kin ci zalinta? Kin ga ki bari, kar ki yarda ki kuma dukanta tunda ba abinda ta maki!"
Ran Mama karama ya bace sosai, ta fuskanci Maman yara, a tausashe ta ce" Maman yara, ki yi hakuri, ama kalmar tsanar da kike fada ta yi tsauri sosai harma tana bani mamaki fiye da tunaninki......, "
Ta ɗan saurara ta sake dubanta ta ce" Anya kuwa rai zai ci gaba da daukar wasu shaguden ? To ai maman yara bana tunanin gangar jiki zai tsani tsanin Ran da ya ratsa jiki ya fito duk tsanani kuwa......, sai dai idan wata sharar ke kama da farmakin nutsuwar yan gwongwon ne zaki ga sun mamaya, Ama duk rintsi sai dai rai ya bace a zartar da hukunci a kuma yi hakuri......"
Ta dubi imtee dake ta shashekar kuka, duba irin na cikin ido, duban da zata iya rantsewa bata taɓa ganin mahaifiyarta ta yi mata shi ba
A kausashe sosai ta ce" du Wanda zai yi maka fada dan ka gyara kayanka ba makiyin ka bane, shekara goma sha takwas kin yi tsufan da ya dace ace zuwa yanzu zaki iya gane mece rayuwa...., !"
Ta dago yar yatsarta ta nuna mata a kausashe ta ce" Bana tunanin zan iya gani in kyale a duk abinda yake ci gaba da wanzuwa a kan ki, wanda ya shafe ki, idan baki je islamiyya ba me zaki anfana da shi gobe kiyama? Ki je ki koyi ilimi, ta yiwu ki gane abinda kike ciki!, ki je ki dauko ilimi, shine kadai abinda na umarceki da shi, idan har kika kiya NUR a nan ne zaki ga kalata, na baki minti biyu ki saka hijabinki ki bi yar uwar ki ku wuce makaranta!"
Daga haka ta juya ta fice daga dakin
Sai dai tana fitowa maman yara na biye da ita rai bace ta ce" Ke ramatu dakata, dakata ki gaya min abinda kike nufi!"
Dakatawar Mama karama ta yi tana juyowa, a lokacin da Sulaiman ya shigo dauke da buhun shinkafa a kafadarsa ya karaso kofar dakin ya sauke sannan ya ja ya tsaya yana kalon su dan tsayuwar tasu ta masa kama da wa'inda ke fada
A tausashe Mama karama ta ce" Maman yara, dan Allah ki yi hakuri, wallahi ban yi mata haka dan in bata maki rai ba, Ama rashin mutuncin Nur yayi yawa ne, Maman yara dan ta ga Bakya son bacin ranta ne har take irin wannan sangartar dake iya kaita ga halaka, ki duba ki gani, shekarunta da ajin da take a boko, ga na islamiyyar bata da wani abin a zo a gani, to shi karatu lokaci baya taba kurewa dan yinsa in dai da rai da lafiya, Ni kuwa in sha Allah Ni da ita za'a ga wanda ya gaza ki barni da ita!"
Fitowar yan matan da jakar karatunsu yayi daidai da shigowar mahaifinsu shi kuwa dauke da kayan miya masu dan yawa, dama kasuwa suka je shi da Sulaimana suka yo sarin kayan saidawar da yake zubawa a kantinsa, shine ya musu cefane na kirki dan a kara dan lasawa yau ma, dama yawanci idan ya samu kudi mai dan auki haka suke yi, wani lokacin har kashin miya ake samu a watsa a girkin, ko a yi dambu ya sha hadi a ci har a mikawa makota, yau din ma cefanen ne harda naman miyar, ya shigo da Salama
Har ga Allah sai da gaban Mama karama ya fadi, nan da nan ta so daburcewa, bale da ta ga irin kallon da ya bita da shi sai da hankalinta ya tashi lokaci guda, uwa uba irin yadda maman yara ta shiga share hawaye ta kunto yan cenji a habar zaninta ta mikawa Imtee ta ce" Ki amsa, idan kun je kin ji ciwon zai kayar da ke ki sayi panadol ko ciwo takwas ki sha, Allah ya gani ina kaunar ki da zuciya daya, sai dai tabas mahaifiyarki tana da gaskiya, ta fi Ni iko da ke a gidan nan, ku je Allah ya tsare"
Amsa suka yi suka wuce, Sulaiman ya tabe baki ya juya ya shige dakin mahaifiyarsa saboda yana son daukan abu a ciki, ko kuwa haka kawai ne baya so a yi maganar a gabansa? Ya san kuwa inda mahaifinsa ya tsaya a nan zai fara maganar nan.
Rai bace ya ce" To, menene? Menene? Safiya ta yi gwana zaki daga min hankalin ko?, wani irin kin fita iko da yarinyar nan? Ke ko kara baki iya ba? Hala zaginta kika yi a kan yarinyar nan? Nuna mata iyakarta kika yi ko?"
Mama karama ta girgiza kai, bayan ta gama mamakin maman yara kamar yadda ta saba ta ce" Yaya zan iya budar bakina in zageta? Ta yaya zan iya zaginta?"
Maman yara ta fashe da kuka tana kaiwa zaune hadi da duban baba ta ce" Da wani abin ai gwara zagin, daga cewa yara su fito su je islamiyya na nuna mata imtee bata da lafiya a barta ta sha magani Shikenan matar nan ta shiga hawa tana sauka da tarin bakaken maganganun da kunnenka ba zasu so ji ba?, a yau harda min gorin ba Ni na haifi imtee ba, harda nuna min sunan da nake kiranta da shi baida wani tasiri ta hanyar kiran imtee da Nur?, tabas kina da gaskiya, sai dai ki sani Allahn da ya baki nima ya bani, kuma d'a daya gari ne in da rai da lafiya, idan imtee ta dawo ta kwaso kayanta ta koma dakin ku, Allah ya rayata, in dai zan ringa ganin wulgawarta ai Shikenan hankalina ba zai tashi ba, Ama ki sani masoyi ba makiyi bane"
Daga haka ta nufi dakinta tana sake daga muryarta wajen yin kukanta.
Gaba daya mama karama sai ta gaza koda motsa yar yatsarta ne
Bale da mai gidan nata ya budi baki ya ringa masifa tamkar zai ari baki, ya tabbatar mata duk ranar da ta yarda imtee ta dauko kayanta da zumar komawa dakinta sai dai ta bar gidan dan ba zata fito masa da fitina a cikin gidansa ta barshi da wahala ba, ya kuma sheda mata yana iya sake kayar da rago ya sakewa imtee sunna daga sunanta na gaskiya wanda aka rada mata zuwa imtee kuma ya ga ubanda ya isa ya hana shi, yaran nan dai ya'yansa ne, bai ga wanda ya isa ya shiga tsakaninsu da uwar gidansa ba, dan haka a kiyaye shi wallahi a kan haka yana iya Salamar mace, in ba ma rashin tsoron Allah ba da ta samu ya'yan biyu ita ta ba kanta ne? Aikin banza aikin wofi kawai.....
Ya karashe yana juyawa bayan ya watso mata cefanen ya fice a gidan dan dama ya barawa kaninsa kantin ne du hankalinsa na cen, dan kuwa ya sha bara masa ya dawo ya tarar da muguwar barna.
Jiri ke dibanta, a hankali bayan ta kwashe cefanen ta nufi dakin nata tana dafa bango
Fitowa yayi kansa a kasa ya ratse ta ya nufi kofa
Ba tare da ta bishi da kalo ba ta samu ta shige dakin da kyar sannan ta duke tana dafe kirjinta dake mugun bugawa.
Bata ji shigowa ba, sai hannunsa da ta ji a saman nata yana kalonta fuskarsa da alamun tarin damuwa
A hankali ta furta" Sule....."
Kansa ya dukar a hade ya ce" Baki da lafiya ne?"
A hankali ta girgiza kai, ta zauna da kyau cike da mamakin ganin wannan lamari, Duda halin da take ciki kuwa, domin ba abinda bai faru ba a gabansa Ama bai taba nuna ya gani Bama bale har ya dubeta
A hankali ta ce" Lafiyana kalau"
Ido ya dan kikifta, sai kuma kasa kasa ya ce" Ba dai wancen yarinyar bane ta ja ake zaginki? Sai na ci ubanta a gidan nan yau, dama ai ke ne, kike fifitata a kaina, idan ta min rashin kunya ku hadu ku rufun min, zata dawo gidan nan ne munafuka, kuma kin ga ki daina shiga sabgar matar cen, gaba daya kama da munafukai take min a kullum ta Allah, baki ga Ni bana harkarta ba?, gaskiya ki daina shiga sabgarta dan sam kamar bata da gaskiya, yaushe zaki iya zagin mutun in ba munafurci ba? Kin tashi kin mika mata y'arki gayanan du ta koya mata munafurci, wallahi dai na fada muku idan na kuma ganin ƙatuwar Y'ar cen ba hijab a layi tabas sai na balata, bari in samo maki ruwan sanyi ki sha ajiye masa cefanansa , ai sai ya sake kin in gani, aikin banza kawai su sako ki a gaba suna zagi, wallahi ki fita harkarsa, ba ke ba shi a gidan nan kar a sa in yi danyen aiki dan kuwa ai kece babata, gaskiya biyayar da nake masa fa ba zata sa eh ina kallo ya wani ringa maki eyane ba, na fa girma sosai tam!"
Bai tsaya ya ji daga gare ta ba ya wuce yana muzurai
Gaba daya sai ta rasa murna zata yi, kuka zata yi, ko alhinin maganganun yaron nata?, tabas Sulaiman na cikin dabar layin nan wa'inda sam basa jin maganar kowa, shi yasa yake abubuwan da basu da kyau ko kadan.
A hankali ta talabe habarta tunani na zuwar mata kamar haka.......... A lokacin da ta samu cikin Sulaiman, irin tashin hankalin da ya faru a gidan ba na wasan yaro bane, har ta haife shi , domin bayan rasuwar mahaifin baban su Sulaiman din ne ya aurota a lokacin da ya samu gidan nan , matarsa da suke tare shekara da shekaru bata samu haihuwar ba tukunan, dan ba abinda bai faru ba har irin yadda yan uwanta ke fadin shine baya haihuwa ya salameta ta auri wani, da zuwan ita maman su Sulaiman din da samun cikin nan, har sai da aka ringa fadin ba nasa bane, sai dai Allah da hukuncinsa Sulaiman da ya zo duniya sai ya zo kamar an yi kaki an zubar na mahaifinsa, tak da tak kamaninsa ke ba yan Barka amsar yaro fa d'an ubansa ne.........., shekara biyu tsakani kuma ta samu wani cikin, a lokacin ita din ma Allah ya azurtata har ta samu aisharta domin tsakanin Sulaiman da A'isha wata tara ne, tsakaninsa da imtee kuwa shekara biyu ne.
Ko a lokacin haihuwar imtee ba karamin dauki ba dadi aka sha a gidan ba, saboda imtee ta ci mahaifiyar Babarta ita mama Ramatun ne, wannan lamari ya kawo rigima kala kala domin maman A'isha kanainayewa ta yi ta nuna a kan me, ta yaya za'a aikata haka? Daga baya sai kawai ta shigo da batun to ta yiwa yarinya nak name da imtee, ba yadda ita maman su Sulaiman din bata yi wajen nuna a'a ita ga sunan da take so a ringa kiran yarinya da shi wato Nur ko khairy , Ama aka ci karfinta aka nuna mata a so danka ma ai kai aka so, bale mahaifinta da aka gama siye masa zuciya da cewar ai ba kamar mai son d'anka, sai kawai yake horon mahaifiyar su nur din cewar ta iya kawar da kai ta iya yin kara a kan wanda ke son d'anta, a dole ta yarda tafiya ke mikewa cikin hargitse da ZARGE kala kala na yau da gobe har zuwa yanzu da ta gama yarda da abinda ke faruwa da duniyar ta kamar wace ake yiwa shigo shigo ba zurfi da lalata tarbiyyar yarinyarta ta hanyar nuna mata kauna ana so a Sakata a uku ta yadda ba zata taba iya kwatar kanta ba a rayuwar yau da gobe??????
To in ba wannan ba Fisabililahi yaya za'a yi ace wai soyayya ce ake gwadawa yarinya mace ba shara, ba wanki, ba girki ba wanke wanke ba koyon tsafta ba duk wani abin alkhairin da aka san cewar shine adon mace, uwa uba ba maida hankali a karatun bokon ko na addinin, kulun cikin sangarta da shirme? Wani irin soyayya ce haka an sakawa y'arta ta cikinta batun ta tsaneta? An saka mata batun bata son ta? An koyawa yarinya rashin kunya?????, imtee na iya sa in sa da du Wanda ta kama, tana iya dambe a duk inda ta kama, tana iya fita ba hijab ba mayafi ta ratsa layi, kai du inda aka ga imtee sai an nunata saboda ko tsarin halittarta ba irin ta A'isha bace, ba zaka taba yarda cewar A'isha ce ta girmeta ba, dan kuwa shiga ido ne da ita sosai da sosai, Ama a haka ake tafe....????, to wai, wa zata fadawa wannan maganar ya yarda da abinda ke ranta bayan hatta gidansu ta gama siye mutanen gidan nasu cewar ana son ta ana son y'arta Ama ita sai wani abu take yi marar dadi...... Shi yasa ta fi gane kwatanta fito na fito dan samawa kanta mafita.. a yanzu, ama tana tsoron hukuncin malam.....
Dawowar Sulaiman da magani ya saka ta mike dole ta amsa ta sha domin a chemis ya amso maganin, sannan ta samu a hankali ta ringa dan jansa da fira tana nuna masa ba laifin mahaifinsa bane, ba kuma na kanwarsa bane, hakama ba na matar babansa bane, an samu rashin fahimtar juna ne kawai, domin ba zata taba so maganar ta yi nisa ba, shi kuwa abinda ya fi tsana kenan , irin yadda shi ba makaho ba, shi ba kurma ba, Ama a kullum mahaifiyarsa ke shigewa bayan wa'inda suke muzguna mata...., karshe mikewa yayi ya fice kawai a gidan gaba daya, wanda a kan idannuwan maman yara ya fice din dan ta dage labulenta tana jira ta ga zata fito ta ɗora girkin ne ko yaya?
Tsaki ta ja, a ranta tana ayyana ' Dan iska kawai, kai ai bakin cikinka kadai ya isa ya kashe uwarka!'
A hankali suke tafe ita da A'isha bayan sun sauko daga islamiyyar
Har yanzu fuskarta a hade take, idannuwanta kuwa tun kumburin kukan da ta yi na Dazu basu saku ba, domin ba wahala take so ba ko kadan
Ita A'isha tana tunanin kar su je gidan su tarar da wata fitinar ne ya sakata kashe kafa, dan har ga Allah ita ba wani son an yi an yin nan take ba,
ita kuma Imtee ta gama fadawa cikin sake saken dake hargitse mata tunani lokuta da yawa, Bama kamar irin wa'azin da aka musu yau, domin bakon malami ne suka yi wanda ya musu wa'azi a kan girma da darajar iyaye a musulunci , a wajen Allah.
Sun shanyo kwana kenan suka dakata sakamakon kiranta da kawarsu ke yi tana dan sauri har ta cin musu tana murmushi ta ce " Sis A'isha, dan Allah ki saka baki mana Kawata ta min kunshin nan, Allah biki ne na manya, ina son halarta cikin shigar da ba za'a raina Ni ba tun daga tufafina har yanayin kwaliyata, na san da ba zata min mak'up ba, Ama ta min kunshin ya wadatar "
Imtee ta lumshe idannuwanta ta ɗan kirkiro murmushi a hankali ta ce" Ama kin san mamanmu ta hana Ni yin kunshi da kitso ko?, ki je wani waje a maki mana "
girgiza kai ta yi ta ce" Ama yanzu mama zata hana ki min Ni? Zan je in tambayeta da kaina"
Da sauri A'isha ta ce" A'a , kar ki damu zamu zo ta maki in sha Allah, kyaleta sai ta maki kunshin nan"
Farin ciki ya sa ta kama hannun A'isha da murna ta sanar musu tana jiran su sannan ta wuce layinsu cike da murna , suka ci gaba , domin basu da nisa sosai da juna, kuma tana ganin motar da yayanta ke ja ta mai gidansa ta cika da zumudi ta shige gidan dan ta san yau kam sai ta more da yan kudade, domin yayansu direba ne, yana jan daya daga cikin motocin gidan wani hamshaki dake cen bayan layi. Wanda tunda ya kauro anguwar ya gama siye gidajen anguwar domin ko gidan su Imtee sai da masu kula da harkar gidajensa suka zo neman babansu ya siyar da gidan ya nuna ko daya ai gidan nan sai dai idan ya mutu magada sa siyar, makotansa kuwa du sun siyar sai shi kadai
Har sun kusa shiga gida a hankali imtee ta ce" Yaya za'a ce wai idan ka batawa mahaifiyarka...wato wace ta haifeka ya zamo tana fushi da kai Allah zai kona ka? Yaya za'a yi ace darajar ta ta girmi ta mahaifi bayan ita tawa sam bata so na?, yanzu ana nufin fa darajar tawa ta girmi ta mamanmu? Ke shaida ce bata so na, bata kaunata, Shikenan sai a hada soyayyar da mamanmu ke min da Tata? Ni kam ko jikina duka kunnaye ne ai ba zan iya lamunta da wata fadar ba!"
A'isha ta dubeta, duba mai dauke da ma'anoni kala daban daban
A hankali sosai dan sun zo daf da shiga gidan nasu ne ta ce" Fadar Allah ce ai aka sanar mana ba fadar wani ba, na tabbata kuwa babu wanda zai tsara dan ya birge mu,....to ke a taki fahimtar ta yaya za'a hada wace ta dau nauyin cikinki na wata tara, wani tudu wani gangare wace jarabawa har kika zo duniya, ta shayar da ke ta kula da ke, da wanda bai yi hakan ba?, ban ce maki girman darajar babanmu bata da girma ba, ban kuma ce maki wai mamanmu bata son ki ba, abinda na sani shine........ko waye tabas zai biyo bayan mama karama a duniyarki ne!"
Daga haka ta shige gidan ta barta tsaye tana kalon bango.........
Shin me yake faruwa ne?
Me yasa abin nan ya mugun tsaye mata a zuciya ne?
Yaya za'a yi a rayuwa ta iya rabar mama karama ne bayan a bayane ta gane cewar idan ta samu dama tana iya kasheta?????
Ya Allah..........💅💅💅💅💅💅💅💅💅💅
*KISAN MUMMUƘE*
💅💅💅💅💅💅💅💅💅💅
_PAID BOOK_
*BY*
_SAJIDA NIJAR_
*Yan Naija Mutanen mu 1k ne a kan wannan account number 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank* sai a bani shedar biya ta layi na kamar haka +22793811618
*Yan Nijar mutanen mu zaku turo da hoton kati ta airtel ta dala dari , wato 500francs cefa a kan Numbarna kamar haka +22793811618*
*Na gode, sai kun zo.....taku ce SAJIDA NIJAR*
Tallah......tallah .....tallah....
*JAMA'A NAZOMUKU DAWANI TSARI NASAMUN KUDI TA HANYAR AMFANI DA WAYAN HANNUNKU
WANNAN TSARIN SHINE METAFORCE
MENENE KASUWANCIN METAFORCE* ????
*Metaforce kasuwancine ingantacce halattacce Wanda yake biya 100 💯 Wanda ake Gudanar dashi da wayar hannu,METAFORCE is also a part of network marketing,is a 100 percent decentralized project da aka daurasa Akan Blockchain technology Wanda babu wani mahalukin daya Isa YAYI editing,hacking ko deleting wani abu acikin sa,Kuma yanada matakai yanada rassa Wanda kowane reshi ka rike a METAFORCE to ka samu GUDUMAR DUKAN TALAUCI*🌎
METAFORCE ANASAMUN KUDI ACIKINSHI SOSAI MATUKAR ZAKAYI ABUNDA AKEBUKATA
zaku iyahada miliyoyin kudi aranadaya acikin wannan kasuwanci me albarka in sha Allah
Duk wacce tashirya zata iya tuntubanmu akan wannan number
09136899615
Hajja Data
*3*
A hankali ta shige din itama, takalmin dake kafarta slipas ne, hakan ya sa ana iya ganin duk wani abu dake kafar hatta abin da ta shafa wanda in dai mutun na sallah baya shafawa, ga kumbunan kafar tata du sun yi zako zako
Kai mama ta dago tana amsa Salamar ta cen ciki itama kafin ta dan zuba mata ido tana binta da kallo har ta dauki hanyar dakin maman yara
Dauke kai mama ta yi zata ci gaba da aikinta ta ji alamun tsayuwar mutun daf da ita sosai
Sake sauke dubanta ta yi a kanta, sai kuma ta zubawa fuskarta ido da irin yadda take ta murza yan yatsunta ama ta kasa budar baki sau daya jal ta yi wata maganar kanta tsaye zuwa gare ta ita mahaifiyarta
Ajiyar zuciya auntyn yara ta sauke bayan ta gama yarda cewar sai fa ta yi mata magana zata iya yi itama, dan haka a hankali ta ce" wani abu kike so NUR?"
Idannuwanta ta dauke a hankali tana jin irin yadda kirjinta ke wata irin harbawa du idan ta kusanci mahaifiyarta....., haka kuma tsoron ta take ji kamar me, to ai mama ta fada mata kar ta ringa matse mata waje wai da tana jaririya akoy lokacin da ta nemi wurgar da ita cikin rijiya dan tsagwaron tsana, dan haka a hankali ta ce" Ba komai......"
Sannan ta ɗan ja baya idannuwanta na cikowa da kwallah
" Ya dace ki daina shafa pentin nan a kumbunanki, ina ganin kin san cewa haramun ne shafa shi, ko Bakya sallah ne Nur?"
Mama ta karashe tana saka tabaryarta ta shiga daka a hankali , hankalinta na kan yarinyar nata, sai dai bata nuna hakan a bayane ba
Samun kanta ta yi da zuba mata ido bayan ta dubi kumbunan nata, eh kwarai ta san cewa haramun ne , hatta tara kumbunan haka ba kyau, to ama ai mama ce ke cewa su yara ne, ba wata damuwa, shi yasa take siya mata ita kadai du ire Iren abubuwan nan, saboda bata ba yar uwarta su.
Juyawa ta yi ta nufi dakinsu , bata cewa mahaifiyarta komai ba, haka kuma yanayin mahaifiyar nata ya tsaye mata a rai sosai.
Bayan ta zauna maman yara ta dubeta ta ce" Me kika je yi wajen matar cen? Wato ba zaki daina matse mata waje ba sai ta ilata min ke ko?, menene take fada maki? Ko fadan da ta saba da wulakanta min ke din da ta saba ne take yi? ........kai Ni kam ina ganin tashin hankali da wannan baiwar Allah, koda yake wanda ya ajiyeta zai dawo ya gama yi mana tsakani da ita, ta fita harkarki kawai bana so, ta bar min tunda ta haifa tace bata so Ni ina so, dan haka ba wanda zai takura min ke in dai ina raye!"
Da farko bata yi niyar bata amsar tambayar abinda ta je yi din ba saboda gaba daya jikinta a mace yake, sai dai da ta ji tunanin da Mama ke yi cewar auntynsu dukanta ta yi ya sa a hankali bayan ta cire hijabinta na islamiyya ta ajiye kudin da Mama ta bata da zata fita sannan ta karasa wajen kwondon dake dauke da kayan kwaliyar A'isha ta duba ta ciro reza a hankali ta ce" A'a, tuna min ta yi rashin amfanin shafa abin nan ga Musulmi koda kuwa bana sallah"
Daga haka ta shige ciki ta zauna a hankali ta shiga yanke akaifun kafafuwanta kafin ta shiga kankarewa tana cire pentin da ta shafa musu da kuma datin dake jikinsu.
Maman yara ta jima a zaune a inda take,
Ganin da gaske tashin hankali ne ke tunkarota ya sa ta mike ta ja abin rufa ta fice a gidan ba tare da ta sanar musu cewar zata fita ba, domin idan har ta kara wasu lokuta gani take yi komai na iya faruwa
Ita kuma auntyn yara girkin nan ta tsaya ta tsara, sannan ta dauko kwanoninta Samira sababi ta wanke tassss ta juye na malan ta kai ta ajiye ta kuma zuba na dakin maman yara ta kai ta ajiye .
Har zata fito ta samu kanta da dan dakatawa, a hankali ta ce" A'isha"
A'isha dake ciki ta mike ta fito tana duban auntynsu bayan ta amsa
A tausashe sosai auntyn yara ta ce" Barci kuke yi?"
A'isha ta girgiza kai tana kallonta
Auntyn yara ta yi murmushi ta ce" Na gama girki, ko na zuba mana mu ci tare?"
A'isha ta yi sororo, cike da tunanin anya kuwa? Idan suka ci abinci da auntyn yara Mama ba zata yi fada ba kuwa?, sai dai irin yadda auntyn yaran ta tsareta da ido irin na Imtee sai ta ji ta gaza musawa, domin wani irin launin ido ne da su mai saka a yi musu biyayya koda ba'a so,
Cikin shaku ta gyada kai sannan ta shige dan fito da imtee
Zuwa mama ta yi ta share karkashin Dalbejiya ta shinfida tabarma, a nata abincin ta zuba musu harda su jan ruwa ta kai ta ajiye tana jiransu da tunanin ta yiwu ba zasu fito ba domin kamar da wasa an kwashi minti ashirin da gayyatar da ta musu na cin abinci