Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kuɗi, duk wannan abin shige mini take son yi, ta ji sirrina". "To hajjaju a shigo da ita sabgar mana" Cikin sauri ta ce "A'a tana da surutu, ga ƙaryar riƙon addini, kin san kuma ƙa'idarmu, muddin aka samu mushikila akwai matsala. Ai zatonta business ɗin nan na riƙe, har take neman yin takar da ni a wasu abubuwan. Ba ta san kare yawa ne kawai ba, da kawar da hankalin mutane". "Gaskiya ne, sabgar tana buƙatar sirri sosai" "Safiyya kin ga an sake samun matsala, yarinyar ba ta yi amfani da turaren nan ba, wanda ya yi amfani da shi daban, ya ce wani aljani ne a kan yarinyar hatsabibin gaske ba zai bari komai ya yi tasiri ba. Kuma wallahi ya tabbatar mini idan aka yi amfani da jininta, za a samu alkhairi sosai taurarinta masu haske ne. Kuma idan aka yi wannan aikin ba za a ƙara bamu wani aikin mai wahala ba. Mun riga mun wuce gurin mun samu sa'a, sai da na ce anya ba sato ta zan saka ayi ba?" "Na shige su ni Safiyya, kuma Jamila ta tabattar mini da ta ba ta turaren har ta na murna" "Wallahi ba ita ta yi amfani da shi ba, an yi amfani da turaren amma ba ita ba ce ba" "Kai wannan wace irin jaraba ce? Ga shi kuma wai ba ta nan an kaita gidan mai magani an barota a can" da sauri Hajiya Sa'a ta ce "Haba dai? A ina ne na ji ko da yadda za mu yi mu samu gurin?" Maman khairat ta ce "Wallahi ban sani ba, sai dai idan ta zo na tambayeta" "To ki yi mata cikin hikima dan Allah, ki nuna mata wata 'yar uwakki za a kai, kar mu bar wani trace da za a gane wani abu" "To shikenan hajjaju bari ta zo, it ma ina daf da jawota cikin ƙungiya, za ta yi mana amfani saboda tana da mugun kwaɗayi daga ita har iyayenta" "Aikuwa nima na gani, yanzu dai a far wannan ɗin" **** Ɓangaren Nana, ta ga abubuwan al'ajabi kala-kala a gidan sarkin baka. A kwana uku da ta yi, tana iya fita da kanta ta zagaya tana ganin marasa lafiya har ma ta yi magana da su, ta basu shawarar su din ga zuwa asibiti. Tana yawan zuwa ganin Kubra, sai dai yanayin da take tarar da ita a ciki, ba ya yi mata daɗi, saboda wataran da sauƙi wataran kuma hauka take yi tuburan. Kullum idan Sarkin baka zai zagayen ganin marasa lafiya, da waɗanda ake kawo masa su ganshi, tare yake yi da ita. Aka kawo wata mata da tsohon ciki tana tafiya da ƙyar, cikinta har rinjayarta yake yi, wai shekarar cikin goma a jikinta, wasu lokutan ya tashi, wasu lokutan ya kwanta a neme shi a rasa. Su na gama yi wa sarkin baka bayani, Nana tayi farat ta ce "Ba ku je asibiti ba?" "Mun je, duk gwajin da aka yi sai ace babu ciki" babar matar ta ba wa Nana amsa. Sarkin baka ya bushe da dariya ya ce "Asma'u ma'u, su Asibiti duk abin da suka zo muku da shi, za ku karɓa ku ce technology ne, mu kuma namu da muke yi, shi ne shirka a gurinki. Shi maganin baturen kin san da me da me ake haɗawa? Kin tabattar da ingancin halaccin sa a addinance? Shi fa ilmi siffa ce ta Ubangiji, kuma yana bayar da ita ga wanda ya so, bai keɓantar da baiwarsa ga farar fata ba kawai, ku baƙaƙen fata ne ku ka raina abin da Allah ya baku na ilmi, ku ka yi amanna da bature ne kawai ya iya" Ya mayar da hankalinsa kan mara lafiyar ya ce "Hajiya a da idan ki na al'ada ba ruwanki, duk gurin da ki ka samu yarda ƙunzugun jinin ki ke yi. Da ƙunzugun jinin hailarki aka yi miki sihiri, saboda a raba ki da mijinki, idan ba ki manta ba, kin yi ta zubar da jini tun yana taya ki neman magani har ya gaji ya yi aure ya rabu da ke. Da ki ka ce ki na da ciki ma rigima ku ka yi ta yi ya ce ba nasa bane ba" cike da amanna ɗari bisa ɗari suka gazgata sarki. Nana ta ce "To kai ya aka yi ka sani, bayan baka nan aka yi?" Ya kalli Nana bai ce mata komai ba ya tashi ya nufi kan matar. Ya saka Salamatu ta ɗebo ruwan magani, aka bawa matar ta sha. Ya dunƙule hannunsa ya buɗe tafukansa aska ta fito, ya saka aka buɗe cikin matar, ya din ga yi mata ƙananan tsagu da askar. Wannan karon sanho ne a jikinsa, (jakar magunguna) zabira (Jakar wanzamai ta kayan aski) A wannan ƙaramar jakar, ya ciro garwashi jawur, ya ɗora a kasko ya zuba wani magani a kai. Take matar ta hau tari, ya kama cikin ya lailaya ya tattara shi guri guda, sai ga wani jini baƙi ƙirin guda-guda yana fitowa daga cikin. Sai da jinin ya gama fita, ya tattare guri guda ya zama wani baƙin muzuru. A take cikin ya baje, Sarkin baka ya danƙi muzurun ya jefa a cikin sanhonsa ya ce "Aljani ne yake ta yi mata wannan siddabarun. Salamatu a kaita gurin su 'yar ƙashi ɗaya, a tsumata zuwa jibi a sallame ta" Sai da Nana ta razana da abin da ta gani. Bayan fitarsu ya kalli Nana ya ce "Idan ki ka kuma ƙaryata ni a gaban mutane, sai na je na ɗaure ki a cikin mahaukatan nan kema" Nana ta ce "Amma ka ce ƙaisar ba zai kamu ba" Ya ce "Zai kamu, ban yi niyyar kama shi bane" Ta sake cewa "Amma ya ake ka ke wannan abubuwan haka? Ta ya ya ka ke sanin abin da baka nan aka yi?" "'yan aike ne suke gaya mini " "Aljnu kenan ko? Haramun ne fa hakan shirka kenan" "Ba shirka ba ne, taimakon al'umma muke yi" "Wallahi shirka ce, har fa tsafi ka ke yi " Dariya ya yi ya ce "A ina na yi tsafin?" "Ga shi nan ina gani kana yi, ya aka yi mage ya fito daga cikin mutum, kuma ya ake yi ka ke tura abubuwa da yawa a cikin 'yar ƙarama jakar nan?" Sarki ya ce "Aljihuna ne da yawa a cikin jakar" "To buɗe in gani" ya yi murmushi ya miƙa mata jakar ya ce "Buɗe da kanki" cike da ƙwarin gwiwa ta karɓi jakar, babu fargabar komai ta fara dubawa. Ya zuba mata ido yana dariya. Sai dai ta zazzage jakar babu komai a ciki. Ta kalle shi ta ce "Wallahi tsafi ne ina magen da ka saka a ciki ya tafi?" Ita kanta Nana tana mamakin yadda ta daina kewar gida gaba ɗaya, take jin kamar ta daɗe da sanin sarkin baka. "Idan kin yadda ki bayar da magani, zan nuna miki yadda nake komai, ki koma gida ki taimaki mutane" Ta girgiza kai ta ajiye masa jakarsa. "Ki je ki huta, anjima tare za mu fita farauta da ke, ki je ki yi bacci yanzu" Ta waro ido ta ce "Da wa za ayi farautar? Amma dai ba ni ba ko?" "Eh ba ke ba" ya bata amsa Ta juya da baya da baya, ta fita. Tana zuwa ɗakin da take, ta ga hayaƙi da wani irin ƙauri mara daɗi, cikin abin da bai fi mintuna uku ba, bacci ya kwashe ta. Da Ƙaisar ta fara tozali, zaune a kan wani dutse a cikin wani rafi, ya miƙe ƙafafuwansa a cikin ruwan masu azabar tsayi kamar itacen dogon yaro. Duk da ta riga ta saba da ganinsa, ba ta fiye razana dan ta gan shi ba, amma biyo bayan tuna mafarkin da ta yi da shi, a cikin sahara ya sanya ta zura da gudu tana neman hanyar guduwa. Ta yi gudu mai nisan gaske, ta ga wani gida, kawai ta faɗa gidan, tana addu'a a zuciyarta amma ta kasa furta ta, a bakinta. Sai dai bayan shigarta gidan, ta nemi hanyar fita ta rasa, kofofi kashi kashi a gidan, duk ƙofar da ta bi babu hanya sai dai ta sake dawowa guri ɗaya. Ta dinga buɗe ƙofofin amma ta rasa hanya. "Ina za ki ne?" Ya tambayeta bayan ya ajiye wata kwalba, jikinsa sanye da fararen kaya yana ɗigar da ruwa. "Yau kuma tsoro na baki? Ko ba ki yi zaton ganina yanzu ba?" Kuka Nana ta saka ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri, kar ka ƙona ni yau ma, dan Allah" "Yaushe na ƙona ki?" Nana ta ce"Ranar da ka zama tsoho ka koma raƙumi, ka yi haƙuri dan Allah" Ya girgiza kai ya ce "Ba ni bane" "Wallahi kai ne" "Ni ban yi wannan tsufan ba ai, ba ni bane" Cikin kuka ta ce "Kai na gani a sahara, ka zama raƙumi kana feso mini wuta" Ya sake cewa "Ba ni bane ba, tawagar buzayen da ki ka gani ne lokacin da ku ka shiga gidan. Ni ban yi wannan tsufan ba dudu sheruna nawa ban fi ɗari biyar da goma ba, yaro ne ni" Galala Nana ta saki baki tana kallonsa, shekara ɗari biyar da goman ne yaro. Tambayoyi ne fal a cikinta amma tana tsoron ta tambaye shi ya ce ta ba shi umarni ya zama hadiminta. Ya ce "Kalli can" ta kalli gurin da ya nuna mata. Suwaiba ta gani tana ta ihu ana danneta, mama na kuka tana tofa mata addu'a, sai fizge-fizge take yi tana kiran sunan Nana. Cikin damuwa Nana ta ce "wai me ya sa take kiran sunana, ba fa ni ba ce ba, ni me na yi mata?" Ya watsa wani abu daga hannunsa a gurin da take ganin su Suwaiba, sai ga wannan bararojin, tana ta zuƙar jinin Suwaiba, sannan jikin Suwaiba na ci gaba da zubar da jini ta huda-hudar nan da jikinta ya yi da ta fesa turare. Ɗif ta daina ganinsu, ta juyo gurin ƙaisar cikin damuwa, sai dai ba ta yi magana ba. "Kin san dalilin da ya sa na ƙyale mutumin nan, da ki ke gidansa? Wasu dalilai ne, ki gaya masa har yanzu bai san ni ba, duk hatsabibancinsa akwai sararin da bai isa ya jefe ƙafarsa ba. Na zuba masa ido ne na ga iya gudun ruwansa, amma dole sai na nuna masa iyakarsa, kuma zan gani tsakanin ni da shi waye zai yi maganin wani, kuma wannan abubuwan da yake yi miki akwai wani abu a ransa za ki ce na gaya miki " "Mene ne a ran nasa?" "Za ki gani, ya ce yau zai tafi da ke farauta, zai ci gaba da nuna miki magunguna. Zan ga iya ƙarshen hatsabibancinsa" Nana ta yi sororo tana kallonsa, duk da tana son tambayarsa, amma tana tsoron ya ce ta ba shi umarni ya zama hadiminta. Ya ce "Wuce ki tafi" "Ai na rasa ƙofar fita" "Bi waccan" ya yi maganar yana nuna mata hanya. Tana fita ta ganta a tsaye a ƙofar ɗakin da take tare da sarkin baka. Yana sanye da shigar hargi(irin shigar da maharba suke yi) Bayansa rataye da kwari da baka. Ba ta iya musa masa ba, ko jin tsoro ko makamancin haka ba, kawai ta saka kai ta bi shi. Daga shi sai ita yana gaba tana bin sa a baya hannunsa da fitila. Wata ƙofa suka je, ya ɗaga asabarin ya shiga, Nana ma ta bi bayansa. Suna shiga ƙofar ta gansu a dokar daji. Sai a lokacin jikin Nana ya hau rawa, tsoro ya kama ta, ta ja da baya ta domin koma amma ta ga babu ƙofar da suka shigo. Ya kalle ta ya ce "Kar ki tsorata, babu abin da zan yi miki, bari na ɗaure dajin" "Ina ne nan?" Tayi maganar cikin tsoro. "Dajin igbele ne, na jihar delta" Ta waro ido cikin kiɗima ta ce "Delta kuma? Daga Kanon mu ka zo delta?" Sarki ya ce "Eh, wata kububuwa nake son kamawa zan yi magani da dafinta. Daji ne mai haɗari ana tsafi iri iri a dajin, amma da na kama Kububuwar za mu tafi" ya yi maganar yana haɗa wuta a gurin, ya zuba wani turare yana kewaye wutar. Ita dai Nana ta yi shiru tana kallonsa. Sai da ya gama sannan ya yi gaba, ta bi bayansa. Gurin wani dutse suka nufa, daidai jikin dutsen akwai wani kogo, ya ajiye fitilarsa ya watsa wani abu a bakin kogon. Ya ciro wata raga a cikin sanhonsa ya kafa a gurin. Nana tana tsaye tana kallon ikon Allah. Ya gama ya ce "Mu je wani dajin na nuna miki wasu abubuwan" Al'ajabi ya hana Nana magana, suna tafe yana nuna mata wasu tsirran yana gaya mata amfaninsu. "Kin ga idan ki ka samu kashin giwa, da hauren toronta, wato namijin giwa, da kashin ungulu, ki ka haɗa su da kaucin kuka, da tazargade da garin ganyen kuka, da ganyen magarya arba'in ki haɗa jan miski, a haɗe su guri guda. Idan aka yi hayaƙin su, duk wani ƙaramin shaiɗani sai ya gudu, ke babban ma sai ya sha wahala wallahi, kuma aljani sai dai ya ganki ya bar ki" Nana ta dube shi ta ce "To ta yaya mutum zai samu wannan abun, duk sai mutum ya yi wannan wahalar? Najasar dabbobi ce za ta hana aljanu shafarsa? Bayan ga azkar da Alqur'ani" Sarkin baka ya yi murmushi, yana son ƙi faɗin Nana ƙwarin gwiwar ta na burge shi ya ce "Hala ke da Ƙaisar yake tare da ke, ba kya azkar da karatun Alqur'ani" Cikin damuwa ta ce "Ina yi mana, amma wasu lokutan idan ban yi ba na fi zama lafiya ma, na fara tsorata kar hakan ya sanya imanina ya yi rauni". Ya yi murmushi ya ce "Magani fa ba ƙarya ba ne ba, kin yarda bature ya baki maganin ciwon kai ki sha ki warke, wannan ba shirka ba ce ko, wannan technology ku ke wa ko?" Sai kuma ta ɗan yi shiru. Ja ya yi ya tsaya, ita ma ta tsaya, hasken wuta ta hango daga nesa, a hankali suka ƙarasa daf da gurin, suka tsaya, amma su na iya hango komai. Mutane ne tsirara sai ɗaurin ƙyalle ja a ƙugunsu, maza da mata su na kewaye wuta kowa da ɗan ƙoƙo a hannunsa. Wani mutum a tsakiya yana ta karanta wasu abubuwa, gefe wata mata a kwance ba ta ko motsi da tsohon ciki a jikinta. Ta ga mutumin nan ya nufi kan matar da wata wuƙa a hannunsa yana karanto wasu abubuwan. Razana ta yi, za ta ƙwala ihu sai kuma ta daina ganinsu, ta ga sun koma dajin da sarkin baka ya yi wa kububuwa tarko. "Idan muka tsaya, ki ka ci gaba da gani, za ki iya rasa hankalinki" Jikin Nana na tsuma ta ce "Su suka kashe matar?" Ya jinjina kai ya ce "Eh, jaririn cikinta za su cire, jininsa za su sha, ƴan ƙungiyar asiri ne. Nan da ki ka gansu manyan mutane ne, da suka sadaukar da lahirar su domin duniya. Akwai 'yan kasuwa a cikin su, da 'yan siyasa" Jikin Nana sai tsuma yake yi, ba ta taɓa tunanin da gaske akwai ƙungiyar asiri ba, ta zata shaci faɗi ne kawai ake faɗa. "Bari mu koma ki kwanta, da asuba zan dawo na kama macijiyar nan, naga duk a tsorace ki ke . Sai dai ina son mu yi wata magana da ke". Jiki a sanyaye ta ce "Wace irin magana ce?" "Ina son ki sadaukar mini da uban duƙusa wato ƙaisar, na din ga aiki da shi!" Littafin nan 1k ne a telegram ta wannan account ɗin 0069685771 Aisha Adam Stanbic ibtc Sai shaidar biya ta Ayshercool 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU AISHA ADAM (AYSHERCOOL) YOTA/002 P14 Cikin hanzari Nana ta ce "Na yarda na amince, na bar maka shi" "Ai ba da baki kawai za ki faɗa ba, akwai buƙatar yin wani aiki, idan kin amince za ki sadaukar mini da shi, za ku rabu har abada" "Eh na amince" Sarkin baka ya ce "Za mu ƙarasa maganar da safe" Kawai ta gansu a ƙofar ɗakinta, suka yi sallama ta shiga ta kwanta. Sai dai jikinta na ta tsuma da tunanin wace matar aka kashe, kuma ake ƙoƙarin cin zarafin gawarta haka. "Hmmm za ki sadaukar wa wani ni ko? Har kin yi sabo da shi haka kin yarda shi?" Ta ji maganar ƙaisar a tsakanin zuciyarta da ƙwaƙwalwarta. "Eh zan sadaukar da kai, muddin hakan zai sama mini lafiya da nutsuwa" ta yi maganar a fili. Dariyarsa kawai ta din ga ji, gidan baki ɗaya yana amsa kuwwa. Bayan ta yi sallar asuba, ta zauna tana azkar bayan ta idar, ta yi shiru tana tunani, addu'a ta din ga yi Allah ya rabata da ƙaisar, muddin abin da sarkin baka zai sakata bai saɓa wa Allah ba, za ta yi domin ta rabu da ƙaisar. Da kanta take zuwa gurin Sarkin baka yanzu, duk ta san hanyoyi a gidan. Kuma ganin ta samu sassauci daga takurar ƙaisar, da sanya mata cututtuka da sauran damuwowi ga abinci tana samu babu mai takura mata da damuwa, ga kuma sukulle da kyautatawar da sarkin baka yake yi mata, sai ta fara sakin jiki da mantawa da damuwar da take ciki. Abin mamaki, yau da Alqur'ani ta tarar da sarkin baka, bugun warshi yana karantawa, sai da ya idar sannan suka gaisa suka fita. Sai da suka fara zuwa gurin da ake harhaɗa masa magunguna, har da injin niƙa a gurin, shi ma ma'aikatan gurin daban, ga tarin saiwoyi da tsirrai. Gaggaisawa ya yi da masu aikin gurin, ya ce "An kawo saiwoyin nan kuwa?" Ya yi maganar yana kallon Salamatu. Salamatu ta ce "A'a sarki, ta rafi ake jira, ba ta kawo ba" "Aljanar nan akwai sheɗainiya, idan ta bari na nemo wani ya ɗebo mini, wallahi sai ta ɗanɗan kuɗarta" Nana ta kalle shi ta ce "Aljana kuma?" "Eh, wasu saiwoyin ai sai dai aljani ya ɗebo, ba dai mutum ba. Akwai abubuwan da a cikin ruwa muke ɗebo su, kuma akwai dai-dai lokacin da muke ɗibar su, idan ba aljani ba sai dai ka nemi masunta, su kuma idan ba su ga dama ba, ba za su baka ainihin abin mai kyau ba" Yana gama yi wa Nana bayani, ya ci gaba da maganar sa. "Akwai masu shanyewar ɓarin jiki, mutum biyu Salamatu a je a duba, idan na aljanu ne, a jira ni ki ba su taimakon gaggawa. Idan kuma na larura ne maza a haɗa musu magani, a ɗauki ɓawon kwakwa, da sassaƙen zogale, da zoɓo da ɓawon abarba, a dafa su sosai, a ƙara ruwa, a din ga basu kofi ɗaya sau uku rana. Ba cin man gyaɗa, ba cin gishiri ba cin kanwa, uzairu ya yi musu ƙaho zan zo na ga jikin nasu" cikin girmamawa ta ce "To sarki" Tun Nana tana mamakin al'amuran sarkin baka, har ta zuba wa sarautar Allah ido kawai Amma duk da haka, Nana ta kan kasa jurewa sai ta tambayi wasu abubuwan, yanzun ma ɗan gyaran murya ta yi ta ce "Sarki, su wannan magungunan da ka ke bayarwa haka da ka, ba ka tunanin ya yi wa mara lafiya illa, a asibiti akwai maganin da idan mutum yana da wani ciwon fa ba a ba shi, ku kuma nan ba tantancewa ku ke yi ba, kuma ba auna maganin ku ke yi ba" Ya gyara zaman sanhonsa ya ce "Ban da sharri irin naki, da kuma abu irin naku na 'yan boko aƙida, da ku ke cewa maganin hausa ba shi da awo, ba yanzu a kunnen ki na faɗi gwargwadon abin da za a ba su ba? Wanda ya sani fa ya sani Asma'u, wanda bai sani ba bai sani ba, galibi gurin masu neman na Abinci kawai ake zuwa, wani koya ya yi amma ba a koya masa maganin yadda yake ba, dan ba kowa ne yake yarda ya bayar da sirrin sa ba. Ni na gada kuma na koya. Bature ya yi nasa ban raina masa ba, kuma nima na yi nawa ba wanda ya isa ya raina mini. Ke shaida ce duk abin da ba ni da maganinsa ina gaya wa mutane. Kuma ni ba dan neman kuɗi nake bayar da magani ba. Ki din ga tambayata abin da ba ki gane ba zan yi miki bayani, amma muddin na ji kushen abin da nake yi, ba zan ba ki amsa ba, kuma kin yi wa kanki, dan ba ki san a ina abubuwan da ki ka koya a gurina, za su iya amfanar ki ba, ko su amfani wani ba" jin sa kawai Nana take yi, tana ganin me za ta amfani wani da wannan abubuwan da babu scientific proof ko research a kan su. Bayan sun gama da nan suka tafi ɓangaren da ba ta taɓa zuwa ba a gidan. Shi kuma garke garke ne na dabbobin dawa da na gida, wani abin ma ba ta taɓa ganinsa ba. Ya din ga nuna mata dabbobin, da magungunan da ake yi da wasu sassa na jikinsu. Yana cikin yi mata bayani, ta ga ya yi shiru ya daina magana, ta leƙa fuskarsa za ta yi magana kawai ta ga ƙwayar idonsa ta koma baƙa gaba ɗaya, jikinsa ya hau tsuma. Cikin sanhonsa ya zira hannu, sai ga shi ya fito da wani shirgegen zaka, ya gaji da riƙa cerarsa jawur da ita. Jiki na tsuma Sarkin baka ya saka hannu ya raba kan zakaran da gangar jikinsa. Ya ɗaga gangar jikin, ya tsiyaye jinin a bakinsa, ya gama ya hau cin gangar jikin zakaran a ɗanyensa da gashinsa da komai yana zazzaro ido. Ihu Nana ta saka tana karkarwa, ta juya za ta kasa da gudu, kawai ta ganta a jikin Salamatu tana shafa mata wani abu. Nana ta juya ta ga ba ta ga Sarkin baka ba, sai ita da Salamatu a ɗakin. Salamatu ta ce "Nana zamanki a gidan nan, ya ci ace kin daina tsorata a mafarki, ki koyi dakiya garin tsoron nan wataran za ki iya zaucewa fa. Shi ya sa Sarki yake nuna miki wasu abubuwan domin ki saba ki rage tsoro" Ajiyar zuciya kawai Nana take yi, cike da tsoron abin da ta gani da ta kasa tuna mafarki ne ko kuma gaske. *** Gaddafi na zaune a rumfar mai shayi, yana jiran a dafa masa noodles da ƙwai ya ci. Babu tsammani sai ga jami'an tsaro sun dira a gurin, tare da Imran. Imran ya nuna Gaddafi aka kama shi, cikin mamaki Gaddafi yake tambayar ba'asin abin da ya faru, amma ba su gaya masa ba suka tafi da shi. Sai da su ka je charge office, sannan aka ce Imran ya faɗi abin da ya kawo ƙarar Gaddafi a kai. Imran ya ce "Yallaɓai, ƙanwata ya ɗauka suka haɗa kai da yayar babanmu, aka kai ta wani guri wai neman magani. Kusan sati guda kenan na yi na yi, su gaya mini ina suka kai ta sun ƙi, kuma ita kaɗai aka baro a gurin babu ɗan jinya". Cikin mamaki da takaici Gaddafi ya ce "Amma ka cika mara mutunci, me ya hana ka saka a kama da Baban, sai ni zaka saka a kama, bayan tare muka kai ta". Imran ya ce "Eh wannan ai ubana ne, kuma Kai ka kawo shawarar a kai ta can ɗin. Ga Suwaiba nan a gidan tana aljanun ita ma, ita baku kaita ba, saboda ita ana son ta ƙanwata ce ba a so, kawai ka gaya mini ina aka kai mini ƙanwa" D.P.O ya ce "Ya isa haka, wannan maganar ta cikin gida ce, kuma shi ma yana da gaskiya, babu yadda za ayi ace an kai mutum gurin mai magani, babu wani nasa a gurin, kuma ba asibiti ba. Ko Asibiti ne?" Ya yi maganar yana kallon Gaddafi. Gaddafi ya girgiza kai. "To ka gani, shi ba ubanta ba ba ɗan uwanta na jini ba, ba ma kwa tsoron ya lalata rayuwar yarinyar. Ga ku a cikin ƙwaryar birni kamar masu hankali, amma kun yi abu kamar mutanen farko. Duk yadda ake ciki wajibi ne gobe ka wuce gaba, zan bayar da mutum biyu a nan, aje a dawo da yarinyar nan, muddin ba ku dawo da ita ba, to wani abun ku ka aikata kuma sai na rufe ku daga kai har wanda ku ka kai ta" Gaddafi ya jinjina kai tare da yi wa Imran wani mugun kallo. ***** Nana a ɗakin da sarkin baka yake bayar da magani ta tarar da shi, yana ganin wata mata da yaronta. Ƙafafuwan yaron tamkar lagwani 'yan sirara marasa ƙwari, da hannayensa. Haka kansa ma ɗan mitsitsi da kaɗan ya fi lemon zaƙi fuskarsa tamkar tsoho abin tsoro yaron. Uwar kuma sai rungume shi take yi cike da so da ƙauna. Sarkin baka ya ce "Wata rana kin kashe gizo gizo cikin dare, a banɗakin ki, lokacin ki na da ƙaramin cikin yaron nan, ba tare da kin

Chapter 11 of 13