku daga dukan sharin abin ki, Allah ya sa mu yi alfahari da ku a nan gidan duniya da kuma lahira " Daga haka ta yi gaba bata kuma matse musu waje ba Tunda ta nufi ciki imtee ta zuba mata ido har ta shige dakin ta, da mamaki ta dubi A'isha ta ce" Anya kuwa lafiyarta kalau? Ko bata da lafiya ne????" A'isha ta dubeta, tana sake zuba musu miya ta ce" Na kula, kamar inda aka kai baiwar Allahn nan bata je cen ba, ama kin ga, in sha Allah zamu zuba ido mu gani, idan har mun hangi cutarwa sai mu janye jikin mu, Ama wallahi kin bani mamaki wai da kika ki ci me kike tunani ne?, kina tunanin zata cutar da ke ne?" Imtee ta dubeta ta ce" Me zai hana in ki yin tunanin zata iya cutar da Ni? Ki duba ki gani baiwar Allahn nan du motsin da zan yi laifi ne a wajen ta a gidan nan, kina gani Mama bata taɓa sa hannunta a jikina da nufin dukana ba, Ama ita fa? Sau nawa tana kai min duka? , ko ɗinki na yi sai tace bai yi ba, ko fita na yi ba hijab sai ta min duka d'anta ma ya min, ai kuwa kin ga dole in kiyaye ta tunda Mama sheda ce ina jaririya tace ta kusan sakani a rijiyar cen dan namiji ta so haihuwa ba ni mace ba!" A'isha ta zuba mata ido, tsoro fal a zuciyarta na irin abinda take gani a kan mahaifiyarta wato mama..... Ita dai mama ce ta haifeta, itace mahaifiyarta, Ama har ga Allah lokuta da yawa takan ji tsoron halayyar mama da irin yadda take mu'amalantar auntynsu harma da tausayin auntyn da kuma imtee na kamata, sai dai ita ta sani karshen alewa kassss, tana kuma tsoron ranar da Allah zai bayyana mai gaskiya a cikin gidan nan, tabasss kowa sai ya ji kunya a gidan nan. A hankali ta ce" Wasu lokutan, kece ke ce min in yi taka tsantsan da lamarin rayuwa....., ke kuma ban san yaya aka yi sam baki iya taka tsantsan da lamarin da ya shafi Macen da ta fi kowa daraja a duniyarki ba.................., uhum bari in kai kayan abincin ciki ki share wajen" Daga haka ta shiga tatare kayan abincin, ita kuma Imtee ta sake binta da kallon mamakin yannayinta kafin ta sauke ajiyar zuciya ta shiga ninke tabarmar tana jin kiwyar yin sharar. A kantin Aban yara Kanti ne dan madaidaici na zana mai dauke da kayan masarufin abinci sai yan slifasss haka na yara da na manya.......wannan itace sana'ar aban yara kuma da ita yake ciyar da iyalinsa gwargwadon samunsa A kofar kantin suka zuba abincin shi da abokinsa amininsa Usman suka shiga ci sunna tadin rayuwa, shi kuwa Sulaiman yana daga cikin kantin yana cin nasa a cikin kwanon yana kallon waya. Fira ta yi fira, malan Usman ya dubi abokinsa ya ce" Yanzu Malan Adamu ba zaka tashi daga anguwar nan ko dan yan yayanka yan mata ka bar wajen nan da ake ta fadin abinda yake faruwa da makotanka na baya ba? Anguwa du an tashi an bar musu sun saye filayen layin Ama kai ka ki ka saida musu?" Malan Adamu yayi dan murmushi yana dubansa ya ce" Wato kana cikin mutanen nan masu daukan jita jitar bakin mutane su rike matsayin makamin yakar kansu da kansu a gaban Allah ko?" Malan Usman ya ce"A'a ko daya, Ama ai ba a Boye lamarin nan yake ba , a bayane yake ko? Ka duba ka ga tsayin ginin cen, ka duba ka ga irin motocin da ake fitowa da su , ba zaka taba gane me da me ke wakana a cikin gidan ba, sai dai ka hangi shigar motoci ko ka hangi fitowar su, kana gani du an saki gidajen da suke mane da naka an yi shaguna sai kai kadai ke nan? Baka tsoron ace tunanin da ake yi cewar a wancen tangamemen dajin gidan yankan kai ake yi a wayi gari su rasa mutanen yankawa su shigo maka gida? Ko kuma maganar da ake yi cewar akoy wata budurwa a gidan dake bin maza kake so idannuwan yayanka su gani har a gurbata musu tarbiya? In dai basu da abin boyewa yaya aka yi du tsayin lokacin nan ba za'a gane waye wa na cikin gidan ba sai bayanan da yaron gidan wancen takaradin da itama bata da kirki ne ya ishe ta ba, yaron nan Anas wanda yake direba a gidan ya fada ko? To ai ko jikina duka kunne ne Ni ba zan yarda cewar wai uwar dake gidan tana koyar da islamiyyar cen ba, harma ace tarin alkhairan da ake yi a islamiyar tasu ce... ba kuma zan yarda cewar d'anta shine mai taimako a anguwar nan ba, kai dai ai ba mahaukaci bane da zaka yarda da abubuwan nan, kai yanzu ko irin yadda direba tsal ba wata tsiya ba yake murza kudi, ya yiwa mahaifiyarsa gini ya zama itama yanzu wai sai masu kuɗi take mu'amala da su ba zai sa ka gudu da iyalanka daga anguwar nan ba?" Malan Adamu ya sauke ajiyar zuciya, a hankali ya ce" Shi dai zato zunubi ne, koda ya kasance gaskiya ne....., kai ka san Ni ba ruwana da jita jita malan Usman, to rayuwar nan ta yanzu ana ta gero ina za'a iya haɗawa da saka ido a abinda ba zai anfani mutun ba?, to kadara ma duka kaf abinda aka fada gaskiya ne, Ni fa Ni suka tardo a nan sai dai mutuwa ta dage Ni ba dai wai dan wannan abubuwan ba, in Allah yayi ta hanyar yanka zan mutu da iyalina fitar zan yi da nufin guduwa in tarda wukar, lamarin rashin ji kuwa da ake kira cewar ana yi a cikin gidan ai zamani ya kawo mu lokacin da sai dai ka bi yan ya'ya da addu'a da nasiha, domin lalata ta gama zaga duk wani lungu da sako da kake tunanin babu, sai dai Allah ya sawake....., haba bari wannan batu mu dibi girkin auntyn yara dan miyarta ta yau yada ka san ta kara kafi zakara dan ta ta yi dan karan zaki a ciki" Dariya suka yi irin ta manya, shima malan Usman din ya bar zancen, domin dama shima mutun ne mai taka tsantsan sosai da kiyaye hakin dan adam, kawai dai malan Adamu ne ya zamo amini na kusa da kusa shi yasa har magana irin wannan ta shiga tsakaninsu.........daga nan sai suka buge da barkwoncin da suka saba har kiraye kirayen sallah ya tashe su. *JAMA'A NAZOMUKU DAWANI TSARI NASAMUN KUDI TA HANYAR AMFANI DA WAYAN HANNUNKU WANNAN TSARIN SHINE METAFORCE MENENE KASUWANCIN METAFORCE* ???? *Metaforce kasuwancine ingantacce halattacce Wanda yake biya 100 💯 Wanda ake Gudanar dashi da wayar hannu,METAFORCE is also a part of network marketing,is a 100 percent decentralized project da aka daurasa Akan Blockchain technology Wanda babu wani mahalukin daya Isa YAYI editing,hacking ko deleting wani abu acikin sa,Kuma yanada matakai yanada rassa Wanda kowane reshi ka rike a METAFORCE to ka samu GUDUMAR DUKAN TALAUCI*🌎 METAFORCE ANASAMUN KUDI ACIKINSHI SOSAI MATUKAR ZAKAYI ABUNDA AKEBUKATA zaku iyahada miliyoyin kudi aranadaya acikin wannan kasuwanci me albarka in sha Allah Duk wacce tashirya zata iya tuntubanmu akan wannan number 09136899615 Hajja Data💅💅💅💅💅💅💅💅💅💅 *KISAN MUMMUƘE* 💅💅💅💅💅💅💅💅💅💅 _PAID BOOK_ *BY* _SAJIDA NIJAR_ *Yan Naija Mutanen mu 1k ne a kan wannan account number 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank* sai a bani shedar biya ta layi na kamar haka +22793811618 *Yan Nijar mutanen mu zaku turo da hoton kati ta airtel ta dala dari , wato 500francs cefa a kan Numbarna kamar haka +22793811618* *Na gode, sai kun zo.....taku ce SAJIDA NIJAR* Tallah, tallah, tallah *JAMA'A NAZOMUKU DAWANI TSARI NASAMUN KUDI TA HANYAR AMFANI DA WAYAN HANNUNKU WANNAN TSARIN SHINE METAFORCE MENENE KASUWANCIN METAFORCE* ???? *Metaforce kasuwancine ingantacce halattacce Wanda yake biya 100 💯 Wanda ake Gudanar dashi da wayar hannu,METAFORCE is also a part of network marketing,is a 100 percent decentralized project da aka daurasa Akan Blockchain technology Wanda babu wani mahalukin daya Isa YAYI editing,hacking ko deleting wani abu acikin sa,Kuma yanada matakai yanada rassa Wanda kowane reshi ka rike a METAFORCE to ka samu GUDUMAR DUKAN TALAUCI*🌎 METAFORCE ANASAMUN KUDI ACIKINSHI SOSAI MATUKAR ZAKAYI ABUNDA AKEBUKATA zaku iyahada miliyoyin kudi aranadaya acikin wannan kasuwanci me albarka in sha Allah Duk wacce tashirya zata iya tuntubanmu akan wannan number 09136899615 Hajja Data *4* A ranar nan maman yara bata shigo gida ba sai da ta fuskanci lokacin malan Adamu na iya shigowa gidan sa harma ya je dakinta dan nemanta ne ta shigo, haka kuma ta dawo ne fuskarta wasai kamar yadda ta sake dauro damarar abinda yake zuciyarta , domin tana zuwa ta dinke a daka da ƴaƴanta ta sake musu wani shirin na kalaman da a yau da ace ta kula basu da mugun tasiri a kan wace ta haifa din ma wato A'isha bale kuma Imtee, sai dai kasancewar yara ne masu biyayya sun saurare ta sun kuma jima a tare da ita har kiran sallar magariba ya sa suka nufi alwallah baki dayansu ba tare da ta takurawa daya cewar ya tashi yayi sallah ba, bayan a da sai ta yi ta surutun yin sallar karshe ma sai ta yi banza da imtee tace da ita tunda yarinya ce ita ta yi zamanta kawai..............., sai dai ta basar bata wani nuna mamakinta na ganin sun yi sallah ba tare da an saka su yi din ba ta ci gaba da zuba ido dan samun lokacin da ya dace ta yi nata abinda ya dace din. Washe gari kusan karfe takwas na safe auntyn yara ta gama share balbalin gidan tasss ta shige wanka ta fito ta saka riga da zaninta sasauka sannan ta dauki litafinta ta zauna kofar dakinta saman tabarma ta shiga karatun addini a hankali muryarta bata tashi sama sama ama idan kana daf da ita kwarai zaka iya jiyo sautin karatun dake fita cikin nutsuwa da kwarewa.......... Kasancewar idan suka fita daga girki tunda safe malan ke fita daga dakin wace ta yi girkin ya koma na yar uwarta ya sa ta sakawa zuciyarta cewar da wahala ta samu abin kari yau, sai ma kawai ta sakawa ranta dangana da tunanin ganin na rana zuwa karfe hudu zuwa biyar din yama, dan wani lokacin na ranar ma baya samuwa domin tsaf maman yara ke yin kwado dan kadan din da hatta malan ba zai samu ba, dan ce masa take yi ya'yansa sun cinye, dole kowa zai san na yi , shi yasa yawancin lokuta idan ta dau girki auntyn yara ke daukar azumi, ko ba komai ta san zata samu lada da nutsuwar zuciya domin ita kanta yinwar na yin tasiri ne idan ba azumi a baki, yau din ma ta tashi da fashin sallah ne kasancewar har yanzu bata shiga monopause ba. Fitowar yan matan cikin shigar da ta nuna alamun zasu fita ne ya saka ta daga idannuwanta ta sauke a kan fuskar Imtee....... Ya Allah, gaba daya yarinyar nan a kamanin mahaifiyarta, wato kakar imtee din babu abinda ta baro, hatta izar da kwarjinin ta kwaso wanda ke sakawa ta ji wani sanyi na ratsa zuciyarta idan ta kalleta.......... Masha Allah tamkar ba cikinta ne ya fito da yarinyar nan ba, Gaba daya imtee ta tsatso kyau da fuzga ne ga idannuwan dake kalonta, tabas halitta ta Allah ce, Allah ya tsara halittar Nur gaba da baya sai fatan Allah ya basu miji na gari daga ita har yar uwarta. Sau biyu sunna hada ido da auntyn yara da imtee , imtee din na gaggawar sada kanta , sai kuma ta ɗan juyar da dubanta tana murzar hancinta har babansu ya shigo kamar yadda maman yara tace su jira shi ya basu kudin taxi, kamar yadda ta tsara masa cewar ta aike su ne gidan bikin aminiyarta da ba zata samu zuwa ba saboda bata jin jiki, bayan tsari ne kawai, tunda yaran suka yi mata maganar sunna son zuwa gidan kawarsu dan su mata kitso da kunshi sai ta amince bayan ta san mahaifinsu ya hana haka din, yace ne shi ba zai hana su yiwa yan mata kitso ko kunshi ba, ama ya zamo an tardo su gida sun yi, ita kuma ta fada musu kar su yarda su yi kitson bati komai tsakaninsu da kawa idan suka anfaneta sai ta biya su, shi yasa yanzu ma da zasu fita ta sake jaddada musu kuma suka yi jiran mahaifinsu ya basu dari biyu kudin abin hawa dan ta sanar masa haka ne kudin motar. Da murmushi ya dubi auntyn yara ya ce" To wai yau ban ga an karya tare irin yadda jiya aka ci abincin rana tare ba auntyn yara da yaranta" Auntyn yara ta yi murmushi ta ce" Ai zamu ci idan suka dawo in sha Allah " Du irin yadda ta so jin inda zasu je su yi din gagara ji ta yi, domin maman yara ta fito ta kasa ta tsare fuskarta daure tana ta tunanin maganar malan da son gane inda ya dosa, Ama ta kasa samun amsar tambayarta ɗan kuwa gaba daya ficewa suka yi, ta san kuwa irin yadda yarinyar nan ke yin ido yanzu da wahala ta wani bata gamsashiyar amsa..........Ama ba komai zata samo amsarta ne da kanta, idan har abinda take hasashe ne kuma wallahi ran kowa sai ya bace a gidan nan. Tana ji tana gani suka yi tafiyarsu, haka ta koma dakin ta domin yau ba itace da girki ba cike da sake sake da addu'ar tsari a cikin zuciyarta. Kasancewar gidan su Kawar tasu du cikin anguwar ne ya sa basu nemi abin hawa ba, duda da yar tafiya haka suka taka suna zantawa har suka karasa gidan nasu A lokacin da suka zo shiga suka samu wata wuleliyar mota a kofar gidan a parke, suka zagayeta suka karasa cikin gidan bayan sun bude get din gidan suka shige, domin gidan su kawar tasu get din mota ne da su, kusan sunna cikin masu maiko maikon anguwar saboda yaronsu dake aiki a gidan da kowa ke son ganin cikinsa na anguwar, wato gidan da kowa ke son sanin me ya kunsa su waye a ciki Ama ba wanda yake da takamaiman amsar da ta dace. A hankali Imtee ke takawa a bayan A'isha kadan, saboda aishan ta yi ta yi su jera ta kiya ta buya a bayanta tamkar wace take jin tsoron kar wani abu ya kamata har suka karasa kofar dakin imtee ta ja ta tsaya, A'isha ta karasa tana yin Salama hadi da dakatawa. Da wani irin farin ciki Fa'iza ta fito tana ihun murna na ganinsu Gaba daya ta rasa wane zata rike saboda har ga Allah bata yi tunanin A'isha zata iya ciyo karfin imtee su zo gidan nan yau ba, sai gashi sun zo din, kai ita ta san cewa an fa gama zata dau ado da wanka yadda ya dace Jansu ta yi madaidaicin falonsu ta zaunar da su sannan ta yi ciki tana fadin tana zuwa Imtee dake kallon kasa ce ta dago a hankali sakamakon mintsininta a karo na uku da A'isha ta yi, saboda tunda suka shigo suka zauna ta sada kai bata daga ba kamar ta zo gaban sirikinta gaisuwar farko din nan A lokacin da ta dago lumsasun idannuwanta da nufin yiwa A'isha hararan da zai sa ta bata lafiya dan ita gaba daya a takure take tunda ta zo , shi yasa bata cika son shiga harkar masu hannu da shuni din nan ba, dan du sai ta ji ta takura idan ta kusanta kanta da daular su, ta fi gane gidansu na laka abinsu da pankar mafici fiye da wannan, a lokacin ne idannuwanta suka sauka a kan wanda ke tsaye yana kallonta Ga dukkan alamu fitowarsa kenan daga dakin dake falon ya ja yake binta da kallon da ya sa gaba daya ta ji ta tsargu.... "Yauwa yaya, dama kai nake dakon jira, yaya kawo kudin mana dan Allah in aiki baratu ta siyo min kayan kunshin , wallahi idan Imtee ta gaji ba zata min kunshin nan ba, ka ga Allah ya taimakeni ta yarda ta zo, plz my yaya........." Fa'iza ta fada tana alamar zata yi shagwabar nan, domin alamu sun nuna kwarai tana yiwa ƴaƴanta shagwaba a cikin gidan su Idannuwansa ya kifta yana sauke dubansa a fuskar fa'iza, lokaci daya kirjinsa na bugawa da wani irin shaukin da ya saka ya damki hannun fa'izar yayi dakinsa da ita yana rage murya sosai ya ce" Fa'iza, wacece wannan? A ina kika san wannan? Menene hadin ki da ita?" Da mamaki kwarai take kallon yayan nata, Cabdijan, to ai dole zata yi mamakinsa saboda gaskiya ƴaƴanta baban yaro ne, tabas ya samu wajen aiki na gani na fada wanda basu rage masa komai na a zo a gani a rayuwa ba, yana murza manyan motocin su, yana murza manyan suturun dake kara janyo masa yan mata ta kowace kofa......, yayansu baban yaro ne da ba kasafai zaka ga ya dubi mace sau biyu ba, kai ko budurwarsa da aka sani a gidan su ita ke fama da ranta, saboda irin yadda yake wahalar da ita har tausayi take basu, gata kyakkyawa da ita mace har mace ama idan ya kiya har kuka yake sakata yayi tafiyarsa sai dai su su rarasheta......,maganar da ake yi ana shirye shiryen kai kudi gidansu ma fa Murmushi fa'iza ta yi tana dubansa ta ce" Yaya kawata ce fa, kawayena ne , yan uwan junna ne, itace nace maka idan Allah ya taimakeni zata zo ta min kunshi na bikin nan" Idannuwansa ya rintse yana budewa lokaci daya ya sake zuwa ya dan dage labulen nan ya leka su imtee dake zaune sannan ya dawo ya zauna daf da gadonsa yana shafa kansa a bayane ya furta" Calm dawn , calm dawn, babu Macen da ta isa ta dubeka ta kasa yabawa a duniya....babu ita" Da mamaki fa'iza ta ce" Yaya, me kake nufi? Kai da kake da fiancé?" Hannunta ya kamo yana dubanta ya ce" Ki rage murya, dan ba zan yarda ki min gangamin maganar da zata shiga tsakanina da yarinyar nan ba, ke Ni fa namiji ne, ina da damar kawo mace hudu a rana guda matsayin matana...., bale idan yarinyar nan ta budi baki tace bata so in kuma fada maki magana ko ke kanwata an gama bale wancen uwar nacin!" Baki fa'iza ta saki tana dubansa Yayi yar dariya ya mike ya bude walt dinsa ya ciro kudin da suka sa fa'iza zarro ido yana kalonta ya ce" A siyo mata duk wani abinda zai sa ta ji dadin zama a gidan nan na ci da sha, kar ki wahalar da ita plz, bari in je in dawo ki tabatar da kin rike min ita har in dawo Fa'iz....." Fa'iza kam ta kudaden nan take, hannaye biyu ta sa ta karɓe tana gyada kai hadi da fadin" Kar ka wani damu big yaya , Allah dai ya dawo da kai lafiya kawai" Murmushi yayi ya sakawa kansa nutsuwa sosai hadi da janyo duk wani ajinsa, saboda ya san cewa idan akoy abinda ke saka shi jan hankalin yan mata bayan wanka da kanshin turare da hawa Babar mota da latsa Babar waya to kuwa ajin da yake ja musu ne....., ya sani ne idan ya ja mata ajin itama tabas ya gama tafiya da ita, ta yiwu zuwa gaba itama sai tana nemansa yana wulakantata tana masa kuka. Ga tarin mamakinsa du irin uban turaran da ya kara a jikinsa a lokacin da ya zo fita ko idannuwanta bata daga ba bale har ta nuna ta san da wanzuwar wani bawa mai rai a wajen...., hakan ya sake daure masa kai da tunanin du inda ta fito wata Y'ar masu kuɗin ce da har ya zamo shi bai isheta kallo ba......... Tabas du irin yadda yake da garatee da yarda da kansa sai da ya ji tsoro tsoro na son kama shi....... Da gaske abinda bai yi zaton haduwa da shi bane ya sarke shi da farar safiyar nan har yake kokarin yi masa kisan mummuken da zai hana shi sukuni. Tabas da ba dan fitar nan da zai yi dan

Chapter 3 of 9