An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
π
π
π
π
π
π
π
π
π
π
*KISAN MUMMUΖE*
π
π
π
π
π
π
π
π
π
π
_PAID BOOK_
*BY*
_SAJIDA NIJAR_
*Yan Naija Mutanen mu 1k ne a kan wannan account number 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank* sai a bani shedar biya ta layi na kamar haka +22793811618
*Yan Nijar mutanen mu zaku turo da hoton kati ta airtel ta dala dari , wato 500francs cefa a kan Numbarna kamar haka +22793811618*
*Na gode, sai kun zo.....taku ce SAJIDA NIJAR*
Tallah, tallah tallah....rabi ka siyar mana
*JAMA'A NAZOMUKU DAWANI TSARI NASAMUN KUDI TA HANYAR AMFANI DA WAYAN HANNUNKU
WANNAN TSARIN SHINE METAFORCE
MENENE KASUWANCIN METAFORCE* ????
*Metaforce kasuwancine ingantacce halattacce Wanda yake biya 100 π― Wanda ake Gudanar dashi da wayar hannu,METAFORCE is also a part of network marketing,is a 100 percent decentralized project da aka daurasa Akan Blockchain technology Wanda babu wani mahalukin daya Isa YAYI editing,hacking ko deleting wani abu acikin sa,Kuma yanada matakai yanada rassa Wanda kowane reshi ka rike a METAFORCE to ka samu GUDUMAR DUKAN TALAUCI*π
METAFORCE ANASAMUN KUDI ACIKINSHI SOSAI MATUKAR ZAKAYI ABUNDA AKEBUKATA
zaku iyahada miliyoyin kudi aranadaya acikin wannan kasuwanci me albarka in sha Allah
Duk wacce tashirya zata iya tuntubanmu akan wannan number
09136899615
Hajja Data
*1*
Kai kawo take ta yi a dakinta, idan ta yi tafiya ta kuma yi sai ta rike karfen gadonta irin gadon karfen nan ta yi shiru kanta a kasa, sai kuma ta sake daga kan nata, ta kuma bin bangon dakin da ido kamar wace ke son karantar wani abin a jikinsa......, sai ta sauke ajiyar zuciya, ta yi haka ya fi a irga.
Shigowarsa ya saka ta juyo da sauri ta sauke dubanta a kan fuskarsa kirjinta na dokawa
Yannayinsa a harzuke yake, fuskarsa ba fara'a ko kadan
Bai ce da ita ci kanki ba ya karasa ya dauki dardumarsa ya juya a fusace da nufin ficewa daga dakin nata.
Da sauri ta furta " Abansu"
Dakatawa yayi ya juyo a fusace ya ce " meye kuma?"
Kai ta fara sadawa kafin ta ce" Dan Allah ka zo mu yi magana"
Rai bace ya ce" Babu wata maganar da zan yi da ke, zan sake maimaita maki, ki daina takurawa y'ayana, ki basu lafiya su huta a gidan ubansu, na gaji da halinki, na gaji da halinki sosai, ki yarda ki kai ni bango, zan nuna maki babu wani abu da zai sa in yi shiru ina kallo ana cutawa yayana in ci gaba da zama da mutun ko waye shi, aikin banza aikin wofi!"
Daga nan ya wuce, kunnayenta na jiyo mata yadda ya ja kekensa ya fice a gidan, ga dukan alamu yau shi zai je kasuwa ba sulaimana ba
Zuciyarta ta gama cinkushewa
Gaba daya bata fahimtar komai a irin lokacin nan
Sai ma da Sulaiman ya shigo yana cika kirji ya bude wajen tufafin mahaifinsa ya dauki jalabiyar mahaifin nasa wace a kanta ne aka yi ba dadi yanzun ya fice yana fito ya zura tun a gabanta sai ta ji kirjinta yayi mata mugun nauyi......ya hayul kayum,
Silalewa ta yi kai a kasa ta saki kukan dake dane mata zuciya domin ji ta yi kamar kirjin nata zai fashe ne,
"Iya miko miko, samodara, iya kali idona....samodara...." Muryar wata matashiyar budurwa ta nufo dakin , lokaci daya wakar da take yi ta koma ihu a lokacin da ya saka hannu ya kwada mata mari da hargagi ya ce" Ke dan ubanki ina hijabinki?, fice a gabana yar kaniyar banza kina tafe kina wurga kafa kamar shanyayiya, ke kam kin ji kunya Ζatuwar banza Ζatuwar wofi......."
Ihu budurwar nan ta saka tana rike kunci, ta sake saka wani ihun tana neman zubewa, hakan ya sa mahaifiyarta mikewa da sauri ta dage labule zata yi magana, sai dai nan take ta ja bakinta ta yi shiru sakamakon abokiyar zamanta da ta fito daga nata dakin tana sakarwa Sulaiman harara ta kamo hannun budurwar nan ta ce" Ka ga sulaimana ka kiyayeni, babu abinda ta yi maka zaka ci zalinta? Ku Shikenan sai ku kawo karan tsana ku sakawa yarinya kamar wace ta muku mugun laifi? Idan ta shiga dakin mahaifiyarta kamar ba ita ta haifeta ba sai kyara sai hantara sai zagi, kai kuwa da ka ganta sai ka kama neman daga mata hankali da cin zali? Hijabin me Allah na tuba, ina y'ar yar nan ina a wani matsa mata da sai ta saka hijabi? Ta ki ta saka hijabin Ka barta abinta in ba haka ba wallahi in sasaba maka a gidan nan!"
Bai ce da ita komai ba ya kada ya fice domin alwala ya daura, hakan ya kular da ita, wato ya mayar da ita shashasha yau Bama zai kula ta din ba ko? sai ma da ta ga jalabiyar mahaifinsa ce a jikinsa sai ta ji ranta na kuna sosai, wato a gidan nan sulaimana ba zai daina saka jalabiyar Malan a gaban idannuwanta ba dan uwarsa ta daure masa ko?
Ta so ta yi fitina a kan hakan, Ama sai ta kade ta ture ta ja hannun yar budurwar nan suka nufi dakin ta tana fadin" Wuce mu je, ban san me zaki je ki yi a wajen makiyiyarki ba( wato mahaifiyarta), kulun fada maki nake yi matar nan da ba dan dole ba da ba zata kawo ki duniya bama, rabon ki rayu a duniya ne ya rantse ya sa kika zo ta tsatsonta, Ama ke sai ki sadadeni ki nufi dakin su dan su hadu su wulakanta ki? Je ki kwonta ki yi barci!"
Y'ar budurwar nan ta ringa sauke ajiyar zuciya na abin kukan da ta yi murya a raunane ta ce" To mama bari in yi sallah, jiya a islamiyya malan yace du Wanda baya sallah a kan lokaci sai ya hadu da azabar Allah bale idan ya balaga, an ce mace da ta fara haila wai ta girma, shine nace to ko dai na balagar nima? Tunda shekaruna sha tara yanzu ai ko?, yace kar mu yi tunanin sallar da muke yi Iyayenmu muke yiwa, alkawari ne da muka dauka wajen ubangijin mu, Allah ne muke bautawa, domin an halicce mu ne dama dan mu bauta masa, wai mutuwa bata kan yaro ko baba, ana yin bari ma wai, haka yace wai idan ka mutu bayan tambayar waye ubangijinka, menene adininka , sallar ka za'a fara dubawa cikin ayyukan ka, idan ta yi kyau to ana yi maka kyakkyawan zato wai, ni du ya dame ni"
Dagowa ta yi ta kalleta shekeke kafin ta dauke kai ta shiga kunna redio bayan ta tabe baki ta ce" ka ji wani sababi, bilahilazi tsaf nake iya cire ki a islamiyar in ga ta hanyar da uban wani zai maki fatan shiga wuta, kin ga malaman nan da neman fitina suke, ke wai dududu nawa kike ne? Shekara goma sha takwas a saka ki a gaba? Sha tarar ma baki cike ba fa, Aikin banza wuce ki kwonta nace ki huta kafin raina ya bace!"
Jiki ba karfi ta shige fale dayan dakinsu ta kwanta saman yar yololuwar katifar su sannan ta shiga neman barcin, duda ba wani jin barcin take yi ba, ama yin nasa ba zai bata wahala ba.....dan maman nasu ta saba sakata barci a ire Iren lokutan nan, takan ce ta kwanta ta huta dan itace yar autarta............. Ta fi riritata fiye da yada take ririta A'isha, dan kuwa A'isha tuni ta dau buta zata yi alwalarta abinta.
A bangaren mahaifiyar Sulaiman da wannan yar budurwa kuwa daki ta koma ta zauna ta sake yin shiru.....
A zuciyarta aiyanawa take yi maganganu kamar haka... ' Shin kowani namiji ne yake da wannan baudaden halin ko kuwa iya mijinta ne?, ......'
Sai kuma ta girgiza kai da sauri sakamakon tuna Marigayin mijinta da ta yi, wanda suka dauki shekara goma sha daya matsayin ma'aurata ba tare da wani abu na wulakanci da tauye haki ya taba shiga tsakaninsu ba.....
To a lokacin da take auren Muhammadu fa, idan ka ga hankalinsu ya tashi yan uwansa ne suka sake dauko maganar haihuwa, wace sam baya basu damar kaiwa ga daga mata hankali yake katse fitinar, duk wani abu idan ya shiga tsakaninsu na zamantakewar yau da gobe zama yake yi ya zaunar da ita su zanta har su samu matsaya guda......., rana tsaka mutuwa ta zo ta shiga tsakani ta yi mata yankar kauna, wanda hakan ya sa bayan shekaru biyu da rasuwarsa ta sake yin wani auren.
A gidan wannan miji nata, uban Ζ΄aΖ΄anta biyu da ta samu da shi, tana ganin rayuwar da take kyautata zaton idan aka ci gaba a haka ta shiga uku ta lalace, ko tace ta gama shiga ukun fa, sai dai gyaran Allah domin abinda take gani itace kadai ke gani, bayan ita babu wanda yake gani, ga shekaru sun riga sun tafi, a yanzu ko ta fita ina zata nufa? Da shekarun nan me zata iya yi????
Da farko dai mijinta, ya zamo irin mutanen nan da suke saka d'a a gaba da kowa, tunda Ζ΄aΖ΄ansu suka fara wayo ta gane cewar a zamantakewarta da mijinta a yanzu idan har zaman lafiya take so dole ta bi ya'yan nan na cikinta kafin a wanye kalau, wanda yau da gobe da irin yadda yake tsireta a gabansu ya sa a yanzu ita da Sulaimana sai su yi sa in sa, dan tsaf yake tsayawa ya yi mata gardamar abu ido cikin ido, yanzu ne ma da sauki sauki idan tace ba zai yi abu ba yake buya ya fadawa uban, kuma uban sai ya nuna ai laifinta ne, ta cika takura, kamar ba ita ta haifi yara ba, ta matsa musu, gayanan ita mai bin sulaiman din ta gujeta ta koma dakin abokiyar zamanta saboda zafin zama irin nata......
Sam babu wanda ke ganin abinda ita take gani, har ya zamo a yanzu da NUR wato imtee ta kai shekarun da a duniyar mu ta hausawa ta gama girma sai fatan shiga dakin miji kuma a cancana rayuwa har mai yiwuwa ta yiwu ....ama uwar rikonta, wace ta janyota jiki, ta nuna ta fi sonta fiye da mahaifiyar da ta kawota duniya, har ake yaba mata ana ganin lalle a yanzu da wahala a samu mata irinsu dake yiwa yarinya kishiya irin wannan a n, bayan ita ta san rikon aikata goshi ne tsantsa ke wakana a nan Ama bata da bakin magana!
Dole ta kirayi wannan riko da haka, domin wani irin riko ne take yiwa yarinyar ba kwaba, ba kyara, ba gyara saima saka wasu irin tunani a kai wa'inda ke Tsoratar da ita, dan kuwa a shekarun imtee fa sai ta biyo layi ba hijabi ta zo gida, wai karama ce yaushe ma aka haifeta. Ga Imtee da jiki irin na ginanun mata, babu inda bai kai tsole ido ba....... Iri irin haka ke saka mata wani shaku da tsoro, sai dai karfin yawun jama'ar da suka zagayeta ya saka mata dari dari da gudun yiwa abin tufka mai kyau ta hanyar fuskantar lamarin, harma da tsoron fito da shi ko yin fito da fito da shi Ιan kar a zageta cewar lalle butulu ce ita ta kasa godewa mace mai son ta.
A yanzu haka abinda ya hadata rigima da mai gidan nata, irin yadda saurayi mai shekara ashirin da daya a duniya kamar Sulaiman ya zamo du idan zai fita sai dai ya ringa zagaye zagaye dan ya samu abin sakawa na mahaifinsa ya saka ya fice abinsa, dan tsabar kiwya baya wanki, harta na kayan zuwa masallacin juma'a a rana irin ta yau mai albarka, duda ba wasu tarin kaya ne da shi ba wa'inda zai rinka tarawa a jaka yana cenzawa ba, Ama yana da daidai gwargwado domin kuwa mahaifinsu fa yana iya hanawa kansa ya musu, domin matarsa ta farko ma y'arta daya rayaya , wato A'isha , sai Sulaiman din nan da kuma imtee hakan ya sa du dan samun da yake yi na shagon saida kayan miyarsa da yan kayan masarufi suke tafiya a bukatun yaran nan,
Dan ma Allah ya taimake su, ba a gidan haya suke ba, gida ne da ya gada cikin gadon da aka raba na mahaifinsa aka bashi, wato gidan mai dauke da daki biyu ne kacal, sai dakin dake zaure wanda a ciki Sulaiman yake da kuma mahaifin nasa domin dakunan cikin gidan biyu ne, na auntun yara ciki daya ne, na maman yara ne mai ciki biyu....ga yan mata sun girma, sai kawai ya zamo zamansa ya fi yawa a dakin zaure...... ai da sai sun shiga tare tare na rayuwa sosai da sosai ko dan kudin haya.
A yanzun ma abinda ya bata haushi katon saurayi kamar Sulaiman ya zo wai wani zai dauki jalabiyar babansa , bayan jalabiyun nan kwaya uku ne da shi du duniya , dayar yakan zauna da ita ne a zaman gida, wace ya dauka din kuwa da ita yake wankan juma'a du juma'a ta Allah, sai wace yake zama a shago ita ta fi mutuwa ma....shine yaron nan ya daga hankalin ita zai saka, dan tace ba zai yiwu ba ba zai dauka na, shine ya yi mata rashin kunya ta hanyar fadin shi fa sai ya dauka, Shikenan daga cewa ya fita idannuwanta ta rufe ita fa ba sa'arsa bace, ya kiyaye harshensa idan yana yi mata magana, ya kiyayi fushinta , shine mahaifin nasa ya tareta da fadin wala haula wala kuwata Ila bilah, zata daga masa hankalin ko? Shikenan ba damar ya zo dakinta sai ta ringa daga masa hankali a kan ya'yansa? To ta ci kanta ta kiyaye shi Ιan a kan ya'yansa wallahi yana iya cira mata cikitin zawarci a yanzu da dukan wani alkhairinta ya kare furfurar tsufa ta gama bayana a gaban gashinta da bushewar hannaye ya sake ta ta je ina?sani ne malam bai yi ba, ko sarkin ta ya yi shi ne mai rikon ta, Kai innalilahi wa Inna ilaihi raj'une, ita kam tana cikin jarabawar dake sakata fashewa da kuka a duk lokacin da ta samu kanta a kaka naka yi ta lamarin cikin gidan nan!
Ta dauki lokaci sosai a dakinta, ga zafin rana irin ta ranar juma'a, gashi ita bata dakin ciki daya ne kuma bashi da wani girma, na maman yara ne kurya da falo
Cikin gaggawa ta fito ta hasa wuta ta Ιora silalan shinkafa sannan ta daura alwallah ta shige sallah dan an fito daga sallar tuni, ba zata so ya dawo gidan nan bata gama abinci ba, duda ta san da wahala ya kuma shigowa gidan sai dare .
Wuni ta yi tana ta aiki, dan kuwa du rashin yawansu gidan nasu wuni ake ana dauke cen ajiye cen, bale ita mace ce da sam bata son dati, hakan ya sa idan girkinta ya zagayo takan hade tun daga Ιangaren uwar gidan nata da nata bangaren da kuma dakin Sulaiman ta share ta gyara ko'ina, dan ta riga ta saba da aikace aikacenta tun da jan sawayenta a lokacin da aka yi mata auren farko ma shekararta goma sha daya ne, dan auren wuri ne aka yi mata, a hannun mijinta na farko ta girma ta yi wayo sai da suka shekara goma tare sannan Allah ya amshi abinsa, a yanzu shekarunta arba'in da uku, karamin jikinta ya sa sam bata wahala wajen motsawa.
Tana aikin tana ta ambaton Allah ne a cen kasan zuciyarta, saboda abinda ke ci mata tuwo a kwarya irin yadda kiri kiri aka rabata da Y'arta kwaya daya mace kuma aka koyawa y'ar rashin jin kai da tausayinta, domin idan aiki zai kasheta a gidan nan imtee ba zata fito ta kama mata ba, hakama Yar uwarta A'isha.
Sai da dare ya tsala sannan babansu ya shigo ya shige wanka, bayan ya gama ya shige cikin sange yayi kwonciyarsa dan har yanzu fushi yake yi da ita,
Tana hankalce da shi har sai da sawaye suka dauke sosai sannan ta tarda shi, ta yi anfani da damar da gareta a kansa har ya zamo garin Allah ya waye yana amsa gaisuwarta da sakewar fuska harma da sakawa aka dibo mata fulawa da kayan miya ta jajaga wainar fulawa aka karya da ita kafin ya fice wajen neman abincinsa, domin har yanzu bai gajiya da fita nema, dan hatta kasuwa yake zuwa a kekensa yayi sarin abinda ba zai fi karfin hawa keken ba , sai idan ya san siyayarsa da yawa ne yake zuwa a motar haya ko kuwa sulaimana ya je ya saro.
Tunda karfe takwas ta yi, auntyn yara ke duba kofar dakin abokiyar zamanta tana jimirin jiran ganin fitowar su imtee dan zuwa islamiyya, Ama shiru kake ji, tunda suka amshi yaji suka ci wainar fulawar nan ita bata kuma ganinsu bama, gashi har karfe tara na neman yi basu fito ba, makarantar da ake shiga karfe takwas da rabi a fito sha biyu, ya zamo dai yaran nan sun gama sabawa da Latin zuwa islamiyya, kai imtee fa hatta bokon ba wani cika zuwa ta yi bama, dan kuwa tsaf safiya ke yi yar uwar ta yi tafiyarta ita ace ta tashi da ciwon jiki ba zata iya tafiya ba, kuma Shikenan ta yi wuninta a daki bama ta fitowa bale har ta kara wani da dauke kara a cikin gidan'''''''''
Cen dai da ta ga karfe taran ta kusa sai ta nufi dakin da sakewar fuska ta yi Salama sannan ta shiga tana sake sakin fuskarta ta ce" Bari mu kara gaisawa maman yara, fatan an tashi lafiya.....? Ni yaran nan nace lokaci fa sai shigewa yake yi , ban ga sun fito sun shirya bama bale su wuce islamiyyar a kan lokaci"
Maman yara ta dubeta, kafin cikin yannayin basarwa ta ce" Au, islamiyya ko? Haka ne ashe yau asabat, to ai inaga sai dai ita A'isha ta tafi, imtee yau tace da kasala ta tashi ba zata iya hayaniyar islamiyya ba"
Da mamaki Mama karama ke kalon maman yara,
Du yadda ta so juyawa ta yi tafiyarta sai ta ji ta gaza
Da farko ta so ta tsaya su fahimci juna da maman yara yada zata tsawatarwa imtee dan ta fito ta je islamiyya, sai ta tuna cewar tabas ihu bayan bugu ne zata yi da batawa kanta lokaci, Sai kawai ta nufi kuryar dakin maman bayan ta saki murmushi ta dage dan yololon labulen dakin, ta ga A'isha na ta shirin tafiya islamiyya, ita kuwa tana kwance saman katifa ta lumshe ido kamar wace take barci hancin nan nata zuwat yana shaΖar nukusashiyar iskar dakin, dan komai a watse yake ba tattara bale shara .......
Bata tsaya bata lokaci ba ta karasa shiga ta daga hannunta ta Dada mata duka a cinyarta fili............π
π
π
π
π
π
π
π
π
π
*KISAN MUMMUΖE*
π
π
π
π
π
π
π
π
π
π
_PAID BOOK_
*BY*
_SAJIDA NIJAR_
*Yan Naija Mutanen mu 1k ne a kan wannan account number 0225962748 Amina Maikudi Abdullahi GT Bank* sai a bani shedar biya ta layi na kamar haka +22793811618
*Yan Nijar mutanen mu zaku turo da hoton kati ta airtel ta dala dari , wato 500francs cefa a kan Numbarna kamar haka +22793811618*
*Na gode, sai kun zo.....taku ce SAJIDA NIJAR*
Bismillah, ya Allah ka siyar mana, ka dafa mana
*JAMA'A NAZOMUKU DAWANI TSARI NASAMUN KUDI TA HANYAR AMFANI DA WAYAN HANNUNKU
WANNAN TSARIN SHINE METAFORCE
MENENE KASUWANCIN METAFORCE* ????
*Metaforce kasuwancine ingantacce halattacce Wanda yake biya 100 π― Wanda ake Gudanar dashi da wayar hannu,METAFORCE is also a part of network marketing,is a 100 percent decentralized project da aka daurasa Akan Blockchain technology Wanda babu wani mahalukin daya Isa YAYI editing,hacking ko deleting wani abu acikin sa,Kuma yanada matakai yanada rassa Wanda kowane reshi ka rike a METAFORCE to ka samu GUDUMAR DUKAN TALAUCI*π
METAFORCE ANASAMUN KUDI ACIKINSHI SOSAI MATUKAR ZAKAYI ABUNDA AKEBUKATA
zaku iyahada miliyoyin kudi aranadaya acikin wannan kasuwanci me albarka in sha Allah
Duk wacce tashirya zata iya tuntubanmu akan wannan number
09136899615
Hajja Data
*2*
Zurbat ta mike hadi da bude idannuwanta lokaci daya tana fitar da ihun jin zafin dukan tana sauke dubanta a kan wace ta dake tan domin dukan ya shige ta gaskiya......
Gaske, ta ji abu mai gigitar da zuciya, gaske ta ji ana neman tarwatsa kwonciyar hankalin ta, to idan ba mahaifiyarta ba anya akoy mai farmakin nutsuwarta a duniyar nan? Babu wanda ya kai mahaifiyarta tsanarta a kaf duniyar nan.
A gigice ta fashe da kuka tana sosa wajen hadi da mikewa tsaye tana neme neme dan gane laifin da ta yi.
Maman yara da ta yi mutuwar zaune ce ta mike har kamar zata kifa ta shigo da sauri tana fadin" Subahanalahi, ke ramatu, me nake gani haka? Me yarinyar nan ta maki tana kwoncinta tana barci ki ratso har nan ki daketa? Wai dan Allah me yasa kika tsani yarinyar nan kamar ba da cikinki kika haifeta ba? Kin uzura mata kin Hanna mata kwonciyar hankali, kin takurata Ko hanya ta haΙa ku sai