Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 9
mace! Da sauri ta mike ta shige toilet. A iya bincikenta bata ga alamar hakan ba, amman duk da haka ta kasa fitowa, taci gaba da kukan tana watsa wa fuskarta ruwa. Jinta shiru ne yasa ya dinga kwankwasa mata kofar ta fito bata jin zata iya amsawa bare tayi abin da yake so. Tayi banza da shi, iya dukan kofar ya yi amman ta ki budewa. Har gari ya waye tar bata fito ba, taci kukanta har ta gaji tayi zaune jagwam hannu biyu a fuska ta rafka tagumi. Tunda safe su Momy suka zo hade da breakfast, koda taji motsinsu bata yi alamar fitowar ba, zamanta tayi abinta. 150 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Momy ta dube shi ta ce, "Ina Mabaruka?" Ya yi murmushi ya ce, "Tana bandaki." Ta kalle shi da kyau "Bandaki kuma, a can ta kwana?" Ya ce yana dariya, "A'a a nan ta kwana, yanzunnan dai ta shiga." Sai can ta fito tana kumbura baki, fuskarta tayi jajir idanuwan kuma sun kumburo da ka gani kasan tasha kuka. Momy ta bita da kallo har ta zauna can ciki ta ce "Ina kwana?" "Lafiya." Kawai ta ce ta kara da cewa "Me ki ke a bandaki tun dazu?" Ta sosa wuya kanta na kasa ta ce, "Abu nake."Ta kura mata ido kawai. Sharifat ko kallonta bata yi ba bare su gaisa, haka ita ma ta share ta a halin yanzun duk abin da ya shafe shi ba sonshi take ba, ba ya burgeta bare ya tsaya gabanta. Tana kallon yanda suke nan-nan da shi ko ya ya motsa sai sun ji menene, me yake so? Shi kuwa idonshi na kanta duk ya ta motsa yana jin matsanancin sonta na fizgarshi. Fushin ma da take burge shi take. Aka tila masa abinci kala-kala ya ci ya gagara kai loma daya bakinsa. Tunaninsa ita ba ta ci ba shi ma ba zai iya ba, dama ita suke tattali ba shi ba da yafi samun kwarin gwiwa da kuzari, me yiwuwa yaci ganin tana ci, amman a halin 151 WAYE ANGON? yanzu ba zai iya ci ba. Maryam Ja'afar Yasa abincin gaba yayin da yake kallonta ta wutsiyar ido. Sharifa ta ce, "Big Bro ka ci abinci mana, yana hucewa." Ya dago yana kallonta tare da sakar mata murmushi iyakarsa fuska ya ce, "To." Kawai. Momy ta ce, "Ko ba shi ka ke so ba?" Ya ce, "A'a ina so." Ta ce, "To maida hankali ka ci ga magungunanka me yiwuwa ma Likita ya sallame ka yau, naga jikin ya yi kyau sabanin jiya." Ya yi murmushi yana kallon Mabaruka da har yanzun fuskarta a turbune take. Ya dubi Sharifa ya ce da ita. "Dauko plate ki zuba abinci kamar yanda ki ka zuba دو wannan. Ta dube shi tana son sanin me zai yi da shi kuma? Shima ya dubeta ya ce, "Yi mana."ta wuce tayi kamar yanda ya ce, ta zuba a plate dinsa ta kawo masa. Ya nuna mata Mabaruka ya ce, "Kai mata." Ta kalle shi da sauri zata yi magana, ganin yanda ya hade fuska yasa ta saurara, amman duk da haka sai da ta ce a shagwabe. 152 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar "Ni zan zuba mata Yaya, ita bakuwa ce da sai an zuba mata? In ta ci cikinta ne fa in bata ci ba wa ta yi wa?" Ya kalleta da kyau sannan ya ce, "Ni taiwa."Ya ki dauke kansa, ita ma ta kura masa ido. Ya ce, "Yes kije kiyi abin da na saka ki." Ta zobaro baki ta wuce. Da zuwa ta dankwafar da shi gábanta ba tare da ta ce komai ba." Ta dawo kusa da kafarsa ta zauna tana turo baki, ya yi murmushi kawai yasan duk abin da take don shi ne, ya dubeta ya ce, "Na gode kanwata."Ba ta ce komai ba. Mabarukar ta dubi abincin ta harare shi, sannan ta dago tana kallon Sharifat din tana hararanta ta ce "Zo ki dauke abincinku ba na so." Kan ta gama rufe bakin taji saukar duka a bakinta kuf! Momyn ta ci gaba da kallonta ta ce "Ba ki da mutunci daman ko, ita tasa kanta ne meye laifinta don ta kawo miki abinci? Kar ki ci wa ki kaiwa in ba ki ci ba?" Ta ci gaba da turo bakin ta ce "To kar kici bar shi don Allah." Ya dubi Momy a marairaice ji yake kamar shi ta daka har sai da ya zabura. Ya ce, "Sorry Mom! Ayi hakuri zata ci ai ba ki ga yanda ita ta dire shi ba ba ladabi ba da'a, dole ne tayi fushi ta ce bata ci." 153 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Fadin maganar da ya yi yasa ta dago ta harare shi ta kauda kai, ya mayar mata da murmushi. Momy ta ce, "Kai rabu da ita, kar taci." Sam bai so haka ba, yana lalla6a kayansa sun zo za su hargitsa mishi ita. Hannu Momyn tasa ta dauke plate din gaba daya ta ce "Mu muna so zamu ci wallahi." Ana dauke abincin ta mike kafafüwa tana turo baki tamkar daman ya tare mata gurin. Ya ce, "Ayi hakuri Momy." Ta ce, "Kai kaci abincinka ka fita bukatar ci." Shi ya sani sam ba zai iya ci ba in har ita ma ba za ta ci ba. Ya sauko daga kan gadon, ya dauki abincin zuwa gabanta, da Momy da Sharifa suka bishi da kallo, me zai yi? Ya tsugunna gabanta fuskarsa sake yana jin wani dadin zuwa da ya yi kusa da ita. Ita ko sai turbune fuska take bata ko kallonsa. Ya ce, "Mabaruka!" Tayi shiru kamar bata gun. Ya sake kiranta a can makoshi ta ce "Na'am." Ya ce, "Menene wai, me ke damunki?" Ta dago tana harararsa, ya yi saurin kama 154 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar kunnuwansa ya ce a hankali "Sorry!" Ta dauke kanta ya ce, "Me yasa ba za ki ci ba, kina son nima kar na ci ko?" Tayi masa banza. Ya sake cewa "Ko ba kya sonsa nasa a siyo miki abin da ki ke so?" Tamkar bata nan bare ta amsa, ya sake cewa "Mabaruka me ki ke so?" Ta ce can kasan makoshi ganin yanda Momy ke harararta "Ba komai." Ya ce, "To za ki ci wannan din?" Kai ta daga kurum don ya kyaleta, ta gaji da maganarsa musamman yanda ya tsugunna gabanta gaf har tana jin kamshin turaren jikinsa me sata tashin zuciya. Ya cè, "Kin tabbata za ki ci?" Ta ce, "Eh." Ya ce, "Sosai fa." Ta daga kai. Ya ce "Yawwa Mabaruka, don Allah kici ba don mu ba, nasan ba mu isa mu sa ki dole ba kiyi abin da ba ki so, amman don Allah zo ki ci don nima na ci, wallahi idan ba ki ci ba ni ma ba zan ci ba." Ta ce a gajiye "Naji zan ci." Ya yi dariya ya ce, "Na gode." Daga haka ya mike ya koma ya zauna. Wani kululun bakin ciki ya tokare Sharifat, mikewa tayi ta bar dakin sam ba za ta iya jurar ganin haka ba. Momy kuwa duk yanda take jin haushinta taji dadi 155 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar 1 ganin yanda ya yi tasan lallai watarana sai son da yake mata ya dawo ita ke masa, a dai juri zuwa rafi wataran tulu zai fashe, Imran ba na yadawa ba ne. Kan dole yasa ta dinga tuttura abincin tana yi tana goge kwalla. Wallahi sam bata jin dadin abincin, duk da yanda aka zauna aka kawata shi tana da tabbacin ba mai dandana abincin ya bari. Idan gasa ake wanda ya girka abincin shi ne zai ci, amman dalilin shi ya dauko shi da hannunsa ya ce taci kuma shi aka dafo mawa yasa take ji ba wani abinci marar dadi a duniya da ya kai wannan. Ko kadan bata jin dadinsa, tamkar tana zuba wuta a cikinta haka take ji har tana fitar da kwalla saboda takaicin cin da take. Shi kuwa ganin tana ci dinne yasa ya samu karfin gwiwa yaci sosai yana ci yana motsa kunne ga dadi a ransa na ganin tana ci ga shi ga ita. Yasan watarana ita zata girka masa suci tare har ma ta ba shi a baki. Ya ci abincin sosai sai da ya kusa tada shi sannan ya saurara. Tura abincin take tamkar ba zata bari ba, tayi alkawarin duk yawansa sai ta cinye ba za ta bari ba, duk 156 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar da yafı karfinta ko da zata yi amai ne, tunda har aka matsa mata sai taci. Don haka ta dinga tura shi tana yunkurin amai, ya tashi zaune yana kallonta yanda take turawa shi ya sani ba da son ranta ba, amman ai bai ce ta cinye ba, ko ya taci ya isa me yasa to take haka? Gani ya yi Momy ta daddage ta kai mata dundu a baya cikin tsananin fushi, saukar dundun ya yi daidai da saukar abincin gaba daya ta amayo shi duk a kan plate din. Ya miken a zabure yana cewa, "Sannu-sannu Mabaruka." Hankalinshi ya tashi ganin tana amai, ya dubi Momy a marairaice. Ita kuwa ta ce "Ke dai 'yar wulakanci ce Mabaruka, kin koshi shi ne ki ke turawa wato tunda ya ce kici shi ne sai kin ci wanda yafi karfinki, ke dai ki bata masa ko? Ya ji haushi? To kin kyauta.Shi yasa nima na taimake ki ki ka amayo shi." Ran Momy fa ya baci, ta dinga fada inda take shiga ba nan take fita ba, kawai ta suri makullin motarta ta fice fuuu! Ita kuwa tana duken ko motsi bata yi ba, tayi face157 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar face da amai idanunta sun sauya jajir saboda bacin rai, a ganinta an takura mata, yanzun in ban da so ake a mata fada, don me zata mata dundu don dai ace bata kyauta ba, kuma duk sanadin Imran.. Ta dago tana kallonsa da jajayen idanunta, kallon na tsane ka. Ya tsugunna yana cewa "Sannu, sannu Mabaruka." Ba abin da ya fito bakinta sai "Na tsaneka! Na tsaneka! Ba na sonka, ka shiga rayuwata, ka takura min daga farin ciki ka mayar min ita zuwa bakin ciki. Sanadiyyarka yau na tsinci kaina mahaifiyata na dukana tana zagina, ina ganin 6acin rai a idonta, wanda da ba na fuskantarshi a gunta, ko kallon banza bata taba yi min ba bare duka ko tayi fushi da ni. Duk kai ka jawo min, don Allah me yasa ba zan tsaneka ba? Me yasa ba za ka zamo makiyina ba? Wallahi ko numfashinka ba na so, ka takura min, ka takura min!" Ta fada da karaji, jikinta har yana rawa hawaye na zubowa. Ya ce, "Me yasa har haka Mabaruka? Wallahi ban yi miki sanadin har haka ba. Ni kawai na ce ina sonki ne, don kuma na ce haka bai isa yasa mahaifiyarki ta dinga miki wadannan abubuwan ba, meye laifina? Ni fa..." 158 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Ta katse shi da tsawa "Na..." ba ta karasa ba ta Kakalo aman ta watso mishi a fuska, tana huci tana kallonsa. Ya yi cak yana kallonta, fuskarshi dame-dame da aman har zuwa rigarsa. Farin ciki ya bayyana fuskarta, ganin ta bata masa rai. Kamar a mafarki taga yasa hannu ya gogo aman na fuskar ya tsotse a baki. Sai da ta rintse ido tsikar jikinta ta tashi saboda kyankyami, zuciyarta ta tashi. Wani aman yazo, tayi saurin tare shi da hannu taci gaba da kallonsa, bai fasa ba sai da ya lashe aman gabadaya na fuskarsa duk yana kallonta. Zuciyarta ta sake tasowa matuka, ta dinga yunkurin zubo da shi, da sauri ya rikota ba shiri taji bakinta cikin nasa yana tsotso, ba ta san sanda aman ya koma ba. Duk wanda ya bata ta a baki sai da ya lashe shi tas ya hade da bakin, ta dinga kokarin kwatar kanta amman ina! Ta kasa duk kokarinta, sai don karin kansa ya sake ta. Ta dinga huci idanunta suka fito tamkar zakanya, tana harararsa yaci gaba da kallonta ya ce, "Ina sonki, na fada miki yafi a kirga na kuma nuna miki shi a 159 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar zahirance, ina sonki bar haka a ranki. Ni Imran ina sonki har abada."Ya fada yana dariya. Takaici ya hanata magana har tana ina ma ta bari ya hada bakinta da nashi tir! Ta dinga tofar da yawu tana goge baki. Mikewa kawai tayi saboda abin ya kaita karshe ta kalle shi da kyau hawayen takaici suka zubo ta ce, "Allah ya isa." Daga haka ta wuce bandaki da gudu, kuka na son kufcewa. Ya yi murmushi ya ce, "Na gode." Bai damu ba, ko a jikinsa da kansa ya kwashe aman ya goge wurin. Koda ta shiga bandakin kuka ta dinga yi kamar ranta zai fita, bata taba jin takaici irin na yau ba, duk yanda take kyamarsa amman ya hada bakinta da nashi yasa mata miyansa. Ta dinga wanke baki tana kuka har sabulu tasa ta dinga dirza, amman sam ta kasa nutsuwa da ta wanke bakin miyansa ya fita. Koda Likita yazo yaga jikinsa ya ce yana dariya "My friend ka warware ko?" shi ma ya yi dariyar ya ce, “Sosai na ware, ina jina zan iya fada da ko da zaki ne." Ya yi dariya sosai ya ce, "Yes! Yes, I see, amman har 160 WAYE ANGON? da taimakon Madam ko?"Ya yi dariya kawai. Ya sake cewa "Lallai ta kyauta." Maryam Ja'afar An ba su sallama a ranar zuwan Rafi'atu kenan, ta tarar suna hada kayansu. Tana kallon Mabarukar tasan akwai abin da ya faru. Suka zauna ta dubeta da kyau ta ce, "Fada min me ya faru? Ko angon yasha dumin amaryarsa jiya?" Wata harara da ta dalla mata sai da ta tsorata, taja baya tana dariya. Ta sake cewa "Ah to, naga sai wani hada rai ki ke nasan wannan ne kadai zai sa kiyi kuka har دو idanunki su nuna. Tayi kwalkwal zata yi kuka, ta dubeta ta ce, "Kema ba ki sona Rafi'a tunda har kina hadan ni da wannan dan iskan ke a tunaninki shi ne Angon?" Rafi'a ta ce, "Ban sani ba, don ba zan iya warware wannan hargitsin ba." Ta ce, "Amman dai kin san Sulaiman shi ne Angon, saboda shi Babana ya aura min ba Imran ba, kuma kowa ya sani mace ba ta daura aure, kin ga kenan iska ya kama. Don haka ba zan taba yarda da shi ba, bare wannan abin da ki ke tunani ya faru tsakaninmu, tunda ba mijina 161 WAYE ANGON? ba ne." Maryam Ja'afar Ta ce, "Eh mace bata daura aure amman ke kin san Baba.shi ya daura muku aure kuma shi ma yana iya daura miki aure." Ta ce, "Ko ma dai menene Sulaiman shi ne mijina ba gidan da zanje idan ba can ba." Rafi'a ta ce, "Shi kenan naji yanzu ma ki tashi ki tafi kar ki makara, amma dan fada min me ya miki har ya sa ki kuka idanunki suka kumbura?" Tsaki taja tare da kauda kai alamar sai ki tayi. Su suka haďa kayansu ko hannu bata sa musu ba har suka gama suka fice, Rafi'atu ta jawo hannunta suka rufa musu baya. A ranar aka sallami Sulaiman saboda sallamar da aka yi wa Imran din, amma yasha duka. Koda ya koma gida Inna ta zaunar da shi gabanta ta miko masa biro da takarda ta ce, "Sakar musu 'ya!" Ya dubeta a tsorace saki Inna? Ni fa ina son matata, ta ya zan sake ta?" Та се, "Та yanda ka fara jawo mana fitina don ubanka so ka ke na kyaleka ka dinga zaryar zuwa kotu 162 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar ana garkame ka a magarkama? To ba zai yiwu ba wallahi. Ga matarka can a daki ita ta dace da kai ba wannan 'yar mahaukatan ba." Ya turo baki "Ni gaskiya ina sonta ba zan sake ta ba, bayan wahalar da na sha ga kudin da na kashe sai su tashi a banza?" Yana rufe baki ta dauka. "Sai a biyaka kayanka, ai ba su ci banza ba, nima ban goyi bayan ka bar musu ba, ni da kaina ma sai in amso su ba a bar musu ba.Ko Samira sai ka ba kayan shi kenan.' Ya ce, "Gaskiya ba zan iya ba, kowa yasan matata ce ni ne Angon."Ta jawo karan dake kusa da ita. "Sai in kwade ka wallahi, kai ne Angon banza! Sakarai fanko, kai kana ganin za a baka ne har zaka iya ja da shi? Shi fa mai kudi ne karfinku ba daya ba, zai iya sayenta da kudi ya dankarawa kotu da 'ya'yanta kudi tuni su ba shi sai dai ka sha kunyar banza. Don haka tun kan ayi ka rabu da ita ka bar masa kawai, ba dai karfin ja da su ka ke da shi ba wahala kawai za ka yi." Mikewa ya yi tare da shurar takalma yana cewa, "Ba zan iyan ba, ina son matata ki min addu'a kawai." Daga haka ya ficе. 163 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Ta dago murya "Sulaimanu ina magana ka sa takalma ka fice ko?" Ina! Bai ji ta ba tuni ya fice. Ta kulu matuka, "Za ka dawo ka same ni don ubanka." Samira dake gefe ta ce, "Kema dai Inna ki kyale shi, in ya sha wuya zai gane shi ya sani tunda an fada masa ya kiji." Ta ce, "Ba zan kyale shi ba, in bar shi ya kare a zuwa kotu ana sakaya shi tun kan abu ya yi nisa gwanda ya دو kyale musu mata ba dai tashi ba ce. ** Tun a mota ta ce ita a sauketa gidan Babanta za sauka. Kallonta Momy bata yi ba bare ta bata amsa. ta Su uku ne a motar da Momyn ita ke tuki, sai ita da Rafi'a shi kuma suna a motar Sharifa. Ta dinga turo baki tana fushi har suka iso, ta fito tana 6ata rai duk suka shige amman ita ta ki shiga, taja tayi tsaye tana kumbure-kumbure. Rafi'a ta ce, "Wai menene haka Mabaruka? Ke dai ba kya jin magana ko tun yaushe ake fama da ke kan abu 164 WAYE ANGON? daya son ranki ki ke bi ko?" Hararar Rafi'ar tayi tare da kauda kai. Maryam Ja'afar Ta ce, "Na gode, na sha fada miki ba zan goya miki baya a kan rashin kunya ba, tuni zan kama gabana. Tunda ke ba kyaji ki zo mu wuce ciki." Kallonta bata yi ba bare ta wuce din, don haka ta janyo hannunta da karfi, amman ta tirje duk iya kokarinta ta kasa janta. Taji haushi matuka, don haka ta sake ta. Ta ce "Shi kenan kada ki shigo." Daga haka ta shigewarta. Koda ta shiga duk suna falo, Mommy ta dubeta ta ce, "Ina Mabarukan?" Ta zauna tana cewa "Ta ki shigowa." Shiru tayi ta rasa me zata ce. Mabaruka na son fin karfinta, shin wai ya zata yi da ita? Daddyn Imran din ya shigo da hancin motarsa, ya fito. Suka yi ido biyu da ita ya karaso har inda take ya dubeta ya ce "Ya aka yi ne Mabaruka ki ke a nan?" Ta ce, "Ba komai nafi son nan din ne." Ya yi murmushi, shi yasan dalili. Don haka ya jawo hannunta yana cewa, "A'a yaushe za ki tsaya a nan kowa na ciki, zo muje." 165 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar Ta ce, "Ni fa in na shiga takura ni suke har dukana take." Ya ce, "Ina nan ba mai taba min ke, zo muje."Yajata. Don dole ta yarda ta shiga din har lokacin fuskarta ba ta sauya ba. Ya zauna yana cewa, "Don me za ku matsa mata har a hanata shiga gida?" Momy ta ce, "Wa ya hanata? Ita ta hana kanta kan shegen kafiyarta." Imran da yake kishingide ya tashi zaune yana kallonta. Suka hada ido biyu da shi, ta dallo masa harara tare da kauda kai, yayin da ya yi murmushi ya ci gaba da kallonta din. Sharifa ta turbune fuska ta jawo waya tasa earphone a kunnanta kar ta saurari me ake cewa, duk don Mabarukar. Ganin yanda ya matsa mata da kallo yasa ta dubi Daddyn ta ce, "Zan shiga ciki in kwanta Daddy." Ya ce, "Ba laifi, jeki ki huta." Ba ta ce komai ba ta mike tayi wucewarta tana harararsa. Momy ta bita da kallo har ta shige dakinta, ta juyo da kallonta gun Daddyn tana cewa, "Sai shegen fadin ran 166 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar tsiya, ban taba ganin yarinya mai kafiya irinta ba." Ya ce, "Za ta bari alamar nasara kenan, zamu sha mamakinta." A nan Imran din ya ce "Ku ku ke damuwa da haka, ku bar ni da ita ni nasan yanda zamu kare." Momy ta ce, "Allah ya nuna min wannan ranar." Rafi'atu ta сe, "Kuma Mabaruka saukin kai ne da ita, abu kadan zai sa ta tsani mutum kuma abu kadan zai sa ta so mutum. Idan ina tambayarta me yasa take son Sulaiman? Sai ta ce min ita har yanzu bata ga dalili ba, ita dai kawai tasan tana sonshi. Na ce ko wani abu nashi ba ya burgeta? Ta ce ita bata ga komai ba, na ce to me yasa ba ta son Imran din? Tayi shiru har saida na taba ta na ce me yasa ta tsane shi? Ta dube ni ta ce, "Ban sani ba Rafi'a, ni dai kawai nasan ba na sonshi na tsane shi, haka nan ko muryarsa bana son ji." Na ce, "Ko wani abu da yake miki yasa ki ke jin haushinsa?'Ta yi shiru, sannan ta ce "Ni dai kawai ba na sonsa." To a haka yasa na ce kamar bata san ma meye son ba, meye kiyayyar ba." Daddy ya yi dariya ya ce, "Zata bambance idan taje 167 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar gidansa." Momy ta ce, "To ta ya ya kenan zata bambance da kanta har tasan meye son bayan tasawa kanta tsanar?" Rafi'a tayi dariya tana kallon Imran, ta ce "Wannan kuma aikin Imran ne." shima ya yi dariyar yana mikewa ya ce, "Sosai kuwa." Momy ta ce, "Ina za ka ne?" Ya ce "Wanka nake so ,, nayi." Lokacin da Rafi'ar ta shiga dakin Mabarukar tana waya ta hau gadon ta zauna tana sauraronta, da Sulaiman ta fahimta suna waya, rabi duk shagwaba take masa. "Don Allah Sulaiman kazo ka dauke ni daga nan, wallahi kokarin raba ni da kai suke, bayan kai ne Angon." Daga can ya ce, "Kada ki damu Mabaruka, kowa yasan ni ne aka daurawa aure da ke saboda Babanki shi ya daura min aurenki, kowa kuma yasan uba shi ke da aure ba uwa ba, babu in da uwa ke daura aure, don haka ni ne Angon babu in da za kije gidana za ki zo." Ta lumshe ido tanajin damuwa a ranta. Ta ce, "Allah yasa Sulaiman, ka dage don Allah kar 168 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar kayi wasa a raba mu." Ya ce, "Insha'Allahu ba mai shiga tsakanin masoya ni da ke." A haka suka gama wayar, tayi lamo idonta a rufe. Rafi'atu tasa hannu ta dauke wayar ta dubeta ta ce, "Mabaruka!" Ta bude idonta tana kallonta tare da cewa "Na'am!c Ta ce, "Na kagara ayi ta ta kare a yanke hukunci a ba mai mata matarsa." Da sauri ta tashi zaune idanuwanta suka yi rau-rau a yanayin tsoro take kallonta, ta ce "Ina tsoro Rafi'a, zuciyata ta dade da karyewa kullum cikin zullumi nake, wallahi ina tsoron kar kotu ta yanke hukuncin da zai yi sanadiyyar ajalina." Ta dubeta da kyau ta ce, "Me ki ke nufi kenan?" Ta ce, "Idan har kotu ta tabbatar Imran shi ne angona zan mutu ne da na rayu da shi." Та се, "Mabaruka kin san me ake nufi da mutuwa kuwa?" Ta ce, "Na sani Rafi'a, don tafi min ko kadan bana jin walwala kasancewar da shi ake rigimar nan, koda muryarsa na tsana bare in gan shi har naje gidansa a matsayin matarsa.' Ta ce, "Shi yasa na kagara a yanke hukunci ke zuciyarki ta huta mu ma mu huta, ki daina daukar 169 WAYE ANGON? zunubbai." Maryam Ja'afar Ta dubeta da kyau ta ce, "Zunubbai kuma, wadanne kenan?" Ta ce, "Kasancewarki tsakanin daya daga cikinsu kina magana ko ma suna taba jikinki alhalin ke matar aure ce matar wani ce ko Imran ko Sulaiman." Ta ce, "Har kina tunanin in nayi magana da dayansu ina da zunubi alhalin bani da laifi, ban san waye angon ba?" Ta ce, "Ban ce dama kina da laifi ba, amman ki taka tsan-tsan har zuwa lokacin da za a tantance waye angon?" Tayi shiru hawaye na kokarin zubo mata, tsawon dakiku sannan ta dubi Rafi'ar cikin mutuwar jiki da kasala bakinta ya yi nauyi kamar zata yi kuka ta ce, "Dole ne daya daga cikinsu, ko Sulaiman ko Imran dole daya za a ba ko Rafi'a?" Ta ce tana kallonta "Sosai, daya ke da mata daya ya kama iska." Hawayen suka zubo ta ce, "Ya zan yi kenan idan Imran aka ba?" "Hakuri mana, ki koya wa kanki sonshi ki hakura da Sulaiman, don samawa kanki lafiya da neman Aljanna. In ji Rafi'atu. 170 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar "Ba zan iya ba Rafi'a, ba zan iya rayuwa da shi ba, ko na awa daya ne." Ta ce, "Za ki iya Mabaruka, an yi sau dubu kuma sun zauna lafiya, in kin gan su za ki sha mamakin soyayyar da suke wajunansu." Ta ce, "Kin san kuwa me ake kira da tsana da rashin so Rafi'a? har abada ba zan taba sonsa ba wallahi." Bakin Rafi'a ya kulle bata da abin cewa, kallonta dai take cike da mamakinta. Ta ce, "Insha'Allahu Sulaiman shi ne mijina, da shi zan yi rayuwata mai kyau da tsafta, farin ciki da walwala." Ta ce tana kallonta "Ni kuma ina miki addu'a Allah yasa Imran shi ne mijinki saboda gujewa da na sani gaba a rayuwarki, kuma shi ne farin cikinki mai dorewa." Kallonta take tamkar ta kife ta da mari, amman ganin ba za ta iya ci mata fuska har haka ba yasa ta mike gabadaya ta diro daga gadon ba tare da ta ce komai ba. Ta ce, "Ina za ki je?" Ta ce ba tare da ta juyo ba "Wanka zan yi." Daga haka ta shige. Rafi'ar ta taso tazo har bakin toilet din ta ce, "Idan an ce ke da Imran kun dace da juna sai ki ce a'a, alhalin 171 WAYE ANGON? Maryam Ja'afar ra'ayinku daya. Yanzu haka shima yana can ya shiga wankan. Haka nan ya ji yana son yin wankan, ke ma gashi nan kin shiga don kiyi kawai don haduwar junanku." Jin wannan maganar yasa da sauri ta saki sabulun da ke hannunta, ranta ya baci ta yayumo tawul ta daura ta fito ta bita da kallo tana cewa. "Lafiya, me ya faru ki ka fito?" Ba ta kallonta ranta a 6ace ta ce, "Na fasa." Ta fara maida kayanta. Rike baki Rafi'a tayi tana kallonta cikin mamaki ga dariya na cinta. Ta ce, "Kanki ya fara tabuwa ko tsanarsa har ta kai haka?" ba ta saurare ta ba ta koma ta zauna bakin gadon tayi shiru. Ita kuma Rafi'a ta ci gaba da magana. "Lallai Mabaruka aiki na gabanki

Chapter 7 of 9