Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yi bismillah ko addu'a shiga banɗaki ba, an yi haka?" Ta girgiza kai ta ce "Sarki ba zan iya tunawa ba" "To an yi, shi ya faɗi abin da ki ka yi masa, kin bugawa jaririnsu takalmi, kin nakasa shi, shi suka ajiye a jikin gizo-gizo yana wasa, ki ka dake shi da takalmi, da kin yi addu'a da ya bar jikin gizo-gizon. Dan haka yanzu ɗan su suka ajiye a jikin yaron naki, jininsa da sauran sinadaran jikin yaron ki, da za su saka ya girma, su yake sha yana girma, dan haka ko an cire aljanin mutuwa zai yi ba shi da sauran mamora sun gama lalata jikin yaron da garkuwar jikinsa" matar ta fashe da kuka ta ce "Dan Allah sarki ka taimake ni" Ya girgiza kai ya ce "Magani kawai nake bayarwa, ba ni da ikon kashewa ko rayawa, zan baki magani ki koma gida, Allah ya baki wani" Nana ta ce "Ya a ka yi ka san aljanin ne a jikinsa, kuma idan ya fita ba zai rayu ba?" Buɗe ƙwaryar can, ki ɗaukko mini habbatussauda, akwai tazargade a ciki da tsakin kuka, da garin farin muski, duk ɗebo su da kan ki ki zo" babu musu Nana ta harhaɗo kayan da ya ce ta kawo masa. Ya zira hannu a jakarsa ya ɗaukko garwashi, ya ɗora a kan wata tasa, ya ɗebi haɗin nan ya zuba a kai. Ko sakan goma ba a yi ba, yaron ya mimmiƙe ya din ga tsala uban ihu. Sarkin baka ya cewa matar "Yaushe rabonsa da kuka, ko ya motsa wata gaɓa ta jikin sa?" Ta girgiza kai ta ce "Ba zan iya tunawa ba, kullum a kwance kawai yake" "To tun da ya yi kuka yanzu har da mimmiƙe wa, kin san ba ƙalau ba, baiwar Allah ki je gida, Allah ya baki wani" Nana a ranta ta ce "Yaro ya ji wannan uban hayaƙin ba dole ya tsala ihun azaba ba". Ya ce "Kamar har yanzu ba ki yarda da abin da ki ka gani ba ko?" Ta girgiza kai ta ce "A'a na yarda" " 'yar wace ɗariƙa ce ke ne?" Ta girgiza kai ta ce "Ɗariƙa ba ta cikin sharaɗin addini, dan haka ni ba ni da wata ɗariƙa" Ya jinjina kai ya ce "Gaskiya ne, kin san kowace ɗariƙa akwai malamin da ta ke yarda da shi, da ki na da ɗariƙa da na ce ki saurari bayanin da wani babban malami ya yi a kan aljanu, amma manta kawai kin tashi lafiya?" "Lafiya kalau Alhamdilillah" ta buɗe baki za ta sake magana ta ga bakin sarkin baka duk jini da sauran gashin zakaran da ya cinye jiya, wanda lokacin da ta shigo ba bu shi a bakinsa. Zabura ta yi ta ja da ba, dan a zaton ta a mafarki ta ga ya ci zakaran ba a gaske ba, kuma da har ma ta manta ma. Sarkin baka ya sanya hannu, ya zaro sauran gashin daga bakinsa, ya kalla ya yi murmushi ya ce "Kar ki tsorata Nana, tun a zuwan ki gidan nan da na so cutar da ke, sai na cutar da ke ta in da uban duƙusa ba zai iya ba ki kariya ba. Har ga Allah bani da niyyar cutar da ke, kuma da gaske na san ba zan iya raba ki da shi ba, amma na rage masa tasiri ta wasu fuskokin daban-daban a tattare da ke. Tabbas na cinye zakara da ransa, kuma uban duƙusa ne ya zungure ni, sai da na yi a gaban ki, dan ki cire yarda da ni kar ki yarda ki sadaukar mini da shi. Da na mallake shi zan ƙara ƙarfi da ƙarin tasirantuwar magunguna na, kuma zan kerewa sa'a tsakanin mutanenmu. Ainihina ɗan wanzamai ne, na gaji wanzanci daga nan aka kai ni bara, na samu karatun Alqur'ani daidai gwargwado sai dai babu sauran litattafai na addini. Azabar yunwa ce ta sanya na fara bin matasa daji farauta, daga baya na watsar da allo na bar gurin malamin da aka kai ni gaba ɗaya, duk mahaifiyata 'yar maharba ce, amma na fi ƙarfi ga ɓangaren wanzanci. Na yi rashin ji, na yi faɗi tashi, na yi wa harkar baka haye, har na so na fi 'yan gado ƙwarewa, hakan ya saka sauran maharba sako ni a gaba, da tsaface-tsaface da ƙoƙarin son kawar da ni. Sun sha haɗa kai domin su kashe ni. Suka yi mini shiri, na zo ba na iya kama komai idan na fita harbi, ga rashin lafiya, dole na bazama neman magani a nan na haɗu da uban gidana, a masu magani ya bani maita, wadda ita ma wasu baƙaƙen aljanu ne suke tasrifinta, ya ƙara koya mini harkar magani, ga wanda na gada na wanzanci a gida. Ya yi mini girkar aljanu na zo na gawurta, na nemi na fi shi ma ko ma na ce miki na fishi ta kaowace fuska, kawai sai ya fara neman ya kashe ni, saboda hassada. Wataran mun fita farauta tare ya rikiɗe ya koma ƙaton maciji ya yi ƙoƙarin haɗiye ni, ni kuma garin ƙwatar kaina na kashe shi har lahira. A haƙiƙanin gaskiya, ba na yadda na bawa mutum duk wani abu da zai cuci mutane a kan zalunci. Ina da tarin aljanu kala-kala da nake aiki da su. Na nemi ki sadaukar mini da uban duƙusa ne domin na ƙara ƙarfin tasirina. Rabona da maita har na manta, tana nan a jikina amma bana amfani da ita, na daina ta'amalli da aljanun maita, shi ne jiya ya zunguri maitar ta motsa mini. Yanzu haka sai na je na yi jinya, kuma zan ja dogon lokaci ban yi aiki ba, sai dai yarana su yi. Hatta Salamatu da ki ke gani ba mutum ba ce ba. Ainihin matar ba ta da lafiya sihiri aka yi mata, ba ta iya komai aka kawota nan. Na saka Salamatu a jikinta take yi mini aiki, Salamatu na fita gangar jikin za ta faɗi ta ci gaba da jinya. Shirin a jikin gawa aka yi mata, aka binne gawar ni kuma ba zan iya sakawa a ciro gawa daga makwanci domin karya sihirin ba, hakan tamkar tozarta gawar ne." Jikin Nana duk ya yi sanyi da jin labarin da sarkin baka ya bata. "Yarinyata da tana raye da ta kai kamar ke, na tafi farauta abokan adawa ta, su ka kasheta da babarta, tun daga nan ban kuma aure ba,, shiyasa na yi iya ƙoƙarin da zan yi na gagare su. Zan saka a mayar da ke gida, ba sai kin yi makonni biyun ba, domin kuwa jiya an turo mini 'yan aike, ana so a haɗa kai da ni, in bayar da jininki, kuma ina da yadda zan yi na bayar, za ayi mini musaya da wani abu mai tsoka, wanda da na so, zan karɓa na bayar da jinin naki na yi maganin uban duƙusa, amma ina jin tausayin ki, ban san gaibu ba, amma akwai yiwuwar kina daf da buɗe sabon babi na ƙaddara, dan zuwanki gidan nan tuni kin yi wa ƙaddarar mukulli" Cikin mamaki Nana ta ce "wace irin ƙaddara ce kuma haka?" "A'a ba ni da damar cewa komai, amma ki tambayi ƙaisar mene ne tarihin kakaninki, za ki ga ta in da zuwanki gidan nan ya buɗe sabon babin ƙaddararki. Babu lallai ki fahimci labarin a take sai a gaba kaɗan za ki fahimta sosai da sosai. Abu ɗaya zan iya gaya miki, nima ina da alaƙa da labarin kakaninki ta wata fuskar" "To kai ka gaya mini labarin mana" Ya sauke numfashi ya ce "Ƙarfin hali kawai nake yi, maitar da take cikina ce take ta wahalar da ni, rabona da cin wani abu da sunan maita na fi shekara goma sha, saboda na sha maganin danne ta, kwatsam jiya na ci na san sai na yi jinya" Nana har da gyara zama ta ce "To ita maitar mece ce? A addini babu maita sai dai kambun baka, to ita a ina ake samun maitar kuma ya ake yin ta" Sai da ya yi dariya, Nana akwai tambaya ba kasafai take barin kanta ya kulle ba. "Tabbas babu maita a addini, sai kambun baka. Maita tsafi ce sihiri ce, wani siddabaru ne da aljanu, da yake ƙara tasirin kambun baka. Ya danganta da wadda ka ke da ita. Akwai wadda ka ke iya ganin kurwoyin mutane, a siffofi na dabbobi, akwai wadda muke amfani da ita mu lalata abu. Idan muka kalli abu, ko ba mu tanka ba zai lalace. Mu kan zuba yawunmu idan ta taso mana a cikin abinci mu bawa mutum, sai ya yi ta rashin lafiya. Ina da jar maita ne, mai bala'in fiye da kowacce tare da wani aljani nake sarrafata, shi ne idan ya buƙaci jini yake zuwa kaina, sai na sha sai ya samu nutsuwa ya sake ni. Ina iya sarrafa maitar yadda nake so, ko shi ne Uban duƙusa ya zunguri maitar a cikina" Nana ta jinjina kai ta ce "To amma ya aka yi ya iya zuwa gurin da ka ke, bayan ka na da magungunan su?" "Ban gaya miki a cikin aljanu irin ƙaisar ba su da yawa ba? Yanzu ki je zan kwanta in huta ne" Ta jinjina kai, ta tashi ta nufi ƙofa, har ta kusa fita ya ce "Ki na ji?" Ta waiwayo ta ga har ya kwanta. "Ki ci gaba da addu'a da karatun Alƙur'ani, duk da idan kin yi kin fi shan wahala, kar ki daina. Kuma kar ki yadda wani abu ya baki tsoro, wasu lokutan da tsoron ka ake amfani a cutar da kai, ki cigaba da addu'a duk tsanani akwai sauƙi a biye. Wataƙila tsanani da ƙaddarar gobe ta fi wadda ki ke ciki yau" ta yi shiru tana jinjina maganganun sa. Ta ɗago ta ce "To na gode sosai da sosai. Ka ajiye mini naman maciji an jima zan zo in gwada ci" ya yi dariya ya ce "Kamar gaske. Zo mu ga tafin hannunki" Ta koma gurin da ta bar shi, ta durƙusa ta nuna masa tafin hannunta hagu da dama. Ya yi shiru yana kallo sannan ya ce " Ki kula sosai zanen X ɗin da yake kusa da layin zuciyarki na nuni da tsagwaron gwagwarmayar rayuwa. sannan layukan ƙasan babban ɗan yatsanki suna nuni da za ki yi wasu tafiye-tafiye, wasu daga ciki na jin daɗi wasu na wahala. Sai kuma alamar ido, da ke babbar ɗan yatsarki da alamar sarƙar da ke jikin babban yatsan akwai wani abu amma ba zan gaya miki ba, shi ma wani karatun ne daban, yana da alaƙa da aure da kuma matsalar iyali" Ta kalli Sarkin baka ta ce "Abin mamakin ka ba ya ƙarewa sarki, bayan layuka ban ga komai a hannun nawa ba, ko kana ganin wani abu da bana gani a hannun, kuma dai sanin gaibu sai Allah ai" Ya kwashe da dariya ya ce "Wani karatun ne daban, duk da na san ji na kawai ki ke yi ba yarda ki ke yi ba. Je ki an jima ki zo ki ci naman. Na so na je da ke taron wasan maharba da muke yi duk shekara, ni ke ɗauke da kambun har yanzu, sai dai ba na iya tunanin bana za ayi wasan da ni, ƙaisar ya yi mini illa. Maza je ki sai an jima" ta tashi tsam ta nufi hanyar fita tana kallon hannunta. Wannan tsohon mai kama da Ƙaisar ta gani, cikin wannan fararen kayan nasa, tamkar yanar gizo gizo saboda tsufa. Sai kuma ya ɓacewa ganinta, a hankali ta ƙarasa ƙofar ɗakin ta ga baya nan, sannan ta fita, tana tafe a hankali tana duba tafin hannunta tana kallon zanukan da sarkin baka ya faɗa, da tunanin shi kuma wani kalar siddabarun ne. Ji ta yi zafin rana ya ƙaru kamar lokaci ɗaya temperature ta canza. Ta ɗaga kai kawai ta ganta a bakin layinsu. Ta waiwaya da sauri ta ga ba ta cikin gidan sarkin baka. Ta sake dubawa ta ga dai bakin layinsu ne dai. Hatta kayan jikinta ba su bane ba, dogon hijjabi ne da aka ba ta take sakawa lokacin salla, sai kuma wata jaka da take rataye da ita ta fata. Ta din ga ƙifta idanunta domin ta ji ko bacci take yi amma ta ga ido biyu ne, kawai ta nufi gida. Ko da ta shiga gidan da sallama, babu kowa a tsakar gidan. Ta sake yin sallama Nasiru ya shigo gidan da gudu ya dawo daga aike, ya ce "Laa mama Nana ta dawo" Hakan ya yi daidai da fitowar Mama daga ɗaki, hannunta riƙe da tsintsiya da abin kwashe shara. Sakin tsintsiyar ta yi tana kallon Nana kamar baƙuwar halitta. Nana ta ƙaƙalo murmushi ta ce "Mama sannu da gida?" "Uban me yasa ki ka dawo gidan nan yanzu?" Cikin mamaki Nana t tsaya tana kallonta. "Ke idan ki na da kunya ma kya dawo gidan nan, duk da ta'asar da ki ka yi?" Cikin mamaki Nana ta ce "Wace ta'asar?" "Ban sani ba" ta yi magana tana ɗaukar wayarta a kan taga" Nana ta nufi ɗakinsu, amma Mama ta dako tsalle ta tare ta, ta ce "Ai kuma zamanki ya ƙare a gidan nan, abin da na yi na riƙon ki Allah ya ba ni lada. Ba za ki ci gaba da zama ki kashe mini 'ya 'ya ba" "Mama kisa kuma? Wa na kashe?" Ba ta kula Nana ba, ta fara magana a waya "Ko ma ina ka tafi, ka dawo ka zo ga Nana ta dawo, ka zo ka fitar mini da ita daga gida, dan wallahi ba zan zauna da ita ba" ta kashe wayar. Nana ta tsaya tana kallon ikon Allah, Fafur Mama ta hana ta shiga ɗakinsu, ba a fi mintuna goma sha biyar ba, sai ga Baba ya dawo gida. Cikin mamaki yake kallon Nana ya ce "Ina Gaddafin yake?" "Gaddafi kuma Baba?" Nana ta tambayi Baba cikin mamaki. "Eh mana, ba wancan jarababben ɗan nema ya kai ƙarar mu ba, wai mun kai ki inda ba a sani ba, aka haɗa Gaddafi da jami'an tsaro a je a taho da ke" Nana ta girgiza kai ta ce "Ni da kaina na dawo, ban ga Gaddafi ba" Suwaiba ce ta fito daga ɗakin Mama, sai da Nana ta tsorata, ta yi wani irin haske, duk da tana shafe-shafe, amma hasken da ta yi, da gani na rashin lafiya ne. "Ka fa san yadda za ka yi da ita, dan wallahil azim ba zan ci gaba da zama da masifa da annoba ba, shi kansa wanda aka ce an kashe ɗin nan, ina kyautata zaton ma ita ce ba wani ba, to wallahi jinin 'ya'yana ba zai shawu a sha banza ba" Baba ya ce "Wai Rabi me yasa ki ke haka? Idan ta bar gidan nan ta je ina?" "Ta koma gurin uwatta, ta je ta sha nata jinin" "Ba zai yiwu ba, har duniya ta naɗe, ba zan bawa maijidda ɗa na ba." Nana ta yi ajiyar zuciya cike da tsantsar damuwa da baƙin ciki. Ya sake kallon ta ya ce "Wai ba makonni biyu aka ce za ki yi ba, me ya dawo da ke gidan nan yau?" "Shi ne ya sallamo ni" ta amsa a hankali. Baba ya ci gaba da faɗa "Wallahi Ina takaicin haihuwar Imarana, ya haɗa Gaddafi da jami'an tsaro, shi kuma an zo nemansa a kama shi ya gudu, yanzu ma kalli 'yan sandan ne suke kirana ga kuma wannan masifar" "Baba a kama shi kuma? Me ya yi?" "Eh ai ke ce mai jin tausayinsa dama, sun haɗa kai da 'yan iskan abokansa, sun kashe wannan malamin naku, ana ta nemansa ruwa a jallo" Nasiru ya yi farat ya ce "Baba ba fa Yaya imarana ne ya yi kisan ba, abokansa ake nema, shi ne ake nemansa dan ya nuna inda suke" "Duk ba abu ɗaya ba ne dai?" Baba ya faɗa cikin takaici. Jikin Nana na rawa ƙirjinta na dukan uku-uku ta ce "Wai wani malamin namu?" Nasiru ya yi farat ya ce "Malam Auwal aka kashe da daddare, ya fita sayayya ana gobe za a kai ki gidan mai magani" Kanta ne ya yi wata irin sarawa, ta yi saurin dafe kanta tana tunanin kamar ta san zancen amma ta manta a ina. Iya ƙarfinta take kokowa tsakanin ƙwaƙwalwarta da zuciyarta a kan sai ta farka daga nannauyan baccin da take yi. 1k ne a kan telegram, ta wannan account ɗin 0069685771 Aisha Adam Stanbic ibtc bank. Ayshercool 08081012143. https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 *AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA 08162859027* *INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK WANI DATTIN MARA SANYI MAI HANA HAIHUWA SA WARIN GABA RASHIN NI IMA JIN ZAFI YAYIN MU AMALAR AURATAYYA FITAR FARIN RUWA MAI WARI KAIKAYIN GABA TUSAR GABA KURAJEN GABA TUSAR GABA BUDEWAR GABA CIWON JIKI RASHIN GAMSUWA* *Maganin sanyi 5k* *Maganin sanyi* *5k* *Maganin ciwon Qoda 10k* *Maganin HepatitisB ASHA NA TSAWON WATA DAYA MUNBADA ANWARKE DA YARDAR ALLAH 40k* *MAGANIN MATA KALOLI DABAN DABAN INGANTATTU MASU LAFIYA DA KARA KUZARI AKWAI NA MATA AKWAI NA MAZA UWARGIDA DA AMARE KU GARZAYO WURIN AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA* *INGANTACCEN MAGANIN GYARAN NONO MAI TADA KOMADAR NONO DA DUK WATA TAMOWA TA NONO ZAI CIKO DA TUWON NONO YA TADA KOMATSEWARSU BANCE ZASU TASHI BA ZADAI SU CIKO SUYI KYAU* *Maganin gyaran Nono 8k* *MAGANIN RAGE TUMBI KODA YAKAI GIRMAN CIKIN YAN BIYU INSHA ALLAH KI GWADA MAGANIN AUNTY ZEE DA YARDAR ALLAH ZAKI GODE* *Maganin Rage Tumbi 7k* *MAGANIN BASUR KODA YAKAI GA YIN TSIRO INSHA ALLAH AGWADA ZA ADACE* *Maganin Basur 5k* *MAGANIN CIWON SUGAR CIKIN IKON ALLAH MUNBADA ANRABU DASHI* *Maganin ciwon Sugar 10k* *08162859027* *09070027627* *Location*KATSINA STATE* *ACCOUNT NUMBER* *8162859027* *ZAINAB SHU AIBU* *OPAY* *OR* *3968303018* *FCMB* *ZAINAB SHU AIBU* *DAN ALLAH IN KINSAN BAKI SHIRYA BA KARKI YI MAGANA DAN ALLAH KIBARI KI SHIRYA AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA TAKUCE SAI KUNZO* BUZU AISHA ADAM (AYSHERCOOL) YOTA 002 BRIGHT PENS 3rd BATCH P15 Suwaiba ta shiga banɗaki ta koma ɗaki, babu wanda ta kula a tsakar gidan. Mama kuwa bala'i ta ci gaba da yi. "Wallahi baban Jamila ba zan zauna da Nana ba, idan ta gama da yaran nan kaina za ta dawo, shi kansa wannan yaron an fara maganar saboda yaƙi aurenta ya rasa ransa". Baba ya ce "A'a Rabi, wannan dai zance ki ne, idan da wanda zai mutu dan bai aureta ba ai Suleiman ne, kuma duk abin da ake yi mata a gidan nan babu wanda ya mutu, dan Allah ki daina wannan maganar" Kamar ta mari Baba ta ce "Abin da ya samu Suwaiban bai ishe ka hujja ba, sai ka buɗe ido ka ga gawar ta tukuna? Ni fa wallahi sai dai ka zaɓa, ko ta bar gidan nan ko ni na bar gidan" "A'a ba za ayi haka ba, yanzu idan ki ka ce ta bar gidan nan ina za ta tafi? Haba Rabi Nanan nan fa 'ya ta ce ita ma. Kuma idan kin kwantar da hankalinki, kin san na karɓi kuɗin auren ta, nan da sati biyu za a ɗaura mata aure, ta bi mijinta Ikko, duk mene ne abin tayar da jijiyar wuya?" Nana tun da ta dafe kanta, ta sunkuya ba ta ko motsa ba, sai yanzu da ta ɗago ta fara magana iya ƙarfinta "Innalillahi wa innalillahi raji'un, dan Allah ku tashe ni daga baccin nan, ya za ayi malam Auwal ya mutu? Dan Allah ku tashe ni kafin ƙwaƙwalwata ta samu matsala, dan Allah ku tashe ni daga baccin nan" ta ɗago da idanunta suka yi wani irin ja kamar za su kama da wuta, hawaye ne tare da mijina suke rige-rigen zuba a fuskarta. Baba ya ce "Nana meye haka? Zuwa islamiyyar na banza dama ki ke yi? Ko ni na mutu ai ba kya yi haka ba" jefar da jakar hannunta ta yi, tai waje. Baba ya bita da sauri, amma tamkar walƙiya bai ga ko sahunta ba. Kai tsaye Nana rukunin ofisoshin malamai ta nufa a islamiyyar su. Malam Nura ta tunkara, babban abokin malam Auwal. Cikin yanayi na ɗimuwa ta ce "Wai an kashe malam Auwal? Dan Allah kai ma ka iya ruƙiyya ai ka na yi mini, dan Allah ka karanta mini koma mene ne ko zai sake ni na tashi daga wannan baccin." Ya ƙarewa Nana kallo, da gaske a ɗimauce take, cikin sigar rarrashi ya ce "Zauna mu yi magana" "Ba zan zauna ba, kawai ka yi mini ruƙiyya na tashi. A nan fa na same shi a ofishin sa, muka yi magana, ya gaya mini gaskiya ba zai iya aurena ba, kuma duk na fahimce shi, ya ce mini zai tafi Qatar, to kuma daga na yi tafiya sai ace mini ya mutu?" "Al mautu haƙƙun Nana Asma'u, mun yi rashin Auwal. Ɓata gari ne suka soka masa makami su ka ƙwace masa waya kafin a kai shi Asibiti rai ya yi halinsa, ki yi masa addu'a" Jikinta na karkarwa ta ce "Ya sayyadi Nura. Na yi rashi ba zan manta Yaya Auwal ba, yanzu waye zai din ga bani addu'oin? Waye zai yadda da abubuwan da nake ji a jikina na ciwo, ba tare da ya ƙaryata ni ba?" Tuni malamai suka cika ofishin, kowa da abin da yake faɗa, wasu na kuka domin mutuwar ta dawo musu sabuwa. Da yawa ba su san ya so ya auri Nana ba sai yanzu. An daɗe ana rarrashin Nana, da yi mata nasiha, ba a taɓa yi wa Nana mutuwa mai shiga jiki ba sai a wannan lokaci, Alkhairinsa kawai take tunawa. Halin da take ciki, bai hana kunnuwanta jiyo maganganun wasu malaman, su na cewa yayanta ake nema ruwa a jallo shi ya kashe Auwwal. Sauti komai ƙanƙantarsa Nana na iya jiyo shi, wasu lokutan da haka take gane ƙaisar na daf da ita. Malam Nura ya saka ta a gaba, ya tafi raka ta gida, suna tafe yana yi mata nasiha. A ƙofar gida malam Nura ya yi mata sallama, ta shiga cikin gida tana taku da ƙyar. Ko sallama ba ta iya yi ba, ta nufi ƙofar ɗakinsu, ta ga an saka tsumma an ɗaure ƙofar ɗakin. Ta ɗauki jakar da ta dawo da ita daga gidan sarkin baka, duk da har a wannan lokaci ba ta san mene ne a ciki ba. Ta fara ƙoƙarin kwance ƙofar ɗakin, jin motsi ya sanya Mama sake fitowa, tana ƙoƙarin nufo Nana tana bala'i. Nana ta ɗago a hankali ta kalli Mama, sai kuwa ta ja ta tsaya, dan ba ta taɓa ganin Nana ta yi mata irin wannan kallon ba. Gani ta yi tamkar walƙiya idanun Nana suka yi. Ta buɗe ɗakin ta shiga ta kwanta. Aka jima Baba ya dawo, dan yawon neman in da Nana ta yi ya yi. Yana dawowa suka ci gaba da faɗa da Mama a kan lallai sai ya fitar da Nana daga gidan. Nana tana ji Baba ya kira Yaya Atine yana roƙonta. Baba ba ya iya waya sai ya saka ta a hansfree, kuma sai ya ta ɗaga murya tamkar yana magana da aradu. "Atine dan Allah idan da hali Nana ta zo gidanki, ta zauna kafin a ɗaura mata aure. Rabi taƙi yadda ta zauna da ita, kin san halin da Suwaiba take ciki" "Wace Nana kuma? Ba tana gidan mai magani ba?" "Ta dawo ɗazu, wai mai maganin ne ya sallamo ta, kuma ga 'yan sanda sun tafi da Gaddafi a taho da ita, shi kuma Imarana ya gudu neman sa ake yi ana zargin sun kashe wannan yaron da ake ta magana a kansa a radio, wanda ya ƙi auren Nanan" Nana na jiyo Yaya Atine, kasancewar wayar Baba a ragargaje take kuma China ce ta na cewa "Taɓ lallai Isa Allah ya jarabce ka, wannan masifar duk a gidan ka? To mai magani ma ya kasa ya sallamo ta balle kuma ni, ya zan yi da ita ina ma na ga gurin ajiyeta? Ka yi haƙuri ta zauna a gurinka kafin lokacin bikin nata" Ya marairaice ya ce "Me nake da shi, ba wani biki aure kawai za a ɗaura su tafi, ai kin san ba shi ne da ni ba" Yaya Atine ta ce "To ai shikenan, amma ka riƙe 'yar ka, ba zan je nima na gogi bala'i ba, dan ni na fara tsorata da al'amuranta" "Amma yay... Ba ta bari ya gama maganar ba, ta kaste kiran. "Ka gani ko? Ita ba za ta karɓi bala'i ba, ni kuma a bar ni da bala'i ya ci gaba da kashe mu ba zai yiwu ba" Sallamar da ake kwaɗawa a waje, ya sanya Baba fita, ya tarar da 'yan sada tare da Gaddafi. Ɗaya daga 'yan sandan ya ce, "Yauwwa barka malam, zamu tafi da kai station ne" Baba ya ce "Saboda me?" "Mun je in da aka ce an kai yarinyar ɗanka ya yi ta raina mana hankali muna yawo,

Chapter 12 of 13