ya dauko KANWAR uban gidansa daga aéroport bane da babu abinda zai sa ya fita ba tare da ya samu matsayar da ya dace da kwonciyar hankalinsa ba.....
......' Wai dama akoy launin Fatar da ba fara tas ba dake da dukan zuciya da dukan idannuwa a duniya? Ashe launin Fatar da ba fara ba raina kanta ta yi har ake hango wata kalar da ba ita ba a gabanta??????......' su ne kalaman da yake ayanawa a zuciyarsa a lokacin da ya tashi motar nan ya dauki hanyar barin anguwar zuciyarsa cike da sake saken da bai taba yi a kan wata y'a mace a duniya ba!
A falon su Fa'iza Muryar fa'iza da A'isha ne kawai ke tashi, sunna fira irin ta yan mata har suka gangara firar islamiyyar da suke yi tare, wace itace karin karfin zumuncin nasu
Mahaifiyar su Fa'iza da ta gama aikinta ta fito suka gaisa da yan matan sannan ta yi waje tana fadin" Fa'iza ki kuna musu tv mana? Sannan ki dafa muku indomi na san sa ci, Ni bari in je nan in dawo kafin yan uwanki su shigo, idan yayanki ya zo kuwa ki amsar min sakon da na fada masa jiya wanda za'a aikawa bafanku kauye"
Fa'iza ta amsawa mahaifiyarta sannan ta dawo da dubanta kan A'isha dake fadin" Yanzu kina nufin za'a saka dokar idan har ka wuce shekara a ajinmu baka yi sauka ba za'a dawo da kai aji hudu?"
Fa'iza ta dubeta ta ce" Haka yayanmu yace, yace ne wai SIR IMAD zai shigo kasar a karshen watan nan, idan ya zo za'a zauna da Iyayenmu a gabatar da komai, in mutun ya yarda d'ansa ya ci gaba da ɗaukan karatu a nan, in baka yarda ba sai ka mayar da yaron ka wata makarantar"
Imtee ta tabe baki hadi da yatsine bakinta ba tare da tace komai ba
A'isha ta ce" Ki ce mu dage, dan gaskiya Ni ina son makarantar nan, ba zan so a koreni ba"
Imtee ta dago idannuwanta ta dauke a fuskar A'isha, a hankali ta ce" So what?.......idan aka kore ki sai a kai mu wata da bata kai wannan tsada ba, ta yiwu kashe kashe zai ragewa baba tsauri ai....karatu kuwa a ko'ina ma yi ake yi sai idan ba'a da niyar yi din tun asali"
Fa'iza ta girgiza kai tana duban Imtee ta ce" Kwarai ko'ina ana karatu Imtee, ama karatun da aka samu daga wajen kwararrun malaman da suka San kansu suke da manyan diploma a harkar addini, wa'inda zasu bi ka'idojin da ya dace dan su koyar da kai adininka wanda shine zai sa ka san kai din da kanka waye da Ubangijin da ya halicce ka ya fi a ganina....., kin kuwa san yayanmu yace harda wata jarabawa da za'a saka wace zata ba daliban da suka samu, damar zuwa Madina dan karin ilimi?,"
"Dan Allah?, wayo rabi ka Kai ni garin Manzo, innalilahi da ban san irin farin cikin da zan yi ba....., to Ama Fa'iza Saudiya fa kike nufi? Zuwa a yi sallah a dawo kadai yanzu ya gagari mai jarin ciyarwa bale zuwa a zauna?" A'isha ta tambayeta cike da mamakinta
Fa'iza ta dubeta da mamaki ta ce" Kina tunanin za'a kawo wannan farin cikin mai tafe da gigitar aljihu a zamanin nan da ake faman na salati a zubawa mai dakon na masara?, a'a, za'a yi komai ne bisa tsarin da ya dace, wa'inda zasu kawo maganar sune masu ya'yan bankin a hannayensu, su zasu ji da yakin dala da kwabon ai"
Imtee ta girgiza kai ta kama dayan hannun Fa'iza ta ci gaba da zane mata shi cikin kwarewa a ranta tana ayyana magana kamar haka' Ai ba da Ni ba wannan kasadar....., baka kai kanka bama an sace ka bale ka kai kanka da kanka? Idan aka zowa malan Adamu ubana da batun na bata a Saudiya ai murna zai yi yace na samu kyakkyawar mutuwa , mutuwa irin ta Saudiya? Hum , ta yiwu bama zan samu fita daga Nijar din ba za'a yi dabgena ko a mayar da ni dokin yan bariki......a je Saudiya lafiya ko na san amsa ba zan amsa ba bale in zama abar farautar yan daba!'
................wannan kenan💅💅💅💅💅💅💅💅💅💅
*KISAN MUMMUƘE*
💅💅💅💅💅💅💅💅💅💅
_PAID BOOK_
*BY*
_SAJIDA NIJAR_
*Yan Naija Mutanen mu 1k ne a kan wannan account number 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank* sai a bani shedar biya ta layi na kamar haka +22793811618
*Yan Nijar mutanen mu zaku turo da hoton kati ta airtel ta dala dari , wato 500francs cefa a kan Numbarna kamar haka +22793811618*
*Na gode, sai kun zo.....taku ce SAJIDA NIJAR*
Tallah.....mun kasa Allah ka siyar mana
*JAMA'A NAZOMUKU DAWANI TSARI NASAMUN KUDI TA HANYAR AMFANI DA WAYAN HANNUNKU
WANNAN TSARIN SHINE METAFORCE
MENENE KASUWANCIN METAFORCE* ????
*Metaforce kasuwancine ingantacce halattacce Wanda yake biya 100 💯 Wanda ake Gudanar dashi da wayar hannu,METAFORCE is also a part of network marketing,is a 100 percent decentralized project da aka daurasa Akan Blockchain technology Wanda babu wani mahalukin daya Isa YAYI editing,hacking ko deleting wani abu acikin sa,Kuma yanada matakai yanada rassa Wanda kowane reshi ka rike a METAFORCE to ka samu GUDUMAR DUKAN TALAUCI*🌎
METAFORCE ANASAMUN KUDI ACIKINSHI SOSAI MATUKAR ZAKAYI ABUNDA AKEBUKATA
zaku iyahada miliyoyin kudi aranadaya acikin wannan kasuwanci me albarka in sha Allah
Duk wacce tashirya zata iya tuntubanmu akan wannan number
09136899615
Hajja Data
*5*
A lokacin da ANAS ya karasa aéroport ya dauki a lokaci mai tsayi yana jira, a kadan awa da rabi kafin jirgin su FARHANA ya sauka, haka kuma tana fitowa daga wajen da yan tafiya ke fitowa ta haɗa masa komai ta zauna wajen vip tana shan ac da jus shi kuma ya je wajen custan din dake duba kaya aka gama aunawa ya kai mota sannan ya zo mata da wani jus din mai sanyi da faro ya dauki karamar jakarta suka nufi mota
Bayan ta shiga bayan motar ya ajiye jakar nata a gaba sannan ya dauki hanyar gidansu yana sauraron yadda take amsa waya a hankali , cike da yanga da kuma alamun ta gaji da zaman jirgin ne ko menene oho.
Tsakanin filin jirgin da karasawa har cikin gidansu ma sun dauki sama da awa daya sannan ya fito ya bude mata bayan ya je yana ciro kayanta dake Boot
A hankali ta fito daga motar ta yi tsaye tana duban sararin samaniya tana auna zafin ranar da ake yi yau a gasarta...........
Idannuwanta ta kai kan mutanen da suke yawan kai kawo a filin gidan , ciki harda almajiran da ta fi tsana na malamin marigayin mahaifinsu, wanda ya riga ya zama ɗan uwansu domin a yanzu haka yana zaune a cikin gidan da matarsa wace ta fi shakuwa da baban ƴaƴansu dan kuwa shi din da kansa ita ta raine shi , ita kuwa yawan zuwan almajiran nan daga cen kauyukan su malan na daya daga cikin tarin abubuwan dake damunta a gidan nan da kasar nan baki daya........, ciki kuwa harda wannan baban hukuncin da yayanta ya yanke ya sayi fili a irin wannan anguwar ta kauyawa ya tada gini ya sayi wani filin ya yi islamiya ya sa aka kwaso su, su , da girmansu da darajar su aka kawo su rayuwa a nan.............ai ba zata taba yafe wannan wulakancin da aka janyo mata ba, shi yasa tunda suka kauro nan bata taɓa yarda kawarta daya ta zo gidan nan ba, uwa uba saurayinta, sai dai ita ta je inda suke dan ba zata taba yarda a ratso anguwa mai kwata a tardo gidan nan ace nan ne take rayuwa ita ba!.
Karaurawar dake sheda bako na son shiga falon , Anas ya dana sannan ya dakata har mai aiki ta zo ta bude ta amshi akwatin bakuwar ta juya sannan ya juyo yana saukowa da nufin tafiya inda ake jiransa, dan kuwa kowa da bikin zuciyarsa da kuma abinda ya dame shi gaskiya.
Hannunsa ta riko tana dubansa kasa kasa sosai ta ce" Anas, wai har yanzu tsohuwar nan da ranta?"
Anas ya zaro ido, sai kuma ya saki yar dariya yana dafe haba ya ce" Kai kai kai, to da ta rasu ai da kin ji........, haba hajiyata saki fuskar mana ke da kika jima baki ga Madame ba?"
Fuskar ta sake tankewa ta sakar masa harara ta ce" ban san ya aka yi bata mutu ba har yanzu, .......hum....kana ji? Ka dawo zamu fita da dare"
Daga haka ta cika masa hannu ta nufi kofar da mai aiki ke tsaye tana jira ta karaso dan ta bude mata saboda ba'a barin kofar a bude sam, ita kuma idan tana nan ta tsani tsayuwar jiran a zo a bude mata, shi yasa tun dazu suke kai kawo dan gudun kar ta karaso basu bude matan a kan lokaci ba.
Tana shigewa Anas ya sauke ajiyar zuciya hadi da yin murmushi ya girgiza kansa sannan ya idasa sauka ya nufi motar nan da sauri yana tunanin tabas karshen watan nan idan aiki ya damke shi sai baba ta gani, saboda ogansa in ya sauko Shikenan bashi da time din kowa kuma, gefe daya kuma yana dariyar uwar dakin nasa da diramarta, wato FARHANA da mahaifiyar babanta, mutanen nan basa taba shan inuwa daya a duniya.......
Da yawa a gidan nan sunna yi mata kallon mutum marar daga kafa, marar hakuri, marar uzuri , mai fada, mai wulakanci....uwa uba mai bin maza kamar yadda kowa ya sani......
To ba wai zai ce a'a ba.
Kawai dai abinda ya sani wata irin mutun ce mai boyayan al'amari kamar yayanta......
Baka isa ka sanar da sirin da ya shafi zuciyarsu ba in ba niya suka yi ka sanshi ba.
Hum................tana yar tsamar nan ne da kakarta, mahaifiyar Marigayin mahaifinta.........
Sam basa shiri, basa shan inuwa daya, bale da muguwar akidar da aka san buzaye da ita na kin auren jinsin da ba nasu ba, wanda a yanzu haka wasun su ke rike da wannan akidar tamkar wata ta addini tsabar yadda suka bata mahimmanci.......ya kawo mata rigima ta kirki sakamakon saurayinta ita wanda ba buzun bane, ita kuma kakar Tata tace sai dai idan bayan ranta za'a yi wannan abin kunyar, shine ita kuma Farhana tace ba damuwa a yi hakuri bayan ran kakar Tata zata yi auren, dan ba gaggawa take yi ba, in dai ba za'a aura mata wanda take so ba lafiya lau ne zata jira.....
Wannan dalilin ne ya sa har yanzu bata yi aure ba, kuma bata da niyar yi, dalilin wannan hukunci na kakarta ta dauki muguwar akida ta hanyar bashi kafar kai kawo da zama abokan siri ita da shi wanda ya dace ace ya zama abokin sirin nan nata ne har sai igiyoyin aurenta sun hau kansa......sai ta fake da haka take tafka tsiyarta da zuwan su ne suke yi mata KISAN MUMMUKE ta hanyar hanata abinda take so, itama take mayar wa da kura aniyarta dan a duniya Mutun daya take tsoro, shi kuma Allah ya sa na dan kasa bane, idan ka ganta a gidan nan tabas ana jin kanshin zuwansa kasa kwana kusa.
Bata ji dari dari ba sai da ta shigo falon nasu ta samu mahaifiyarta zaune saman darduma mai laushin gaske hannayanta rike da Alkur'ani mai girma, fuskarta a sake sosai , sai dai ba dariyar ganinta take yi ba, a'a , fuskar ce koda ta so daurewa taushi da sanyin hali ke hannata zama turbuk din nan , koda cikin fushi take kuwa ba lalle ka ga fuska ta yi irin muguwar hadewar nan kamar an aiko wa da mutun da sakon da ya gigitashi ba.
Murmushi ta sakar mata a lokacin da ta karaso da sauri ta duka gabanta hadi da kama hannayenta a tausashe sosai ta furta" Anna......"
Murmushi Anna ta sake fadadawa da shi, a nutse ta saka hannayanta ta janyota jikinta tamkar wata Y'ar baby ta rungumeta a jikinta sosai a tausashe ta furta " Farhana, sannu da sauka....., yaya aikin? Yaya gajiya?"
"Mtssssssssssssssssssssssssssss!" Uban tsokin da ya fito daga dayan bangaren ya sa Anna sakin Farhana da sauri hadi da rike Alkur'aninta da kyau , da idannuwanta kuwa ta ringa yiwa Farhanan alamun ta daga mata kafafuwanta, Ama da yake yarinyar nan ba ji take yi ba sai kawai ta share ta yi kamar bata gani ba ta sake dora kanta a gefen kafar mahaifiyarta ta yi shiru , bata tashin ba, haka kuma bata gaisar da wace ta yi tsakin ba dan sarai ta san du duniya a yanzu itace kadai ke iya yi mata wannan takakiyar .
Kai Inna Hajiya ta girgiza tana duban Anmy ta ce" Tun farko daga gareki ta samu sangarta, a wajen ki ta ga raina ni, a dole a yanzu ta ci gaba da min kallon banza, sai ki umarceta ta tashi ta je ta yi wanka ko zata zubar da du abinda ta kwaso, kina saman salaya ne zaki yarda ta rabeki bayan kin san cewa ta dauki zina ba a bakin komai ba?, Allah ya kyauta!"
Daga haka ta juya ta karasa ta dana lft ya bude ta shiga ta dana matakalar karshe inda dakinsu yake , nata da na jikanta dan kuwa a shekarunta in ba dan hutu da ni'imar lafiya da wasun ke samu da shi ba da yanzun ko yar yatsa ba zata iya dagawa ba, sai dai cikin ikon Allah tana duduken nan take du masifar da zata yi, ta muryarta ba zaka taba gane shekarunta ba, sai dai idan ka ganta zaka yarda cewar shekaru fa sun ja.
Shiru ne ya wanzu a wajen bayan ta haura sama,
Farhana kanta a kasa tana tunani kala kala ciki harda yaya aka yi du aka kwashe mutanen kirkin famillynsu suka rasu aka bar wannan ? Ita kam du ranar da tsohuwar nan zata mutu sai ta fi kowa farin ciki
" Ki tashi ki je ki yi wanka ki yi sallar azahar lokaci ya shige tuni" mahaifiyarta ta fada a tausashe ba tare da ta ba yannayin fuskarta mahimmanci ba, gaba daya ma nunawa ta yi bata gane halin da ta shiga ba, hakan ya sa ta mike ta nufi lft din itama tana cire abayar dake jikinta ya rage dogon wando da yar riga a ciki ta bude ta shige sanan ta haura nasu bangaren, wanda a nan ma akoy dakin yayansu da na matarsa a falo na biyun dake saman, wanda ba cika aiki suka yi da shi ba, sai idan baya kasa in sun ga damar zuwa suke aiki da shi, shima ba kullum ba, dan bangaren su daban yake da na ANNA.
Murmushi Anna ta yi ta ci gaba da karatun da take yi a nutse ba tare da ta bari wannan yanayin ya hargitse mata farin cikin dawowar y'ar tata ba, ta sani ne kowani tsanani yana tare da sauki, kuma in Allah yayi duniya dan manzo wata rana sai ta ga Farhana a kan hanya madaidaiciya.
A gidan su Fa'iza
Kusan karfe biyu na rana Imtee ta gama yiwa fa'iza kunshin , dan ma bata da sauki ne da tuni ta gama shi, sai dai basu tafi ba saboda mahaifiyar su fa'izan tace su zauna tana zuwa, duda sun nuna aa tafiya zasu yi sai fa'izan ta nuna musu mamanta ba zata ji dadi ba idan ta zo ta tarar da sun yi tafiyarsu, a dole suka zauna din suka ci gaba da yar fira suna zaman dako har suka yi sallar azahar sannan suka sake jira kadan su gani, idan bata shigo ba sai su tafi kamar yadda Imtee tace.
Basu jima sosai da yin sallar sallar azahar din, sai ga yaya Anas ya dawo da tarin ledoji ya zube su a falon gaba dayansu sannan ya zauna hankali kwonce yana sake bin Imtee da kallon da ya sa ta ji gaba daya ta tsargu , domin du yadda ta so basarwa sai da ta gane ita din dai ne yake kallo da irin kallon nan da ya wuce misali
Dan tsaki ta ja kasa kasa wanda ya saka shi sake zarro ido yana kallonta kafin ya kalli Fa'iza da mamaki ya ce" Sister, da gaske alamu sun nuna zamana a nan na takura kyakyawar fulawar nan"
Imtee ta dan sake dubansa sai kuma ta mike tana gyara hijabinta da kyau, kasa kasa sosai ta dubi aisha tace" Ki sameni a gida"
Fa'iza da kunshinta ya bushe ne ta mike tana duban Imtee da mamakinta ta ce" Dan yayan nawa ya zauna da mu ne ranki zai bace? , Imtee yayana ne fa"
Imtee ta dubeta, a hankali zata yi magana, salamar mahaifiyarsu ta katse musu hanzari, shi kuwa ya sake gyara zama yana sakin murmushi zuciyarsa fari tassssss yana tunanin wannan ai ita ce ta dace da shi ba kowa ba, domin shi lamarin ta birge shi yake yi ma.
Amsa sannun da yan matan ke mata take yi kafin tace" A'a, yaya na ganku a tsaye, hala har tafiya ce? Fa'iza ina fata kin basu abinci?, dama nace su dakata ne dan yayanku ya zo in amshi kudin kunshin in bata, ƴaƴansu dan bani dubu guda ka ji?"
Da sauri A'isha ta dubi mahaifiyar su Fa'iza sannan ta dubi Imtee da ta ɗan yatsina baki alamun firar bata yi mata ba, sai dai bata nuna komai ba , ko dan ta ga baba ce mahaifiyar ta Fa'iza?
Dan murmushi ta yi ta ce" A'a mama, ai ba dan ta biya mu muka zo ba, kawarmu ce kyauta muka yi mata, zamu wuce mama mun gode"
Ai kuwa ta yi mamaki maman ta su Fa'iza, fa'izan kuwa sai alamu take yi mata cewar ta daina maganar kudin ama sai mamansu ta kai dubanta wajen Anas da ya ciro yan dubu dubu har goma yana miko mata ta karba tana zare daya da nufin tursasa su su amsa ne ta ji yace" Mama, dan Allah hade musu duka, su hau abin hawa, ba biyan su za'a yi kudin kunshi ba, ai.....a gaskiya......idan biyan za'a yi kudin sun fi haka ko Imtee?"
Imtee ta dube shi ido cikin ido a karo na biyu, bata ce komai ba sai kawai ta juya tana sake baza hijab dinta ta yi waje ba tare da ta amshi kudin da yake so lalle ta amsa ba
Kasa zama yayi ya mike da sauri ya bi bayanta, hakan ya sa suka bi shi da kallo su Dukansu
Da sauri ya sha gabanta yana kallon irin yadda ta ɗan tsorota na tare tan da yayi haka kikam
A hankali ya sassauta yannayin damuwar dake fuskarsa a tausashe ainun ya ce" Tun kafin ki san ni zaki fara tsanata?, me zai hana ki fara bani dama , idan kika san waye ni in bai maki ba sai ki tsane ni? Koda yake sani ne baki yi ba, idanma ke Bakya so na ba komai, Ni zan hade na mana so din na mu biyu kin ji kyakyawar flower......"
Tunda imtee take, bata san da ranar da zata zo irin wannan har zata tsaya haka kusa da kusa da namiji ta ji kalaman bakinsa har karshe ba, tana da farin jinin maza su nuna suna son ta sosai, sai dai bata da sakewar fuskar da zata ce musu koma meye bale har su samu damar haurawa wajen da take yawan tunanin cewar ba wata zuciya mai iya karbar so, dan akoy wani dan acaba da ya taba biyota ta ringa jifansa, ba shiri ya tafi yana tunanin ashe mahaukaciya ce?????
Ita fa, ta dauki cewa ba wani so a cikin zuciyarta, kai zuciyar bata da wani amfani sai wanda zata buga dan anfanar da gangar jiki, daga wannan ba wani, sai gashi lokaci daya ta ringa sauke dubanta a kan fuskarsa har ta samu kanta da jin kunya na son lulubeta............
A hankali ta ɗan sake ja baya, kasa kasa sosai ta ce" Ama ka ga irin tsayuwar nan ta gaf da gaf bata dace ba ko? Ni ai ba muharamarka bace ka ja baya kadan plz."
Ja bayan yayi yana murmushi sosai, sannan ya sake saka hannunsa ya ciro wasu kudaden masu yawan da bai irga ba ya miko mata yana duban yannayinta, dan ya riga ya san cewa a duniya mata na sakin fuskarsu gaban ya'yan banki koda kuwa basu so sakin ba.
Kudin ta kala kafin ta dube shi da yanayin tsoro a fuskarta ta ce" Wai na meye wannan?"
Kudin ya kalla shima , a hankali ya ce" So nake yi ki saka a jakarki, bata isa ta saka mu aiki irin wannan bata biya mu ba, idan ya so Ni sai na shiga ta biya Ni!"
Kai Imtee ta girgiza a hankali ta ce" Ba abinda zan yi da su, kuma gidan mu ba sai mun hau abin hawa ba, kusa ne.....thank you"
Daga haka ta zagaye shi ta nufi fitar , sai dai a hankali ta samu kanta da dan juyowa......
Ai kuwa yana tsaye ya soke hannunsa a aljihu sai murmushi yake zubawa
Samun kanta ta yi da sauke boyayan murmushi kafin ta daga kafarta da sauri ta fice jikinta har yana din kwasar rawa
Har ga Allah bai iya lura da A'isha ba har sai da mahaifiyarsa ta tsaya daf da shi ta ce" Me Kenan?, wasu kudin ka so bata????"
Tamkar an girgiza shi ya dubi mahaifiyarsa da sauri lokaci daya yana sauke ajiyar zuciya
A hankali ya nufi falonsu, ita kuwa tana biye da shi har ya je saman kujerar ya fadi yana kai hannunsa wajen zuciyarsa ya ce" Anya kuwa akoy wata halitta mai sakani bugun zuciya irin wannan yarinyar?...... A gaskiya duk rintsi sai na aureta, tabas wannan itace ta dace da Ni!"
Daga Fa'iza har mamansu mamaki ya gama kama su
Mahaifiyarsu ta Dube shi ta ce" ANAS, ka farka daga mafarkin da kake yi, dan Ni ba zan taba iya bari ka bar yarinya yar gidan manyan mutane mai son ka, mai bin ka, a kan wannan yarinyar ba, kai kuwa ka san ina ne gidan su?, itace fa y'ar gidan mutumen nan da ya ki siyar da gidan gadonsa wa mai gidan ka, mutun sai taurarar akida , basu da komai, basu tara komai ba, basu ba kowa ajiya ba, dama sun amshi kudin nan da na tabbata yau take sallah a gidan su, ka ga, ka rufawa kanka asiri ka zubar da maganar ta a nan inda ka dauka, Ni banma san jarabar da ta sa Fa'iza ke son yaran nan ba, gayanan zaki daga min hankali saboda yayume yayumen ki!"
Kwarai Anas yayi mamakin jin yarinyar nan bata fito daga gidan masu da shi ba, Ama kuma ya mika mata ya'yan banki mikaku sababi tasss haka ta ki karba............
Wauh.......................
Shine abinda yake maimaitawa a cen karkashin zuciyarsa ............., hakan ya sa sai da mahaifiyarsa ta gama zagayenta ya mike yana duban kanwarsa ya ce" To kuwa in sha Allah Allah ya kawo musu mai kudi direban OGA, in sha Allah zata huce takaici yarinya tunda na shigo rayuwarta, kai musulunci duniya ne da bai haramta auren talaka ba, da tabas sai na take doka na dauko IMTEE ........"
Sai kuma yayi wani shiru yana duban Fa'iza ya ce" Wai meye sunanta na gaske?"
Fa'iza ta sauke ajiyar zuciya, ita dai har ga Allah bata zumudin lamarin dan kuwa shi da kansa yayan nata mutun ne mai shegen leke leke, shi da kansa bai fa san adadin yanmatansa ba, duda yannayin da ya nuna a kan Imtee bata taɓa ganin ya nuna a kan wata Macen ba, sai dai shi fa mai hali baya daina halinsa, bale shi da ya gama yardarwa kansa cewar shi wani kwaro ne , ai dole ya hangi mace a matsayin hular da yake iya cirewa a duk lokacin da ya so ......sai dai anya kuwa Imtee zata amince da wannan lamarin??????
A sanyaye ta ce" Tana da sunnaye har kwaya uku, mahaifiyarta da ta haife ta tana kiranta da NUR, ko tace da ita KHAIRY, ita kuma mamanta, wato