Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 10
komai ba, kawai ka janye kalmar nan ta b'arauniya daka fad'a min." Hannayenshi bibbiyu ya rabka a k'ugunshi ya dafe jajayen idonshi a kan ta, ba alamar wasa a tare dashi yace" Ke 'yar garin nan ce?" K'urawa fuskarsa ido tayi ba tace komai ba, ganin bata da niyyar magana sa茂 ranshi ya sake b'aci, a harzuk'e ya cabki hannunta da nufin fitar da ita, da k'arfi ta fincike hannunta tana mai kallon inda ya rik'e, wani abu ta ji kamar wutar lantarki tana janta. Kallonta ya shiga yi shi ma da tunanin ko dai abinda ya ji ita ma ta ji? Tsaki ya buga kawai ya juya ya sake shigewa ban d'akin zuciyarshi kamar zata fashe. Ayam ma na ganin haka ta ja k'afarta data mata nauyi ta fita ita ma, a bakin k'ofar ta samu su Deeyam suna jiranta, da zumud'i Sabrine tace "Ya dai? Me ya faru 脿 ciki?" Shiru tayi sa茂 sauka a matakalar data shiga yi, Deeyam ce tace "Ya muka ji kinyi ihu? Ko dai d'an hannu ne shi ma?" Babu wacce ta amsa ma har suka koma ta inda suka fito suka koma d'akinsu suka kwanta, amma Ayam sai tayi zaune akan gado ta zabga tagumi tana sake kallon wuyan hannunta daya rik'e. *A* wajen Umad ma saida ya ji an rufe d'akin ya fito, wajen hoton ya k'arasa ya durk'usa ya shiga tattare glass d'in, a kwandon shara ya zuba sannan ya d'auki hoton yana kallo, cikin yarenshi yace " *Majka* (uwata), kiyi hak'uri ba laifina bane, waccen mahaukaciyar ce da ban san me ta zo nema ba." Ba tare daya saka kaya a jikinshi ba shi ma ya zauna kan gadon yana ta kallon hoton nan, so yake yayita zazzaga masifa ko ya ji sauk'i, amma dake mutum ne ba mai hayaniya ba sa茂 kawai yake ta tsaki shi kad'ai. Sai dai ya k'agu gari ya waye ya bincika ya ji wacece wai ita d'in? Da wannan tunanin har bacci ya d'aukeshi bayan ya tofe jikinshi da addu'o'in tsari. *Washe gari* Zazzaune suke a cikin aji kowa na mazauninshi zaman mutum d'aya, sunyi shiru kuma sun nutsu suna sauraren jawabain ban kwanan da malam Pedro ke musu, yana gamawa yayi murmushi a harshen fransanci yace "To d'alibai, ni zan tafi yanzu, sai mun sake had'uwa da ku, ina muku fatan nasara." A tare dukansu suka amsa da "Za mu yi kewarka malam." Dariya yayi wanda hakan yasa Ayam juyawa ta kalli Deeyam cikin rad'a tace "Malam Pedro na dariya dama?" Dariya Deeyam tayi a kan idon malamin, harara ya galla musu yace "Hirata kuke ko?" Da sauri Ayam ta girgiza kai alamar a'a, shi ma girgiza kan yayi yace "Na sanki fa Ayam, da ni d'in nan ragon namiji ne da kin jima da sani hauka." Girgiza kai ya sake yi yace "To d'alibai, ni zan tafi na bawa sabon malamin ku dama ya shigo dan ya gabatar muku da kanshi." Hannu ya d'aga musu ya nufi hanyar fita, su ma hannun suka shiga d'aga mi shi, tun bai k'arasa fita ba Ayam ta mik'e ta tsaya a inda ya tsaya shi ma, irin tsayuwarshi tayi da yanda yake cije fuska ta tsuke baki ta fara magana kamar yanda yake alama tana kwaikwayonshi tana fad'in "To ni zan tafi, wani aiki ne ya taso da ake neman agazawarmu, amma ban ji dad'in rabuwa da ku ba musamman da shekara ta kusa k'arewa, amma duk da haka..." Mik'ewar da duk sukayi d'aliban suna gaishe da malamin daya shigo yasa Ayam k'amewa tare da bud'e baki irin" Na shiga uku." Cikin sand'a kamar wacce k'wai ya fashe ma a cikita shiga takawa har ta zauna teburinta, tana jin takon takalmin malamin suna bada sauti d'a茂 bayan d'aya, saida ya tsaya tsakiyarsu sannan ya musu izinin zama. Shiru ajin ya d'auka bayan sun zauna, shi yana k'are musu kallo su ma suna k'are mishi kallo suna fahimtar wane iri ne shi ? Zaiyi dad'in sha'ani ko kuma d'aurarrar fuska ce dashi kamar malam Pedro. Ba tare daya juyar da kanshi ba iya idonshi kawai ya zuba mata, fuskar nan tamau da ita ba alamar annuri cikin dakusashiyar murya mai firgitarwa yace "Ya sunanki?" Kamar sauran d'aliban ita ma d'aga kai tayi ta kalleshi dan son sanin da wa yake, idon da suka had'a yasa gabanta tsinkewa ya fad'i tare da kad'awar kayan cikinta, 脿 take kawai ta tausayawa kanta, marairaicewa tayi tana matse k'afafunta daga sama, wuwulk'ita idonta ta shiga yi cikin daburcewa da sark'ewar murya tace "A.. Yam." Wannan karan d'auke idonshi yayi daga kanta ya sake fad'in "Sunanki?" 'Yar k'walla kawai ta ji ta zo mata a kan kunci, a sanyaye ta sake maimaita "Ayam." Takowa ya fara yi zuwa gabanta, da sauri ta sauke idonta tana kallon teburin, saida ya tsaya daf da teburin 脿 mugun kausashe yace "Ayam, baki da sunan uba ne?" D'aga ido tayi da sauri ta zuba cikin na shi idon, hawaye taji kan kuncinta suna kwaranya, sosai maganar ta mata zafi, amma saita shanye tunda malaminta ne a aji, kanta sadde k'asa tace "Ayam Utais." Cikin tsananin bala'in haushinta da yake ji 脿 tsawace ya buga teburin da take zaune 脿 kai da hannu cikin d'aga muryar data sa ajin amsawa baki d'aya yace "Ayam Utais, ba'a koya miki tarbiyyar mik'ewa tsaye yayin magana da malami ba?" Tunda ya buga tebur d'in yan matan ajin wasu sukayi ihu wasu kuma suka k'ame, kamar dai Ayam da ita ma k'amewar tayi amma fa kuma idonta cikin na shi. Abu d'aya ya zo masa a daidai lokacin, maganarshi da babban malamin shi a sanda yake son sanin alamomin da zai ganeta, a yanzun da abun nan ya faru sai ya tuna sanda malamin yace _"Had'uwarku ta farko ba zata bada k'ayatarwa ba, saidai 脿 wurinka da zaka aje hankali, kowane motsinta zai baka al'ajabi, a zahiri mace ce kamar kowace mace, tana jin tsoron abinda zai tsorata kowace mace, saidai ba komai ke tsorata ba, akwai b'oyayyar jarumta a tare da ita, abinda ya cancanci ya bata tsoro ba shi ke tsorata ba kai tsaye, wanda kuma kai zai iya kayar maka da gaba, sa茂 kaga ita abin ado ne a gareta, saidai fa duk da haka mace ce mai birgewa, saboda tana da abinda duk wani namiji yake tsananin so ga 'ya mace."_ A lokacin tambayar daya masa ita ce _" Menene shi abun?"_ Murmusawa malamin yayi sannan yace _" Rauni, tana da rauni, dan bata iya kare kanta ga duk wani abun cutarwa."_ Ajiyar zuciya Umad ya sauke ya mik'e daga rusunawar da yayi 脿 ranshi yana fad'in" Ba ita ba ce, wannan ba zata tab'a zama Zafeera da ake fad'a ba." Sake kafeta yayi da ido yace "Jiya da dare me ya kaiki d'akina?" Zaro ido tayi tana kallon shi kamar taga bak'uwar hallita, sororo tayi ta rasa bakin magana, kallonta ya sake yi yace "Cire hular kanki, ki zama daidai da sauran d'aliban." Tsura masa ido tayi a ranta tana tunanin watak'ila fa son takura mata yake saboda yanda suka fara had'uwa, to amma ita ma zata ji dashi a haka, a hankali tasa hannu ta cire hular ta kan ta. D'an zaro ido yayi yace" What?" Jinjina kai yayi a dak'ile yace" Kin kad'e." A sanyaye ta turo baki gaba tace "Sorry sir." Juyawa yayi ya kalleta yana rumgume hannaye da mamakin yanda ta gagara mik'ewa tsaye sannan ta masa magana, ita wacece? Sauran d'aliban ya kalla yana sauke hannayenshi daga k'irji yace "D'alibai, sunana Umad Wudar, sabon mai koyar da ku, ina fata zaku bani had'in kai mu k'arasa zangon shekarar nan daku lafiya, ina so ku d'auke ni a matsayin malaminku mai sauk'in kai a aji, amma a wajen aji zamu iya zama abokai, hakan zai k'ara mana fahimtar juna kuma ku ji a ranku daidai na ke daku, kun fahimta." A tare cikin d'aga sauti suka ce" E malam." Jinjina kai yayi ya nuna d'alibin farko yace" Ku gabatar min da kan ku." D'ai bayan d'aya suka dinga mik'ewa suna fad'in sunan su, saida aka kawo kan Ayam ta mik'e ta fara fad'in" Ay..." Da hannu ya mata alamar zauna tare da fad'in" Me ye abun dad'i a sunan naki da zan ji shi sau biyu? " Idonta tar a cikin na shi tace" Sorry sir." Girgiza kai yayi tare da jan tsaki ya kalli Deeyam dake bayan ta yace" Uhum!" Mik'ewa tayi ta fad'i sunanta, har zata zauna yace" Ana koyar daku turanci ne a nan?" Girgiza kai tayi tace" A'a malam." Kallon Ayam yayi ya yatsina fuska a zuciyarshi yace" Gidan uban wa ta iya sorryn?" Haka aka gama gabatarwa ya shiga darasinshi ba tare da b'ata lokaci ba, awa uku suka d'auka ba hutu ba shan iska, gashi in suka had'a ido da ita sai ya galla mata harara, ita kuma haka kawai taji kamar ta samu abokin wasanta, ta k'i d'auke idonta daga kan shi sai binshi da kallo take. Saida ya dubi agogon dake tsintsiyar hannunshi sannan yace" D'alibai ina ga anan zamu dakata, shin da mai tambaya a darasinmu? Ko kuma wanda bai gane wani abu ba?" Girgiza kai sukayi dan magana ta gaskiya sun fahimci darasin shi sala-sala, dan haka da ya ga babu mai tambaya ya juya da niyyar tattara nashi ya nashi. K'afa d'aya kan d'aya ta d'ora ta rumgume hannaye a k'irji tace" Sir ina da tambaya?" Wani iska ya feso ba tare daya juyo ba dan yasan ita ce, saida ya sauke nufarfashi ya saita nutsuwarsa ya had'e b'acin ranshi sannan ya juyo a dak'ile yace" Uhum." Duk da ba ita yake kallo ba sai yaji gabansa fad'uwa yake kamar mai jin tsoron tambayar da zatayi, cikin siriryar muryarta tace" Sir, indai har dorinar ruwa kakkausan jiki ne da ita ta yanda alburushi baya mata illa, kenan wane irin makami ne zai iya cutar da ita kai tsaye?" Kallonta yayi wannan karan kallo irin na k'urilla, kamar sub'utar baki yace da ita" Bomb." Da mamaki a fuskarta tace" To amma yallab'ai ai mu ba'a yarje mana aiki da bomb ba." Wani tsakin ya kuma ja ya juya zai d'auki jakarshi ta sake fad'in" Yallab'ai tambaya ta gaba?" A hassale ya juyo yace" Ina jinki." Cike da son danne dariyarta tace" Ka fad'a mana zakanya tafi zaki iya farauta, me yasa to duk da shi ne namiji kuma sarki?" Tsurawa fuskarta ido yayi dan ya fahimci ba shashashan tambayoyi take yi ba, cikin d'an saita muryarsa yace" Saboda shi zaki baya son jin rauni a jikinshi, sannan yana da son hutu kamar yanda yake da jin izza ksancewarsa sarki." Jinjina kai tayi sannan ta sake fad'in" To amma kuma me yasa zaki baya mu'amula da zakanyar da bata kusa cimmasa a shekaru ba?" Tarr! Ya kalli k'wayar idonta mai kama data mage a cikin dare, sauran d'aliban ya kalla sannan ya kalleta yace" A nan ajin nasan babu wacce ko wanda bai balaga ba ko?" Ihu suka saka tare da fad'in" E yallab'ai." Jinjina kai yayi fuskarshi ba alamar fara'a sannan ya sake kallonta yace" Zaki ai sarki ne, jarumtarsa da yarda da kanshi yasa baya tarayya da wacce yasan ba zata iya d'aukarsa ba." Cike da gadara ya juya ya d'auki jakarsa inda ajin ya kaure da ihu da maganganu, saida ya fita a ajin Ayam ta mik'e tsaye akan teburin tayi wata irin k'ara tare da tintserewa da dariya tace" Yan mata wai kun yarda?" Duk yan matan ajin suka amsa mata da" A'a." Wata ihu ta sake yi tace" Ni ma ban yarda ba, abinda na yarda da shi shine mace rijiya ce, kowace irin guga aka zura mana zamu karb'a kuma mu bada ruwa." Caraf a kunnen Umad da bai k'arasa fita ba, juyowa yayi ya kalleta, samun kanshi yayi da sauke idonshi kan 'yan tsiraun nonuwanta dake cikin rigar kayan makarantar, yan firit da su ta yanda zai iya had'esu duka biyu a tafin hannunshi kuma ba lallai su cika masa hannu ba, a hakan ma dan yana tunanin ta saka bras wacce zata k'ara mata aukinsu, girgiza kai kawai ya sake yi yana jan tsaki yace "Baki san me zaki yake nufi ba." Keb'antaccen gurin cin abincin malamai ya nufa, bayan ya gabatar da abinda yake da buk'ata sai kuma ya kasa ci ya tsaya amsa waya, Haman ne ya tambaye shi "To ya sabon aikin na ka?" Girgza kai yayi yace "Ba dad'i." Dariya yayi daga b'angrenshi yace "To amma ka fara abinda ya kai ka ne? Akwai wani abu daka fara samu?" Shiru yayi tare da sauke ajiyar zuciya, jin bai amsa mishi ba yasa Haman sake fad'in "Lafiya ko Umad?" Shafa sumar kanshi yayi wacce har yanzu yake takaicin rabashi da ita da akayi sannan yace "Tana jaririya fa ta b'ata, kuma babu wani wanda yasan wani abu a kan ta, ta ina zan ma fara nemanta a Larhjadin? " Dogon tsaki ya ja wanda hakan kamar d'abi'arsa ce kafin yace "Ya binciken da na saka ka? Ka samu wani abu ne ?" Cike dta karsashi yace "E yallab'ai, yanzu haka ma zan je wajen wani ne dan samun wasu bayanai." Jinjina kai yayi yana shafa sajenshi yace "Duk yanda ake ciki ka sanar min." Bai jira amsawarshi ba ya datse kiran ya aje wayar gefe, cike da k'yank'yami ya fara cin abincin, duk da tsabtarshi da kyau da kuma dad'i, amma shi dai bai masa ba ko kad'an,haka ya d'an tsakura ya mik'e ya bar wajen. *Alhamdulillah* 01/01/2022 脿 11:31 - Mom Khalid: 馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈� _*LU'U LU'U*_ 馃懇鈥嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈煈┾€嶁潳锔忊€嶐煈� *NA* _SAMIRA HAROUNA_ _SADAUKARWA GA_ *'YA'YA NA* 馃挮鉁� *TAURARIN MARUBUTAN NIGER (ASSO.)*馃専 _(Tsintsiya mad'aurinki d'aya)_馃 鈽� *[ T.M.N.A]* 鈽� 馃摉馃枈锔� https://www.facebook.com/Taurari-marubutan-niger-111773560677003/ _Alhamdulillah, Alhamdulillah, Alhamdulillah, hak'ik'a Allah abun godiya, bayan share wata uku na dogon nazari da samun gamssashen hutu, hazik'ar ta sake dawo mu ku da wani sabon nagartacce kuma zak'wak'urin labari mai taken *LU'U LU'U*, kai dai daga jin lu'u lu'u kasan akwai magana a ciki, rubutun littafin zai zo muku daga alk'alamin marubuciyar nan dai da kuka sani mai *Badak'ala*, *Jihadi* da kuma *Matar mutum*,ma'ana dai ta ku *Samira Harouna* (Meeranku馃榿, Yasin ta ku ce), nasan kunsan labaran kuma kunsan me suka k'unsa, Dan haka zan ce ku garzaya da gudu Dan ku samu rabon karanta n'a ku Lu'u lu'u._ _Farashin mai sauk'i ne masoya, ga duk mai son ta samu n'a ta zata biya naira 200 kacal, ga Yan k'asa ta Niger kuma abar alfahari na zaku biya 400f cfa kawai, soyayya Dan Allah tana saka komai, k'awaye na ku zo mu tafi tare da ku, Dan ba zan Bari a barni a baya ba._ _Yan Niger zaku tura katin Airtel ko Moov akan wannan lambar, *94-98-56-52* sai ku tura shaidarku ta wannan lambar *88-35-50-01*._ Yan Nigeria kuma zaku tura ta wannan asusun *3120244299* Amina Maikudi Abdullahi First bank. ko kuma Recharge card na Mtn Akan lamba 080-38-85-69-44. _Masoya Yan mutan Niger sai mun ji daga gareku, mutanenku ne dai._ _Bismillahir rahamanir rahim_ *6* Fitowarsa tayi daidai da k'arasowar su Zafreen zasu je b'angaren su Ayam dan ganawa da wata k'awarsu, zasu wuce shi ma zai wuce kawai Zafreen ta k'ura masa ido, baki da hanci ta saki tana binshi da kallo, cike da birgewa ta juya saboda har yayi gaba ba tare da sanin me take ba tace "Wow! Amma malamin nan ya had'u." Laika ce tayi saurin kallonta tace "Gimbiya Zafreen, kina nufin ya birgeki ne?" Juyawa tayi ta kalli Laika tace "Sosai ma, idan har zan iya yin aure to shi ne mijina." Murmushi ta saki ta kalli k'wayar idon Laika tace "Ina zuwa." Kafin Laika tayi wata magana har Zafreen ta tafi da sauri tana fad'in "Malam, malam ji mana." Tabbatarwa da yayi da shi ake yasa shi dakatawa ya juya, a tsanake ya shiga k'are mata kallo, tabbas kyakyawa ce data amsa sunan kyakyawa, komai na ta yayi kuma y had'u, bata da makusar da duk namiji mai son more rayuwa ba zai so samunta ba. Kayan jikinta sun nuna mishi a wani b'angaren take nata karatun, ga kuma wani yankakkan gashi dake kan ta mai kalar ruwan d'orowa wanda haka kalar idonta ma suke. Iya fatar jikinta ta nuna masa ita ma yar hutu, ko 'yar hamshak'in mai kud'i, ko 'yar mai iko ko kuma sarauta, tana k'arasowa ya sake gyara tsayuwarsa. Saida ta zo daf da shi sai kuma sai ta ji wani kwarjininshi ya kamata, kanta sadde a k'asa ta shiga doka murmushi, cikin sanyayyar murya tace "Malam barka." Fuskar nan a had'e ya amsa da "Uhum." Duburburcewa tayi ta shiga rausayawa kamar zata taka rawa, kame-kame ta fara tace "Am.. Dama dai... Ni sunana Zafreen Musail, gimbiya Zafreen Musail." Tsura mata ido, da fari dai ya d'auka mai hankali da ilimi ce, ashe ba haka bane. In banda abinda me ye abun birgewa a cikin nuna kai waye kai tsaye? Saidai yayi farin ciki da haka, dan tabbas idan bai samu 'yar uwar ta Zafeera ba, to kan ta zai *d'auki fansa*, dama ya fi son d'aukar fansar ne ta hanyar Zafeera saboda ita yaga an fi cin buri a kan ta, amma wannan ma zai iya maleji da ita madadin yayi biyu-babu. Wani d'an siririn murmushin mugunta ya sakar mata a dak'ile yace "Barka princezna, haka kuke fad'a a yarenku na slovaque ko?" K'ara washe baki tayi kamar zata fad'a masa tace "E yallab'ai, ka iya yarenmu kenan?" Shu'umin kallo ya mata yace "E, yanayi ne yasa na iya." Sake fad'ad'a murmushi tayi tace "Am...Yallab'ai, zan iya rok'on wata alfarma?" Da ido ya mata alamar "Ina jinki." Mamaki ne ya kamata ganin wannan ma yana neman ya fi ta shan k'amshi, basarwa kawai tayi tace "Zamu iya zama abokai?" Yatsina fuska yayi kamar ya ga abun k'yama yace "Hakan ai ya sab'awa dokar kowace makaranta." Tab'e baki tayi tace "Karka damu yallab'ai, indai ka amince wannan ba matsala bane, mahaifina shi ne sarkin Khazira, duk wata masarauta a k'asar nan a k'ark'ashin ta mu masarautar take, dan haka zan iya yin komai da nake so." Sake b'ata rai yayi yana mai jin wani takaici fiye ma da wanda ya ji yayin had'uwarshi da waccen tamatsirin, dan gaba d'aya wannan magana take ta alfahari da d'agawa wacce babu tunani a cikinta. Girgiza kai yayi ya d'an juya zai bar mata gurin, da sauri tace "Yallab'ai ya haka kuma? Baka ban amsa ba." Juyowa yayi a kasalance ya kalleta, lumshe ido yayi yace mata "Kiyi hak'uri." Juyawa ya sake yi yai tafiyarshi ya bar ta nan tsaye, haushi ne ya kamata ganin yanda ya cizgata a gaban mutane, fuska a kumbure ta juyo ita ma rai b'ace ta nufi wajen su Laika dake tsaye suna kallon komai daya faru. Tana isowa ganin yanda take cika tana batsewa yasa a cikinsu babu wacce ta tambayeta lafiya? Dan zata iya juyewa a kan su, a tsiyace take tafiyar kamar zata tashi sama inda suma suke biyarta a haka. Daf da bakin k'ofar shiga su Ayam su kuma zasu fita rakata kiran Momma, a rashin sani Sabrine da Zafreen suka bangaji juna, da k'arfi Sabrine tace "Aouch!" Zafreen kuma a mugun tsawace tace "Ke!" Kafin kuma kowa ya ankara Zafreen ta kwad'awa Sabrine wani wawan mari, ihun da tayi a firgice yasa Ayam waro ido ta sauke akan Zafreen d'in, a karo na biyu Zafreen ta sake d'aga hanu zata mari Sabine tana fad'in "Ke har wace..." Cak maganar ta tsaya mata, dan bata san lokacin da Ayam ta rik'e hannun na ta ba kuma har da nasarar marinta a fuska. Dafe kuncinta tayi tana kallon Ayam dake dafe da kafad'ar Sabrine tana fad'in "Kiyi hak'uri kinji, ke ma ai kina da gata." Kamata tayi zasu wuce ka rantse da Allah bata san me tayi ba, duk k'awayen kuma sun yi mutuwar tsaye saboda ganin girman lamarin, musamman ma Laika ta fi kowa tsorata, a sukwane Zafreen ta shak'i wuyan rigarta cike da masifa tana fad'in "Ke kin..." Yanda Ayam d'in ta zuba mata ido ta kalleta sai abun ya gigita Zafreen, yanda idonta masu launin nan mai ban tsoro suka samu sirkin launin ja na b'acin rai, sai kawai ta ji gabanta yayi wata mummunar fad'uwa, kamar wacce mai fad'a a ji ya bata umarni sai ta shiga zame hannunta a jikin rigar Ayam d'in, hakan ya ba su Ayam d'in damar k'arasa ficewa a wurin. Da kallo suka bisu har da ita Zafreen d'in data sake dafe kunci tana murzawa a hankali, ta ji zafi sosai na marin nan, yau ma sai suka fasa shiga kamar dai jiya suka juya da sauri suka bi bayan Zafreen dake tafiya har da gudu gudu. *Shigarsa* ke da wuya d'akinshi ya bud'e taga kenan ya hangi Zafreen zata mari Sabine a karo na biyu Ayam ta rik'e hannun kuma ta mareta, duk da b'angaren malamai da b'angaren su Ayam d'in ba wai yana kallon juna bane, kamar kusan a jere ma suke saidai akwai ginin babban ofishi a tsakaninsu (zauran malamai). Yanda ya ga wannan abu da tuna had'uwarshi da Zafreen d'in sai ya ji gabanshi ya fad'i, a yanayin da bai saba da shi ba ma'ana tsoro yace " Wai *wacece ita*?" D'ora hannunshi yyi a kai yace "Tsarki ya tabbata ga Allah." Maganar gaskiya ko shi da ke namiji ba zai iya marin Zafreen ba, dan tana da kwarjini da izza wacce kana gani kasan ta samo asali ne daga gidan sarauta, musamman ma ita da mahaifiyarta Juman 'ya ce ga sarkin Egypt (Ya akayi ka sani? 馃), sannan mahaifinta ma sarki d'an sarki kuma jikan sarki. *Ayam* kam suna fita Deeyam a mugun tsorace ta rik'o hannun Ayam tace "Ayam kinsan me kika aikata kuwa? Ita ce fa naji ana rad'e-rad'in gimbiya ce." Saida ya zage hannunta daga na Deeyam tana karbar wayar da mai kula dasu ya mik'o mata ta d'ora a kunne tace "Then." Da mad'aukakin mamaki Deeyam tace "Ayam ba wasa nake ba fa, gaskiya nake fad'a miki." Cikin muryar kuka Sabrine da marin ya gama gigitata tace "Gaskiya Ayam da baki mareta a kai na ba, zaki iya shiga matsala." Ko kulasu ba tayi ba sai ma saka lambobi da tayi suka ji tace "Yes Momma na, barka." Jim tayi alamar tana saurare daga gurinta kafin tace "Momma ina Pah?" Kyab'e fiska tayi tace "To gaskiya ni dai ki fad'a masa ba zan hak'ura sai ya zo gobe ya kawo min kyautar k'ara shekarata." Yanda Momma ta amsa mata yasa Ayam yin jim, sau da dama tana mamakin wasu abubuwa da iyayen na ta ke yi mata, da zaran zata fara tunanin haka kuma sai suyi gaggawar katseta, yanzun ma dai yanda ta bata amsa da dole ma ya amsa kiran sarauniyarshi ba shi ya d'auki hankalinta ba kamar yanda ta ji k'amshin gaskiya da kuma b'ari na tsoro a muryarta. A daddafe ba tare da karsashin da suka fara magana ba ta yanke kiran ta aje wayar, dafe gaban goshinta tayi zata tsunduma tunanin me hakan ke nufi ? Kawai Deeyam data damu sosai cikin d'aga murya tace "Ayam, hanklinmu a tashe amma ke waya ma kik..." Wani bahagon kallo Ayam ta mata tare da nunata da yatsa manuniya, cikin sanyayyar murya kuma a tausashe tace "Karki sake d'aga min murya, ni ba 'yarki bace." Jakarta ta d'auka wacce ta aje akan tebur d'in da wayar tangarahon ke kai, ko rataya ta batayi a bayanta ba ta juya a sukwane ita ma ta bar wurin a dole suka bi bayanta cike da zulumi da jinjina isa irin ta Ayam. *Egypt* Cikin girmamawa yaron na shi ya kalleshi cikin d'ard'ar d'in ta yanda zai karb'i abinda ya zo masa da shi yace "Shugaba na, sak'o ne daga Giobarh daga sarki Wudar, ka min izinin karanta maka abinda takardar ta k'unsa?" Duk da ya ji shi sarai amma ka rantse bai ji me yace ba, ci gaba yayi da wasarshi da wani k'aramin k'wallo na kwalba mai kamar *Dutsen Diamond*, matar dake zaune gefenshi cikin fararen kaya na yadi da kambunta a kai mai kalar gwal ce ta kalleshi a tausashe tace " *Bukhatir*, ka saurari abinda ya zo maka dashi mana, ka

Chapter 4 of 10